[6:47PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [1:20PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
01
ina farawa da gargadi nasamu labarin wani yana copy na novels dina yana turawa face book inakira gareka daka bari banhana katurah face book bah amman idan kasauya wani abu koda kalma dayane wlh banyafebah Allah ya isah
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHEEEM
darene mai kumshe da iska mai matukar sanyi kasancewar yanayine na hunturu iska saikadawa yake kowanne yakame cikin dakinsa ya lullube dare yatsala sosai inda kowama yadade dayin barcin bakajin komai sai kukan karnuka inka debe Haidar dayake kwance samar yar katifarsa banda tsaki babu abunda yakeyi
duk bayan second daya saikaji yaja tsaki yamuskuta gefensa inda take barci hankalinta kwance batamasan yanayibah sai sharar barci take yasakeyin tsaki nikam anhadani da jarabah nagudu bantsirabah nagudo gida dan inrage zafi gashi nan kuma ankuma lakabamun wata
yasake jan tsaki kuma ma wai wannan yarinyar sa ar fati za ace itah ce matata niwama zantunkarah da wannan maganar nasan muddin dad yaji wannan zance kona lahirah saiyafini jin dadi
yasake yin tsaki nikam nashiga tsaka maiwuya gashi yanzu jibi zanje gida wlh danasan hakan zata faru babu abunda zaikawoni wannan kauyen dahar za a hadani da kaya danni wannan kayane aka jijjibamun kuma daukarta zaimun wuya “”
yalumshe idanunsa”” yasake budewa ganin haryanzu babu alamar barci a idonsa kodai intafi inbarta ne??? amman kuma idan nayi haka bankyautawa hardo ba””amman kuma aishima bai kyautaman bah haka akeyi babu shawara kawai ya aurah man yarsa saikace nacemasa inaso mtsw
nidai wlh yacuceni bansan yanda zanyibah taya zan fuskantarda family dinmu banida hannu cikin wannan auren sadaka akabani itah wannan sadakar kam tanada wuyar karbah”””yasake juyawa yakalleta inda tahangame baki sai kwasar barci take sai abun ma yabashi dariya wai matar sa ni Haidar ko a mafarki akace zan auri wannan aisaina yi musu”” dawannan tunanin Haidar yakwana baifargabah saiyaji ana kiran asalatu mikewa yayi yadau buta yafita
saida yayi alwala sannan yadawo dakin yatasheta zumbur tamike zata zurah dagudu saida yariketa ke lfy ninefah natasheki kiyi sallah tana mutsut tsuka ido taturo baki bana sallah ai…ido yazaro waje ganin yarinyarda batayi shekarah sha ukubah waibata sallah tokan wane dalili?????
Aisha………..gentle
08069067379
[2:35PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
02
yasake dubanta karo nafarko daya kalli fuskanta yakawarda fuskarsa gefe bangane baki sallah ba meyake damunki dayahanaki sallah””cikin jin kunya tace aini bangirmabah ido yasake zarowa jin maganarta
bakaga ladiyo bah wata jijjibah da itah tana iyah kadakaifa amman itah ma bata fara sallabah saida akayimata aure ta haihu sannan “” kaga kuma ni karamace koh????? tayi maganar tana kallonsa takaici kam baibar Haidar yakoma kantabah yanufi hanyar waje
baki ta hangame tana buga hamma takoma saman dan gadon karanta takwanta taci gaba da barcinta” tafiya yake yana tunanin maganarta wai bata isah sallabah?? aikam akwai babbar matsala agabansa wannan yarinyar tace bata isah sallaba
idan yakaita gidansu yakenan wai ashe haryanzu akwai kauyenda akeyin haka yarinya harta haurah shekara goma tace bata isah sallah bah dawannan tunanin yakarasa masallaci koda yaje liman kawai yatarar sai wasu daidaikun mutane
yayi tsaki cikin zuciyarshi sukam wasu mutanen sai du a i tunyaushe akayi kirah amman masallaci baifi mutun biyarbah sunacen sanyi yahanasu fitowa shaidan yana buga masu gangarsa”” saida yayi tahiyatul masjid sannan yazauna yana lazimi tsawon mintuna goma mutun biyu ne suka shigo ciki harda hardo”baban mairo
liman yatashi yatada sallah kwata kwata sahu dayane akacika koshi baicikabah saida akakusah gama sallah””bayan liman yasallame kamar kullum Haidar ya amshi lasifika yafarayi masu wa azi”” akan muhimmancin sallah cikin jam”i
yaku yan uwana musulmai kusani sallah cikin jam”i yanada dumbin lada Allah subuhanahu wata ala yayi hani daga barin sallah cikin jam”i Allah yanacewa acikin suratul bakarah”” bisimillahir rahamanir raheeem fa akimun salata wa atu zakata warka u ma arraki in”” fassara kutsaida sallah kubata zakka kuyi ruku”i tare damasuyin ruku”i
kala rasulullahi S A W
allamana sunanil hudah wa ina minsunnanil hudah assalatu fil masajidi tazi yuhzani fihi wamaminkun min ahadin ilah walahu masjidi fibuyutihi alau sallaitun fi buyutikum atarartum masajidakum taraktu sunatan nabiyukum S A W walau taraktumsunata nabiyukum lakafartun
fassara…
abunda akenufi da sunanil hudah sanudai itah sunnanir huda sallah cikin masallacinku da ace daidaga cikinku ace yanada masallaci acikin gidansa amman baya sallah ciki saiyayi cikin gidansa yabar masallacinku hakika yabar sunnar manzon Allah. S A W wanda yabar sunnar manzonku hakika yakafurta Allah yakiyashemu
Aisha…………………gentle
[3:19PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
03
Acikin wata ruwaya manzon Allah yanacewa inna ashkalil salatil munafikun sallatul isha i” wasallatul fajri walau ya alamuna mafihima la atuhuma walau habwa”fasara manzon. S A W yanacewa sanudah karancin sallah ga munafuki sallar isha i da sallar asubah da ace zakusan abunda yake tsakaninsu wlh dazaku sallacesu koda dajan gindine”””
aduk lokacinda zamu kwanta barci musaka abu azuciyarmu idan harkasa abu aranka insha Allah da lokacin abun nan yayi zaka sami kanka kana maitashi shaidan yana sagal tardamu lokacinda ake sallar isha”i zakasamu wani alokacin ma zaije masalisah wajen firah
bazai kwantabah saidare sai alokacin zaiyi sallah wanima bazaiyibah shikenan sannan sallah asubah lokacinda zaiji ana hayya alassat alokacin zaisake juya kwanciya musamman yanzu da yake lokacin hunturune ruwama wuyar tabawa sukewa wani
kusani abunda za afara tambayar dan adam ranar alkiyama sallace idan tayi kyau hakika kayi nasara idan tabaci hakika katabe kuma kayi hassara yan uwana musulmi muji tsoron Allah mudaina wasa da sallah Allah yabamu ikon aiki da abunda muka saurara anan zan dakata Assalamu alaikum yanzu daidaikum mutane suke shigowa suna tada sallah kasancewar hargari yafara dan haske
kuma yau sunajin kunya jin anyi wa azi akan sallah kowanne kansa done yake dawanda yaji dadin wannan wa azin dama wanda baijibah wadanda suka sabah zuwa yana karasu karatu suka matsa wadansuma tambayoyine abakinsu
malam hardo yayi murmushi yana kallon Haidar har abadah yasan bazaitaba dana sanin aurah masa yarsa mairo dayayibah yasan bazai tabayin nadamar hakabah anan gaba duk da baisan asalin Haidar ba baisan ina yafitobah
haka zalika baisan iyayensaba amman yadauki yarsa yabashi saboda kyawawan halayensa yasan yarsa bazata taba kuka anan gababa yayi mata kyakkyawan zabi sama da yayyuntama
yasake nisah wa akaro nabiyu Allah daiyabiyaka Haidar dawannan tunatarwar taka yana nan zaune har haidar yagama biya masu sannan yataso zuwa wajen surukinsa yaduka harkasa cikin girmamawa yagaisheshi ya amsa da fara arsa yana tambayarsa ya kwanan amarya”” yayi murmushi kalau baba
yanisah Haidar tafiyarka tana nan kuwa jibi??? yanisah insha Allah hu baba””to amman dai da matarka zakatafi koh ko anan zaka barta?????gabansane yabada rasss yadan sosa kai kamar yace bada itah zanibah amman bazai iyah kallon idon hardo yacemasa hakaba yanisah abba zankara kwana biyu dai inga yanda za ai
inda halin muje taren saimuje tare da itah saiwani yabini yaga gidah”” ah ah wlh Haidar basai wani yabikabah kaida matarka wlh nayarda dakai dari bisah dari nasan bazaka taba cutarda mairo bah kuma naji dadin bayaninka wan nan yanuna kobayan idona bazaka cutarda mairo bah
Allah yayi maka albarka ameeen baba nagode Allah yabar girma yamike nabarka lafiya yafito yasaka takalminsa zuwa gida dasallamarsa yashiga still tana nan inda yabarta sai sharar barcinta take ahankali yataka inda take yaduka
sannan yadan bubbugata”firgigit tabuda ido wayyo Allah inna na!!!!kirjinta sai halbawa yake ganinsa duke kusa da itah tashi tayi tamatsa baya yabita da kallo kamar taga dodo yanda take zare ido”’yace lfy????tayamutsa fuska kamar taga kashi meyasa katabani kasan dazuma saida karikeman hannu
wlh saina fadawa baba kai dan iskane ido yaturo wajen jin. abunda tafada taci gaba kakirah sunana aizan tashi amman saika tabani idan nasamu ciki mezancewa innah na saita fashe da kuka tsuru yayi yana sauraren ta shikam yabanu Allah yahadashi da jarabah YAR SADAKA!!!!!!
tabdi indai irin wannan sadakar ce wlh akai kasuwa shibaisan wani abu rikicibah wai itah wannan yarinyar batasan komaibah auren kawai akamata
Aisha………………..gentle
[3:50PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
04
yasake kallonta inda take kuka yayi karfin halin magana danace kiyi sallah ashe bakiyibah shine kika koma barcin kiko??? baki taturo waikai bakon nan wlh kacika takurah Allah ni saidai inkoma gidan mu idan takurani zakayi
kadameni sainayi sallah bayan nafada maka ban girmabah”” yanda tayi maganar sai abun ma yabashi dariya mikewa yayi zairiko hannunta alamar tazauna meyatuna saikuma yajaye hannun sa itah kam harta kara matsawa
yakalleta zauna nan muyi magana to yakoma saman katifarsa yazauna ganin batada alamar zama sai alokacin tazauna”” yakalleta intambayeki mana jiya daza a kawoki nan me baba yace maki???
tamurza idonta sannan tadaga kanta sama kamar maitunanin wani abu yauwa natuna cewa yayi waikai mijinane ko???? kuma wai inyimaka biyayya haka yace ko???waikuma shima take tambaya yayi murmushi agaskiya wannan yarinya akwai wauta kamar yarfari
ashe magabar ba azuci yayita tafito waje saiyaji tace wlh kamar kasani niyar farice tayake hakorah har dimpul dinta suka lotsa””amman nibanda wauta fa kawai anacewa inada wautane””u um gani bagwanin surutubah
wannan kam kamar taci kan aku yace naji sannna kuma mai abban yacemaki”??? hakanan kawai yace saitayi shiru cen tace yauwa yace inkasakani abu inyi kuma ko???? yakuma kallonta to inhakane tashi kije kiyi sallah idan kuma ba hakabah zansanarda baba
nasakaki abu bakiyibah” ah ah kada kafada mashi wlh tsoron shi dukana zaiyi “”to idan bakiso infada mashi tashi maza kiyi sallah mikewa tayi tafitah tadauki butah tayo fitsari saida akafara kuskure baki sannan akawanke fuska akawanke hannuwah
sai akawanke kafafu akazubah wa kai ruwa sannan tayi dakin tasaka hijabi tafara sallah yana kwance rigingine ido nuwansa suna kallon rufin dakin baimasan tagama sallah ba saidai yajuyo baigantaba.
yanashirin mekewa saiga halliru yayan mairo yakawo masa furah ya ajemasa suka gaisa sannan yafitah yadade yana kallon furan sannan yasa hannu yadauko yabudah sabuwar furace taji nono ga sukar nan baidamu dasaka sikaribah yadauki furan sa yasha haryakoshi ya aje ragowar””
tashi yayi yafito waje acen kusan shiga gida yahangota tana wasa da wata sunata gudu yagirgiza kanshi sannan yafitah hanyar wajen daji yayi”””wajen wata katuwar bushiya wajen yakasance kamar majalisah
akullum zaka wuce wajen zakasamu mutane cinjim kamar wajen wa azi dakaga wajen kaga matattalar yangulma dazunde wajen maya rabo da mutane hakan yasa yakoma kamar wata yarkasuwa ana saida abubuwah da dama akwai mairake dawani maishago
wasu yan matan kuma anan suke saida gyada ayah alale danwake ragadada dadai sauran kayan kwalam idan darema yayi anan ale wasan dandali””‘matasa masu zaman kashe wando duk nan ne matattararsu””
Aisha………………….gentle
[4:17PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
05
kamar kullum ma suna zaune suna firah lado yayi tsaki yakalli habu waikasan wanene mijin mairo???ya murza gyada yajefah bakinsa yana taunawa ah ah wlh bansanibah itah da akaiwa aure jiyah ina zansan mijinta “”lado yasakeyin tsaki wajen daurin auren bakaji ance haidar ba duk
karkarar nan waye mai irin sunansa”” yakalleshi lado wane haidar in badai wannan dan birninba????yatabe baki saikayi shidai din nake nufi kadubi dan Allah irin sonda nakeyiwa mairo amman yahanani itah wai inbari idan rabonace zaikaiman itah ina zamana
gashi abunda hakurin jiran yajaman””bello ne yasa bakinsa aikaine dan wahala duk karkarar nan waye baisan sale bah da irin soyayyar da yayiwa habi amman rana tsaka hardo yabawa audu kuma kasan shibama sonta yakeyibah
tanko yace todai waiku ina ruwanku dashi dayayansa kowa agarin nan yasan halinsa bawai mairoce tafarko bah kuna damun kanku ne akan abunda baishafekubah”” lado yace bawani kawai yadauki yarsa yaba wanda baisanibah
mudamuke cikin gari yasanmu yasan iyayenmu amman yadauka yaba bako wayasanima kodan yankan kaine yagudo garinsu shine yazonan waidan samun gidin zama harda wa azi yakeyi amasallaci
shiyasani banazuwa saiya gama haukarsa ma nake zuwa “”habu yace barshi dai nasan meyasa yabashi auren mairo sabodah kwadayine yana ganin kamar wannan dan birnin zaifumu kudi baisan burgar banza bace baida ko sisi
daidai kawowar haidar kunsan idan ana iska babu inda magana bata kaiwa har inda bakai zatobah tundaga nesa yakejin firah su”””lado yace ai idan baiyi hankalibah saiyarasa yarsa danni banyarda da wannan Haidar din ba
idan ba dan kungiyar tsafibah kaga mutun dakyau kamar ankerashi cikin injin kamar dan larabawa amman yazo kauye irin wannan yazauna kuma yanacin irin abunda mutanen karkarar nan sukeci kaima kasan badan Allah yake zaune damubah
akwai wani mugun nufi dayakeso yayi akan mairo kuma ni wlh haryanzu inasonta””:hardo kawai yacuceni amman mairo ai dani tadace”” habu yasake watsa gyada bakinsa yatauna “”‘kaidai kabarshi ayidai mugani idan tusa zata hurah wuta munanan zai korota da takardar saki
wannan gayen zai iyah zama da yar kauye” tankone yakyafato habu yana masa nuni da Haidar daya kawo saitinsu suka saki fara a ah malam ne barka da safiya yamika masu hannu suna gaisawa habu yace ya amarya gaskiya ina tayaka murna dasamun wannan yarinyar
mukammu munyaba da hankalinka “” kaf kauyen nan babu wanda yadace da itah saikai kobah hakabah yayi magana yana kallon sauran yan majalisar sukace hakane kam habu maganarka dutse
Aisha………………….gentle
[4:45PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
06
Haidar yayi murmushi wanda yasake fitoda tsantsar kyansa yashafo sumarsa data kwanta lif saman kansa bakikirin sai sheki take””yakalli habu yace nagode sosai my frnd”” habu ya kalli lado lado yakalleshi
azuciya yace kaddai yaji abunda nace gashi yazageni da yarensu”” yayi saurin kirkiro murmushi wlh kam haka akayi muna tayaka murna “”aibakasan wani abubah kaf kauyen nan babu wanda baya yabon halinka Allah dai shibiyaka
Haidar yasake murmushi yace tnx abokina yadan dafah kafadar habu ”habu yasake zaro ido kuma dai!! anan yayi masu sallama yakama hanyarsa saida yawuce lado yayi tsaki yace kaga yanda jikinka yake rawa habu kamar kaga wani mala ika
habu ya kalleshi lado aikasan tsoro inamine idan bakayi wasabah wannan saiya tsotse maka jini niban gasgata kyansabah saiyau wlh”” kuma zamansa nan banga yarage komaibah kamarma sake masa kyau akeyi
bello yace togashi nan daiyadawo aikam habu yakama bakinsa yana kallo hanyar bakowa gaba daya suka tintsire da dariya suna tabawa ganin habu yatsorata daganan akasake firah habu yace yaufa akwai gwangwaje wa adandali
lado yace tame kenan??habu yace waikai bakada labarin yau su jummala ne zasuyi wasa aikam nihar nasamu kudin liki wlh jiya nasiyarda kajina biyibah kudin suna gida cikinsune ma nasiya mana wannan gyadar
Bello yace kacedai nima intanadi nawa dankam kallo bazai barni tashabah da abani labari gwanda idona yaganemun”” watace tazo siyen sikari shago suka bita da kallo harta siya tawuce”” habu yace kalleta dan Allah babu abunda tarasa amman wali yasaketa nibanga abunda yarinyar nan batadashibah
tanko yace waikana nufin indo ce tagidan malam dahiru?? kwarai kuwa itah ce kaga duk ta lalaceko? aidayunwa yake barinta kai intakaice maka lbr dukanta yake kamar jaka kuma tamanne masa kaga yasaketa amman haryanzu tana nan tamanne masa
saikace shine namiji kadai aduniya jilokacin tana budurwanta yanda yayita rawar kai akanta samarinta wajen guda nawa amman duk yakasasu sumadai dan sunga yanada dan rufin asirine yana sakar masu daula kunga tanashiga yakama bakin aljihunsa
lado yace waikai habu yamagar mariya kuma???’yanisah kaidai kabari sai anjima idan munhadu dandali. kace zamusha kallo suka sadariya anan sukacigaba da firansu
Haidar ne zaune gindin wata bishiyar mangwaro yadan kishingida daga nesah yana hangen shanunda suke ta kiyo yayi murmushi dayatuno da firan samarin nan daya gani duk da baisan sunansubah zamansa kauyen
daidaiku kawai yasan sunansu koshi idan akace yanuna maisunan bazai nunabah”’sudai mutane abunda baishafe subah shisuke safarwa kansu wayarsa yadauko kasancewar cikin garin babu sabis saiyazo gindin wannan bishiyar shiyasa kullum nan ne wajen firarsa
Aisha………………….gentle
[9:47PM, 11/12/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
07
Nomber mom dinsa yakamo yadanna calling sannan yakara akunnensa ringin daya tayi saigashi tadauka yana murmushi yace salamu alaikum”” adaya bangaren aka amsa wa alaikumus salam””
mom yakike yagida?? qalau nake Haidai dafatar kaima dai lfy kake???? yalaso labbansa dasuka bushe qalau nake mom”” saikuma sukai shiru tanisah wai Haidar yaushe zaka dawone kasan fa jibine daurin auren ka” duk da yasani amman hakan baihanashi jin faduwar gaba ba
yanaji kuma kayi shiru Haidar kasan halin alhj abu kadan zaihayeka da fada ni wlh banso tafiyar nan takabah haka kurun kana zaman zamanka kayi kaurah dan kawai za ayimaka aure kuma kasan babanka bazai fasa yimaka wannan auren bah
dan haka akayiwa sauran yan uwanka kuma kaima dole kahakurah”” yabata rai mom nasani kuma ina nan tafe;;takatseshi yaushe??? saurah kwana biyu daurin auren fah amman babu ango yakakeso infuskanci babanku idan haryagano auren nan kakewa gudu
ni banason harkar ganin laifi kuma duk abunda alh zaiyi fada shikake burin yi kayi hakuri kakarbi hamida amatsayin matarka dama dai yar uwar kace dama wata barece kace wani abu toduk tushen dayane menene laifin hamida dazakace bakasonta!?
mom nidai abar wannan magana injindai dady baisan inda nazoba???? wazai fada masa yarufeshi da fada amman wlh tunjiya naso kiranka wayar taki shiga waimadai wane mugun kauyene wannan wanda babu savis sai anfita daji????yamuskutah ummah danisah fah nayi nesa da gida sosai ina zari’a kauyen akan hanya yake kusah dawani kauye giwa
kaidai kasan wannan kauyen niban ma tabajin sunan kauyen bah””dajin sunansa mugun dajine amman kuma kake zaune tsawon sati uku”” yanisah wlh mom inacikin matsala anan din mah”” saikuma yayi shiru
matsala kuma Haidar tame?saida yayi nazarin maganar sannan yanisah ummah andauraman aure anan garin ai zaune take saigata tamike tsaye tana buga sallallami tadafa kirji aure kuma haidar??? dakai dawa kuma yaushe aka dauran auren????
amman haidar kadaukowa kanka jidali wh babu ruwana da fitinar gwaggonka””yaja numfashi mom kitsaya kisaurareni nasan kece kawai zaki iyah rufaman asiri batareda kowa yasan halinda nakecikibah”
wa??? ni Haidar babu ruwana acikin wannan tashin hankalin kasan akan wannan dalilin zai iyah shafuwar aurena???kayi tunani dakyau babanku idan yayi magana babu wanda ya isah yasakashi yachanjata ballantana kaihar kazo masa dawani zancen kayi aure
waimashin haka akeyin aure babu dangin ango towaye yazama waliyin ka???? kuma a ina kasamu kudin aure tunda bada kudi dayawa katafiba????yanisah mom baban tane yazama waliyina kuma shine yabiya sadaki babu ko nairata YAR SADAKA!!! ce kuma ni mom wlh banasonta amman bansan yazanyibah
YAR SADAKA!!! kuma???? a inakataba ganin anyi sadaka. dadan mutun kamar dai yartsana zaiyi sadaka da yarsa???? wlh kuwa mom haka yakeyiwa yayansa anan yakwashe labarin kaf zamansa garin yafada mata yacigabah nasan kece kawai zaki sama man mafitah dan banada kamarki mom plz kitaimakeni wlh banason dad yasan wannan al amarin””
taja doguwar ajiyar zuciya shikenan gobe kagyara kabiyo hanya dakai da itah ninasan yanda zanyi amman katabbatar kadawo gobe “”wow tnz mom shiyasa nake kara sonki wlh Allah dai yabar mana mom dinmu
tayi murmushi itah dai tanason Haidar duk cikin yayanta yafisu natsuwa da tunani shibaida wata abokiyar shawara idan ba mahaifiyar shibah duk wani abunda zaiyi saida saninta
Aisha…………………gentle
[7:22PM, 11/13/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
08
sunyi sallama ya aje wayan yana murmushi hakika dabadan mom din saba yasan saiya kade har ganyensa muddin dad yaji abunda yafaru bazai taba yarda cewa YAR SADAKA!!! cebah zaice wlh da saninsa hakan yafaru waye Haiydar?????
Alhj Abubakar mai shadda shine asalin sunanda ake kiran sa yayi siyarda shaddo di alokacin yana saurayi shiyasa sunan yabishi haryanzu bai bacebah duk da kudin da yakedasu ayanzu
Alhj abubakar su hudune awajen mahaifiyarsu hajiya balkisu”” wadda suke kirah da ummah ”auwal shine nafari sannan umar sai abubakar sai autarsu huraira mahaifinsu yarasu tunkafin karfinsu yakawo”” Alhj auwal shine na fari. matansa biyu hajiya rabi da hjy saratu ” rabi itah ce babba yayanta biyar hudu maza dayace mace”” dahir kabir kamal kasim sai khadija
saratuce amarya yayanta uku mata biyu sai namijin ne auta””waleed zainab da Aisha” “” alhj umar matansa biyu hjy uwani tanada yaya biyar. hameed sai sa”eed sannan kausar da fiddausi sai na”ima
matarsa tabiyu maimuna”yayanta biyu maza” is”haka da ibraheeem”” alhj Abubakar matansa biyu hjya safiya itah ce uwar gida”” yayanta shida hudu maza biyu mata “” nuradden. Ahmad” Usman sai Haiydar. farida sai auta. kursum””
hjy haleeema itah ce amarya yayanta uku daya namiji biyu mata”” muhammad sai asiya sai autarsu zulaihat”hjy hurairah wadda zuke kirah da gwaggo hure yayanta biyu muh”sen sai hameeda””
family ne maicike da farinciki da fahimtar juna Alhj abubakar gidansa yana nan nasarawa katon gida naji dafadi kowaccce tanada bangarenta inda yayansu maza bangarensu daban matan ma haka
duk sati sukanyi meetin na family dinsu anan gidan ummah dake G R A kusa da gidan Ahj auwal idan akwai wata matsala anan kowa zai fadeta asamu mafitah bakatabajin wani abu yakunno kai harwaje ajiya wani sa in ma ko mahaifiyarsu bazatasan abunda yake tsakaninsubah
gwaggo hure macece maishegen son abun duniya itah dai taga nata yasamu ga bakar masifah kwata kwata muh’sen baigado halintabah amman hameeda kamar tayi kaki tatofar” yayansu kam yanbokone kamar yanda iyayensu sukai boko
gwargwadon hali sunbasu tarbiya dan duk yayan gidan kusan makaranta guda ake sakasu har islamiyya kafin mace tayi aure saita sauke alkur ani sannan tanada digree akanta”” sabanin hameeda dabata dauki karatun islamiyya abakin komaibah kuma gwaggo tadaure mata gindi
Alhj abubakar duk da yana kusan karami acikinsu yanada zafi kusan ma yafi gwaggo hure danshi idan yayi magana daya tobaya sauyata
Aisha……………….gentle
[8:49PM, 11/13/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
09
Sunyi shawara atsakaninsu yazu rika aurawa yayansu aure cikin danginsu saboda kara dankon zumunci”dahir shine ya auri farida. yayansu biyu amira sunan mahifiyarsa aka sakamata rabi atu suna kiranta da ameera namijin ne safwan””
sai kabir da fiddausi dansu daya abdallah sannan nuradden da khadija yayansu uku biyu matane yan biyu hasana da husaina sai gambonsu bilya”ahmad da zainab dansu daya bello
kuma suna zaune lafiya da fahimtar juna baka samun wani sabani atsakaninsu kuma kusan dama tunda aka fadamasu sunason junansu kuma haka sukai biyayya bakajin wani sabani kuma basu hanaka idan kanada ra ayin yin wani aure kafitah waje kayibah amman tilas auren fari yar gida zaka aurah
su haidar sune akan layi duk da haidar yafitah daban acikin su baifiye yawan zama agidabah hameda tana mutuwar sonsa shikuwa babu wacce yakejin haushi sama da itah saboda rashin kamun kanta
bata cikin jerin matanda yakeso duk da balaifi tanada irin nata amman shikam batai masabah batada wani abudazai gani atare da itah wanda harzaibashi sha”awa ana haka sai
suka hada taro kamardai yanda suka saba bayan anbude taro da addu”a Alhj auwal yafara gabatarda dalilin zuwansu wajen kamar haka nasandai kusan kunsan dalilin zuwanmu nan baiwuce akan matsalolin mubah
kamar kullum tunda Allah yanuna mana kun kammala karatunku lfy kundawo gidah””)yanzu sai maganar aure kafin kufara aiki “usman”” yadago kai yakalleshi na am abba””yanisah munyanke shawaran zamu hadaku aure da yan kannenku kamardai yanda akaiwa yannenku gasu nan kuma harda karuwa
usman dakai da Aisha” kamal da na”ima hameed da kursum. muh’sen da asiya is”hak da zulaihat. Haiydar da hameeda”‘
tunda yafara maganar gaban haidar yake dukan uku uku danshikam kaf yayan gidan baiji yanason kowabah tunda yaji ance dashi da hameeda zufah yafara karyo masa “” inashi ina wannan fitsararriyar yarinyar baigama tunaninbah yaji muryan mahaifinsa
ina fatardai kowa yaji abunda muka yanke kuma biki nanda wata biyu”danhaka kuyi kokarin sasanta kanku kafin lokacin ina fatar kuma zakuyi zaman lafiya kamar sauran yan uwanku”” idan akwai mai magana toyatashi yayi gaba daya falon yayi tsit
inka dauke haiydar dayaketa fifita da hannunsa sakamakon zufanda yakaryo masa “” mom talurah dashi sarai kuma tasan dalilin hakan dantunda take dashi baitaba nuna yana son wata acikin gidan ba hasalima mugun hausin hameeda yake ganin yanda gwaggo hure tasakantata yarinya bata ganin girman kowa sai fitsara ko shigar kirki batayi dan itah bata damu dasaka kayan mu na hausawabah kullum cikin kananan kaya kamar diyar arna
Aisha…………..gentle
[1:53PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
10
Alhj ya kalleshi haiydar lafiya kake ta zufah haka?? ah ah bakomai abba””shikenan babu mai magana??? kowa yayi shiru daganan suka cigaba da tattaunawa akan maganar haiydar mikewa yayi yafitah mom tana ganin haka tamike tana turah cikinta haihuwa yau ko gobe””
afalon kasa tasamu haiydar zaune yajingina kansa da kujerah yana jijjiga kafa”” kusa dashi tazauna hannunta dadorah saman kafadarsa sai alokacin yadan buda idonsa ganin mom dinsa yasa yadago””
yadanyi murmushin yake”” itah madin. murmushi tayi ganin yanda haiydar yake nema yaboye damuwarsa wanda kuma bazata boyubah duk yanda yakeda damuwa bazata taba boyuwabah garetah
Haiydar kayi hakuri nasan damuwarka duk akan wannan maganar ne dama nasan haka kuma kai kanka kasan baku akafarayiwa hakabah dan haka hakuri zakayi karungumi hameeda dama Allah yakaddara itah ce matarka
fuska yayamutsa” mom inaso kigane wani abu wlh banason wannan.auren kokadan bawai auren ne banasobah”itah cedai banaso nifah wlh mom angama dani arasa wacce za abani sai wannan yarinyar kekanki kinsan irin yarinyarda nakeso
kuma kina gani hameeda batada kodaya cikin abunda nake bukata “”yayi tsaki shikenan wannan abu ba al adabah”” bakomaibah amman adauki abu dauran azimun wanda ba addini bane”
tasake yin murmushi akaro nabiyu tana kallonsa haiydar nasan haka nasan hameeda batada tsarin abunda kake so ajikin mace amman kasani wannan hukuncin bawai nawabane ko naka na iyayenkane
kuma kasan babu wanda ya isah yahana wannan abu sai wani hukuncin Allah kayi hakuri kaji wlh banason kana saka damuwa aranka kaji tashi kacigaba da harkokin ka zantayaka da addu”a kaji haiydar
aduk lokacinda yadau zafi idan mom tana kwantar masa dahankali zainemi damuwa yarasa shiyasa baida wata abokiyar shawara idan ba itah”bah”yana son mom dinsa sosai kamar yanda itah ma take sonsa””
mikewa yayi yana murmushi to mom nibari infitah “”to adawo lfy dan Allah kasaki ranka kaji yana gyada kaiyafita tabishi dakallo harya bace ta girgiza kai haiydar kenan dadina dakai akwai saukin kai amman kanada naci akan abu
bana tunanin babanka zaiyarda dawata magana idan bata auren nan bah addu”a kawai zanyimaka amman ninafison farincikinka akan komai””tashi tayi zuwa sama”abangaren su hameeda kuwa suna komawa gida tayi tsalle tadane gwoggo
muhsen ne yayi magana keji wai kamar zaki karyata kewai yaushe zakiyi hankali kullum girma kike amman kina harkar kananun yara”kai kai dakata meye haka jikinka tahau ko nawa???? nifah wannan abu dakakewa yata yana damuna kamar bayar uwar kabah??
fitarmun daga ido wlh “”haba hjy wlh kidaina sakanta yainyar nan duk abunda tayi saikirika daure mata gindi nidai wlh gaskiya nake fadamaku yasakai yafita gwaggo hure tabishi da tsaki
Aisha……………..gentle
[2:58PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
11
tasake kankameta wlh umma naji dadi dakika ce ahadani da ya haiydar inasonsa sosai””shakuruminki ainasan kinasonsa shiyasa nace yadace ahadaku”” tayi mar mar da ido”” kuma ni ummah Allah bazan iyah zama da kishiyabah
ah sha kuruminki ai bake bazama da kishiya dan uwankinefah kuma yayanki aibai isah yakara aurebah saida izininmu””kikwantarda hankalinki kinji tayi murmushi tasake rungume gwaggo
duk yanda Haiydar yayi danya kawarda damuwarsa amman abun yafaskara kullum abun dada kunar ransa yake kwance yake saman kujerar falonsa yayi matashin kai da hannun kujerar daya hannunsa yana saman cikinsa daya kuma yadorah saman goshinsa
shikawai yasan irin damuwarda yake ciki gashi auren sai dada matsowa yake amman kokadan yakasa jin son hameeda cikin zuciyarshi daidai da kwayar zarrah baiji digon sontabah duk da mom tana kwantar masa dahankali yasauke ajiyan zuciya
wai saiyaushe su dad zasu gane andaina irin wannan auren yanzu zamani yasauya baidace anayiwa yara irin wannan bah tunda ba addini bane kuma ba al adabahshin basa tunanin idan wani yanason wannan wani zaiso kowafah da irin zuciyarsa
tsaki yaja..nikam duk ni akacuta gaskiya gashi tunda akasaka rana tabi duk tadameni yarinya babu kamun kai kamar bamacebah yana zancen zucinsa taturo kofah dasauri tana kwala masa kirah idanunta yakai saman kujeran dayake kwance dasauri takai wajen taduka kanta tadorah sakan kirjinsa””tana masa shagwaba. ya Haiydar tundazu naketa nemanka
cikin hanzari yadago tare da tureta ransa inyayi dubu yabaci cikin ido take kallonsa yazaka tureni ya Haiydar nifah matarkace”” tsawa yadaka mata kebanason shashancin banza”” haka akakoya maki taki tarbiyar saiki bari sai andaurah duk iskancinda zakiyi saikiyi amman bayanzubah meyasa kebakisan mutuncinki naya macebah
toni banada. wannan dabi”ar idan kekinga wannan waye wace nibanaso barganin ina kyaleki waimadai bana hanaki shigoman daki kai tsayebah batare da sallamaba??? waye yabaki izinin shigoman daki haka kawai kokina bina bashine
wlh wannan takuran dakikemun tafara isata..wai dolene saina soki nace bana sonki bana sonki kiyiwa Allah kibarni na sarara mana aurene dai andage dole saina aureki naji zan aureki amman dan Allah kibar zuciyata tasarara haka haba””ana mace babu kodan jan aji
ya Haiydar da bakinka kake budawa cewa baka sona???ah din nafada ko akwai abunda zakiyine??? mikewa tayi tarike kugu naji baka sona amman wlh dole ka aureni kokaki ko kaso kuma dole muyi rayuwar aure dakai
saikowa yasan ni matarka. ce kuma wlh saika soni saikayi abunda zakayi amman aurene babu fashi”kawai dan Allah yadorah man sonka ne shiyasa kakeman wulakanci ainima bani nasakawa kainabah
kuma wlh zuwa dakinka yanzu nafara bazan baribah sairanarda akadaurah mana aure””dakake zancen wai banda jan aji menene abun jan ajin tunda ni matarkace ainaga angama komai saurah fatiha kawai yarage
murya ta kwantar ya Haiydar nibansan meyasa bakasonabah menene narasa ajikina kallenifah tafara juya masa mazaunanta tana gyara rigarta yanda dukiyar fulaninta zasu fito amman ko dass haiydar baijibah tamkar ma yana kallon namiji dan uwansa
Aisha…………………gentle
[3:31PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
12
yasaki wani murmushin yake shikam abun natama yadaina bashi haushi dariyama take bashi tsaki yayi yamike tsaye yatako kusa da itah yanda zasu rika jin numfashin junansu yanuna mata hanyar waje””.naji duk abunda kikace gahanya nan agaida gida””
tsayinta tayi batada alamar ko motsawa balantana tasaran tafiya hakan yahasaloda haiydar hannu yasa yaturota waje yakulle kofarsa hannu yasa yadafe kansa wai wannan wace irin jarabace mace zata rika biyar namiji””yasake jan tsaki wlh indai ninema garin zan barmata
sai ankusah bikin zandawo basaitagannibah sannan zata zo saman kujerah yafada yana maida numfashi gaba daya kansa yadaure bayajin nishadi kokadan”tsaki yaja sannan yamike yabude kofah bangaren mom yatafi baisameta falon kasabah hakan yasa yahaurah sama “” zaune yasameta saman kafet din falonta nasama saman kujerah yazauna tare da huro iska tabakinsa
yajingina jikin kujerah””tunda yashigo take kallonsa tasan akwai damuwa afuskansa gashinan tanuna tayi murmushi sannan takirah sunansa”” haiydar’yadago kai yakalleta sannan ya amsa na am mom””lfy dai naga yanayinka yasauya????
yayi tsaki kema dai mom kinsani duk ranarda kikaga damuwa afuskata fiye da wadda nake ciki wlh wannna yarinyar ce mom ya akeso bawa yayi daransa wlh kokadan mom nakasa sakawa raina son wannna yarinyar
kullum halayyarta dada tsanarsu nake batada kamun kai kwata kwata dame zanji da kakabamun itah da akai kokuma dayawan naneman datake “”agaskiya nagaji zansamu dad inshaida masa nifah bana kaunar auren nan””yayi maganar yana kallon mom data saki baki tana saurarensa
haba haiydar kana ganin wannna shawarar zata bulle dakaine??? tokasani muddin kasanarda dadyn ka wannna maganar zaiyi mugun saba maka kuma zai iyah ma maidoda auren kusa kusa yaga iyakarka”” karadai kayi hakuri kafin ayi auren nan kataushi zuciyarka tafara sonta
inason kakoyawa zuciyarka son hameeda dankuwa aurenku babu fashi kasan Allah yanda suka dauki wannan abu badawasaba kafin kaima ai haka dahir yayi yariga yakamu dason wata yar makarantarsu”” babu irin tashin hankalinda baishigabah amman alhj babba yasa kafa yature
kai intakaice maka labari harsaida aka kwantar dashi asiviti ranar da akakwantar dashi aranar aka daurah aure cewar alhj babba idan yana iyah wa yahadiye zuciya yamutu”” toyanzu bagashibah yayansu biyu kamar ma ba ayibah
hmmm naji duk wannan mom amman airayuwarshi datawa ba iri daya bace ”haiydar haryanzu kakasa gane abunda nakeso kagane saiyaushe zaka gane illar fitarda rashin sonda kakeyiwa hameeda kasanifah. idan wannna maganar tafita akwai matsalafa!!!
ina sake baka hakuri kadada tausar zuciyarka “”yanisah naji mom amman inaso kiyiman wata alfarma daya””tasake kallonsa tame kenan haiydar? inaso dan Allah kiyarda inbar garin nan””‘kirji tadafe bangane mekake nufibah haiydar kabar garin nan kamar yaya kanaso farincikina yayi kaurah kenan???
mom bawai intafi shikenan bah ina nufin indanyi nisah daganan kozan samu sanyin zuciya kafin auren nan wlh muddin ina kallon wannna yarinyar nasan akwai matsala bazan iyah tausar zuciyataba kiyarda dani mom albarkarki kawai nake bukata
kinsan yarda zaki fahimtar da dad kada yagano hakan plz mom kece kawai zaki iyah shareman damuwata””tanisah um um Haiydar inajiye maka abunda zaije yadawofah””‘kana ganin barin garin nan zaisa hankalinka yakwanta???? insha Allah mom kidai tayani da addu”a
shikenan yaushene tafiyar kuma wanne gari zakaje??? um mom saidai nagani yanzu zanje wajen fadil idan nadawo zan sanardake garinda zanje amman gobe nakeson tafiyar””shikenan Allah yakaimu to ameen mom yamike yayi mata sallama yasauko
Aisha…………………gentle
[4:03PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
13
kaitsaye dakinsa yanufah saida yasakeyin wanka kananan kaya yaska yafito das dashi yadauko wayansa yakirah fadil yana dauka yace yadai mutumina kana ina??daya bangaren aka amsa ina gidah mana ina kake tsammanin zanje””k ganinan shigowa
fadil shine abokin haiydar tun suna yara karatuma tare sukayishi yanzuma suna shire shiren fara aikina babbar asiviti “”babu nisah tsakanin gidan su fadil da haiydar gidan dake tsakaninsu baiwuce gida shida ba
dayakai kofan gidan baishigabah anan kusah da gidan akwai wata bishiyan bedi anan yajingina yakirah shi awaya bajimawa yafito yakaraso inda yake yana fara a ango kasha kamshi hannu yabashi suka taba
yadai ango naga sai bannar rai kakeyi nina dauka idan nayimaka kirari zaka hadani dako yar 5k ce””tsaki haiydar yayi yana kallon wani guri daban yace menene abundahar zan barnar da kudina akansa””*Allah dai yakyauta aida inbada nairah akan wannna kirari kara tafadi insan hasararta nayi
yayi masa duban rashin fahimta haba haiydar wai kana nufin haryanzu kananan akan bakarka? yace har gobema””)yanayin yanda yayi maganar yasa fadil yin dariya””yadafa kafadarsa mutumina zuciyar nan taka tanada wuyar sha ani” wai saiyaushe zaka koyawa zuciyarka hakuri dadangana!!! yace babu rana indai akan wannan yarinyar ne kama daina bata bakinka nifah banji inasontabah kokadan
kuma banajin zansota koda anan gabane kaga mubarma wannan maganar danni bashine yakawo nibah”” kasan meyakawoni””??? yayi murmushi ina kuwa zansani mukarasa ciki saimuyi magana”” ah ah barni anan ma ya isah sauri nake akwai inda zanje
kafansa yadora saman bishiyan yasake jinginawa jikinta “” wlh fadil sonakeyi inyi dan nesa da gidah kafin auren nan”” nalurah zama na anan yanasakani inajin tsanar yarinyar nan amman idan nayi nesa da itah nasan komai zaizoman dasauki yakake ganin yadace????
fadil yanisah yana kallon haiydar dariyace taci kafinsa saida yayi mai isarsa sannna yakalleshi haba haiydar ina tunaninka da natsuwarka suka tafi”” yanzu akan dan wannan zakabar garinku kayi kaurah zuwa wani gani tome kake gujewa auren??? ni wlh danine kai nasamu za aman aure wlh hankalina kwance
bansan wuyar komaibah saidai iyayena suyiman namaso ace nine kai wlh haiydar kam baki yasaki yana sauraren maganarsa saida yayi shiru sannan yakalleshi kagama???toni banaso kuma ni ba aman gwanintabah kaga idan bazaka bani shawarabah akan nisantar wannan yarinyarbah
kadaina bani shawara akan fuskantarta ”kasandai kaibanayimaka haka “”cool dwn mana. abokina nimadai kawai neman. tsokanane amman nadaina tunda bakaso yanzu yakakeso ayi??? yauwa kokaifah sonake kafadaman sunan garuruwa bananan kusabah amman nafison kauye naji ana cewa zaman kauye akwai dadi sosai
nima zan jarrabah ingani koda damuwarda nake ciki zata ragu”” yanisah eh toh kasan dai kusan ince dagani harkai bama abota zama kasar nan bane kaga kuwa bansan sunayen kauyukka bah amman mai aikin gidan mu inaji suna labari sunan garinsu
umm umm kaga sunan garinfa yashigemun “”yasake yin tunani yauwa funtuwa”” acen akasamowa hjya itah kuma gaskiya tanada hakuri idan tana bawa su aneesa lbrin garin nima nakan saurara amman kana ganin zaka iyah rayuwa garinda bakasan kowaba haiydar???
Aisha………………..gentle
[4:31PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
14
manta kawai abokina inane kuma funtuwa???? yace toh nan fadai wlh bansan ko awanne gari akebi zuwa cenbah amman kabari zan tambayi itah mai aikinmu idan tafadaman zankirakah awaya insanar dakai”” yaushene tafiyar??yashafo sumarsa gobe nakeson tafiya insha Allah””
ah kace tafiyar dai kakawotah kusah amman dad yasan da tafiyar kuwa??? kai ina zanbarima yasani duk wannna abunfah baimasan inayibah mom ce kawai tasani kasanfa dagakai sai mom kune kawai kukasan sirrina bayanku babu wanda yasani sai itah yarinyar
danyauma saida nafada mata dantabatamun rai.. yana kallonsa yace meyasa zakayi haka bakajin tsoron tafadawa babarta itah kuma tasanarda dad?? toya zanyi fadil kaikanka kasan bana mu amala da mata kokadan banason mace tana. matsowa inda nake amman wannan yarinyar datashigo burinta daya shine tafada saman jikina itah kenan kullum shigar kananan kaya kamar ba yar musulmabah
zakaga tafadoman cikin daki ba sallama bata tunanin awane yanayi zata sameni itah baidametabah wannan kake tunanin zan iyah rayuwar aure da itah haba kwata kwata batada halin macenda nakeso zan aurah”” sanin kankane atsarina banason mace maitsayi sosai tojita dan Allah kamar falwaya tatafi kodan lankwasa babu””
inason mace maihaske amman bana bleaching ba amman itah idan kalurah maitake shafawa”” inason mace ma abociya gashi maibaki dasantsi itah kuwa guiguice saidai tayi kari dana doki””inason mace mai cikakken dirin jiki komai najikinta daidai yanda idan naganta tundaga nesah yanayina zai sauya
itah kuwa batada kodaya idan ma naganta daga nesa raina yake baci kafin ma takaraso inda nake”matarda zata kasance burin rayuwata itah ce wadda zankalli cikin idonta inji nakasa natsuwa gaba daya na urorin jikina sudaina aiki to wannan itah ce irin matarda nakeson mallaka
takasance maitarin ilimin addini koda kuwa batada na boko nibandamubah””inaso takasance maijin kunya akoda yaushe duk wadan nan abunda nalissafo kafadaman daya wanda hameeda take dashi bayan iskanci da wulakanta mutane””
gashi yanzu dad yabata man tsari gidana dana gama banaso kowace mace tashiga cikinsa sai wacce zuciyata takeso amman gashi dad duk yarusah man tsarina”‘yayi tsaki nikilantama bazan zauna kasar nan bah idan mukabar kasar cen tayi harkarta inyi tawa idan nafita aikina bazan dawobah saitayi barci kaga kowa zaiyi harkarsa
harkafin insamu cikar burina dankuwa nibansan nayi aurebah saina mallaki mace mai irin siffofinda na zayyana maka yanzu””fadil yajinjina kai to Abokina Allah yanuna mana wannan ranar muje intaka maka
dan Allah kada kamanta fa katambayeta dan komai yaunakeson shiryashi gobe indau hanya “”shikenan bazan mantabah saikaga kirana harkusan gida yakaishi sannna yadawo duk wani shirye shirye yakammalashi
zuwa dare saiga wayar fadil cikin sauri yadauka lokacin yana kokarin shiga gida dad yana kiransa””yadauka yadai mutumina nihar ina shirin bugamaka sammako dasafe tunda najika shiru” yayi dariya afuwan wlh kwata kwata nama manta saiyanzu abun yafadoman arai “” aidole ka manta tunda bakai ne cikin damuwabah metace maka???
Aisha……………….gentle
[8:13PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
15
yayi dariya najidai tace ta zaria zakabi garin yananan gaba da zaria kadan””k yatace maka yanayin garin??? ah toh banyi mata wannan tambayarbah idan kaje ai zaka gani dakanka bah.. toshikenan nagode saimunyi waya dad yana nemana
shikenan angon hameeda”” tsaki yayi yakashe wayarsa dama fadil yasan haka yayi dariya haiydar kenan “” da sallamar sa yashiga bangaren dad dinsa mom tana kusa dashi kasa yasamu yazauna sannan yagaida dady din””ya amsa”” sai shiru yabiyo baya””yayi gyaran murya mamanka tacemun zakaje katsina wajen gwaggonka” shine take fadaman nace bari inkiraka inji kwana nawa zakayi dan karkaje kayi zamanka””
yasaki murmushi jin abunda mom tace yace eh dady bajimawa zanyibah insha Allah bazan wuce ma sati daya ba”yagyada kai shikenan amman dai kaje gidan su hameeda ko???? gabansane yabada rass yadan sosa kai ah ah dad naga tazo dazu ai mezaisa kuma intafi””
yayi murmushi shikenan amman aikaga sauran yan uwanka suna zuwa tadi amman kai kosau daya bantaganin kajebah kodai zabin namu baiyi maka bane???yakirkiro murmushin yake ah ah dad nina isah kuyiman zabi ince banaso kawai dai naga tana yawan zuwa gidan nan shiyasa nima bana zuwa
kuma koda najema bana samunta agida”” yagyada kai nafahimceka haiydar Allah yataimaka idan kaje kagaishesu nasan koda zanfitah office baka tashibah kuma kafin indawo nasan kawuce”” yaduka zasuji dad nabarku lafiya mikewa yayi yana maijin dadi akan abunda mom dinsa tayi masa
saida yakai bakin kofah yadan waigo yasan shitake kallo haka kuwa shitake kallo tana murmushi babban dan yatsansa ya daga mata alamar jinjina tasaki fara”a
tun cikin daren duk wani siri dazaiyi yagama kammalashi hatta kudin da zai bukata saida yatanadesu
fatanshi daya Allah yakaishi lafiya. saida yawatsa ruwa sannan yakwanta saman lafiyayyen gadonsa yasaukarda ajiyan zuciya daga gobe nahuta da kaya idan tazo bata samenibah saitayi tazama adakina””
da wannan tunanin barci yayi awon gaba dashi bashi yafarkabah sai asubah yayi alwala yawuce masallaci dama al adar sace koda angama sallah baya dawowa gidah sai yasamu malam yakarashi karatun littafansa
sai takwas yake barin masallacin yakaraso gida kaitsaye dakinsa yanufah yatarar har ankawo masa break f dinsa saida yaci yayi nak sannan yakwanta bajimawa barci yadaukeshi
saikusan shabiyu yafarka
Aisha……………….gentle
[6:48PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [8:47PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
16
Agurguje yayi wanka sannan yashirya manyan kaya yasaka harda hula dinkin yayi masa kyau sosai yafito zuwa bangaren mom dinsa afalon kasa yasamu kursum tana kallon more than love”tana ganinsa tasaki fara a yaya ina kwana
shima murmushi yayi lfy qalau amarya”” murmushi tayi tarufe fuskanta”” yaya wai katsina zakaje wajen gwaggo dan Allah katafi dani inga sister jamila”” ido yaware ah ah nibabu inda zanje dake kinaso hameed ya iskomu cen idan baigankibah
kai yay wlh bazaima bimubah nidai inshirya zaka dani??ah ah kursum kafin injefah zanbiya wajen wani abokina kuma kinga baidace inje dakebah kina mace kiyi hakuri idan sukazo biki aizaki gansu kinji!baki taturo. tunda bazaka danibah nahakurah yayi dariya mom tana samane????
ah ah tana kichin inkirah maka itah ne?? ah ah bari insameta acen yanzu kursum gaki zankadediya dake amman kuma bazaki iyah taya mom aikibah saidai kibarta tayi”” sai na gani idan kikai aure wazaije yadinga girkawa hameed
la yaya nizanyi masa mana wlh itah mom cewa takeyi wai ban iyah bah bazan yiwa mijinta jagwalgwalobah shiyasa nikuma nadaina zuwama””muryan mom sukaji dake dawa haka sarkin surutu kedai kursum bakinki ko ciwo bayayi””
la mom nidin aikuwa banada surutu kamar ya Haiydar””tana murmushi takaraso inda yake dakyarma tasamu tazauna saman kujerah tana kallonsa yagurfana kasa yagaisheta ta amsa da fara a shirin kenan kai yagyada insha Allah mom amun addu”a
kada kadamu aduk inda kake kana tare da addu”a ta tanaso tatambayeshi wane gari zaije amman kursum tatsaresu da ido shiyasama bata tambayeshibah yamike mom bari intafi kada dare yamun akan hanya”” shikenan inazuwa””
kichin takoma tadauko masa babbar kula danbun naman kazane yaji kayan hadi sai kamshi yake ya karba yana murna kai ammanfa nagode mom ”kursum tamike taleko kai kai yaya duk ina zakaje dawannan danbun nidai kasammun idan ya hameed yazo anjima inbasa shima yanason dambun nama
kokallonta baiyibah yakulle kular”” nahanaki mom dina tamun idan kinada zuciya kema kishiga kichin kiyiwa saurayin naki”mom dai dariya kawai take yanda haidar yake wasa da kannen sa duk yan gidan basu cika sakar masu fuskaba
tace amman haiydar kafin kawuce kasamu maman zulai kuyi sallama””insha Allah mom zanje””saimunyi waya’to Allah yakiyaye yace ameen yasakai zaifita kursum takwala masa kirah kamar wanda yake nesa da itah yawaigo lfy dai wannan kiran
bafa hameed bane yarinya”” ya haiydar nidai baka baniba naga kasakai kafitah waidama dan wannan ne kike kirana?to nahana kizo kikwata mom natafi””to haiydar Allah yakiyaye saida yabiya bangaren maman zulai sukai sallama tace idan kaje kagaishesu yadade cen ma suna wasa da zulai yana tsokanarta wai yaga tana haske koduk zumudin auren ne
kai yaya””wlh dason zolaya kake ina maganar zumudi tunda ba zabin raina zan aurabah”” dam dam yaji akirjinsa ashedai bashine kawai yakekin wannan auren ba amman kokadan zulai bata nuna bata ra ayin auren ba
yasha ganin is”hak yazo firah yanda suke firah cikin jindadi da annushuwa kamar dama sundade sunason junansu ashedai taciki naciki nidai inaganin kokarinwadanda suke iyah boye damuwarsu
Aisha………………gentle
[11:49PM, 11/14/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
17
nikam ai damuwata bazata taba boyuwaba musamman ma akan abunda banaso”yakalleta kina nufin bakyason is”hak??? tayi murmushi adakam bana sonsa yaya amman yanzu nafara koyawa kaina yanda zan soshi ganin banida wata mafitah face bin umurnin iyayena
tunda kowama haka akaimasa niwacece dazan bijirewa umurninsu”” yajinjina maganarta abunda tafada gaskiyane shikanshi yanaso zuciyarsa tayarda dahakan amman taki abu daya kawai yasani shine bayasonta kuma bazai taba sontabah
mikewa yayi yana kallonta agaskiya naji dadi. maganarki zulaihat wannan yanuna baki bar tarbiyanda iyayen mu suka bamubah nibari infita yakalli hjy nizan wuce to haiydar Allah yakiyaye hanya kagaishesu”haka yafito yana tunanin magan ganun zulaihat
agaskiya tayi dogon nazari kuma tayi hankali wajen tilasta wa zuciyata abunda bataso toni meyasa tawa zuciyar takasa yarda dahakan???? duk yanda naso indasawa zuciyata son hameeda sai injima tsanarta tadarsu sakamakon inji sonta
saida yabiya dakinsa yadauki kayansa sannan yafito yatari dan adaidaita sahu yace yakaishi inda ake shiga motah yace k haumuje”” harsuka kai tashar mota tunanin maganar zulaihat kawai yakeyi sunki subar zuciyarsa yana zuwa cikin sa a kuwa mota tacika mutun daya akejirah
yabiya dan adaidaita sannan yashiga motar karen mota yakarbi kudin motah motah tatashi kowa yana harkar gabansa wadansu suna danne danne waya wasu surutu suke wasu kuma sundan fara gyangyadi”” wasu suna kallon titi yanda mota take keta daji bishiyoyi gasunan kamar anshukasu
wasu kuma suna sauraren gulmane”inkadauke haiydar dagaba daya tunaninsa baya cikin motar yanakan tunanin auren da za aimasa gaskiya yayi wauta mezai hana yazauna shima kamar yanda zulaihat tayi watakil shima yajiyanason auren
wata zuciya tace anya kuwa???? aiduk abunda baka sonsa zaiyi wuya kasoshi musamman itah datakeyin dabi”unda suka sha banba dawanda kakeso wacce zaka auradin tamallakesu”” yasauke ajiyan zuciya yakai kallonsa saman hanya yana kallon yanda itatuwa suketa rangaji kasancewar iskanda akeyi
yanzu tunaninsa daya”” yazaiji agarinda zaije kozaiji dadin garin ???tunani kam bazai bar zuciyarsabah dama yasan haka tunranar da aka saka wannan ranar dama yasan karshen farincikina kenan
sunyi tafiya mainisah wasukam sun dade dayin barci ankai zariya wasu sunfara sauka””ansoma tafiya shidai haiydar kallon hanya kawai yake andan taba tafiya banisah wani yace driver daka wuce giwa kadan zaka ajeni”” haiydar yadade yana nanata sunan cikin zuciyarshi
giwa giwa giwa dagajin sunan wannan kauyen nasan kila zaiyi dadin zama
Aisha……………………..gentle
[6:48PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [4:58PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
18
Andan taba tafiya maidan nisah aka kawo dan kauyen driver yatsaya mutumen yafita shima haiydar yafita driver yakalleshi malam ba funtuwa zakajebah??? baikalleshibah yace ah ah dama anan zan sauka yadau kayan sa kawai yabi hanyarda yaga mutumen yabi
batareda yasan inda zashibah yakai daidai saitin wata bishiya saiyayi tsaye yana tunani anya kuwa baiyi wautabah dagajin sunan gari kawai zaice anan zaisauka fuskansa yarufe ganin iskanda yataso gashi har anyi la asar yadubah agogon hannunsa karfe biyar harda minti goma
to ina zaije bari kawai yaje gidan mai unguwa yasandai bazai rasa wajen zamaba””‘kafin gobe yagani idan garin baiyi masabah yakarasa funtuwa yana yanke wannan shawara saiga wani dattijo zaiwuce yayi masa sallama.. haiydar yaduka harkasa yagaishe shi
daga ganinsa daga daji yadawo danga karanan akansa yasaukarda karan yakalli haiydar daga ganinsa kam badan garin bane ya amsa lfy qalau dan samari daga ina kake haka kazo kan hanya katsaya””???
yanisa baba ni bakone daga kano nake yanzun nan mota ta ajeni garin nan kuma bansan kowaba ina neman gidan mai unguwane kozan samu inda zan zauna kafin intafi”dattijon yajinjina kai yasake duban haiydar yace taso muje
dama yakawo kusa da gida anan yabar karan nasa yana gaba haiydar nabinsa harsuka kai cikin wani zaure suka shiga yace masa bisimillah hannun dama yabi wata hanya haiydar yana binsa suka kai wani waje dakine daya sai bayi yacema haiydar tsaya nan inazuwa
haiydar yana nan tsaye yana karewa wajen kallo ginin kasane amman wajen ashare yake tsaf kaman akwai mutane awajen bajimawa saigashi yadawo tare dawata yarinya fara siririya ma abociya siririn hanci da kyawawan idanuwa tana rike da tsintsiya yace shiga mairo kishare maza ina zuwa”” to baba dakin tashiga tahau shara
duk dabawani datti sosai bayan tashare saiga dattijon yadawo dawata tsohuwar katifah ungu mairo shimfida masa”” takarba tashimfida””sannan tafito baba nagama””intafi wajen wasata ko?yayi murmushi kedai bakyajin magana yanzun nan naji ana nemanki cikin gida kije makaranta maza jeki wajen innarki ki karbo masa furah da ruwa to tace taruga dagudu
yabita da kallo yana girgiza kai sannan yamaida kallonsa wajen haiydar wanda shima din suyake kallo yayi mumushi bisimillah yaro”” haiydar yadauki kayansa da sallama yaduka yashiga dakin
yana yatsina fuska wace kaddarace takawoshi nan tunda yake baitaba tsammanin zaishigo irin wannan garin ba kuma wai anan zankwana??? kayansa ya aje yasamu gefen katifar mai kamada tabarma yazauna dadari dari ma yazauna samanta dattijon ne yashigo rike da fura yarinyarda aka kirah da mairo tana rike da ruwa
da sallamar sa ya ajefuran itah ma ta aje yakalleta maza maza kidauki allonki kiwuce makaranta kada infito insameki wajen wasar nan kinajinako” to baba sannan tasakai tafita”yamaida kallonsa wajen haidar yaro baka fadaman sunankaba???
Aisha………………gentle
[5:24PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
19
yayi murmushi baba sunana haiydar kuma ni dan kano ne nayi sha awar zuwa kauyene dalili inajin ana fadar kauye yanada dadin zama shine nazo indanyi hutu anan dama funtuwa zanje sainaji wani yace asaukeshi anan nima sainaji ina sha awar zama anan din”” yayi shiru
dattijon yayi murmushi ikon Allah malam haiydar kana iyah zama kuwa akarkara kaida kasaba dazaman birni inakai ina zaman daji??? haiydar yayi murmushi haba baba kuda kuka zauna balantana kuma ni””
ai idan har kuzaku iyah rayuwa anan nima zan iyah dan babu abunda nafiku dashi nima mutun ne ai kamarku”yajinjina kai dajin kalaman haiydar suna cike da ilimi daga ganin yaron yafito gidan manyan mutane yakalleshi
hakane maganarka haiydar nidai sunana shehu amman anakirana da hardo ni bafulatanine nima zamane yakawo nan amman asalina badan nan bane ina tafiyane daga gari zuwa gari danazo wannan kauye saina zauna naji dadin garin kaga har antara iyali mata na uku kuma inada yara sunfi ashirin jikoki bansan iya karsubah
wannan dakin ma dakake gani dakin yayan mairone dasuka zauna da matarsa yayi nashi shine suka koma yatashi maigari bayanan yayi tafiya shiyasa nasauke ka anan idan haryayi maka kazauna harsanda zaka koma “”
haiydar yaduka yana godiya amman naji dadi sosai baba Allah yasaka da alhairi ameeen ameeen kaga bari inbarka kasamu kahuta yamike yafita anan yabar haidar kamar yafasa ihu waishikam yazai iyah zama wannan gari haka???
yadauko furan da aka ajemasa cikin kwanon ruwa sabo dal ganin tsabtar sa shiyasama haiydar ya iyah shan furan bayan yagama yafitowaje akofar gidan yasamu wani yaro yakirashi yace dan Allah shiga wannan gida kasamoman ruwa zanyi alwala yace toh dagudunsa yashiga gida
yasamu innar mairo tana tankaden garin tuwo yace wai wani dan birni yace asammasa ruwa zaiyi alwala cikin sauri ta aje rariyar tadauko buta tacika masa itah daruwa tamika masa yakarba yakawowa haiydar yakoma cikin gidan saida yataba ruwa sannan yayi alwala
saida yayi tambaya akanuna masa masallacin simadin ginin kasane amman babu rufin sama gakuranan dayawa sai wadansu tabarmi duk sun yage haka yayi sallolinda ake binsa yana nan zaune har akai magrib maifita masallacin bah
kuma baisan kowabah kowa yazo saidai yabishi da kallo””saida akai isha i hardo yakarasa inda yake “”yana murmushi wai haiydar kaine zaune anan tundazu naketa neman yayi murmushi yabashi hannu suka gaisa yace ai baba tundanashigo nan banfitah ba””
haba kaiko tahaka yazaka gane dadin garin kazo muje inhadaka da halliru yayan mairo yarika zagawa dakai kana ganin gari tare suka fito masallacin zuwa. kofar gida yace shiga ciki inazuwa bari in nemo shi kai kawai haiydar yagyda yashiga ciki yasamu ankawo masa abinci harda fitilar kwai”yayi murmushi kawai ko abincin bai kallabah furan kawai yasha sannan yazauna
Aisha……………….gentle
[6:05PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
20
baijima da zamaba saiga hardo yayi sallama tare da halliru haiydar yabashi hannu suka gaisa hardo yace to haiydar gadana halliru duk abunda kakeso katambayeshi kada kaji kunyar komai yakalli halliru
kaikuma ga haiydar nan karika yawodashi yana ganin gari yace to baba anan yabarsu yafita halliru yakalli haiydar yana murmushi taso muje yanzuma anfara wasa adandali bamusu kuwa haiydar yataso suka fito sunfara tafiya halliru sai zubah masa surutu yake banda umm ah ah ko eh babu abunda yake gamashi dashi
halliru yakalleshi haiydar kamar surutu baidamekaba nikuma gani akwai surutu”” yayi maganar yana kallonsa “”yayi murmushi bakomai abokina.inajinka ai nima inada surutu kawai kasan bakunci saimutun yayishi kona kwana dayane
hakane kam amman haiydar zaka iyah zama garin nan kuwa???batareda ya kalleshibah yace saboda me kafadi haka halliru? yace naga cimarmu dataku badaya bane kamar bazaka iyah cin abunda muke cibah
haiydar yasaki murmushi maidan sauti yace haba kaikuwa kaiya akai ka iyah cinsa??shima yayi murmushi yana kallon haiydar aikaga nina saba kaikuma baka sababa” yace indai dan wannan ne kada kadamu nima kwana biyu zansaba bakasan nima masoyin furah bane hardai wadda aka kawoman dazu nibantabajin fura mai dadi kamartaba kaman damun injin
halliru yayi dariya daidai sunkusa ga dandalin danga hayaniya nan haiydar yakallah yana jinjina yawan mutanen wajen halliru yana hango talatu yasaki fara a yana kallon haiydar yace nifa nahango mutunniyata””haiydar yace kenan tafiya zakayi kabarni yace ah ah muje kayi kallo mana
yaja hannunsa zuwa inda suke rawa gaba daya hankalin yammatan da samari yadawo wajen haiydar wadan dasuke gefe suna firah da samarinsu suma suka gangaro dandalin”” anata sowa ganin talatu tashiga fagen rawa akafara sakin kidah
talatu ce tafara waka””ahayye mui gada adandali sauran suka amsa ahaiye mui gada adandali””ahayye mui gada adandali””kowacce acikinmu zatazo tayi gada “” gada adandali””saina zabi nawa yammata dukka ku kauce sauran suka amsa gada adandali
ni imfadi nawa!gada adandali fadesha munaji gada adandali”” sahibina halliru taso gada adan dali taso taso muyi wasa gada adandali duk acikin mata ni namasu zarra ahankali take wakar tana takawa zuwa wajenda halliru yake shima saiyabiyo bayanta yana takawa
gaba daya matan wajen suka rangada guda”” halliru yafara zubah mata kudi shima yana takawa aikam mai haiydar zaiyi inba dariyabah harda hawaye ganin yanda halliru yake gantsare gantsare yana rawa kamar bace daganan aka tsaida kida
daganan wata tashigo akacigabah dakidah kowacce haka zatayii da itah da saurayinta harsuka gama haidar dariya kamar cikinsa zaifashi bayan angama rawa yammata suka kebe da samarukkansu suna tadi shidai haiydar gefe yakoma yana kallonsu ko ina kagani yammatane da samari saiwasu yanmatan dasuketa shawagi gaban haiydar
Aisha…………gentle
[6:37PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
21
Atunaninsu kozai taya shikam ko kallon arziki ma baiyi masubah”yana nan tsaye saiga wata tazo gabanshi kansa yana kasa tadan leka tayanda zata ganin fuskansa tace la ashe kaine aini dama tunda nahangoka nasan kaine dan binninda nagani dazu gidan mu””
yadago kaiyakalli mai maganar yakirkiro murmushi danshima yaganeta yace mairo yaushe kika zonan?? tace tundazu nake nan muna cen dani da kawata munashan rake aitunda kazo naganka dakai da yayana””
yayi murmushi toni ina raken tawa???? baki tarufe yokuyan binni maizakuyi da rake kuma kuna shuka rakene????”” yayi murmushi ah ah amman aimuma munashan raken”” tabdi to aini kaga nariga nashanye ko??? kuma niyanzu banida kudi dasai insiya maka amman kabari gobe idan naje gonar babana zandibo maka maiyawa ko???
wai itah wannan yarinyar komai nata tambayane duk tayi magana kuma saita tambayi mutun yasake kallonta shikenan nabari hargoben amman kinga dare yayi kije gida hakanan… baki taturo kaidan binni nifah banajin barci kuma larai bata gama firah ba dasai mutafi
yayi shiru sannan yace kebakida saurayine???? fuskarta tarufe da tafin hannunta tana dariya wai itah kunya yasake tambayar ta zatabashi amsa saiga halliru yakaraso inda suke””ah wacece nake gani haka kamar mairo”” tayi dariya yaya nice baka ganenibah???
yace haba auta aikocikin duhu ina ganeki mekikeyi anan ?? takalli haiydar nima dan binni nagani shiyasa nazo inda yake”” yace auta bahaka ne sunansaba sunansa haiydar”” tayi shiru saicen takalleshi amman dai wannan sunan turawane ko????
haiydar yayi dariyar da baima shiryabah tace gaskiya sunan akwaiwuya nidai dan binni zance yafi sauki ko??halliru yayi murmushi shikenan auta maza kitafi gida haka dare yayi tace to takalli haiydar dan binni sai da safe baima amsaba taruga dagudu tabi hanyar gida yabita da kallo yana gyada kansa
saikusan shabiyu sukabar dandalin zuwa gida anan sukai sallama yashiga ciki shikuma halliru yawuce dakinsa”” hakadai haiydar yaketa rayuwa agarin har tsawon sati daya yanzukam yasake dasu sosai kamar dama yasansu
kullum yana zuwa dandali tare da halliru akai akai yakanshiga cikin gidan yagaida matan hardo”suna zaune gindin bishiya da safe ya kalli halliru yace wainikam garinkun nan ina ake samun service tunda nazo banyi waya gidabah nasan hankalin mom dina yana kaina
yace meyasa tunda kazo baka fadaman ba taso muje yamike suka kama hanya saida sukayi tafiya mainisa sannan suka kawo gindin wani icce anan suka tsay haiydar yakunna wayarsa
mom dinsa yafara kirah kirah daya kuwa tadauka kakyauta haiydar haka mukayi dakai kasa duk hankalina yatashi tunranarda katafi kullum cikin aikin neman layinka nake amman akashe nakirah fadil shima yace baisamunka
kanacen hankalinka kwance mukasakamu adamuwa””” yayi dariya kwantarda hankalinki mom inanan lafiya qalau wlh “” kiyi hakuri babu service ne garin shiyasa nima nadamu sosai inji muryanki”” baka damubah haiydar daka damu dabaka nemi wae kayi zamankabah kosau daya aisaika kirani insan kana lfy
ayiman afuwa mom kaina akasa insha Allah hakan bazai kuma faruwabah tubah nake””tanisah shikenan dafatar dai babu wata matsala””yashafo sumar kansa yana kallon halliru dayake cintar kananun duwatsu yana jifah dasu yalumshe idonsa
Aisha……………..gentle
[7:07PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
22
Qalau nake wlh mom ” yadai yanayin garin yanada dadi??? yace sosaima mom hardai idan mukaje dandali inda suke wasan gada tsakanin yan mata da samari kamar kada sutashi wlh”” mom tayi dariya lallai kazama dan kauye yanzu kana nufin kauye kake zaune???? yagyada kansa kamar tana kallonsa
mom yanayin kauyen akwai dadi wlh daganan sukacigaba dafirah sundade yana bata labarin yanayin garin bayan sungama yakirah dad shima sundade suna firah yakirah fadil yana dauka yace wata sabon gani aini nadauka funtuwa tayi dadi kamanta damu harnacewa mai aikinmu kodai idan bako yaje garin su mantawa yakeyi dakowa
haiydar yafashe da dariya kai mutumina baka rabo wlh da abun dariya aini bama funtuwa najebah wlh””:habadai to ina kuma kalula nidama nasan bazaka iyah zama funtuwabah kadai fadane kawai””yayi murmushi saboda shiba gari bane bako????
ah ah bancebah kada kasa yan funtuwa sujini kawai dainaga kamar bazaka iyah rayuwar cen bah”” haiydar yayi murmushi maidan sauti yace inanan wani dan kauye kusa da giwa karamin kauyene sosai akan hanya yake fadil kam yacika da mamaki yace dagaske kakeyi haidar???
yace kwarai kuwa kasan me kuwa wani taimako nake so kaman”” fadil yace name kenan yace zanshiga zaria gobe inaso inbude accaunt turoman kudi inason yin amfani dasu””yace shikenan sainajika goben yace to sundan taba firah sukai sallamar sannan yakalli halliru
yace nagama mujeko tare suka jero suna tafiya harsukakai haka kuwa akayi tunsafe yatafi zariya tare da halliru yabude accaunt sannan yakirah fadil yafada masa accaunt nmber nashi yaturo masa dubu dari uku
baima karbesubah sai washe gari yakoma yakarba dubu hamsin yana dawowa yace halliru yarakashi wajen abba yadanka masa kudin yana so agyara masallacin su duk abunda yake bukata asaka hardo yakalli haidar yace amman aikudin nan sunyi yawa haiydar
yace ah ah baba aizasu shige asaye bulo gobe afara muga inda zasu tsaya hardo harda kuka yayi wajen godiya yanata saka masa albarka amman yace kada yafada kowa cewa shine yabada kudin kawai yace wani bawan Allah yabayar
haka kuwa akayi washe gari aka rushe masallacin akafara gini ba kakkautawa dashi da halliru sukeyin banruwa idan ma aikatan suntafi aka maida sallah gefen masallacin cikin kwana biyar akagama komai. akabuga kwano saida yashiga zariya yasamu masu gyaran wuta akayi wayarin akasaka fankoki yasiya masu jen sabo hul babba
gaba daya masallacin kafet aka malala ga lasifiku manya manya””akabuga kantoci ya fanso alkur anai dayawa ya a aje da littatafai kodan masu karatu duk wannan tahannun hardo suke zuwa babu wanda yasan waye yakeyi
amman kam haiydar yasha albarka kowa sai sakawa bawan Allah nan albarka yake anan masallacin haiydar yake zama yana karatu kullum har limamin garin yalurah dashi yanemi yadinga yimasu wa azi duk safiya suma sukaru da iliminsa baiyi musuba kullum dasafe yakanyi wa azi har wasu sukanzoma yakarasu karatu
Aisha………………gentle
[7:37PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SAKADA!!!💭
23
Ahakadai haryayi saurah kwana goma bikinsu gashi mom saidamunsa take yadawo hakanan yasamu baba yasanar dashi yanaso yakoma garinsu wani sati yakama kenan saurah kwana uku bikinsa amman baisanarda baba auren sa za ayibah
hardo yace bakomai Allah yakaimu”” kwana biyu dayin maganar gidan akafara biki shidai baisan abunda yake faruwabah amman yadaina ganin mairo kwana biyu dakullum itah take kawo masa furah kuma itah take cika masa tulunsa daruwa amman yanzu saidai hardo yaturo kanwar mairo halira tana zubah masa
yanaso yatambayi ina take saikuma yaga menene amfanin tambayar yakawar da abun ana saurah kwana biyar tafiyarsa yana zaune adaki saiga halliru yashigo da sallamar sa yakawo masa waina”” irin ta biki manya manya”” yasamu waje yazauna
haiydar yabi wainar da kallo yace ina kuma kasamo waina haka halliru??yayi murmushi waikai bakasan biki akeyi agidan nan ba????haiydar yayamu tsa fuska biki kuma??:aure ko suna??? halliru yace aure “”haiydar yakada kansan wazaiyi aurene???
halliru yagunci wainar yakai bakinsa yana kallon haiydar yace mairo!!!! dam dam gaban haidar yafadi yace mairo fa kace itah wannan yarinyar nawa take dahar za aimata aure???? halliru yayi dariya yace sha uku take dasu dama da shabiyar akeyiwa yayan gidan nan aure itah ce kawai batakai shabiyar din ba
haiydar yajinjina kai yana tausayinta wai itah wannan yarinyar dako wanka ba agama mataba za ace wai za ayimata aure??? yakalli halliru yace anan garin mijin nata yake daiko???? batareda yakalleshibah yace to gaskiya bansanibah””
haiydar yayimasa duban rashin fahimta bangane bakasanibah kana yayan nata kace bakasan wanda kanwarka zata aurab!!!halliru yayi murmushi ganin yanda haiydar yake kallonsa yadafah kafadarsa yace wlh idan kayarda haiydar bansanibah kaibama nibah kosu innah basusan waye mijin taba hatta itah mairon bata sanibah babane kawai yasani”ko angon ma baisaniba
maganar saitasoma tabawa haiydar dariya wai kowa baisanibah hatta angon toya za ayi aure haka???? kamar dama halliru yasan abunda haiydar yake tunani yace nasan kana mamaki ko????amman ba abun mamaki bane haka baban mu yake yiwa yayansa aure,,haiydar yace tayaya????
Aisha………………..gentle
[8:05PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
24
Hardo shine sunanda ake kiran baban mu amman sunansa na asali shehu wasun suna kiransa malam asalinsu fulanin dajine daga adamawa suke sunayin kaurah daga gari zuwa wani gari kasancewar basa zama cikin gari sunfi yin tungarsu cikin daji
har Allah yakawoshi nan garin yazauna yanada mata uku tafarko sunanta ladidi muna kiranta da gwaggo tanada yara guda goma sha biyu hudune maza takwas duk matane
maibimata sunanta harira muna kiranta iyya”itah yayanta shida dayane namiji sauran duk matane saita uku sunanta shatu muna kiranta inna itah ce tahaifeni mu bakwai ne adakinmu shida maza mairo ce kawai mace
yanisah aduk lokacinda yaran gidan mu suka isah aure baba baya barinsu firah da kowa idan ma yasamu kina firah zaikarasa wajen yacewa saurayin shibaya barin yayansa firah kada kasake zuwa idan rabonkace kana zaune zaikawo maka itah
yakalli haiydar wanda shiharyanzu baiji inda labarin yadosabah amsarda yakeson samu haryanu baisamubah yaci gaba lokacinda raliya yar gwaggo ta isah aure yasanarda su zaimata aure
dama suma sunsan haka duk da bada dadin ransubah haka yahado mata kayan fita biki kala uku dasauran kayan da ake bukata su sarka yan kunne takalmi man shafawa daduk abunda kasan anahada lefe daidai gwargwado yanda akeyi anan karkarar
haka yayi mata sannan yasayi kayan dakinsa na mata saisauran kayan aiki dama uwar diya tanadasu yasiye goro yararraba yasanar gobe akwai daurin aure masallaci washe gari kuwa akataru ajen daurin aure shine yazama waliyin ango liman shine yazama waliyin amarya akayanka sadaki baba yabiya
sannan akatambayeshi sunan angon yace usmanu haka aka daurah aure batareda kowa yasan angobah akaci akasha kowa yakama gabansa gidan amarya saibiki akeyi da dare yayi akashirya amarya
gwaggo tana kuka batasan inda za akaimata diyar tabah baba yayiwa amarya hudubah sannan suka fita babu danrakiya yatada mashin dinsa tahau suka dauhanya harkofar gidan su usmanu yatsaya da mashin dinsa suka gangara dakafa
yayi sallama kofar gidan mahaifinsa malam mudi yafito yana ganin hardo yasaki fara a ah yaukaine agarin mu cikin daren nan bisimillah wuce ciki mana yayi murmushi ah ah basaina shiga cikibah ina usmanu yake????
yace aikuwa bayanan amman nasan yanzun nan zaidawo nadan aikeshine baima gama rufe bakin nashibah saiga usmanu yana ganinsa yace ah baba kaine agarin namu yaduka yagaisheshi
Aisha………………..gentle
[6:48PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [9:20AM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
31
Sunanan tsaye saiga habu yadawo yadauki ragowar kayan haiydar yace harda wannan idan zaka dauki ragowar kawuce da itah yace toh yallabai ina kasamu wannan yarinya kyakkyawa haka?? yasakeyin murmushi malam habu dai kanwatace baka santabah to to sannu yarinya batako kalleshibah yadau kayan yawuce
baikalletaba yace idan yazo kibishi zaikaiki wajen mamana yasakai zaiwuce kawai yaji anriko hannunsa wani yarrr yarrrr yaji harsau biyu baiwaigoba yace lfy?? dukawa tayi kasa tafashe da kuka saiyaji tausayinta baidace yayi mata hakabah waigowa yayi shima yaduka yace meyasakaki kuka idanunta tadago tace kayi hakuri
yace mekuma kikamun??? tace naga aikana fushi tundazu bakamun dariya “”yayi murmushi banajin dadine shiyasa””tace amman ainaga kayiwa wannan cewa damai gadi tacigaba kayi hakuri dan Allah wlh bazan sakebah
yajaye idonsa daga barin kallonta yana kallon gefe yace nayi hakuri amman kidaina rashinji kinga yanzu ba garinku kikebah idan kika cika surutu dariya zasudinga maki”” tace tonadaina amman kayi hakuri yayi murmushi yasa dan yatsansa yagoge mata hawaye itah ma murmushin tayi dinpul dinta suka lotsa
mikewa yayi yana kallon habu dayake kallonsu yadan waske kashiga da itah yajuyo wajenta ina kankanar ki kokin manta da itah amota????tace menene kuma haka?? yace abarda kika siya dazu?? tace ainayarda itah tunda nabaka kakisha sainayar nima””yaso yatambayeta meyasa tayar alhalin tanason abarta amman ganin kallonda habu yake masa yasa yayi cikin gida dankarya harbo wani abu
yakalleta mujeko yarinya yana gaba tana binsa saikallonta akeyi yanda taketa rabon idanu hartanacin tuntube harsuka kai bangaren mom aikam suna shiga kallo yakoma sama waishaho yadau giwa saurah kadan yawu sudinga gudana irin yanda mairo tasaki baki mom tana ganinsu tasaki fara a gashi tayi nauyi sosai ahankali tataso tariko hannunta tacewa habu dauko kayan nan
yadauka yana biye dasu harsuka shiga wani daki karamin dakine amman guda daya sai tolet yanada gado sai kujera biyu da kayan kallo tace zauna yata mairo kam sai kalle kalle takeyi habu ya aje kayan yafita””tamike ina zuwa tafita itah dai mairo komi batace bah har mom tadawo da kaya ahannunta kursum tana biye da itah da abinci tana ajewa tajuya saboda kawayenta. suna jiranta zasu wajen diner
mom tazauna tana kallon mairo datake kalle kalle itah kadai tasan abunda take sakawa aranta hakika wannan yarinya itah ce kalar matarda haiydar yakeso saidai baigane hakanba ganinta yarinya amman wannan idan tagirma tawaye akwai kallo agaba tasaki murmushi takalleta yata yasunanki””
sai yanzu mairo takalleta tayi murmushi ina wuni”ta amsa lafiya qalau tasake tambayarta akaro nabiyu tace mairo sunana” mom tayi murmushi todagayau kada insake jin kince sunanki mairo maryam sunanki kinji duk wanda yatambayeki kice maryam
kaita gyada mata tace sunan da dadi kuma”” tace eh mana”yanada dadi amman akabata maki suna yanzu ga abinci nan kici kishiga tolet kiyi wanka kisaka wadan nan kayan kidebe najikinki””tace menene kuma tola?? mom tayi murmushi tace wajen wanka ta nuna mata
tace to amman dai kece kika haifi dan binni ko?? naga kuna kama dashi sosai,, tayi murmushi sannan tamike kici abincin dai kihuta”to kawai tace tabuda abincin tafara lodawa itah dai bata tabajin irin wannan abuba kamar wainar fulawa kuma kamar wainar shinkafa… tabdi yan binni sunacin dadin su nima nasan bazan dadebah zankoma kamarsu
ai wlh koda tsiya bazan koma garin mubah taci gaba dacin sinasir dinta tana gamawa tahaucin waina nan take cikinta yabatse sai tasha ruwa sannan takwanta saman gado waita huta aikuwa saibarci bata farkaba sai magrib
tana tashi tashiga tolet din aikam duk da bawani haduwa yayiba saida tayi kauyanci taba nan taba cen itah dai bataga ruwa awajen ba todame zatayi wanka tsaja tsaki tadawo warta daki tana nan zaune kamar mujiya sai kalle kalle take cen saiga mom tashigo da sallamar ta ah maryam haryanzu bakiyi wankan ba?
mutane sunyiman yawa saiyanzu nasamu nafito” tace ainashiga banga ruwabah””wai ina dan binni ne??? tace yana dakinsa tashi innuna maki yanda zakiyi tana gaba mairo nabinta abaya harsuka shiga saida tanuna mata komai sannan tafita tabarta saida tasake yin tabe tabenta sannantayi wanka
tasaka kayanda aka ajemata kursum ce tashigo takawo mata abinci tafita tuwon shinkafane yayi laushi. damiyan alayyahu saida taci tayi nak takoma takwanta bata sake farkawaba sai safe kullum dai haka take kuma daga daki sai daki bata lekowa ko kofar waje
haka zalika batasake dorah idonta akan haiydar ba kuma bata damubah yau dubban jama a nesuka halarci daurin auren haiydar&hameeda usman &Aisha hameed&kursum muhsen & asiya is”hak&zulaihat
Aisha…………………gentle
[6:28PM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
32
Akan sadaki nairah dubu hamsin kowanne ango kagani bakinsa har kunne sabanin haiydar dayakejin kamar yafasa ihu yanajima kowanda yake gidan yari yafishi jindadi hahahha haiydar kenan haryanzu yaki saduda”fadil saibashi baki yake yadan saki fuskarsa kada mutane su gano akwai wani abu yace sugano mana ina ruwana
fadil yayi dariya wlh haiydar kukan dadi kakeyi nigani koguda daya banda amman kaidakakeda biyu malam kana rainawa”” cikin zolaya yayi maganar haiydar yayi tsaki wlh aini kara kowama dani kana ganin kamar wai gatane nibana murna da wannan auren ganin yana nema yasa wasu suji fadil yaja hannunsa suka shiga mota kunsan dai duk wanda zaiyi aure yanayin dinkinsa na shadda fara tass ango haidar kam kinsa shaddar sa yayi wani yadine daya shiyo baki mai ratsin ruwan anta shiya saka amman kuma saiyayi masifar karbarsa
farin mutun acikin bakin kaya kunsan bakaramin kyau zaiyibah suna shiga mota haiydar yajingina jikin motar yana maida numfashi jiyake zuciyarsa tana tafasa shikam fadil ido kawai yakebin abokinsa dashi
yakirah sunansa haiydar bai amsaba saida yasake kiransa sannan ya amsa amman baikalleshibah shimadin baidamu darashin kallom nasa dabaiyibah yaci gaba haiydar idan dai zakaji shawara kadaina nuna bakason auren nan maganadai takare anrigada andaura”” yarinyar nan kanwar kace kuma jininkace kasan babu maganar saki atsakaninku to idan kuwa hakane menene nanuna bacin rai tunda kasan bacin ran naka bazai haifar maka dakomaibah sai damuwa
babu yanda zakayi ayanzu saidai kayi kokarin koyawa zuciyarka sonta ina rokonka dan Allah kada kabari mutane su fuskanci wannan lamarin duk da nasan wasuma sunsani dankuwa baka gayyaci abokinka kodayabah bayan ni koni dan muna unguwa dayane
sannan katsallake zuwa wani gari baka dawobah sai ana saurah kwana uku bikinka kana ganin kakyauta kenan koka dauka dad yaji dadin abunda kayi yadafashi dan Allah kayi hakuri kaji mutumina yanzu muje gida kashirya muwuce wajen diner
haiydar saurarensa kawai yakeyi saida yasake magana sannan yace muje batareda yakalli inda fadil yakebah shima murmushi yayi yaja motar sukabar wajen wanda duk sauran mutane sun watse
acen bangaren amare kuwa
biki kam yayi biki amare sai kai kawo sukeyi anci kwalliya takece raini nahango su maman son beauty chuchu ansamu abunda akeso wato shinkafa lodawa kawai takeyi bata kodaga kai nahango su maman shakur da hauwa jabo su anty benazir kam ana gefe ankame dankunsan su manyane
nahango amare sunyi anko cikin wani farin less mai shegen kyau kaida ganinsa kasan yakai wajen 100k saidaukan ido yake sunsha gwaggaro nikam aiyar kallo nazama sai shiri suke da alama wajen wata diner zasu kowa sai shirye shirye yake sauran yan matan kuma ankon atanfane ajikinsu ja mairatsin fari da baki itah madai babaya ba dan itah ma tahadu””
kowa kagani fuskarnan cike take da annuri mairo ma tayi kwalliyarta irin tasu amman tana zaune cikin daki itah abunda yadameta tanaso taga dan binni amman komai kama dashi bata ganibah kuma gashi ko mom bata ganinta abunda yake kawota dakin kawomata abinci saidai takan leko akai akai taganta
acen bangaren gidan su gwaggo shima cike yake tam da makota da abokan arziki zata aurarda yayanta biyu gwaggo baki har kunne kamar tazubah ruwa kasa tasha harda kidan kwarya akayi gwaggo kam andagar gaje anyi rawa an jijjige sai barin kudi takeyi
su. kausar luv da unigue sune gaba gaba wajen rawa waisune yan taya gwaggo murna nidai nace uhum kudai kufadi abunda yakawoku”” bangaren amarya ma tana falon gidan babba da itah da kawayen ta sunata shirin zuwa diner
watace tayi sallama tashigo aida gudu hameeda tadaneta tana murna taja hannunta suka fita zuwa dakinta
Aisha………………..gentle
[7:00PM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
33
Saida suka je harkuryan dakin ta saman gado tazube tana maida numfashi tace saukata kenan fah dan Allah bani ruwa indan sha tace. shegiya tare kike da mutumen ne “”tace wlh ah ah acen nabarshi dakyarma wlh yabarni inzo bikin nan kinsan bazai iyah koda kwana daya batare danibah
hhhehehhe kice dai kin kamashi ahannu kudai kunajin dadinku”” tace kekumafa hameeda kiji tsoron Allah kema bagashi kinkama haiydar ba tace uhumm inazuwa baridai inkawo maki ruwa “”tace kicedai akwai labari??? sosaima da dimi diminsa makuwa kedai jirani indawo..
tafita tana dariya tacire gyalenta dan fitsitsi ta aje tana kallon dakin yanda yatsaru hameeda tanajin dadin ta wlh”” daidai shigowarta ta aje mata ruwa da abinci ruwan tafarasha sannan tabuda lemu tana sha tace kinga kuwa yanda kikai ja hameeda wlh kina cikin jin dadinki
hameeda tamere baki jindadi kuma name ni wlh bakisan duk atakure nake agarin nan ba namatsu mubar kasarnan indan huta da wannan takurin kinsan mutanen nan badama kayi abu za asanya maka ido” kinsan Allah wancy kamar ina daure gidan yari nake jina””
haba hameeda keda kike amarya waikekam saida kika auri guy din nan kika huta ashe aiki yayi kyau ‘baki ta tabe ina kuwa aikinsan dai komai wlh babu wani aiki guy din masiffen ne wajen addu”a yawuce saninki duk inda naje ke intakaice maki lbri har maiduguri naje amman babu wani haske
duk inda naje cewa ake baza a iyah aiki akansaba saboda baya wasa da addu”a kawai dai yanabin umurnin iyayen sane dan bai isah yayi musu akan maganarsubah”” wancy ta gyada kai tokina ganin zamanki garin nan bazai tona asirinkibah???
tayi dariyar mugunta aini nan dakike ganina wlh nasan abunda nataka kamar yanda kika sani tsuntsu biyu najefah da dutse daya””tace banganebah hameeda tace hmm waikina dauka inason haiydar ne???? ai idan baki mantaba nafada maki babu wacce haiydar yatsana aduniya sama dani!!
na auri haiydar ne saboda cika burina guda biyu ada lokacinda nake nan ina mutuwar son haiydar nidai yayi mun sosai amman tunda naje america nadawo saina gane bawai sonsa nakeyibah kawai ina sha awar sane dana biya bukatata dashi shikenan nagama dashi kuma
burina kuma nabiyu nayarda da auren haiydar ne saboda nasan baya sona kokadan kinga zansamu damar yin duk abunda naga dama bazai damubah bazaisamun ido akan abunda nakeyiba nayi amfani da auren haiydar ne saboda in kauda tunanin duk wani mai tunani inyi wasa da hankalin masu hankali
domin cigaban boyuwar sirrina nasan idan na auri wanda yake sona bawuya zaiganoni kuma kinga idan yaganoni daidai yake da fallasar asirina kuma ni bana fatan hakan har abadahh takai karshen maganar tana kallon wancy
tagyada kai lallai kuwa kinyi dogon tunani kafin ki aiwatarda haka ashedai kwanyarki tanaja mutuniyar sukayi shewa suka taba”” tace to amman kina ganin zai iyah barin kasarsa ta haihuwa zuwa wata kasar idan kuma baida ra ayin hakan????
tace wannan ma saida nayiwa tubkar hanci dakyar nasamu wannan aikin yakamashi bari kigani goben nan zamubar kasar nan kuma dazaran munbar nan shikenan duk sauran aiki zanyi nasara akansa”” ke shegiya kiraga masa haka mana””
wani?? kinkuwan makudan kudinda nayi hasara akansa ??ai wallahi kona lafirah saiyafishi jin dadi nibata wasa bace haryake wani shashshareni idan naje wajensa yanamun wulakanci
Aisha………………..gentle
[7:39PM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
34
kinga hanzarta kici gashi har hudu tayi wajen diner zamuje “” ah ah ni iyah lemun ma ya isheni kedai jeki kishirya muwuce”to tace sannan tamike saida tayi wanka akayimata makeup tafito fes da itah nikaina nasan yau idan haiydar yaganta saiya saki baki. karyar cewa yake baya sonta
yaukam saiya kusa sakin layi tahadu iyah haduwa kam itah ma less ne tasaka saidai ba kalan nasauran ba nata jane mairatsin fari gwaggaron tama jane daratsin fari karamar jakartama jace takalmanta masu tsini kamar cinke suma ja kai wayaga amaryar haiydar nikam nace duk tafisu haduwa””
kafin sugama shiri har shida tayi sauran amarekam harsun jima da tafiya su hameeda ne kawai basujebah”” katon hotel din da akeyin diner awajen yayi matukar kayatuwa da kayan alatu gawasu fulayoyi suna fitarda wuta gwanin bansha awah acen saman steep angwayene da amare kowanne yana zaune gefensa nadama amaryansa gefensa nahagu kuma babban abokinsa
kowanne yana manne da amaryarsa inka debe haiydar dayake zaune dashi da fadil kawai daka kalli fuskokin amaren da angwaye zaka hango tsantsan farinciki kumshe afuskansu sabanin haiydar dakamar an aikomasa da mala”ikan mutuwa fuskarnan batada sauran annuri amman kunsan duk yanda ango yake dole hasken angonci ya bayyana
goshin haiydar sai kyalli yake kamar tauraro kusan ma dukyafi sauran angwayen haska waje anfara gabatarda abunda yakawosu inda masu daukar camera saiyi suke masu vidio ma haka daganan akasaki kida
yan matan amarya suka fara chashewa wata tauraruwace tashigo inda gaba daya kidah yatsaya chak!!! kallo yakoma wajenta tana tare da mukarrabanta abaya less dinta sai wal walniya yake bakinta harkunne dakaganta kasan tana kumshe cikin farinciki ahankali take takun kasaita
saida takawo tsakiyar holl din akasaki kidan amaryace amaryace””hameeda ce amarya”gaba daya wajen yakaure da hayaniya jin muryan shaha rarren mawakin nan ali jita yafara wake hameeda kowa sai kallonta yake sabanin haiydar daya dauke kansa shi kwata kwatama bata burgeshibah
ali jita yacigaba dawake amarya daganan yadawo kan angonta harzuwa kan sauran amare kusa da haiydar tazauna itah ma akacigaba da chashewa””bayan ali jitah yagama wakarsa aka umurci amare sufito daidai tare da angu nansu sutaka rawa
daibayan daya sukayi amman banda haiydar dankam cewa yayi shibaimasan yanda ake rawabah’fadil yace naji baka iyah rawaba amman kafitah kotsayene kayi kada kabatawa yarinyar nan tsari”” nabata tamutu ma idan tana iyah wa. aharzuke yake maganar dakata fadil danka takurani shiyasa kamatsaman inzo diner???? idan baso kake wlh intafiba kakyaleni babu inda zani idan taji zata iyah tafita itah kadai tataka””
fadil yagirgiza kai yakalli hameeda yace kije da kawayenki idan ankiraku””ta make kafada No fadil karka damu nikaina bana sha awan yin rawar takawar da fuskarta
Aisha…………………gentle
[8:17PM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
35
Fadil baiji dadin abunda haiydar yayibah duk da yasan sauran mutanen wajen bazasu dago shibah tunda sunsan ustaz ne sunyi mamaki ma dayazo wajen diner abunda basu sanibah haiydar kuwa gwanine wajen rawa kawaidai dan baya murnane da auren amman fadil yasan ya iyah rawa
dankaryaja magana datsayi kawai yakyaleshi””haiydar kam ko ajikinsa shibai damubah””:haka akagama diner kasancewar anfara kiran magrib kuma da anyi magrib za ayi walima daganan saikai amare amman walimar matane kawai””
kowa yaci yasha harmasu boyewa cikin hijab suna boyewa ina hangosu su unigue da khairiyya hardasu maman son amara kirjin buki koba a gayyacetaba saitakai jiki kunsanta akwai kwadayi uwah ummi sareef nidai nace kuyi ahankali idan kuwa bahakabah yau akwai tashin dare heheheh
anwatse wajen diner angwaye suka dauki amarensu suka wuce haiydar kotakan hameeda baibiba yashiga mota yayi gaba ko fadil baijirah ba dama kowa cikin motarsa yazo fadil ne yamaida hameeda gida yanata bata hakuri itah cewa take wlh bakomai fadil nagode da nuna damuwarka akaina
ana yin magrib suka wuce wajen walima amman banda hameeda saikarfe tara aka tashi kowa yaje wajen haramar sallah suna gamawa amare sukahau shiri. zulaihat da kursum da asiya. mota daya suka shiga gaba daya gidan alhaji auwal suka taru babban falo inda akeyin taron family
da angayen dakuma amaren harda iyayen su alhj auwal yafara bude taro da addu”a sannan yafara akan mahimmancin zaman aure dakuma hakuri dajuna yayi masu nasiha mai zafi inda amare sunakuka yajawa angaye kunne akan hakuri da kannensu kuma duk wanda yayi badaidaibah kana iyah kawo kararsa duk ranarda za”ayi meeting na family kubar ganin wai yannenkune kuka aura hakan bazaisa kudingayi masu abunda kukaga damaba idan suka kawo kararku wlh sainayi mugun saba maku kukuma kada kudauka kannen kune aimunada incin yimasu duk abunda mukaga dama to bazamu dauki wannan ba
sauran iyayen suma sukayimasu tasu nasihar daganan aka umurci kowa yadau amaryarsa yayi gida da itah haka suka mike usman yana gaba Aisha tana bin bayansa tana kuka””suna fitah waje yasunkuci matarsa saicikin mota kafin sauran sufito shikam haryadau hanya
suma kowanne yadau tashi suka wuce duk haiydar ne akabari karshe yashiga mota yazauna yana jiranta tadade tsaye ganin baida niyar bude mata sauran angayen sukam daukar matansu sukai itah gashi ko arzikin bude mata motar babu haka tabude tashiga yaja motarsa dakarfi kamar zaitashi sama
aini jinayi kamar inciji haiydar shikomai akai ba aburgeshi😁😁
Aisha…………gentle
[6:49PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [8:53PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
25
ya amsa dasakin fuska malam mudi yayi masa barka da auradda yarsa dayayi yayi murmushi yace aimunama tare da itah tanacen nesa dasu yakirah ta takaraso taduka tagaisusu malam mudi ya amsa da fara a yace dada amarya yausaigidan miji ko
tayi murmushi taboye fuskanta yace kiyita hakuri kinji zaman aure dan hakurine yinayi bari nabari tarabaki dakowa yayimata nasiha mairatsa jiki usmanu yamike baba bari inshiga gida “”yace ah ah dakata aiwajenka nazo saiya koma yaduka
yayi gyaran murna nasandai kunje daurin auren ta kuma bakuga angon ba malam mudi yace hakane hardo yajinjina kai yace usmanu kaine Allah yabawa wannan yarinyar nabaka itah sadaka usmanu kamar ya kuwata dan dadi damacen yana sonta kawai dai baitaba furtawabane
malam mudi kam bakinsa yaki rufuwa dama ashe daurin auren dansane yatafi baisanibah sai zubah godiya suke da malam mudi da usmanu saida baba yasake yimata nasiha sannan yabarta yadawo gida sai washe gari mukasan waye mijinta
dayake usmanu gidan su babban gidane anan akabashi daki akayimata jere suka tare cikin gidansu gashi yanzu yayanta biyar dashi amman kosau daya bata tabayin yajibah suna zamansu lafiya haka baba yakeyiwa yayansa duk wacce yasan ta isah aure kuma duk suna zaune lfy harda karuwa
waikarka dauka wasu kudi yake dasu dayakeyin haka wlh kodaya kawai dai ra ayine danbawata sana a yakeyi mai karfiba noma ne saikuma kiyo saidai duk ranar asabar yana siyen dabbobi yadaure ranar larabah yaje kasuwar cikin gari yasiyar
kaji takaitaccen labarin gidan mu haiydar yanisah yana jinjina lamarin hakika bakowane uba zai iyah yiwa yarsa hakabah haba dai kamarba yar mutun bah amman daikuma yana taimakawa wadan da basudashi dankam yayansa babu wacce take da muni indai kamarsu daya da mairo
yasan kyawawane dama yayan fulani aihaka suke yinin ranarkam haka haiydar yawuni da tunanin maganganun halliru har akai azahar baima fitah masallacinba yaga anfara taruwa fitowa yayi waje saboda manyan mutane haka yayita gaisawa dasu haryafita acen bangaren dama yahangi halliru dasu lado da bello da tanko yakarasa wajensu yabasu hannu suka gaisa
yadade tsaye sannan yasamu wani dan dutse yazauna mutane sunata taruwa dayawa har akacika wajen daganan akasoma daurin auren anfadi sadaki hardo yabiya yafadi sunan angon
daganan aka daurah aure akaita fitowa da waina jibi jibi kowakam sai kwasar gara yake akawatse ana Allah sanya alhairi daganan su haiydar suka wuce yawo dashi da haliru yau rafi suka nufah dama sukanje akai akai
suna tafe suna taba firah amman hankalin haidar kwata kwata bayajikinsa wai mairo aure??? rayinyarda iyakarta sa ar fati kanwar fadil nawa take itah shikam mamakine kawai aransa
halliru yalurah dahaka yayi murmushi haiydar da alama haryanzu maganarmu tadazu itah take maka yawo cikin zuciya””yamaida kallonsa wajen halliru yana lumshe ido ya akai kasan haka???)yayi maganar tareda dauke kansa
halliru yayi murmushi ainaga yanayinkane tunda mukayi maganar kakasa sukuni kodai akwai wani abune??? haiydar yayi murmushi maidan sauti duk da baigano inda maganar halliru tanufah bah yace ah ah bakomai kawai mubar maganar
halliru yace shikenan sukaci gaba da tafiya suna kaiwa halliru yahango budurwansa yayi wajenta harta dauko tulu tana ganinsa tasaki fara a shiya saukar mata da tulun suka dan haye sama saman wani dan dutse suka zauna
acen nesa dasu haiydar yazauna yana tsintar duwatsu kana na yana jefawa cikin ruwa idan yajefah daya saiyayi wajen minti biyar kafin yajefa wani idan kalurah dashi kaman hankalinsa yana wajen ruwan yanda suke gudu gwanin ban sha awah amman kwata kwata
hankalin haiydar baya wajen tunaninsa yana wajen mairo da akaiwa aure waishi menene nashi nadaukar damuwa yasakama ransa???? shikanshi yakasa gane hakan kawaidai abunda yasani yanajin zafi cikin ransa yarasa dalili
Aisha……………gentle
[9:17PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
26
Kodai tausayintane yakeyi? to akan wanne dalili babanta ma baiji tausayintabah saini yanata kokarinkawarda tunanin aransa amman yakasa. saidayaji muryan halliru yana kiransa yafarga yace taso mudan takamata kaga ankusa la asar
baice komaibah yamike suna gaba yanabinsu abaya harkofan gidan su saida tashiga gida sannan suka juyo zuwa masallaci acen sukai alwala danhar angama kirah saida yayi tahiyatul masjid yazauna bajimawa akafara sallah
anan suka tsaya yana kara halliru karatu dama duk bayan sallar la asar yake karasa basa fitah masallaci saibayan isha”i suje dandali”yau haiydar jinsa yake sai ahankali kamarma bazai iyah zuwa dan dalinba
saibayan isha”i suka wuce dandali shidai haidar baima tsaya wajenba cen nesa dasu yazauna bayason hayaniya yau baimasan tsawon lokacinda yayi awajenba saida halliru yace haiydar taso baba yanata nemanka”duk da baisan dalilin kiranba yasamu kansa dajin faduwar gaba
tare suka biyo hanya harcikin gida hardo yana tsaye halliru yace gashinan baba yace toh halliru yajuya yafita sannan hardo yace masa mushiga ciki suka shiga tanacen saman gadon kara wanda haiydar baisan da zaman sabah yasamu saman katifar yazauna
hardo yanisa nasan zaka cika da mamaki jin ina kiranka yanzu alhalin bansabah kirankabah cikin wannan lokacin haiydar yagyada kai””yaci gaba dazu kaje daurin auren mairo?? haiydar yayi murmushi ah naje abba”” yace kasan waye mijinta???nan madin murmushi yayi ah ah abba
yanisah tare dakiran sunansa”” ya amsa yace kaine wanda Allah yazabawa mairo gaban haiydar yabada rasss rasss cikin sauri yadago fuskansa yana kallon hardo da ace akwai wadataccen haske adakin da zaifahimci rudaninda haiydar yashiga
nan take zufah yafara karyo masa tako ina hardo yacigaba hakika haiydar nayaba da hankalinka da tunaninka kuma nasan. banyiwa yata zaben tumun darebah ina fatar zaka karbi wannan sadakar da hannu bibbiyu
haiydar yasa gefen rigarsa yashafe zufah dakyar ya iyah harhado kalamai dabazasu wuce goma ba yace nagode abba ‘hardo yaji dadi sosai yace ina fatar banshiga rayuwar kaba??? yace bakomai abba aikaima ka isah dani tamkar mahaifina kake kuma nagode insha Allah bazaka taba dana sanin auraman yarkabah
karfin hali kawai yakeyi wajen yin maganar kada hardo yagano yanayinda yake ciki yayi murmushi nagode haiydar dajin kalamanka ga mairo nan nabaka itah amana nasan zaka kula da itah kaita hakuri da yarintarta yace bakomai abba saida yasake yiwa mairo nasiha sannan yayi masu saida safe yafita
Aisha………………….gentle
[9:49PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
27
haiydar tamkar yadaura hannu aka yakwatsa ihu wannan wace irin kaddarace abunda yagudoma ashe wani tsautsayin ne zaikuma taronsa yakalli inda take zaune duk ta takure jikin bango tana lullube cikin hijabinta mai kyau abun ma saiya bashi dariya wai wannan ce matarsa???
tashin hankali dama wannan kaddarar ce take nemansa tataso dashi tundaga kano yazo inda take lallai Allah mai ikone duk abunda zaifaru rubutaccen abune amman ni yazanyi da wannan yarinyar ina zankaita haka yayita sake sake aransa tun mairo tana gyangyadi harta zame tayi kwanciyarta shima yadade zaune sannan yakwanta yaukam ko kayan jikinsa baicirebah hhmmm
*******************************************
ganin ansoma kiran azahar yasa yabaro dajin yadawo baiwuce dakin ba masallaci yanufah bayan angama sallah yana fitobah yahadu dasu lado. sunata dan kauce kansu dan sunsan yaji abunda suke fada dazu
*******************************************
baikoma takansubah yakama hanya saiga halliru yace wai ina kashigane haiydar tundazu naketa nemanka????yakalleshi yana murmushi wlh nadan fitane nayi waya da mom dina ” yagyada kai dada jiya saikaga ankawo maka mata dama ashe kaine angon bamu sanibah
*******************************************
shima dariya yayi yace aiyanzu kunsani ko???)*yace ah munkuwa sani to Allah yasanya alhairi yasanyawa auren Albarka haiydar yace ameeen kokadan haiydar bainunawa halliru bayason auren nan ba
*******************************************
aganinshi kamar cin fuskane idan yace bayason kanwarsa yace yanzu ina zakaje??? yace zankomane inyi shirin kayana mom tace lallai inkoma gida gobe””:halliru baiji dadibah dan yasabah da haiydar sosai yace yanzu idan kaje sai yause kuma wlh banaso katafi
*******************************************
haiydar yayi murmushi nikaina banason rabuwa dakai halliru amman aikasan dole indawo tunda nadauki iri sukai dariya suka taba tare suka karasa gidan angyara komai anyi jere maikyau ansaka gado babba da karami
*******************************************
halliru baima shigabah yawuce acen saman kujerah yahangota tanata kuka yadade tsaye kafin yatambayeta lfy kike kuka???? taci gaba da kukanta saida yasake tambayarta sannan tace ba babane ba yaman fada waidan nafita wasa cikin gida”wai anan zanyita zama nikadai kuma alhalin bakowa tunda kaima katafiyarka ko??
******************************************
yayi murmushi dan dai wannan kawai kiketa bannar hawayenki??? cewa yayi idan nasake fitah saiya dakeni kuma ni tsoron duka nakeyi zaka bari yadakeni????yace ah ah yanzu kidaina kuka tashi maza kiwanko idanunki kizo zamuyi magana to tace sannan tamike zuwa waje
bajimawa tadawo takoma inda take tazauna shima saman gadon yazauna yakalleta natsayin mintuna komai yake tunani oho yakawarda fuskarsa yace kishirya kayanki gobe da safe zamuje garin mu wajen iyayena amman banda muguwar wasa kinji kuma banason yawan surutun nan naki
tayi murmushi dinpul dinta harya lotsa binni zakaje dani????kaiya gyada mata kinason zuwa ko????tace ah yace to kihada kayanki gobe zamutafi yamike yafito waje saida la asar yasamu hardo yayi masa bayani yace bakomai wlh fatansu dai Allah yakaiku lafiya
Aisha……………..gentle
[11:40PM, 11/15/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
28
Yasake yimasa nasiha kuma harcikin ransa yaji nasihar sosai yinin ranar kam kowa agarin sukuku jin labarin haiydar zaitafi masu daukar karatu wajensa jisuke kamar karyatafi duk wani shiri dazaiyi cikin daren yagamashi yau yaso zuwa dandali jin wasar da za ayi amman yakasa ganin yanda halliru duk yadamu yayi ta tausar sa dakyar yasamu yahakurah koda sukaje dandali har ankusa gama wasa basu dade acenba suka dawo gida
hardo yana zaune adakinsa duk matansa sunanan yakirasu yayi masu bayanin gobe haiydar zaikoma garinsu kuma da matarsa zaitafi gwaggo ta mere baki yanzu saboda Allah malam duk abun nan dakakeyi bai ishekabah saika sayarda yarka???
yayi mata kallon rashin fahimta yace kamarya saina siyarda yata shi haiydar din ba mutun bane??? mutun ne mana amman kasan wannan abun baidacebah kadauki yar cikinka kabaiwa bako wanda bakasanibah bakasan inda yafitobah bakasan danginsabah kawai ganinsa kayi haba malam
dan dai kawai kai bakasan zafin haihuwa bane kawai kana ganin sune kamar daga sama suka fado dankawai kaga dan birni jikinka narawa zaka aura masa yarka””adai bar yabon dan kuturu wlh nibanyarda da wannan yaron ba
idan kuntaka hardo yatanka binta kawai yake da ido saida tagama iyya ta kama umm ke yaya aikingama bakin magana ninasan saboda kudinsa yabashi itah kuma dagani kinsan kudin jinine bana Allah da Annabi bane yasaurayi kamar wannan zaibar birni yazo karkarah yazauna haba aidole adasa masa alamar tambaya
itah dai innah batace uffan bah” sukawai suketa zubarsu hardo yanisah yace wai atsakaninku waye yadau cikin. mairo sukayi tsit””yacigaba toko wacce tadau cikin ta gatanan bata isah tahanani abunda nayi niyyabah
kuma itah batayi maganaba saiku sani infika agola da rabon gidah meyadameku yata cefa????banason irin wannan dagayau idan bazaku saka albarka ba kukama bakinku””gaba daya sukai shiru gwaggo tamike um bari kugani inkama gabana
itah ma ai uwar sanaben duk bakinku daya ganin yarta ta auri dan binni barin murna kike saikinga ankawo kan yarki zaki gane tayi gaba nabarku da alhairi””” iyya tamike nima ai yaya bazama zanyibah mezan tsinta anan adaiyi mugani idan tusa nahurah wuta
takaba kai tayi dakinta akabar inna kawai duke gaban malam tsawon mintuna ashirin sannan yace bakice komaibah shatu??tayi murmushi banda abunka malam mezance kaida yarka??niko kadan banajin haushin abunda kayi nasan bazaka taba kai yarka inda zata halakabah
nikaina nayaba da hankalin yaron batun yauba fatana Allah yabasu zaman lafiya”” hardo yayi murmushi ameeen ameeen shatu tashi tayi tarufo masu kofah dama yau itah takeda girki””hardo yanason shatu fiye da sauran matansa kasancewarta mace mai saukin kai dakawarda kai gaduk wani abunda baishafetaba
Aisha……………….gentle
[7:57AM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
29
washe gari amasallaci bayan angama sallah yayi masu wa azi sannan yanemi gafara duk wanda yayiwa laifi yayafe masa wasukam harda hawaye makiyansa dadi sukaji kamar wani abu yatare masu agarin haka aka hada masa shatara ta arziki kwai kusan kwarya ashirin yasamu ga nono innah harda guzurin kan dawo
su gwaggo kam sai zundenta suke wai ansaida yarta danjin dadi harda bada tukuici duk inda mairo zataje nan makota taje sunyi bankwana da mutane duk inda taje cewa take binni zani wlh..
sukam dariya suke mata yand tahaukace kanzuwa binni hardo saida yabawa haiydar hatsi su masara da dawa da gero yace ah ah abba nida nazo amotar hayya ina zankai wadan nan nadai gode halliru kam kamar yayi kuka haka yakeji bandama haydar yanayi yana bashi baki
har tasha ya rakasu innah kam kolekowa batayibah hardoma baijebah halliru ne kawai sukaje tare saida suka shiga gari yadauko ragowar kudinsa yadau dubu biyar sannan yaja halliru gefe yabashi yace ka damka wannan kudin hannu abba dan Allah kace yakara yaja jari insha Allah bada jimawaba zandawo naso intafi dawani yaga gida amman abba yace ah ah
halliru yakalleshi shikam baitaba ganin yayan masu kudi da irin halayyar haiydar ba saida yayi hawaye wajen godiya suka shiga mota baibar wajen ba saida motar tatashi yana daga masu hannu saida yadaina ganin motar sannan yajuyaa
mairo kam uwa chuchu tashigo binni sai raba ido take itah tunda take bata taba zuwa nan bama daga garinsu sai kasuwa saikuma kauyukan dasuke makotaka dasu kuma dakafa ake zuwa idan takalla nan takalla cen shikam haiydar hankalinsa yana wajen wayarsa yana latse latse””
sunfara shigowa zaria tahangi wani gidan mai tasaki baki saita kama rego kanta harya kere na haiydar yadago fuskarsa yana kallonta ta yake hakorah kai dan binni nifah banson kallo kaga abinda nake kallo kawai… yayi murmushi to bazaki kalla kina zaunebah sai kinyi dogon wuya sai anmaki dariya ace baki saba shiga motaba
saita gimtse dariyarta tawaigo bayanta haka kuwa mutanen cikin motar itah suke kallo saitaji wani iri tagyara zamanta tabuga uban tagumi tana binsu da idanuwa kamar wacce take neman wani abu tamaida hankalinta wajen haiydar dan binni menene wannan dakake tabawa??? takai hannun ta tashafo waya
yasaki murmushi yace waya ce “”tace waya kuma me akeyi da itah yanda tayi maganar gaba daya saida yan motar suka saka dariya lallai wannan tacika yar daji baki taturo nan take idonta yacika da kwalla haiydar yasausauto da muryansa yadan duka wajen fuskarta menene kuma nakuka???
badariya sukemun ba? sauran hawayen suka karasa gangarowa yace kece kika sakasu dariya kinata surutu bakisan ba a magana cikin mota ba idanuwanta ta dago dara dara dasukeda ragowar hawaye tace aibaka fadaman bako????
tunda muka shigo daka fadaman ba a magana aibazan yibah ko??? amman dan kawai nayi cikin rashin sani zasuman dariya”” yace idan fah kina daga murya zasukuma yimaki dariyan
Aisha………………….gentle
[8:28AM, 11/16/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
30
dama kuwa yan motar susuke saurare suka sake fashewa da dariya yace kada kidamu kidaina kuka kuma nahanaki yawan surutu amman bakyaji tayi mui da bakinta juyowa tayi dakanta gefe tabar kallon haiydar din
duk wanda sukai ido biyu dashi tagallah masa harara tamurguda baki saikaga yakauce idonsa daga kanta””batasake cewa uffan ba ahankali tasoma gyangyadi tana fadawa nakusa da itah haiydar yana lurah saiyaji wani abu yataba zuciyarsa wanda shimadin baisan namenene bah saida yagyara mata zama tadan bude idonta tasake rufewa
ahankali takwanta saman kafadarsa wani yarrrrr yaji cikin jininsa wanda tunda yake baitabajin irin saba”” yadago ido yakalleta””menene dalilin shigarsa wannan yanayin akan karamar yarinya yayi dan tsaki mara sauti nimezanyi da wannan
barci yayi dadi su mairo akazube saman cinyoyin haiydar hannuwanta tasaka tarungumo kugunsa haiydar jiyayi kamar zai suma waimene ne wannan abun dayake masa yawo cikin jini yakasa gane komenene ahankali yadagota yamaidata saman kujeran sannan yasauke ajiyan zuciya yadainajin xuginda jininsa yakeyi
saida suka shigakano sannan tafarka aikam saitasake komawa bakauyarta babu ruwanta koda dariya zasu mata amman kallo bazai barta bayaba saida akasaukesu kafin haiydar yafito itah tafara fitowa sairaba ido take yadauko kayansu amman yawaiga gabass yamma babu mairo
kansa yadafe da hannunsa wannan yarinya tana nema ta haukatani yayita nemanta cikin tashar babu mairo yabawa wani ajiyan kayansu cikin sauri yajuya duk motocin dasuke wajen saida yayita lekensu amman komai kamada itah hankalinsa inyayi dubu yatashi yadafe kai kamar yafasa ihu yanzu mezancewa iyayen yarin yarnan daga fitowa mota indau kaya ace tabata
kamar daga sama yaji tace kai dan binni ganinan fah cikin sauri yawaigo yaganta tsaye tanashan kankana”” saida yasauke ajiyan zuciya jiyayi kamar yafalla mata mari yadan daure fuska ina kikaje?? tadaina shan kankanar tace danafito mota shine naga wannan tayimasa nuni da kankana inata kiransa insiya baijiba haryafita shine nabishi saida nahada da guduma koda nadawo wajen da aka ajemu bangankaba
shine nake nemanka kada kabata.baisan sanda yayi dariyabah waishine zai bata”tace ungu kasha karagaman kokallonta baiyibah yadaure fuska yayi gaba tabishi abaya hayar tax yayi yazubah kayan amotah shi gaba yazauna itah kuma tana baya
yace yallabai ina zamu”” yace nasarawa babu wanda yasake cewa uffan harsuka kai unguwa kofar wani katon gida suka tsaya duk acikin jerin gidajen unguwar shine nafarko wajen tsaruwa mairo kam kamar idanuwanta zasu fado kasa wajen kallo shiyafara fitowa sannan itah yabashi kudin sa maigadi dagudu yazo yana kwasar gaisuwa haiydar ya amsa malam habu munsameku lfy””
wlh qalau ango “”aina dauka saimunzo biko ana saura kwana uku biki amman bakazobah har anfara shagali gida cike yake dayan biki”yace tofah ashe badamar inshiga ciki azuciyarsa yayi maganar yakalli habu danshiga da kayan nan wajen hajy yace angama yallabai
yadauki kayan ango ango ainiranar daurin aurenka wlh sainayi rawa yallabai ainafi kowa matsuwa ranar tazo haiydar yayi murmushi to habu Allah yakaimu yawuce yana fadin ameeen ameeen dai yallabai
Aisha……………………gentle
[6:49PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [11:21PM, 11/17/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
40
tasake lumshe idon ta takwanta saman ‘kirjinsa ahankali tace my dear” yace na am”” tace wai yaushe zaka fara fita dani yawo mudanga gari tunda nazo banje ko inabah”” yayi jim sannan yace yawo kikeson zuwa???’kai kawai tagyada masa yace k kibari sai gobe kinga yau inada nyt duty amman gobe free nake
koya kika gani juyowa tayi da sauri tasakar masa kiss yalumshe ido yabude tace tnx my dear”” acen kasan makoshinta tafurta iluv u “yaja hancinta mee2 tasake rungumeshi shima saiya rungume kayarsa”” yinin ranar tare suka yishi sai dazai fitah suka rabu
yana fitah itah ma tafita dan dama duk ranarda bagida yake kwana ba itah ma ba anan take kwana ba”washe garine suka fara zaga gari dashi da itah tana makalkale ajikinsa basu suka dawo gidaba sai karfe takwas na dare”” sunsha yawo kam duk wannan yana dai daga cikin tsarin hameeda suna dawowa tayi dakinta shima yayi nasa dakin
saida tayi wanka aka saka abubuwa a ehem ehem yanda bazaidan ganebah taci kwalliya kusan turarenda tafesa kamar companyn buga turare wasu irin arnakun kayan barci tadauko nafitar hankali fararene amman dasu darashin su duk daya
komai najikinta abayyane yake gata mace dirarra malam humm nikaina saida nahadiye yawu balantana haiydar nasan saiya suma. takalmi masu tsini tasaka suma farare tadauko lemunta na kwali guda biyu koda tazo falon tasameshi yayi kwance da alamu duk gajiya ce wanka kawai yayi komai baisakaba gajeren wando ne kawai jikinsa
gefensa. tazauna tana sakar masa wani shu umin murmushi tamika masa lemun mai sanyi gajiyar da yayi aiyana bukatar abu maisanyi batare da wani kokontobah yakarba yafara sha yana kallonta itah ma tanashan nata tana kallonsa tagefen ido
saida yashanye gaba daya yayi cilli da kwalin yayi ajiyan zuciya sannan yajawota yarumgume yayi mata kiss nagode kamar kinsan ina bukatar abu maisanyi”” batace masa komaibah burinya daya dama yasha kuma tunda yasha magana takare”
sannu ahankali yafarajin tsikar jikinshi tana tashi yarrrrrrrrr itah ma maganin yafara yimata aiki nantafara shafarshi ahankali”” ya lumshe idonsa wani irin dadi yakeji yana tsargawa harcikin kwanyarsa kaman yafasa ihu dan dadi”” nantake yafara mayar mata da martani”” dama hakan takeso suka fara tsotsar junansu sundade cikin falon kafin yamike
yadauketa sai dakinsa saman gado yajefata itah kam tagama jikewa shikawai take jirah dan gab take da nuna masa tamafishi jikuwa wanda bahakan bane haiydar gaba daya yafita hayyacinsa duk abunda yakeyi bama cikin hankalinsa yakebah
yanda yakeji muddin baijishi jikin maceba zai iyah mutuwa”” tunda yafara aiki bakakkautawa itah ma hameeda ba abarta abayaba babu maganar gajiya dan abunda tasaka masu alemu koda sun gaji zasuji wata sha awar tataso masu
kai intakaice maku labari kwana akayi anayin abu daya saikusan asubah suka saurarawa kansu abun yayi matukar bugar haiydar kasa tashi ma yayi dama wannan damar sukeso yakasance yana cikin janaba tayanda aikinsu zaitafi daidai yana gamawa sai barci “” hameeda tazame jikinta tana kallonsa tahaukace dawata shu”umar dariya haiydar kashigo hannu kenan
Aisha……………..gentle
[12:41PM, 11/18/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
41
Haiydar baitashiba sai karfe bakwai da rabi”karo nafarko da sallar asubah tawuceshi wannan mafari kenan haiydar yawayi gari da mugun son hameeda kamar yayi hauka kaida za a tambayeshi aduniya wayakeso yanzu hameeda zaice
sannan kuma zuciyarshi tacika da tsoronta dakuma shakkar ta gaba daya yaji ko kwakkwaran motsi bazai iyah yibah muddin tana kusa dashi bayan yayi wanka yayi sallah yashirya ganin harya makara
afalo yasamu yar laushin tana kwance tana ganinsa tadaure fuska”” inazaka haka??? yayi murmushi rankiyaye kema aikinsan inda zanje bakiga harna makaraba amman baki tashenibah”” tamere baki kamanta banci komaibah??? yasakeyin murmushi banda abinki hameeda saina tashi zakice haka kullum kafin ma natashi aiharkinsa ankawo maki abinci””
tayakuna fuska niduk abincin wannan hotel din baimunba bana sha awan cinsa.ai naga akwai kichin anan kaje kanemo abunda zaka dafaman yunwa nakeji”” tana kaiwa nan dazancenta tajuya baya makar maibarci
yajuya kawai yafita saida yaje kasuwa yasiwo kayanda duk ake bukata yadawo tana kwance inda yabarta yace mata gasu nasiyo””!bata juyobah tace kaje kadafaman indomie dasauri minti goma nabaka idan kagama kasameni adaki””tashi tayi tashigewarta daki
yadade tsaye yana tunanin wannan lamari kuma shibazai iyah yimata musubah kichin yashiga ya kunna gas shima yarasa ta itah zaifara abunda baisaba ba ruwa yafara zubawa yanika kayan miya yajuye sannan yasaka mangyada da magi suna fara tafasa yazuba indomie minti biyar tayi yajuye cikin flat yayi hanyar dakinta yana tafiya yana zufah saboda wahala yasa gefen rigarsa yashafe kwance yasameta tayi daidai saman gado
ya aje sannan yakalleta angama “”tajuyo katabbatar tayi dadi?? zurum yayi dankuwa yasan dakyarne idan zatayi dadin tasake tambayarsa yayi dariyar yakce eh tayi mana”” cikin kasaita tasauko da kafafuwanta kasa tace mikoman yaduka yadauka sannan yamika mata
cokali daya tayi tafurzar”” tana tari cikin hanzari yamatso yana yimata sannu tace ruwa ruwa dagudunsa yaje firij. yadauko ruwa saida tasha tana sauke ajiyan zuciya wani masifaffen yaji kuma ga gishiri tadago idonta cikin fushi menene haka haiydar nema kake ka kasheni ko???
yamarairai ce fuska haba hameeda yazanyi inkashe abunda nafiso duk duniya wlh bahaka bane kinga bansan yanda akeyibah dakin hakurah nayo maki takeaway kamar yanda mukeyi kullum amman kikace ah ah amman kiyi hakuri baza asakebah”””
ta ballah masa harara wanda saida yasauke idanunsa daga kallonta tace dauki tsiyarka banaci jeka samoman abunda zanci yunwa nakeji to kawai yace yadau indomie n yafita bajimawa yadawo yakawo mata gashi saikiransa akeyi. hospital amman yakasa kodaga wayar agabanta tana kallonsa dasun hada ido saiya done kansa wata dariyace tazoma hameeda “””takanne cikin zuciyarta tana cewa haiydar kenan wannan suman tabine akan abubawanda na tanadar maka saikayi danasanin aurena duk da ba ason ranka kayibah
saida tagamacin abincin ta tasha ruwa sannan takalleshi kanshi yana kasa tace matso nan haiydar bamusu kuwa yamatsa kamar wani jela hannu tasha ta zuge wandonsa baice mata cikankibah tadago takalleshi tayi wani shu umin murmushi tace abun nakeso zansamu????
yace daguduma idan harkina bukata ta rausayar da kai oyah to abani babu musu kuwa yahaucire kayansa suka lolaya duniyar ma aurata nidaikam dariya nakeyiwa haiydar sainaga yanda zai karke da hameeda……………………..
Aisha……………….gentle
[3:05PM, 11/18/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
42
Saida suka gama holewarsu sannan yatashi yayi wanka yawuce asiviti itah ma tana ganin yafitah taje ta dado wankanta taci diresin tafitah “” makaranda yayi yasoma yasamu matsala yana zuwa dakin tiyata yashiga “”
bashi yafitobah sai wajen la asar yinin ranardai baihutabah harzuwa dare””karfe takwas daidai ya iso gida amman baisamu hameeda ba hakan yayi masa zafi zuciyarshi sai kuna take yayi tsayin awa daya yana jiranta amman batadawobah
hakan yasa kawai yaci abincinsa ya ajemata nata sannna yashiga wanka bayan yafito jallabiya yasaka yakoma falo yayi kwanciyarsa tunani fal aransa ina hameeda taje hartakai dare haka kuma yaushe tafita??? inakuma taje yanata jerowa kansa tambayoyinda bazaisamu amsarsubah sai abakin hameeda””
sai shabiyu tashigo gidan ta dade tsaye akansa baima sanibah dan barci yadaukeshi. takirah sunansa sannan yatashi yashafo fuskansa yakalleta hameeda daga ina kike cikin daren nan????shiru taimasa yaci gaba
haba hameeda dahankalinki kina matar aure zaki fita bada izinin mijinkibah kuma kikai haryanzu kina waje kinkosan ko karfe nawa yanzu????? takai kallonta ga agogon bango dayake manne abangon falon tace shabiyu da rabi saikuma akayi yaya nifa kaga banason sa ido wlh
shikenan balailai mutun yafitah sai antitseshi da tambayar ina yaje ina dai ba aikena kayibah kaidakafitah tambayarka nayi ina kaje??? ya marairaice murya haba hameeda aini kinsan iyakata asiviti bayan nan wlh banazuwa ko ina”tamere baki kai akeji nidai nafada maka banason sa ido ehee idan kuma kasan takurani zakayi kawai kasakeni taja tsaki tayi shigewarta daki
cikin hantsari yadago kai yana kallonta yana maimaita abunda tafada waiya saketa datasan abunda yaji aransa lokaicinda tafadi hakan dabata fadaba jiyayi kaman andau guduma anbuga masa azuciya yadade cikin falon jiki asanyaye yayi hanyar dakinta
lokacin tafito wanka tana tsane gashin kanta yayi tsaye yana kallonta duk cikin secnd daya jiyake ansake lunka sonta cikin zuciyarshi ko inda yake bata kalla bah saida tagama tasaka kayan barcinta tahaye gado ahankali yasoma takawa zuwa bakin gadon yazauna yayi shiru saida yayi karfin halin hadiye wasu busassun yawu sannan yakirah sunanta bata amsaba yaci gaba””
hameeda fushi kikayine??? nan ma bata tanka masabah yace kiyi hakuri idan maganata takona maki rai banfadetaba dankiji zafi nafadi hakane saboda irin sonda nake maki hameeda kinzama bugun zuciyata wlh bazan iyah wuce dakika dayaba akowace rana batareda tunaninkibah
acikin kowane kif tawar idon sonki kara kaimi yake acikin zuciyata yinin yau bayan tunaninki banyi wani aikibah tunaninki yafimun duk wani aiki dazanyi”rashin ganinki shine yatayarmun dahankali amman plz kidaina fushi dani kinji
:hannunsa yasa yajawota zuwa jikinsa tamuge masa hannu kaga kakyaleni banason kana matsowa kusa dani “””murya araunane yace saboda bakya sona hameeda???? saiga hawaye a idon haiydar
wannan maganar taki daidai yake dakidauko mashi mai tsini kidaba a zuciyata in mutu insan bana raye balantana harkin kasa kusantar inda kike””yasauko daga saman gadon yaduka plz hameeda kitaimaka kiyi hakuri””tayi shu'”umin murmushi nayarda zan hakurah amman da sharadi””kafin ma takarasa yace saradin menene wlh zanyi idan harzaki hakurah””
tace daga yau karkasake tambayana ina naje kaikoda bankwana gidan nan ba banason katambayeni ina naje’kuma kada kanemeni”yace indai wannan ne insha Allah zan kiyaye’;tayi murmushi shikenan yace kinhakurahn tagyada kai yace to inzo mukwanta nan ma kaitagyada masa
saida yayi dan ihun dadi yahau saman gadon yarungumota yaujinsa yake cikin wani yanayi na sha awa amman fir hameeda tahanashi wai itah tagaji dayawa kome ya gajiyarda itah din oho haiydar harda kuka yamata amman taki bashi kayan”” ga cikinsa sai ciwo yake saijuyi yake saman gado itah kuwa goganyar tuni tayi barci
Aisha……………gentle
[6:50PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [5:28PM, 11/18/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
43
Saikusan asubah yasamu barci yadaukeshi sai asubah yafarka”” yauma kamar kullum saida tasa yadafa mata abinci duk da baci zatayibah kawai bataso yasamu hutune hakadai rayuwar ma auratan take tafiya yana kiran su dad da mom akai akai amman kosau daya baitabah tambayar ina mairo ba shiyama manta dawata aba wai mairo
rayuwa kenan maman zulaima tahaihu namiji akasamasa suna abdurrahman mairo anmaida hankalin wajen karatu bata wasa amare duk sun kamu bakamar kursum dan itah cikin wahala yake bata”” akwana atashi babu wuya wajen Allah mairo angama primary har ankaita jss 1
Aisha tahaihu mace anyi biki akasakawa yarinyar bilkisu suna kiranta ikram”” sati biyu tsakani na ima da kursum suka haihu duk maza kwana hudu da haihuwar asiyama tahaihu mace sai aka game sunan rana daya dandan kursum. mudassir dandan na i ma ” abubakar ana kiransa.ameer diyar asiya ameena
saida sukayi arba in zulaihat tahaihu amman abun baizo daraiba “mom daikam abunsu haiydar yasoma damunta ganin sauran duk sun haihu amman itah yaki maidota gida koso yake saita haihu ganin baida niya yasa tayanke shawarar kiransa
mairo tana gefen ta tanayiwa su hassana wasa takirashi kirah daya kuwa yadauka yana zaune kasa hameeda tana kwance saman kujerah yanayi mata tausa yadauka cikin girmamawa yagaisheta ta amsa da fara anta sai shiru yabiyo baya
takirah sunansa haiydar” na am mom””tanisa wainikam nace yaushe zaka kawo hameeda gida tahaihu kokuma sokake tahaihu kasarda batasan kowaba..yakai kallonsa wajen hameeda itah mashidin take kallo da alamun tuhuma afuskanta dantasan maganarta akeyi
yamuskuta ai mom ai ”aime haiydar ???baka lissafin kwananku nawa rabonku danan shekara harda wata bakwaifa” kodai tahaihune kakasa sanardani””yasosa kansa ah ah wlh mom yama za ayi hakan tafaru bada saninkubah
to agaskiya kudawo gida hakan nan nidai nafison ganinka kusa dani nitun farko ba ason raina kayi tafiyar nan ba”shiru yakumayi yace mom wlh batada ciki da akwai aizan fada maki”” batada ciki haiydar?kodai wani abu kake durawa yar mutane tunda bakasonta
yayi murmushi kodaya mom inason matata kuma inason haihuwa da itah Allah ne kawai baikawobah kitayamu da addu’a jiki asanyaye tace ai addu’a kullum cikinyimaka itah nake haiydar Allah yakawo masu albarka yace ameeen sundade suna magana sannan yayi sallama da itah yana kallon hameeda yana murmushi
yace kinji mom ko wai itah harta dauka kinada ciki” nikaina gaskiya nafara damuwa da rashin samun cikin nan naki duk da bana wasa yayi maganar yana kallonta takasan ido””tamere baki aikuwa idan nikake jirah inhaifah maka yara kanada aiki abunda haidar baisaniba kwayoyi takesha akwaima cikinda batasan dashiba saida yakai wata biyu tazubar dashi dan kam muddin tahaihu akwai matsala
shin waye mai cikin tsakanin haidar da alhaji hamza???wannan abu zaizamo mairudani agareta shiyasa tazubarda cikin shikanshi alhaji hamza bayason cikin acewarsa yara sun masa yawa””shiyakaita akacire cikin batareda haiydar yasan komaibah
Aisha……………….gentle
[8:10AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
44
Azuciyarta take wannan zancen amman afili saita marairaice fuska kamar zatayi kuka wlh nima ya haiydar abun nan yasoma damuna inason haihuwa sosai yanzu gashi wadan da akai mana aure tare duk sunada yaya nibandasu
kawaisaita fashe da kuka haiydar duk ya haukace yanata bata hakuri tace yanzu gashi mom dinka takaigayin magana nasan saura kiris ma tace kayi aure idan niban hauhubah “” habadai aibabu wanda ya isah yasakani naimaki kishiya” tambayata anan ga haiydar shinya manta da mairo ne kokuwa itah ba matsayin mata ya ajetaba
plz kidaina kuka indai akan mom ne ma kike damun kanki harkike zuvarda hawaye tokibari nasan bazata taba tilas tani inyi aurebah tunda ba itah zata zaunamun da matarba kiyi hakuri kinji idan ma daukan wayar yana bata maki rai sai indaina dauka idan takirah””
tarausayar da kai ah ah banceba sokake azageni ace na asirceka?? koma wa yayi saman kujera yazauna sannan yarungumota waye zaifadi hakan inbamu saba dashiba kenifah duk duniyar nan bayan ke babu wanda nakeso zan iyah sabawa da kowa akanki wlh
da inga hawayenki kara rayuwar kowama tabaci tadago ido takalleshi dagaske kake?? kaiya gyada mata yana lumshe”ido”tasake kankameshi tana murna”” shima farinciki fal kirjinsa yafarantawa wacce yakeso rai
mom ce zaune tana kara mairo karatu”” bayan sungama takirah sunanta maryam tace na am.. sannan tamaida kanta kasa taci gaba kinga aurenku yanzu shekara biyu harda wata biyar”” nasan hankalin iyayenki yana tashe ganin haryanzu baki ba haiydar”
ta nisah shikuma gashi yayi zamansa acen wai aiki yayi masa yawa “” danhaka nakeso tunda kunsamu hutun boko kigyra jibi direba zaikaiki gida”nasan kinyi hakuri maryam amman inaso kikara bisa ga wanda kike dashi sannan aduk inda kike kizama mairike sirrin mijinki kada kibuda baki kisanarda wani ga halinda kike ciki da mijinki
anason mace mairike sirrin mijinta kekanki idan kika kasance haka zakisamu soyuwa azuciyarsa ina fatardai kingane”” mairo tagyada kai insha Allah mom aduk inda nake zan kasance maiboye sirrina ” nakuma gode da irin sonda kike nunamun sai hawaye shar shar
hakika ya haiydar yayi dacen samun iyaye nagari wadan da sukasan darajan mutane har abada bazan taba mantawa da abunda kikamunba kin maidani mutun wanda ada nake cikin duhun jahilci”” ko sallah ban iyah ba balantana alwala”” amman tasanadinki gashi na kusa sauke al”kur”*ani kullum addu”a agareki bazai wuce neman gafarar Allah ba nagode sosai””
amman mom ya haiydar yasan da tafiyana idan baisanibah nahurah haryadawo”” mom ta dade tana kallonta tana murmshi sannan tace yasani shima yayi man kwatancenda zanyiwa driver kada kidamu kinji yata”” murmushi tayi nagode mom
mikewa tayi zuwa daki mom tabita da kallo tana murmushi tana shiga ta aje kur”anin saman kujera tafada tanata kuka zuciyata bakiman adalcibah mezaisa kikamu dason abunda baidamu dakeba baima daukeki amatsayin macebah
yanacen tare dawata sunacin soyayyarsu”” kuka take maidan sauti tasa hannu tatoshe bakinta kada mom taji abunda yake damun mairo kenan kullum dare saitayi kukan rashin haiydar”” adakam batasan komai akan soyayya ba amman zuwanta jss one tadada wayo saboda tahadu da gogaggun kawaye masu samari kullum zancensu akan samarinsu da irin yanda suke buga soyayya
tun sunayi abun yana bawa mairo haushi harta soma saurarensu idan sunayi saitayi zugum tana kallonsu tana murmushi itah ma saita hango kanta tareda ya Haiydar dinta suna soyayya”” tun abun baizamar mata jikibah harta saba ranarda basuyi firan soyayya ba saitaji duk wani iri
Aisha………………gentle
[8:41AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
45
akullum mafarkinta baiwuce na haiydar ba inama zataga hakan azahiri datafi kowace mace sa a acikin duniya zuciyanta tana karyewa duk sa inda tatuna shifah yana tareda wata yama manta dake inbanda haka tunda yaje kosau daya kintabajin yace inakike???? idan ma zaki fitarda ranki akansa kifitar
wani kuka yake taso mata maicinrai “” cikin tane yasoma murdawa”” tayita murku susu itah kadai cikin daki”” saigunjin kuka tace””husainace tashigo dakin taga tana kuka”” dagudu tazo tafada jikinta tana tambayarta anty waye yadakeki kike kuka”” cikin gwari gwari take maganar kai kawai tagyada mata alamar bakomai itah ma saita fashe da kuka
kukantane yarude gidan har mom dake zaune falo taji tataso zuwa dakin dasaurinta ganin husaina tayi jikin maryam tana kuka “”oh waike husaina meyasa kikeson kukane”” tanuna mairo dayatsa “”mom tace maikuma antyn tayi indai kune aibabu maishiga tsakaninku harzata juya saitaga mairo tacigaba da murkususu
dan karfin hali waidataga mom shine tacije kada ta fuskanto abunda take ciki wata kara tasaki jin yanda cikinta yakatsa nan take tazube sume dagudu mom takarasa inda take tana jijjigata jini tagani saman kujeran wannan yanuna kenan maryam tafara al”ada dasaurri tadibo ruwa tafesa mata taja ajiyar zuciya ahankali tasoma bude idonta dantaji kaman ancire mata ciwon
tayunkurah zata tashi saitaji sanyi cikin jikinta zaninta dasauri tamike tana ganin jini takoma tazauna kanta akasa duk kunyar mom yakamata ashe dama wannan ciwon cikin na al”adane”” mom taja hannun husaina suka fitah babu jimawa saiga husaina da pat da fant guda biyar takawo mata sannan tafita
tashi tayi tashiga tolet takimtsa kanta ta goge kujeran””nikam nace kokin goge bazan sake zaman kujeran nan ba saidai inzauna kasa”” murmushi kawai tamun takoma dayan kujeran tazauna kasa fitah waje tayi wata irin kunyar mom takeji
wannan dalili yasaka mom tadaga tafiyar su kwana hudu tayi wankan tsarki””amman mom bata sanibah saida taje dakinta akan batun tafiyar tasameta tana karatun Alqur”ani tana ganin mom ta”aje karatun kanta yana kasa
takirah sunanta maryam”tace na am amman bata dago kantaba””tayi murmushi wai wannan kunyar tamenene shikenan kinsakawa kanki takurah kullum kina daki kamar gareki farau”” kidaina haka kinji nimafa macece kamarki kisaki jikinki dama nazone akan maganar tafiyarki kishirya anjima dreba zaije dake kasuwa kiyiwa yan gidanku siyayya
komai isashshe zaki siya mijinki yaturo kudi yace abaki dan haka kisai duk abunda kike bukata”” tasunkuyarda kanta nagode mom Allah yasaka da alhairi”” mom tace ameeen”” nidai inadaga gefe dan nasan ba haiydar dinda yaturo kudi itah dai bataso aga laiin dantane
haiydar din ma dayamanta dawata aba mairo harzai turo kudi akanta mom bataso mairo tagane haiydar baisonta gudun nan gaba dan idan har mairo ta kullaceshi zaiyi wuya tasoshi anan gaba abunda mom bata fata kenan “”darana tashirya mom tabata dubu dari drever yakaita kasuwa atamfane jikinta amman saita dorah after drss dan kayan sun kamata sosai
bata saka mayafiba tayane kanta da gyalen rigar kawai nikam nace yausokike kihada hadari akan hanya itah kanta tasan ba karamin kyau tayibah nikaf tasaka saita koma balarabiya sak
Aisha…………………..gentle
[9:25AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
46
Duk dahaka saida tasamu tsaraban yan kallo wadan da basu gani saisun kalla har wasuma suka kasa hadiye kwadayinsu suka tunkareta ko kallonsu batayibah dan tasan matsayinta bawai budurwa takebah
shaddodi tasiya da atanfofo sai takalma namaza dana mata sai sabulai sarkoki kayadai kam saida tacika but din mota gaba daya saida takashe kudin suka biya akaloda masu kayan bayan bt suna kokarin fitowa wani yabiyota
yana magana bata tsaya takalli ko inda yakebah..shikuma baifasa biyantaba harbakin botar tabude tashiga zata kulle yarika murfin motar yadan gurfano tayanda zata ganshi gayen kam yahadu iyah haduwa yace haba malama inata magana amman kinkyaleni plz idan bazaki saurareniba mezai hana kibani adress din gidanku
kayi hakuri ni matar aurece daga haka batasake cewa uffan ba”yasaki murfin motar taja takulle driver yaja motar suka wuce anan suka barshi sororo anya wannan dagaske itah matar aurece?? kai banyardaba wlh
bazan yarda tawucenibah komawa yayi dasauri yadauki motarsa yabi bayansu suna tafiya yana binsu harsukaki gidan acen nesa dasu yatsaya wannan yarinya gidan nan take saida suka shige sannan yakarasa da motar sa
yayi hon maigadi yabude masa yafito suka gaisa kaitsaye gidan yanufah shashen mom yashiga inda yaga tashiga lokacin yayi daidai da tacire nikaf””ya salam wannan wace irin halittace nayi gamo da itah idonta tar akansa taganeshi dasauri tamike tana nunashi da yatsa batayi maganaba saiga mom tasauko
tana ganinsa tasaki fara a”” ahh kasim kaine agidan damu”” jintakirah sunansa yasaka mairo tasauke hannunta tana maimaita sunan kasim kasim toshi kuma waye agidan “” mom tazauna saman kujerah kasa yazauna yana gaisheta tatambayeshi mutanen gidan yace kalau
tace aini nadauka kamanta damu kudai bakwason zumunci tunda haiydar bayanan kundaina zuwa”” yayi murmushi yadan sosa kai ayi hakuri mom insha Allah za a gyara ayukkane sukayi yawa wlh
takalli mairo “” maryam harkun dawone kaitagyada mata dan itah gaba daya tatsure da ganinsa”” mom tace bakiga kasim ba dan uwan haiydar ne “” tasaki murmushin yake sannu ko”” yace yauwa”” tadauki jakarta tayi daki yabita da kallo
hakika tunda yake baitaba ganin mace maicikar halitta kamar wannan ba to ina kuma mom tasamu wannan yarinyar????kamar jinsin larabawa shidai baisanta agidan ba duk da bazuwa yakeyibah
lallai shikam yayi matar aure duk da gidansu auren dangi ake yasan bazaisha wuyabah zaishawo kansu sukansu idan sukaga zabinsa yasan zasu yaba sosai yayi murmushi yana kallon kofar dakinda tashiga”” shiru natsayin mintuna hankalin kasim kwata kwata baya jikinsa saida mom tayi magana yadan zaburah itah ma tafahimci hakan tace lafiyadai kasim
yasosa kai babu komai mom nizan wuce “” tace to agaida gida””yamike mom banga yan biyubah”” tace ah wlh suna bangaren maman su”’ yace ok zanshiga cen ai tace to idan kakoma kagaida hajiya da innah yace zasuji tafiya yake yana waigen dakin kozata fito haryafita yasauke ajiyan zuciya Allah ya mallakamun ke maryam
yalumshe idonsa bangaren maman zulai yaje suka gaisa yadauki yan biyu yana masu wasa dazai tafi yaciro kudi sabbi ful yan dari dari yabasu sannan yayi mata sallama yawuce dagudu sukayi bangaren mamansu lokacin mairo tadawo falo suka fada jikinta suna murna
tace inye husaina waye yabaku kudi haka kuzo muraba”” suka mika mata kowa yana cewa nashi zata dauka mom dai tana kallonsu tana dariya tace wai wayabaku kudi””suka hada baki a kacim””(ya kasim)
saida gaban mairo yabada rass gudun kada mom tadago ta tayi saurin saita kanta”tamika masu kudinsu tace kurike har gobe saimuje shago kusiye abunda kukeso”” sukayi tsalle ki”ajemana to”” tace toku kawo ta amsa suka dane saman cinyarta suna bata labari
washe gari duk wani shirye shirye tagama tahada kayanta dazataje dasu kana nan kayane jikinta riga da wando yan indi”a sunyi masifar kama mata amman rigar tadan sauko tarufe mazaunanta ganin bamaishigowa gidan shiyasa bata damubah
tana gama gyaran tadauki gyalenta karami tayafah tafito falo tana jawokofah shima yana kunno kansa falon tsaye yayi yakurah mata ido. wannan wace irin halittace datake nema tahanani sukuni”” itah ma idonta yana kansa sauke kwayan idonta tayi daga barin kallonsa tajuya zata koma zaikirah sunanta saiga mom tafito””
mairo takoma warta daki”” tanajinsu dashi da mom wai abinci yazoci tayi murmushi akwai kuwa bari inzubo maka yaso takirah maryam danshinema yace mata yunwa yakeji dakanta tadibo masa takawo masa
yaci abincin sosai harda falfesun kayan ciki
Aisha………gentle
[10:16AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
47
Yayi nak yayi hamdala hankalinsa yana kofar dakin yauma saidai yakarace zamansa mairo bata fitobah yagaji yayi ma mom sallama yatafi zuciyansa sai zugi take masa meyasa maryam takeson wahaldani kodai inkirah broth insanar dashi watakil shizai taimakaman insamu cikar burina
kai amman banason wani yasan wannan sainafara samun soyayyarta tayanda bazan sha wahalabah wajen samun amincewar su dady”” yana kwance jikin kujeran motarsa yake wannan tunanin inaduwansa lumshe bakomai yake hangeba sai surar jikinta tayi masifar kyau cikin kananun kaya
Allah yanunamun kinzama mallakina yayi murmushi maidan sauti sannan yatada motarsa yabar gidan cike da shaukin kaunar maryam”nikam nace wai zancen banza idan ma kasanarda haiydar aisaiya kusan kasheka””
washe gari da karfe goma har mairo tagama shiryawa mom tabata dubu dari taje dasu koda zata ba wasu sannan takara mata dawasu kayan turare da atampodi bayan motah aka loda wasu dan bt din yacika gaban mota tashiga suka wuce tana dagawa mom hannu yan biyu kam basu tashi barcibah
dan idan suka tashi bazasu barta tajebah mom tasan idan suka farka yau akwai rigima sabuwa dan dasun tashi dakinta suke zuwa sai idan sun tarar tana boko suyita kuka kuma ranar sukuku zasu yini hartadawo””
kwatancenda mom tayi masa yanda haiydar yafada masa hakan yayi dayawuce zariya saiya fara tambaya baisha wuyabah akanuna masa hanya ana kawowa kauyen mairo tagane tasaki murmushi wani dadi taji yakumeta yauzataga innarta wayyo dadi””
tanata nuna masa hanya harsukakai kofan gidan”” innah tana zaune tana nasa danwake gwaggo da iyya saizuba mata habaici sukeyi gwaggo tace iyya waikinsan wani abu?tace ah ah saikin fada””hmm wai saboda ba asan ciwon haihuwabah daga ganin kudi akadauki ya akabayar ashe sun siyarwa maiyankan kai
suka kwashe da dariya kicedai ana nan a nakukan bakinciki”gwaggo tamere baki aikuwa kuka yanzuma suka fara ba ana mana kuri wai yarta ta auri dan binni ba aikam ga inda kwadayin ya kaisu yanzu babu ya babu mijin
suka sake kecewa da dariya aiduk wanda yace tukunyar wani bazata tabsheba yakwana dasanin shima tasa haka aimu karamu muna ganin yayanmu wanda kwadayi yaja kuwa saidai yaga kayanta da aka jibge asoro suka sake tafawa suna dariya
inna daikam kokallon inda suke batayibah inda sabo aita saba dawan nan arashin tunsunayi afakaice amman tasan da itah suke harsun dawo sunayi afili itah kuwa bata damuwa dan ba itah kadaiba har hardo basu baribah shima baikomawa takansu
taci gaba da nasa dan wakenta hayaniyar yara sukaji awaje ana kiran ga mairo ga mairo aida gudu suka doshi kofar gida suna rigenge tsakanin gwaggo da iyya suka fita soro sunata rabon ido sudai basuga mairoba tagefensu taratsa bayan sun gaisa tayi cikin gida
sunata regen mota suga inda mairon zata bullo ganin yara sun zagaye motar sai kallo suke suna shafawa amman shiru babu mairo gwaggo ta kunduma ashar dan ubanki bazaki fito bane munata jiranki sauran yaran suka dunguma cikin gidan
gaba daya sukabar bakin motar sukayi tsaki suka shiga cikin gida idan uban naki yazo aidole kishigo gidan muna fuka kawai suna shiga gidan suka tarar da itah kusa ga innah suna gaisawa tana zaune saman kujerah yar tsuguno
takalli yaran tace ina babana yake????sukace yana daji sai yamma zaidawo””tace gona yaje ko fadama???? sukace fadama tamike bari inje na matsu inga babana sudai su gwaggo baki suka saki suna kallon ikon Allah anan nufin wannan ce mairo yarinya kamar balarabiya
ina sukam basu yarda mairo bace””inna tace mairo bazaki zauna kihuta ba daga zuwanki zaki fitah tajuyo wajen inna bakomai inna babana nakeson gani wlh abani ruwa inkaiwa driver dan yau zaikoma shi innah tashiga daki tadibo ruwa tabata takaiwa driver yasha yayi hamdala
yace kisa yara sudauke maki kayan nan kada inyi dare akan hanya; tace yara bazasu iyah dibansuba kadibamun muje dakin inna na yace kina ganin dagirmana zanshiga gidan mutane”” tayi dariya aibakomai muje shiyarika daukan kayan itah ma tana rikawa
harsuka kwashe su gwaggo kam ido suka turo ganin yanda ake fitoda kaya kaman wani babban shago xa a buda harbakin motah tarakashi tayi masa Allah yakiyaye yadau hanya itah kuma tayi hanyar fadama duk inda tayi binta kawai ake da kallon
har takai fadaman bataga hardo ba yana kurya gyalenta tacire tasha damara dashi takaryo sandar rake ta aje gefe cen tahango wata karama siririya dagani zatayi zaki takutsa kanta cikin raken tana tafiya hartakai kusa da itah ta karyo
tafito tanasha halliru ne yaji motsin mutun yace baba kamar dawani acikin fadamar nan naji motsi”hardo yake saidai idan awakine wazai shigo yanzu tunda sunsan ina nan”” tasake hango wata takama takarya tanada kwari sosai taki karyuwa ga karamar tanasha kuma duk ta bata mata jiki nidai nace kekuma daga zuwa kauye kinkoma yar kauyenki sak
dakyar tasamu takarye saida tace wash wlh saina shaki tunda kikaban wuya””saiyanzu hardo yaji magana tare sukazo wajen ganin sandar rake sukayi zube harguda biyar tanata kiciniyar cire wata saida taballo sukam tsaye sukayi suna kallon ikon Allah
tawaigo kenan tagansu tace la ya halliru ashe kaima kana nan tafito tana dariya hardo yace wai mairo ce ????tayi murmushi nice mana baba baka ganenibah””halliru yana rike da baki yace auta dagaske kedince”tace kai ya halliru idan bani bace to wacece
hardo yace saukar yaushe????
Aisha……………gentle
[10:47AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
48
Tayi murmushi yanzun nan wlh baba ina wuni””cike yake da mamaki yace lafiya qalau baitaba saran ganin mairo awannan lokacinbah. yace ina haiydar din tare kuke dashine??? tace ah ah baba aiki yayi masa yawa shine yaturoni tare da driver harma yawuce shi
ah dawuri haka meyasa bakice yabari yakwana bah? baba aicewa akayi yadawo yau yace toh muje gida” taduka zata diban raken halliru yace ah ah auta bari indaukar maki aikin wuce daukan rake ahanya la yaya aiba wani girma nayibah ko????hardo yace ah ah kingirma mana mairo kidaina shan abu ahanya kinji
tace to saita kaikaici ido.su tagutsiri rake tana taunawa ahankali harsukakai gida suna tafe suna gaisawa da mutane kofan dakin inna halliru yazube mata rayen tazauna saman kujerah tanasha
suna gaisawa yana tambayarta mutan gidan tace kalau suke duk suna gaisheku tace inna sakoman dan waken fah shinake jirah”” innah tayi dariya ainaga kintasa rake gabanki nadauka itah zakisha kikoshi “”ai innah rake bata maganin yunwa kwadayinta nake tunda nabar garin nan bansha rakebah ina ma zanganta tunda ba fitah nakeyibah daga makaranta sai gida
inna tazubo mata danwaken tamotsa tafaraci hardo yace kice dai mairona yanzu tayi hizifi goma”” tayi dariya hartadan kware saida tasha ruwa tace baba hizifina arba”in wlh kuma inazuwa makarantar boko yanzu ajina daya babbar makaranta damunkoma hutu zanshiga aji biyu
kicedai kinzama malama kai alhamdulillah naji dadin wannan batu Allah yasakawa haiydar da gidan aljanna suka amsa da ameen banda gwaggo da iyya wadanda bakinciki kamar zai kashesu shine malam yadauki mairo yabawa dan maikudi sukuma ya aurah wa yayansu yayan talakawa inda ake daka da sussuka yayansu duk sun kode amman itah gatanan jikinta sai sheki kaye kama diyar turawa
aiwannan zaluncine meyasa itah ma bai aurah mata kamar yanda ya aurawa yan uwanta yan karkarar ba saida tacinye danwakenta sarai hartana neman kari hardo yace kizubemata duka mana kisake dorah wani tunda akwai garin tace ah ah baba kadan zata karamun nakusa koshi ai
yace to yakalli halliru jeka kakamo zabbin nan kuda uku yanzu kayanka agyarawa mairo””aikam gwaggo tayi tuma tace wlh baza a yanka kodayabah muda yayan namu suke zuwa ko sauro kataba cewa akama ayanka masu saida wannan tsiyar tazo zakace akamo ayanka mata
kamar yanda ba ayankawa yayan muba babu wacce za a yankamawa dan batafisu zanen takashibah.kowama yarasa”” hardo yakallesu yace saboda kune kuka siyamun zabbin???? kufadaman akwai wanda yabani kwandalarsa””halliru yace baba kama barsu bari inje gidana inkamo mata
yajuya hardo yakirashi bar kayanka kaji halliru Allah yayi maka albarka jeka kakamo man nawa sainaga wanda ya isah yahana a yanka yakallesu dakuke ikirarin yayanku banyanka masubah ina sallar datawuce kowacce guda biyar na aika mata dasu itah mairon nakaimatane???
abundama baku sanibah ni wlh dasunan mairo nasiye su hatta san cen danake kiwo na mairo ne dakudin da mijin ta ya aiko dazaitafi dasune nasiya mata ina mata kiyo yana kaiwa nan tazancensa yashige warsa daki
Aisha……………..gentle
[11:22AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
49
gwaggo da iyya suka hau bakinsu har makota anajinsu dama ansan haka tunda sukaji labarin mairo tadawo sukace yau akwai rikici agidan cen takatanta suke rego yanda gwaggo take tada jijiyoyin wuya
waidan kawai za ayanka zabbi guda uku”mu za ayiwa sanabe ina ruwan mu da mijin tane yabada kudin aimuma munada hakki dasu babu wanda yakoma kansu mairo ma daki tayi shigewarta itah dai tana mamakin wannan kiyayyar dasuke nunawa innarta duk da itah bata nuna jin zafinsu akan komai
kusan ma zaman hakuri take agidan badan haka da tuni masifar su gwaggo tafitar da innah dan gwaggo da iyya kansu hade yake komai tare sukeyi ganin sune masu yaya mata dayawa kuma koda yayansu sunkawo masu abu daki suke shigewa kada inna tagani itadai bata damubah
idan yayansu suka kawo masu turmin atamfa haka za aitayiwa innah habaici waisu sunhaifi yayanda suke kawowa aishiyasa akeson diya mace itah wata daya tasamu amman tasiyar da itah saboda abun duniya bata komawa kansu
itah ma innah dakin tashiga sukaci gaba da gaisawa dayarta duk da suna karkara innah bata damuwa tana nuna kin kulawarta akan yarta duk da wasu sukanyi ko oho da yayansu mata waisu fulani itah kam sam kodanta nafari bata kunyarsa balantana autarta””
halliru yakamo zabbin yayanka matarsa yakaima talatu tanata tura cikinta dayafara fitowa yataimaka mata suka gyara zabbin tasoya su. yasiyo kayan miya akayiwa mairo girki ana magrib yafita saida akai isha i yadawo yadauka yakaiwa mairo saida innah tadauki biyu tabawa gwaggo daya iyya daya tabarma mairo daya
dama mairo bawai kwadayin naman takebah haka tadan tsattakurah tabarta barci takeji saiyanzu takejin gajiyar motah saman gadon bonon inna tayi kwanciyarsa saita fara sana artata wato tunanin haiydar
yau abun yasha banban dana kullum data rufe idonta tahango fuskansa yana murmushi saitaji tsikar jikinta tatashi yarrr wannan kuma bakon al amari dayake shirin faruwa dani na menene””duk yanda taso takauce tunanin amman abun ya faskara gaba daya jikinta yamutu tsabar sha a wace tataso mata
har wani lumshe ido take najin dadi kamar tana kusa dashi ganin tana nema tafita hayyacinta yasa tafara kwararo addu”a saida tasamu natsuwa sannan barci yadauketa”
‘kasim ne kwance saman makeke gadonsa inda tunani yayi masa yawa yau yaje gidansu maryam amman baigantaba duk zamanda yayi ko motsinta baijibah kodai guduna take shiyasa taki fitoa dan tasan zanzo???
yaso yatambayi mom saikuma yaji kunya kada tayi saurin harboshi””bayason kowa yaharboshi harsai yasamu ya kanainaye zuciyarta sannan komai daga baya zaizo dasauki idan har maryam tana sona bazata iyah rabuwa dashi ba saina dasa mata soyayata
idan sukaga nashiga wani hali ina shirin rasa raina aidole suhakurah dan nikam bazan iyah hakurah da itah ba kota halinkaka saina mallaki ma abociya wannna surar yayi murmushi maidan sauti yajawo filo ya rungume””
.Allah yasa aduk inda kike kema kina cikin tunanina yalumshe ido yatafi duniyar masoya tareda annurin zuciyarsa””baijimaba barci yadaukeshi tare da mafarkai masu dadi tare da madubin idanunsa””washe gari da fara a yatashi kaman wanda akaiwa albishir da aljanna
bayan tayi sallar asubah bata kwantaba ganin innah keda aiki tace takawo itah tayi tace ah ah kibarshi kihuta kije kikwanta tace inna na iyah fah kikawo itah tadama masu koko inna tatoya kosai bayan sungama tagyara dakin innah sannan tayi wanka tashirya cikin less ja mairashin baki tayi kyau abunta
bayan takarya takwashe kayan sannan tabuda kayan da tazo dasu tafara rabawa saida tadaukarwa hardo shaddodi kala biyar takalma taki uku innah ma haka game da sarkoki hardo kuma hula guda biyu
Aisha………………..gentle
[11:55AM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
50
Tadaukarwa su gwaggo kala biyu da. sarka daya sai sabulun wanka sunki daya da turare da takalma taki daya dakanta tayi sallama dakinsu takaimasu gwaggo kam sai washe baki take tana cewa angode kaikai wadan nan kaya haka dayawa”” itah dai batace masu cikankubah
haka ta warewa yan dakinsu yayyenta kala daidaiya da takalma sannan tabawa kowane daki na yayansu mata da maza sauran sabulayya da turarukka akayita rarrabawa makota
gida yacika cinjim kowa zuwa yakeyi yin godiya kayan arzikin da aka aika masu. itah dai mairo banda murmushi babu abunda takeyi tasha Albarka kuwa kamar me
hardo kam kamar yazubah ruwa kasa yasha wadanda suka masa arashi har awaje saida yakai masu sabulai da turare suji dadin sake masa arashin suce yasaida yarsa yan nenta har wadanda suke dan nesa da gari sunsamu labarin haka kuwa duk sunzo kowa sai murna yake ganin kayanda tabasu inna harda kukan dadi tayi ganin yanda mairo take harkawa kamar tauraruwa asararin samaniya
saida mutane sukadan rage tace inna banga laraiba tun jiya””innah tayi murmushi aikuwa kina ganinta. yau kinsan tayi aure. watan shara””wata aurah innah???tace lado ta aurah amman banan garin sukebah acen nesa damu suka koma amman nasan datasamu labari zaki ganta
batama rufe bakintaba saiga larai aikuwa tabuga tsalle suka rungume juna suna murna gefen gado tazauna innah fitah tayi tabar masu dakin larai tanata dube dube”” mairo tace mekuma kike dubi haka????
tace yayyarki mana kobaki haihu bane???? tayi murmushi haihuwan lafiya kuma larai yausha har akayi daren balai gari yawaye???? tabdijam kina nufin baki hauhuba kodai magani yake baki dannaji ance yan birni basason haihuwa””
,mairo tayi dariya kinganki ashe haka kika koma larai??ni wlh banason wannan zancen kunya nakeji”” wane irin kunya kuma mairo ke komunan damuke karkara bamajin kunya wlh bakiga yanda muke soyewa da lado ba’bakinta tarufe nidai kada kikoyaman iskanci sukayi dariya
ina dada baku hakuri akan wannan dakuka samu kuyiman afuwa rashin jina dabakuyi jiyabah whatsapp dinane yayi expire
ina matukar godiya akanku dawadanda suke jin dadi damasu zagina duk ina godiya sannan masu cewa inturah masu. yar sadaka ta privt idan nace bazan turaba kuga laifi harma ku gayaman bakar magana”wlh jiya maganarda wasu suka gayaman ta batan rai akan wanne dalili kaishikenan duk abunda kayi bakayi wa wasu daidai
idan zan iyah tambayarku cikinku akwai wanda yake biyana???? ko akwai wanda yataba siyamun data kokuma yabani wani abu????cikinku akwai wanda yasakani????nifah nasaka kaina basakani akayibah. tunkafin infara novel din nan saida nafitarwa kowa da hakkinsa cewa bazanyi sendn ta privt ba. idan mutun zai karanta yakaranta a group idan bazaka karantabah kabarshi ba dole bane ba ra ayine
amman duk da haka bantsiraba shikenan typn din badole bane kowa yana iyah karasa cikon labarin dakansa kuyiman apuwa ina sonku masu son labarin nan hardaku masu zagina ina sonku amman labari yakai karshe wanda yaji zai iyah yakarasa dakansa
Alhamdulillah
Aisha…………………………gentle
[6:50PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [9:58AM, 11/17/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
36
ko kallon inda take baiyibah harsuka kai gida yanayin fkg yabude yafita saida tadan jima amotar sannn itah m tafita zuwa bangarenda akaimata jere dan haiydar cewa yayi baigama gyara gidan ba kuma tunda bazama zasuyi akasar ba basai angyarabah tunda akwai bangare bangare dayawa agidan kuma bakowa
sai agyara mata daya dad yace shikenan badamuwa akai mata jeren ta abangaren yana shiga dakinsa yanufah itah ma tana bayanshi tayi haryan wani daki duk da batasan konata bane
tana turawa taga kayanta tayi murmushi sannan takarasa shiga itah kam kokadan bata damu da abunda haiydar yake mataba saboda wannan kiyayyar itah ce kawai damarta ta boye sirrinta muddin yakamu dasonta to alkadarin sirrinta zai tarwatse
saida tayi wanka sannan takwanta bajimawa barci yadauketa sabanin haiydar dako runtsawa yakasayi aure biyu kuma ciki babu zabinsa yadafe kansa Allah kasawa zuciyata son hameeda kodan gudun abunda zaije yadawo
nasan idan su dad sukasan banasonta akwai matsala kuma ni duk yanda zanyi in tilasta zuciyata tasota itah kuma taki yarda da hakan bansan daliliba agaskiya bankyauta mataba yasauke ajiyan zuciya zangwada inga kozan iyah Allah kasa insota
to haiydar dai ya saduda bari muga kuma yazaman zai kasance””mikewa yayi zuwa dakinta yaturah kofah saiya sameta hartayi barci yadade tsaye akanta sannan yafito yakoma dakinsa yayi alwala yana nafil fili””
cikin dare mom tatashi da nakuda”” dad yakirah mmn su zulai itah ma cikinta yadn taso ba sosaiba tace alhj akirah haiydar muje asiviti mom tariketa tagirgiza mata kai””nakudarce tataso zangu zangu cikin ikon Allah tasuntulo yarta kyakkyawa haiydar sak kamar yayi kaki
saikuma gawata maman zulai tayanke ciki tagyara wajen da yara sannan akakaiwa dad yaga kyautarda Allah yayimasa yakai kallonsa ga agogo jin anfara kiran sallar asubah yamika mata su takwantar saman gado mom tasha tea sannan takwanta
saida gari yawaye yangida sukasan anhaihu”” haiydar ayau yaso barin garin amman yafasa ganin mom tahaihu sundan gaisa takalleshi ina hameeda ne bakuzo tareba??? yayi murmushi barci take mom””
mom tace waikai tunda kakawo maryam bakataba zuwa katambayi ina takebah”” yace maryam kuma wacece maryam mom??? taharareshi matarka mairo mana”” au na manta wlh mom kinsan sha anin biki yace tana ina????
tadauke kallonta daga gareshi tana dakin kasa nakusa dana kursum mikewa yayi yafito zuwa dakin yaturah kofah yashiga tana zaune saman gado tana ganinsa ta kwalalo ido dan binni kaine?? yayi murmushi sannan yakaras saman gadon yazauna nine mana kokinga nasakene????
tayi dariya ah gashi nan naga kayi haske kuma kakara kyau”” ko??? zaman me kike cikin daki kekadai bakisan mom tahaihu bane.. tace dagaske??? kaiyagyada mata”” tace nidai dan binni kamaidani gidan mu”” gabansane yabada rasss wannan yarinya tana shirin ballo liki
Aisha…………………..gentle
[10:37AM, 11/17/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
37
yakalleta saboda meyasa kikeso inmaidaki gida akwai wani abu da akemaki gidan nan ne??? kaita girgiza tasoma hawaye tunda nazofah kullum ina cikin daki daga kwance sai zaune kumani inason zuwa wasa ”wasa kuma haba mezaikaiki wasa da girmanki haka
gaskiya kidaina banaso idan kuma baki dainaba zanje insanarda abba nasaki abu kince bazakiyibah” dan Allah dan binni kayi hakuri nadaina kaji” yayi murmushi shikenan tace ina matar ka dan binni naji maroka suna kiran sunanka sunacewa ango”
yadanji faduwar gaba saikuma yadake yakalleta tashi muje wajen mom kinsan dai nace maki banason yawan surutu ko”tace yihakuri shiya fara fitah sannan tabi bayanshi suka haurah sama dakin mom tana zaune tare da maman zulai suka shiga haiydar yace mom gatanan
mom takalli maman zulai namanta infada maki gatanan. maganarda mukai dake ranar da alhaji “” tasaki fara a shin itah ce wannan “” mom tagyada kai”” tace amman zata iyah kula dayaran nan kuwa?? mom tace ahankali aizata iyah”” takalleta maryam kigaisheta mana dukawa tayi tace mata ina kwana “” ta amsa fuskarta sake
hannun ta har rawa yake tatashi tadauki jaririyar takurah mata ido Allah ya azoma mairo son yara tanaso innar ta tahaihu tadinga goyawa amman tundaga gareta innah batasake haihuwaba takurawa jaririyar ido kamar dan binni””ta ajeta tadauki daya sudai binta kawai suke da kallo tayi murmushi
takalli mom tace wanan tafi kama da dan binni”ko ?? kalleta kigani mom tayi musmushi”” tace wlh dagaske dubaka”” daidai tajuyo inda yake taga yana hararar ta bashiri tasa hannu tarike bakinta”” babu wanda yalurah da kallonda yamata bata sake cewa uffan ba””
yace mom bari indan fitah anan yabarta yakoma bangarensu dakin hameeda yashiga yasameta tayi wanka tana kwalliya tsaye yayi akanta yana kallonta””tawaigo da murmushinta shima saiya mayar mata gabanta ne yabada rasss bata taba tsammanin zai mayar mataba
ahankali yatako inda take tayanda harsuna jiyo nunfashin junansu cikin ido yake kallonta yalumshe ido yabude ahankali yadago habarta yayi kissing labbanta idon ta lumshe sannan tabude yace mrng””
tayi murmushi ina kwana dear”” yadan matsa lafiya qalau ya bakunta”” tayi murmushi ainan gidane banida bakunta”” kaiyagyada”kishirya ga break dinki afalo idan kingama kije kiga mom tahaihu”” tace. to yajuya yafita tabishi da kallo tana murmushi saida tashirya cikin kananun kaya tafita yana zaune cikin falon yana latsa computer yadago kai yakalleta yakawarda kansa””
kujerar kusa dashi tazauna bayan tadauko abun karinta takalleshi bisimillah”” yace naci nawa tundazu yamaida hankalinsa wajen abunda yake saida tagama takwashe kayan sannan takalleshi natafi yace k hartakai kofah kome yatuna yace tsaya ina zuwa”” yakulle computer yace muje ko
tare suka jerah har bangaren mom kamar dama haiydar yasani har amare sunzo kuma dad ma yana nan ganinsu tare bakaramin dadi yayi wa mom ba tasan yanzu haiydar yahakurah yafara son hameeda” mairo datake cen gefen mom tadukarda kanta kamar tayi kuka haka kurum taji tanajin haushin wannan data jera da danbinni
haiydar kusan hankalinsa yana wajen mairo ganin yanda tasunkuyarda kai kamar tayi kuka saiyaji badadi yasan hakan yanada alaka da shigowarsa tare da hameeda kenan yarinyar nan kishi take???tabdi aikuwa akwai sabon aiki itah karama da itah tana kishi””
yayi hanzarin barin kallonta kada yan dakin suhankalto”yagaida dad da sauran yannen sa suma kannen sa suka gaidashi daganan yafita zuwa gidansu fadil gidansu mom kullum cike yake da mutane kamar ana biki kowa yadauki yan biyun bazaiso ajesuba
Aisha………………..gentle
[11:08AM, 11/17/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
38
sati yana zagayowa akai taron suna amman ba a sauyawa yaran sunaba ambarsu da sunansu hassana da husaina”” mairo yanzun tadan sake tana fitowa cikin mutane amman batadaina dari dari dasubah kuma tana kokarin kama bakinta dayawan surutun ta gudun kada dan binni yafadawa abbanta
biki kam yayi masha Allah gwaggo ma tazo dasauran matan family suna zaune adakin mom takurawa mairo datake gefen mom rike da hassana ido suna hada ido taballah mata harara bashiri mairo tadauke kanta
gwaggo tayi tsaki wai wannan yar wacece haka ina kukayi baki yan karkara???? mom takalli gwaggo takalli mairo tayi murmushi ta dafa kanta yatace maman hameeda mekika gani???? tayi tsaki ke aje rayinyar nan kibar dakin nan muna fuka saibin mutane take da kallo mairo ta aje tasauko tana tafiya tana kallon mom tana kallon gwaggo idanunta cike da hawaye tafita
mom bataji dadin abunda gwaggo taimatabah amman yazatayi bataso tanuna damuwarta kada maryam tarainata saida tafita sannan takalleta agakiya maman hameeda banji dadin abunda kikaiwa yarinyar nan ba amanace awajenafa narabota da iyayenta da yan uwanta
agaskiya nibazan dauki wulakanci akantaba zan iyah juran komai amman banda na muzguna mata””gwaggo tagyada kai um lallai maman kursum akan wata banza zakiyi man masifah waimashin metazoyi gidan nan???kula da yarana tabata amsa atakaice
tayi shewa samun wuri “”waisani infika agola da rabon gida” ashema yar rainoce aka kawomaki akanta kike wani tada jijiyoyin wuya”” kada kimanta danfa gidan dan uwanane sainaso zanbar wani yasha inuwar gidan nan itah dai mom batasake cemata uffan ba”” tanata sababi suma sauran matan ido suka bita dashi dansun san hali yanzu zunasa baki zata dawo kansu tayayata gidan
dan itah abundama baikawo kallobah saita maidashi na tashin hankali waidan ma itah ce karama acikinsu da ace itah ce babba wlh datasaka duk ansaki matan duk ranarda suka danyi fada dan babu ranarda zataje gidan batareda anyi fada da itah ba
abun yazamar mata jiki kullum masifah bakinta kociwo bayayi sudai basu koma takantaba sukacigaba da firansu hakan yasake kular da itah tamike tsofaffun muna fukai wato ga mahaukaciya dan nazo gidan ku to ai damar abun bagidan ku bane gidan yan uwana ne kuma kunsan ciki daya bawasa ba zandawo insameku da daidai tawuce fuuuuuuuuuuu kamar kububuwa
suka bita da ido kawai suna jinjina masifah irintata yanzu daga ganin yarinya saita haike da masifah Allah waddaran naka yalalace hakadai aka watse taro mairo bata sake lekowa ko kofar wajebah
bayan kwana uku dasuna duk wani shirye shirye haiydar yagamashi yaujirginsu zaidaga zuwa india yagama shirya kayanshi hameeda tashiga gida tayi sallama da kowa. acen tabarshi wajen dad yayi masa nasiha mairatsa jiki
akan yarike ta amana karyaga yabar kasar inda batada kowa yasamu damar muzguna mata yace insha Allah dad zankiyaye adai tayamu da addu”a yace ai haiydar addu”a muna nan muna tayi maku Allah ya albarkaci aurenku yabaku zuriya dayibah
yace ameeen dad sannan yamike yace zamu wuce yace to Allah yakaiku lfy amman dakun sauka dan Allah kayi kokarin sanar damu yace insha Allah dad yawuce zuwa bangaren mom
Aisha………………gentle
[11:53AM, 11/17/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
39
Zaune yasameta falon kasa tana rike da hassana mairo tana kujera mai zaman mutun daya rike da husaina tana mata wasa””yaduka yagaida mom”ta amsa badai harkun shiryabah???)yace insha Allah mom””takalli mairo tace maryam bakiga haiydar bane sai lokacin takalloshi tace ina kwana batadamu dazai amsabah tamaida hankalinta wajen hussaina yace lfy qalau batareda yakalli inda takebah
mom tace to ajiyar kafa???? sai alokacin yakalli inda mairo take yadauka sutake kallo saiyaga hankalinta baya ma wajensu yamaido da kallonsa wajen mom yace mom nabaki itah” tace haka kafada???yashafo sumar kansa yana murmushi
tace shikenan nikuma nakarba hannu bibbiyu amman fa dasharadi kar insake inji kadawo daga baya kace inbaka”” yayi dariya mai dan sauti sannan yamike mom bari inwuce tace to shikenan Allah yakaiku lfy sai lokacin mairo tadago fuska dasauri takalleshi tafiya zakuyi
kai kawai yagyada mata tace wayyo nima zanbika dan binni”yataka kusa da inda take yaduka yana kallonta har tasoma hawaye yasa yatsansa yagoge mata hawayenta kinsan.fa banason kukan nan kidaina kinji
tashare hawayen nadaina tozaka tafi dani???yace badadewa zanyibah zandawo kinji bakina tare da mom dinabah kuma ga kannen ki nan kiyita daukar abunki kafada ta make””.nidai zanbika””shiru yayi danshi yama kasa abunda zaice mata””
mom tana zaune tana kallonsu yasake kallonta yanzu niban isah ince kiyi abu kiyibah ko????tayi shiru shikenan bari inje insanarda abba kawai tadan turo ido yi hakuri dan binni bazan sakebah kaji”” amman dai batareda wannan matar zakajebah ko???daga mom har haiydar sun gane wacce take nufi
yayi murmushi meyasa bakyaso intafi da itah???tabata fuska nidai kawai banason inganta kusa dakai tana yin maganar taboye fuskanta da hannunta””dashi da mom sukayi dariya yace shikenan bazanje da itah bah kinyarda intafi???? bata bude fuskaba tagyada masa kai”” yace tokimun addu”a
tace Allah yakiyaye hanya”” yace ameeen ameeen “”yamike sannan yakalli mom datake kallonsu yayi mata sallama yafita driver ne yakaisu airport basu dadebah jirginsu yadaga zuwa india”” mairo tayi kewar dan binni kwana biyu
mom tasa. nuradden yasaka mairo islamiyya sannan yasamu maikoya mata lesson gida gashi batasan komaibah yakaita makaranta dakyar yasamu akasakata primary 5 acewarsu batasan komaibah amman cikin ikon Allah dayake tanada kwanya tafara koyan abubuwa
tabangaren mom kuwa tana iyah kokarinta wajen nuna mata abunda bata sanibah hatta girki idan mom zatayi tare suke shiga da mairo””yanzukam mairo an iyah sallah hartakai hizifi biyar sai murna take itah ma ta itah karatu gata dason shiga mutane duk gidajen amare takanje amman basosaiba koshi sai idan mom ta aiketa tareda driver
tsangwama kuwa awajen gwaggo kamar yanzu tafara duk ranarda tazo gidan bazaka sake ganin mairo tsakar gidabah sai tatafi”” haiydar yanayin waya akai akai amman haryanzu baitaba tambayar ina mairo ba duk da yana cike da tunaninta tun ranarda suka rabu harsuka kai india babu abunda yake tunani sai maganar ta
acen bangarensu hameeda kuwa duk wata soyayya haiydar yana nuna mata amman wajen kwanciyane ba wani haske kuma itah tamatsu ta dandani zumarda take son dandana aduk lokacinda taganshi jitake kamar tatashi dakanta tanuna masa zakuwarta akansa idanunta suna kan…………. tana hadiyan yawu amman shi haiydar har yanzu baikawo ranarda zai kusancetabah
idan suna taba wasanninsu. kafin kace me gaba daya hankalin hameeda yatashi kamar wacce takeshan wani abu saidai kawai yarungumeta su kwanta wannan abun yana matukar damunta “” yauma kamar kullum tana zaune saman kujerun dasuke cikin hotel din acikin wata rumfa daga cen gefenta ruwane kwance suna gudu wasu suna wanka aciki saigashi yafito dagashi sai gajeren wando da singlet dinsa fara yayi kyau yayi haske
yau dutyn dare yakeyi tunda yanufo wajen idonta yana kan…………….. sai murmushi take kujeran da take gefenta yazauna yakalleta barka da hutawa”” tace yauwa tashi tayi takoma saman cinyarsa tazauna tayanda zata itah gogar ta kodan sanyi taji
aranta
hannuwansa yasa yarungumo cikinta itama saita dafa hannuwansa “” gefen wuyanta yayi mata kiss talumshe ido tabude inama zaisan abunda nakeso inama zaibani abunda nakeso tunkafin innema agaskiya hakurina yakare yauzanfara amfani da maganin nan dankomai yatafi daidai………………..
Dan Allah masu karatu kuyi hakuri da iyah wannan dakuka samu wlh banda chaji dakyar ma idan zanyi wani anjima amman idan nasamu chaji zakujini idan kuma bansamubah sai gobe idan Allah yasa munadarai da lafiya ina baku hakuriiii pls
Aisha…………………gentle
[6:50PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [11:35PM, 11/20/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
51
Haba yazaki rufeman baki ai gaskiya nafada muda muke sabon shiga mukasan dadin abun kedama kika tsufah kina wani wayancewa nizakiyiwa kirsa””mairo tayi dariya aranta tace dole kam tundake mijinki yasan da zamanki ninawa mijin aidani da banza duk daya ina nakai matsayinda zai kwanta gado daya dani
aini wlh koda hannu na kawai yarika aranar zanyi farinciki nasan bazan taba ganin wannan ranarba saidai amafarki” amman afili cewa tayi nidai kidaina Allah kada su inna suji” larai tace tosujimu mana aidama sunsan ana haka suka aurar damu
kenifah nan dakike ganina wlh ko agaban waye zan iyah rungume lado dariya kamar mairo takai kasa lallai larai tazare haka aure yamaida itah”” itakam binta kawai take da kallo batasan wannan maganar ba kara tura mairo take kogin son haiydar
larai tace tsayanan wlh nalurah kehar yanzu baki shigo birniba muma damuke karkarar munfiki wayewa keyanzufa namiji yafison mace mai soyayya dakuma iya abun kindai gane””
ah ah niban gane komaiba kekikasan abun dan Allah nidai abar wannan firah kamo wata”hmm munfasan irinku mairo amman anbarta saikuma sukai shiru larai tace dan Allah kawata bakizo mana da kayan arzukka ba”mairo tayi mata kallon rashin fahimta menene kuma kayan arzukka????
ta harareta waike mairo haryanzu kina nan ayanda kike””” haba larai aikedince bazakiman magana tayanda zanganebah kinaceman kayan arzukka ina nasansu””shikenan naji bari in maki gwari gwari””‘kayan gyara mutumen “”
nan ma mairo baki ta mere dan itah bata gane komaibah tace idan bazaki fadaba kirike abunki””larai tace saidai na fayyake maki to kayan mata nake nufi”:hakin maye” tsaki mairo tayi kyaji dashi nidai idan bazakiman maganar mutanen arzikibah toki bari
ai wannan idan mutun yazauna dake sati daya saiki maidashi dan iska “””larai sai dariya take ganin yanda mairo take fuskewa kamar batasan dadin abunba”” tace wlh ni dariya kike sakani mairo kuma wlh kedin bakya wasa kina wani wayan ceman
mairo komawa tayi saman gado tayi kwance idanuwanta alumshe haiydar kataimaki rayuwata kadawo hakanan wlh zuciyata tana gab da bugawa akan begenka narasa sukuni dajin dadi idan har bana gani annurin fuskarka
yanda sonka yake yawo cikin jijiyoyin jikina na tabbata jini baya yawo kamar sonka”” banajin akwai safiyarda zata waye har dare yayi batareda nayi tunaninka sama dasau goma ba”” inasonka haiydar nabaka kaina da gangar jikina””wasu zafafan hawaye taji sunabin kumatunta
larai takirah sunan ta tadan razana tafakaici idon larai tagoge hawayen tace yadai kawata???? tace ah ah naga kinyi shirune kuma ainabar maganar ko??? tace keba komai kawai nagaji da zaman ne shiyasa nadan kwanta ya su inna da lado”
tace qalau suke wlh yanzun ma saida nabiya wajen innah kafin inzonan sunadade suna firah saikusan la asar tayiwa mairo sallama
Aisha………………..gentle
[12:54AM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
52
washe garima saida larai tadawo sukasha firah abunsu magana dai biyu saitasaka zancen aure mairo dai shashsharewa kawai takeyi amman kamarma tafi larai shiga shaukin kaunar mijinta kullum inna cikin damawa mairo magani take itah dai kawai karba take tanasha amman tasan baida wani amfani agareta tunda batada miji. amman bayanda ta iyah hakan take karba tasha
babu wanda. zaifuskanci tana cikin damuwa koya kuwa kaso itah kadai tabar damuwar aranta satin ta biyu gida saiga driver yazo daukanta dama tasan zaizo duk tagama kimtsawa kudinda tazo dasu bata taba komaibah ta damkawa innah rabi tabawa hardo dubu talatin
innah tace ah ah itah mezatai da kudi taba hardo yasiyawa mairo wani maraki su gwaggo tabasu dubu biyar biyar sauran dubu goma tabawa yaya halliru. sun hada mata shatara ta arziki nono da kwai.da manshanu sai daddawa da kubewa “”
innah tasake bata wasu kayan tace idan taje tadinga sha tace toh amman itah kam bazata iyah ba aisai mom tadauketa batada kunya but din motarsu saida akacikashi tab da tsaraba tana kuka tabar gidan jitake kaman karta tafi su gwaggo kam ko Allah kiyaye basu matabah banlantana subata ko kanwar naira biyar harbakin motar innah tarakata tana bata hakuri dayi mata nasiha akan tarike mijinta dakyau
tanata sharar hawaye haka driver yatada motar. yan kauyen saidaga mata hannu sukeyi harsuka hautiti driver yafara shallah gudu tun tana hangen sorayen garinsu hartadaina gani tasauke kanta wasu hawaye suka zubo mata shikenan kuma bansan ranarda zansake dawowaba
shiwanda nake zaman danshi bana gabanshi wlh badan karatunabah babu abunda zaisa indawo wannan garin””amman kuma aikinason sa danhaka kidaina damuwar kanki kome zaimaki tunda kinasonsa wani bangare na zuciyartane yasanar da itah hakan””
takuwa yarda dawannan tasaki murmushi ahankali tace inasonka haiydar dina “”balallaine wani yaji meta fadaba idan bakusa kake da itah ba kwanciyarta tayi saman kujera tana tunanin bugun zuciyarta babu jimawa barci yayi awon gaba da itah. bata farkabah har aka kawo kano batasanibah saidai taji tsayuwar motah sannan tafarka
tayi mamakin saurin isowarsu lallai driver yayi gudu sosai dasauri tabude marfin kofar tayi cikingidan dagudu batasan da mutunba saidai kawai taji sunyi karo ido tazaro dasauri tana kallonsa shima din itah yake kallo””tayi masa kyau sosai tace sorry broth””
tagefensa taraba tawuce cikin falon. bata damuda ya amsaba anan tabarshi tsaye yaluntse idonsa sannan yayi tariyan baya. ana kawowa inda suka kaurah saiya rumgume hannuwansa yana murmushi jiyake kaman itah ne ma yarungume
yadade tsaye wajen sannan yajuya yafita”” tanashiga tafada jikin mom tana murna” mom da fara arta mutanen zariya ansha hanya””tace mom inasu hassana ??? mom tayi murmushi sunajinki ainafada masu yauzaki dawo shine suka shige daki wai fushi suke
mairo tayi dariya tadan daga murya””ina kuke yan matana kunsan bazan iyah rayuwa batare dakubah kuyi hakuri kuzo wajen antynku”” ko inyi kuka saita fashe da kuka kamar gaske tsakanin hassana da husaina aka kama rigenge zuwa wajen mairo suna kawowa tachabe guda tadagata sama tasakar mata kiss sannan ta ajeta tadauki dayar itah ma amman saita kasa yimata kiss dankuwa tana masifar kama da ya haiydar dinta
tana kallonta tana lumshe ido bata sararba kawai taji ta manna mata kiss abaki nan take jikin mairo yafara shok haiydar ne take gani amatsayin hassana tarungume hasana tana kuka ba yan biyu ba hatta mom saida tashiga mamaki””
tace lafiyarki kuwa maryam kike kuka”bata dauka falo takebah azatonta tana dakintane itah kadai tashare hawayen mom ina kukan missing din yam matana ne wlh nayi kewarku sosai tasaukarda husaina bari inje inwatsa ruwa mom””
to maryam idan kinfito ga abincinki nan nizan hausama “to kawai tace tayi dakinta saida tawatsa ruwa tayi sallah sannan tafito diner taci abinci mom tahada mata abinci mairai da lafiya
Aisha…………………gentle
[9:49AM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
53
Tana kammalawa saiga driver yana shigowa da kayanta saida yakawosu gaba daya tace yatsaya tadimar masa kwai da mansha nu yanata godiya sauran kayan kuma tayi masu kaso biyar biyu tahadesu waje daya na mom sauran kuma daya gidan su kasim daya na gwaggo daya gidan alhj umar
sannan takirah mom tanuna mata aikam mom dadi taji kamar me ganin maryam tayi hankali hartasan abunda yakamata””tace to yanzu ki aje nasu zuwa gobe idan kinhuta saikije dakank kikai masu tace to mom
haka kuwa akayi washe gari tasakasu amota gidan su kasim tafara zuwa dama tana zuwa gidan amman basosaiba hjy rabi maman kasim bangarenta tanufah tana zaune cikin falo tana ganinta tasaki fara a maraba lale da maryam
saukar yaushe???ta aje kayan hannunta tana dariya wlh jiya nadawo momy ashe kinsan nayi tafiya””ah wlh innah ce tace akiraki shine dana kirah take fadaman kinje ganin gida””ya mutanen gidan “”qalau suke suna gaisheku bari inleka wajen innar sauri nake ga kayan kunan tamike
ah ah hardamu wadan nan kaya kai Allah yasanya alhairi mungode””tamike sannan tashiga bangaren. saratu tagaishe ta sundan taba fira tafito saiga mman kasim da kayan tazo dasu bangaren hjy saratu anan tabarsu sunata godiya tayi bangaren innah
kwance tasameta tana barci da sallama tashiga amman bata tashiba gyalen ta tacire tadauko rob ta gogama hannun ta tana dadda nawa innah kafarta ahankali ahankali cikin barci innah taji ana tausa mata kafa hakan yanayi mata dadi amman tasan babu maiyi mata hakan sai mai rainon. safiya
kodai acikin mafarkine tanaso tatashi amman bataso tatashi tausan yawuceta saita cigaba da barcinta duk da mairo tasan driver jiranta yake batayi yunkurin tashiba cen dajimawa sai innah tafarka aikuwa saitaga mairo
tayi mika sannan tatashi zaune mairo yaushe kika dawo? tace ina wuni dai innah”lfy qalau yar nan shine zakije gida koki sanarda mutane ??? afuwan innah wlh nadauka mom tasanar daku amman kiyi hakuri kodan banje dake bane nasan fa kindade rabonda kishiga mota’tana maganar tana dariya
innah tayi murmushi aikuwa kinfara halin naki amman dagani ansan kinfi kama da wadanda basu shiga motah “”mairo tayi dariya innah bari inwuce gidan baba zanje yanzu saidai ranar weakend zakiganni zanzo inmaki yini””
ainikam dama safiya zata bani ke danafi kowa murna””mairo tana dariya tace nikam bazan iyah kwana daya da mai taribah aisaiki hanani barci tayi maganar daidai takai kofar dakin tace innah saina dawo dadan saurinta tawuce innah tabita da kallo tana murmushi yarinyar nan akwai saurin shiga rai gata batada fitina rayuwarta asaukake
saida ta leka shashin maman kasim mom nina wuce”” to maryam kigaida maman taki zataji tazuwo shikuma daidai yakawo gaban tane yayi dukan uku uku wai wannan wace kaddarace kullum yanason shigowa rayuwata wani mayen kallo yake binta dashi kanta yana kasa taraba tagefensa zata wuce
yayi saurin shan gabanta”” maryam dan Allah kisaurareni tun aranar zuciyata taki yardarmun cewa ke matar aurece
Aisha……………….gentle
[10:29AM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
54
kitaimakaman kisaurareni wlh nakasa gamsar da zuciya tadaina biyanki tunda bakyasona dan Allah maryam kada kisa zuciyata tasha wahala kada kihorani akan rashinki wlh zuciyata zata iyah shiga wani mummunan hali
ahankali yarage tsawonsa yaduka gabanta dasauri taja baya tana girgiza kai”” kasim so nawa zan sanar dakai ni matar aurece ranar ma nafada maka kayi hakuri abunda kawai zan iyah cemaka kenan sannan akullum maganata bazata wuce wannan ba ni matar aurece tayi gaba dadan gudun ta tana kuka yabita ta kallo wasu hawaye yaji sun tsiyayo masa wannna wace irin masiface dama haka zancen yake da a ke cewa duk abunda kayi sai anmaka
kasim yakasance kyakkyawane ajin farko yahadu sosai yanada kyau amakarantarsu yammata suna mutuwar sonsa fiye da kansu yasan gidan su auren zumunci ake masu shiyasa baidamu da yan matabah matsalarshi wulakanci
kome takamar kyanki da cikar dirinki idan kika tunkareshi da maganar soyayya cikin mutane zai diz gaki mata sunsha dukawa agabansa suna rokon soyayyar sa koda ta maganace amman kokallon inda suke bayayi
abokinsa manir yana sanar dashi kadaina yiwa mata haka wlh bakyau ina jiye maka Allah yahoraka ta wannan hanyar”” yayi murmushi idan nace inason watan ne Allah zaikamani dasonta ko??to bama zanso kowace diya maceba
kamanta gidan mu auren zumunci ake mana kaikoba hakaba nibanada ra ayin ganin mace ince inasonta kagane idan ma natashi aure iyayena zanbarwa zabi kaga kuwa bazan wahala asoyayya ba””,manir yayi murmushi naji abokina amman akalla kadaina wulakantasu
nikaina bana jindadin abunda kake masu jiya fa wannan yarinyar har yawu ka tofar mata kuma kasan duk cikin schl din nan tafi kowace mace aji da kyau kuma ga ilimi amman kayi mata haka “”yahura iska ta bakinsa kaga manir mubar wannan maganar tashi muje lab mikewa. sukayi tare suka wuce duk inda suka gilma mata idonsu yana kan kasim
yanisa tareda mikewa yakarkabe guiwarsa lallai yau yayarda da maganar manir gashi kuwa tafaru baitaba tsammanin zaiso wata diya mace aduniya ba wannan kuma wace kadarace mai daci Allah kabani ikon cinye wannan jarabawar ka mallakamun maryam
fasa shiga bangaren su yayi yakoma dakinsa yakwanta babu abunda yake tunani sai maganganun maryam suke masa yawo azuciya””saida taje gidan alh umar takai sannan taje gidan gwagga gabanta sai faduwa yake dantasan haduwarsu bata kyau
dama bata taba zuwa gidan ba saiyau tadauki kayan tashiga ahankali take tafiya kamar wacce kwai yafashewa yanda kirjinta ke bugawa da ace zaifito tili dawasu sun dauka dj akeyi. bakin kofar shiga ta tsaya tadan dafe kirjinta tarufo ido tana addu”a sannan tadanji saukin bugun kirjin tayi shahada tashiga
tanata kwada sallama amman shiru hakan yasa tawuce falon tanacigaba dayin sallama gwaggo ce tasauko tana ganinta ta daure fuska to yar matsiyata meyakawoki gidan nan zaki dameni da kuwwa duk kincikaman gida
mairo kanta yana kasa taduka gwaggo ina wuni muryanta har rawa yake “”tace fy mekikazo yinan kozuwa kikai nima kishafaman mugun talauci irin na iyayenki hawayeni suka tsiyayo mata “”tace kiyi hakuri gwaggo aikoni akayi”tsawa ta daka mata ke rufeman baki munafuka kodai kika aiko kanki ganin wadayi dan inyabeki ko tobari kiji bana kaunar ki banason koda kwayar idona taganki
keni inda inada iko aida tuni. nakadaki kinkoma rugga” mairo kukanta yadan tsananta tasaka gyalenta tatoshe bakinta gwaggo sai surfa mata masifah take tamike zata wuce gwaggo tace ke!!!!!!!
cikin razana tawaigo wakika ajewa wadan nan matsiyatan kayan “”cikin in in na take magana dama dama kayan danazo dasune nakawo maki”” batama karasaba gwaggo takarbe sai akafada maki nima matsiyaciyace kamar iyayenki na rugga wadan da basuda komai sai shanu
ko anfada maki inason kayan barane maza maza kikwashe wannna tsiyar daga falona wlh ko in tattakaki kuma dagayau idan nasake ganin kafarki agidan nan sainaci ubanki shegiyar yarinya mayya kawai dankina ganin kin lashe kurwan yaya da safiya kina ganin nizaki iyah lasar tawane maza dauka kibaceman dagani yar matsiyata
dukawa tayi tadau kayan tafita tana kuka driver yana ganinta yasan dama za a rina dan ko gida yana ganin yanda gwaggon take hantarar ta har agabansu yayi mamaki datace yakawota gidan ta aje kayan sannan tashiga yaja motah saida suka fara tafiya yasoma bata hakuri
maryam hakuri zakiyi itah rayuwa dama tagadi haka amman gwaggo abunda take baidacewa shikenan dan mutun yana karkashin dan uwanta tadauki karantsana ta azamasa nibanga aibunkiba dahar mutun zai tsaneki
Aisha………………….gentle
[11:10AM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
55
Keda abuma baisha maki kaibah waima batare kukeba tana haka inama ace akarkashinta kike ainasan da wulakanci yafi hakama Allah yakyauta kiyita hakuri watarana sai labari dakin samu miji kinyi aurenki aishikenan bazata sake ganinkibah
itah dai mairo batace masa komaibah ganin sunkusa kawowa gida yasa tagoge fuskanta kada mom tagane tayi kuka kotakan kayan batabi ba dasuka kai gida tashige bangarensu cikin falon tasamu mom dayan biyu suna ganinta suka rugo saman jikinta suna murna anty ina kikaje””tace wajen allurah kokunaso mukoma suka ce ah ah mukam tana dariya taja hannunsu suka zauna saman kujerah
mom tanata binta da kallo tace maryam lafiyarki kuwa??? kaita girgiza bakomai mom”haba maryam kada kimaidani karamar yarinya mana menene zaki boyeman bayan naga chanji afuskanki fadaman me gwaggon taimaki?
dan dama mom tasan sai gwaggo kam tayi murmushi wlh fa bakomai mom ahanyane naga wasu suna bara abun tausayi shine nayi kuka ina tausayinsu baki ganibah mom ” tagyada kai um lallai sunada bantausayi amman kinsan karya batayimaki kyau’
shikenan driver ne yayi sallama yashigo da kayan mom kam dama tasan haka tarasa wacce irin tsana hure takeyiwa maryam waidan ma batasan kishiyar yarta bace to idan tasani yazatayi ya aje sannan yafita zatayi magana saiga dad yashigo
yan biyu dagudu sukaje suka fada jikinsa dad oyoyo yadagasu dai dai sannan ya aje mairo tagaidashi sannan tamike zuwa dakinta yabita da kallo yadawoda dubansa wajen mom yace me akayiwa wannan yarinyar???
mom tatabe baki mefa akaimata wanda yawuce kanwarka ” yarinyar nan kayanda tazo dasu daga garinsu tazauna tayi masu kaso biyar nan gidan biyu sauran gidajen duk taje takai masu harda hure waishine zata korota duk da taki fadaman me akamata wai masu bara tagani ahanya suka bata tausayi hartayi kuka
amman tunda naga wadan nan kayan sun dawo nasan akwai abunda tayi mata nibansan abunda maryam tataremata ba bata bataci bata bata sha ballai suturah amman tasa yarinya agaba banda mugayen magan ganu babu abunda takeyiwa wannan yarinya kuma ni wlh sunamun ciwo araina tamkar ni akeyiwa
alhj yadan sausauto da murya haba hjy duk hakurinki ina yake kinsan halinta batunyaubah nina rasa inda tayo gadon wannna bakin halin nata kuma kinsan bahalin kanuna tayi kure yanzun nan zataje tahadaka da innah kuma kinsan sarai yanda innah takesonta fiye damu bata yarda da laifin ta kokadan zata iyah sabawa dakowa idan dai akan hurene dan haka nidai hakuri nake baku
itah maryam tadaina zuwa gidan ta sannan idan tazo gidan nan takomawarta daki harta tafi”mom tamere baki aikaine bakasan hure ba tunranarda take nuna mata kiyaya yarinyar nan dataganta take shigewa daki amman har dakin take binta taci mata mutunci wannan rayuwar har ina ni wlh hakuri na yakusa karewa
alhj yayi ta tausarta yana bata hakuri dankuwa bayaso hure ta fadawa innah hartasan akan wata bare aka cima yarta mutunci abun bazaiyi kyauba saida yaga mom tasauko sannan yace to atashi abani abinci yunwa nakeji tayi murmushi muje ai yana bangarenka tare suka fita zuwa bangaren shi harda yan biyu
akwana tashi babu wuya wajen Allah yanzu gashi har mairo tayi candy anashirin zuwa ss 1 tadada gogewa tayi ja kirjinta ya cicciko kaman yafasa yafito waje idan kakalleta saikayi marmarin sake kallonta. kowanne saurayi yana mutuwar son ta hakan yasa mom tace tarika saka hijabi idan zata fita tasa aka dinka mata hijabai manya””abangaren islamiyya ma tasauka tana karatun littafaine da kuma hadda
tagefe guda soyayya haiydar tazamemata wata halitta atare da itah kusan itah ce rayuwarta zuwa yanzu tagama yarda muddin babu haiydar bazata iyah rayuwabah amman kuma tasakawa kanta dangana tafitarda rai zata sake ganin sama ganin yanzu ko wayarda yakeyi akai akai yadaina yanzu sai ayi wata biyu uku baikirah mom ba kuma itah idan takirashi tajitah akashe
abun itah yasoma damun ta yanzu gashi su kursum harsunada wani cikin amman haiydar haryanzu shiru tarasa wazata yiwa wannan maganar ganin su duk babu wanda yadamu koda darashin zuwan haiydar gidan ne abunda bata sanibah gaba daya ankulle bakinsu dady bazasu tabayin magana akaiba ko itah yawan addu”ar da takeyine shiyasa sihirin baiyi wani tashiri akantaba
tabangaren kasim kuwa haryanzu soyayyar maryam tana nan daram azuciyarsa duk da haryanzu takasa aminta dashi duk yanda yaso yafuskantarda itah sonda yake mata bata gane hakan batama tsayawa balantana taji me zaifada cikin hakan yakoma karo karatu tare da soyayyar maryam aransa kuma yakudiri aniyar daya dawo zai sanarda mom dinsa kome zai faru yafaru danshikam baiyarda maryam tanada aurebah
haiydar anacen indi.a yazama bawan hameeda babu tausayi agareta duk wata bauta sakashi takeyi kuma idan yagama yabiya mata bukatarta fita datake yi yawo kuwa sai abunda yaci gaba watarana saitaje tayi kwana biyuma bata gida…………..
Aisha……………….gentle
[6:50PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [10:50PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
61
Tayi shiru batace komaiba yasake dauketa da mari bamagana nake makibah kifadaman gidan ubanda kikaje tana kuka ni ya haydar banje ko inaba”” rufeman baki yanzu daga ina kike kuma da izinin wakika fitah
kayi hakuri””ke rufeman baki sakarya kawai yakaba kansa haryakai kofah saikuma yatsaya batareda ya waigo yace duk abunda kike kishirya jirgin safe zamubi mukoma cen gabansu inyaso kiji dadin gantalinki yana kaiwa nan yafita
tsaye take sororo awani bangaren taji dadin komawarsu gida kodan tasamu tarabuda alhj hamza amman wannan sabon yanayinda haydar yashiga bata gane masabah harya iyah daukan hannu yamareta
jiki asabule tashiga dakinta tahada kayanta gaba daya kudinta dasuke cikin accaunt wadan da tasama ga alhj hamza taturasu cikin accaunt nata dayake kano duk wani shiri aranar tagamashi takirah wancy tafada mata komai kuma tanaso idan tasamu dama su hade. zata koma wajen boka dan aiki ya warware
koda tagama shiri har dare yayi wanka kawai tayi takwanta sai barci dama tagaji batasan ma dawowar haydar ba saida safe yatashe ta shihar yayi wanka baikalleta ba yace kina bataman lokaci nafada maki jirgin karfe bakwai zamubi gashi saura kwata idan kuma kasar bata ishekibah intafi inbarki
agurguje tawatsa ruwa tashirya sukuku take yakalleta yakawarda kai idan kakalleta kamar wata mumina nan kuwa mugun nufinta yafita yawa suka kwashe kayansu yakulle wajen yakaiwa masu kula da wajen mabudan su””dama asivitn dayake aiki suka bashi wajen dansu ka idarsu harta motarda zaka hau daga asivitin ake baka
karfe bakwai daidai jirginsu yadaga zuwa najeria haydar zuciyarsa fal farinciki kaman yazuba ruwa kasa yasa baisanarda kowa zuwanshiba sai bayan la asar suka sauka yakirah driver yazo airport din yadaukesu tunda suka shigo jirgi dama baisake cemata uffan ba harsuka sauka
driver yana zuwa yazube yana kwasar gaisuwa ranka yadade kayi mana saukar bazata yayi murmushi yana kallon shi haryanzu dai kana nan dasurutunka””aikuwa yallabai aisai abunda yakaru badai yaraguba yadauki kayan yasaka bayan bt abaya tazauna haydar gaba
suna tafiya yana zuba masa surutu yana bashi labarin abunda akayi bayanan shidai murmushi kawai yakeyi suna sauka gida yayi shashensu suka shiga wajen duk yayi kurah kaitsaye dakin sa yanufah itah ma tayi nata dakin ruwa yawatsa koda yafito driver yashigo masu da kayansu yadauki nasa yasaka daki yashirya cikin kananun kaya
bayan yakawo masu kayansu yadauki dunkunan daya karbowa mom yashiga yakaimata takwalawa mairo kirah ta amsa mom assgmnt nakeyi wlh'”inazuwa”ta aje tafito tamika mata dinkinkine aka anso maki wow mom wlh naji dadi
tadauka tayi daki da gudu ta bude kayan tana duddubawa dinkin yayi kyau tadauki wasu riga da siket.na shadda ruwan anta bari insaka wadan nan ingani tasakasu tana juyawa kai wlh telan nan baitabayiman dinkinda yaburgenibah sama da wannan tajuya takalli yanda mazaunanta sukayi dass asiket din
Aisha. Ibraheem
[11:20PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
62
dasauri tafito tana cewa mom kalli yanda dinkin yayimun wlh yayi kyau tana dan juyawa tana nunawa mom”tsaye yayi jikin kofah baki bude yanason yin sallama amman muryansa takasa wacece wannan kamar maryam din sa
ya salam haka takoma daman???wasu yawuni sukazo masa yahadiye mom taganshi amman saita fuske kamar bata ganshibah tasan yashiga wani yanayi dariya tana nema ta kubce mata ganin yanda yasaki baki yana lumshe ido yana budewa
mairo sam bata lurah da mutun ba saida tasake juyowa kamar ance daga kanki tar idanuwansu cikin najuna”‘baisan sanda yasakar mata lallausan murmushiba””wai anya ba mafarki nakeyibah haydar dinane yadawo “”” jitake kaman taruga tarungumeshi tanuna masa yanda take kaunarsa
dayanda tayi kewarsa azuciyarta dadine kamar yakasheta amman afili kuwa saita mere baki takalli mom kinga dinkin ko” gaskiya telan nan yanzu ya iyah dinki tashigewar ta daki tana shiga tayi tsalle tafada saman gado tana murna
wayyo dadi yau Allah yasake nuna mata fuskar masoyinta ba a mafarkibah tama rasa inda zata saka kanta dan murna”sai murmushi takeyi itah dakai””kokadan baiji dadin abunda maryam tayi masaba
yadanji dass aransa kardai yarinyar nan tayi fushi gaskiya nima bankyauta mataba jiki asabule yakaraso cikin falon yazauna mom barka da yamma””tace yauwa saiwani sharewa take yace mom dan Allah kiyi hakuri nasan kina fushi dani amman wlh bayin kaina bane kwata kwata banida niyar barin garin nan tun farko
amman dare daya nawayi gari naji natsani garin nan gaba daya hankalina yakoma india nikaina ina mamakin yanda namanta da kasata kwata kwata plz mom nasan babu wanda zaidamu dani sama dake kuma kinsan halina fiye danikaina dan Allah kiyi hakuri kunsan dai da da mahaifi sai Allah nan take mom ta ware harsuna firah
yace mom taimakaman da ruwa wlh kishi nakeji ta kwalawa mairo kirah ta amsa sannan tazo mom gani””ta kalleta bakiga haydar bane “”tadan tabe baki naganshi mom sannan tadan kalleshi ina wuni””yayi murmushi gaisuwar ma saida akaroka mani tobanaso
kafada takada alamar bata damubah takalli mom gani tace samowa yayanki ruwa batace komaibah tamike yabita da kallo idanuwansa sunakan mazaunanta wani yanayi yakeji ajikinsa sai hadiyan yawu yake agaskiya akwai ni ima awajen cen harya hango kanshi cikin kayan dadin yayi murmushi yalaso busassun labbansa
mom talurah dashi gaba daya hankalinsa yana wajen mairo tafito kichin rike da flat sama ta azo ruwan da lemu da karamin cup”idanuwansa suka sauka kan kirjinta nan take yaji wata sha awa tataso masa yafara lumshe idonsa
suna hada ido taga yana kallonta saita murguda masa baki yayi dan murmushi mai sauti”gabansa ta duka ta ajeye flat din gaba daya saman dukiyar fulaninta suka bayyana daman kayan sun dame da jikinta ya salam wannan yarinya sotake inshiga wani yanayi kamar ma da gayya tasaka rigan tazuba masa lemun tamika masa
kwata kwata baima lurah ba takalleshi taga hankalinsa baya tare dashi taduba taga meyake kallo saitaga yakurawa kirjinta ido wata kunyace takamata
Aisha. Ibraheem
[12:00AM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
63
Da daya hannun tasa tajawo rigan sama sai kuma yaji kunya ganin tagane abunda yake kallo yamika hannu ya karbi lemun har yatsunsu sukadan gogi juna dukansu wani sako yaciyarci zuciyar su ba kamar haydar dayaji wani abu yatsarga masa har cikin kokon ransa
ya kurba lemun idonsa yana kanta mikewa tayi takomawar ta daki yabita da kallo ita dai mom tamaida hankalinta wajen kallon labarai har yagama zamansa na falon mairo bata sake lekowaba ana kiran magrib yatashi yaje yayi alwala yawuce masallaci
acen suka hadu da dad danbaimasan yadawoba sai bayan isha”i suka dawo gida mom harta hada masa abinci.saman diner yahau yaci saida yayi nak. yadawo saman kujerah yazauna yan biyu sunata kallon shi yace kuzo mana hassana ta make kafada husainace kawai taje
yace aikuwa nazo da kayan wasa da sweet ke kawai zanbawa itah ma hassana taruga zuwa inda yake mom sai dariya take masu muhd ne yayi sallama yashigo yabashi hannu suka gaisa bigbroth yanzun nan dad yake ceman kadawo””
eh wlh muhd harka kammala karatun ko?? kusa dashi yazauna eh wlh broth ainajima dadawo wa””k Allah yataimaka sukacigaba da firansu rabi duk akan karatune mairo tana jikin kofar dakin zaune ta kussuwar gambun take kallon haidar
tana murmushi itah dai bakinsa yana matukar burgeta dan karami dashi gashi jajir kamar na mace Allah yayiwa haydar kyau sosai tamkar shiyayi kansa ganin mom tanufo dakinta yasa tayi saurin komawa saman gado tarufe idonta kamar maibarci
mom taleko maryam yaubazakiyi kallo bane kohar kinyi barci?? tadan muskuta kamar barcin take da gaske mom barci nakeji gobe dawuri nakeson zuwa sch”” tace shikenan sannan takoma
haydar yaso sosai maryam tafito idan yana kallonta yana samun natsuwa aransa zuwa goma. muhd yayi masu saida safe yafita bajimawa mom tamike tadauki yanbiyu takaisu daki tayiwa haiydar saida safe tahaye sama
tashi yayi yanufi kofar dakinda take yaturah yashiga saiya sameta tana barci yadade tsaye bakin kofar ahankali yasoma takawa zuwa kandagon yadan duka yakurawa fuskanta ido
gashin idonta zara zara yakwanta saman fuskanta hankalinta kwance baisan sanda ya manna mata kiss akumatubah sannan yamike yafita yarufo mata kofah saida yafita sannan tabude idonta tasafo inda yayiwa kiss ta manna abakinta
tayi murmushi tarungume filo ina sonka hayda dina. inama ace yauka kasance akusa dani wani shauki takeji yana dibanta”tamkar haydar din ne agabanta ta lumshe ido tabude Allah yabarmu tare dakai guy dina barcine mai dadi yadauketa
abangaren haydar kuwa yana zuwa yashigewar sa dakinsa yacire zanen gadonsa yahau kakkaba duk saida yakakkabe kurah yadauko wani zanen yashinfida. sannan yashiga wanka bayan yafito yayi nafila yana mai rokon Allah kada yasha wahala wajen samun hadin kan maryam
agaskiya yana matukar bukatar mace akallah yayi wata biyu baikusanci hameeda ba yama daina sha awar ta kwata kwata amman yau yana ganin surar jikin maryam gaba daya yaji yakasa natsuwa
yadade yana kwararo addu a sannan yashafa yahaye saman gado amman barci kir yaki zomasa sai faman juyi yake duk inda yajuya saiyaga surarta tanayimasa murmushi
Aisha. Ibraheem
[10:01AM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
64
Saikusan asubah barci yadaukeshi da asalatun fari. yafarka yayi alwala yawuce masallaci acen suka hade da fadil bayan haske yafito tare suka fito masallacin fadil yace wai yaushe kasauka amman baka fadaman ba
yayi murmushi jiya wlh amman da yamma ainaganka da nazo sallar magrib kafin in farga harka tafi yagidan ya umma… qalau wlh aikai wlh bakada mutunci yaushe rabon dakaje kagaisheta amman aikana ganin bahaka nakeyibah
haba abokina mantar kawai insha Allah zanzo kada kadamu””saina ganka zan yarda yanzu kadawone nan gaba daya kozaka koma???haba koda nace maka zan koma aizakace nayi hauka kasan dama ni bana ra ayin yin aiki wata kasa bansan dalilinda yasa kawai naji ina sha awar barin kasar nan ba
amman yanzu nadawo jibi insha Allah zankai takarduna idan asivitin da kake aiki nasamu to idan kuma wata daban ne shikenan””k Allah yakaimu amman nidai nafiso kayi asivitin mu wlh tana bukatar kwararrun likitoci kuma nikaina aiki yayi man yawa kaga idan kaje sai muraba indingayi da yamma suwa safe kaikuma da safe zuwa yamma kafin nima inyi aure
yakai masa dukan wasa yana dariya yagoce ah mana kasan innayin aure dole awatse wannan tsarin dannima inrungumi matata yanzu zanyi maka afuwa dankai biyu gareka yauwa mutumina ya maganar mairon ka””fuska yatsuke kaga fadil kada kasake kiran matata mairo maryam ne sunanta
ah tofah ashedai yanzu anfara sonta ” yadan tsaya da tafiya daidai sunkawo kofar gidan su””wlh fadil idan kaga yanda takoma yanzu saikayi mamaki nikaina kasa ganeta nayi jiyafa saida nashiga wani yanayi amman da alama zansha wuya kafin tayarda dani””yayi dan tsaki kuma wlh abokina ina bukace da itah
fadil yadan gyara tsayuwa to ainaga mata biyu kake dasu sai kakai sha awar ka agun dayar kafin wannan tasamu””yadan bata fuska aibazaka gane bane akwai wani abu dabason sanarda kowa wannan sirrinane banajin zan iyah fada kawai dai ni maryam nakeson dandana ni’imar ta
fadil yayi dariya mutumin kaima yanzu kashiga layi kenan’ bahaka bane ina cikin tsarin masu yawan bukata akalla yanzu nayi wata biyu banyiba hakan yasa harnasoma ciwon ciki kuma nasan kome nene tun acen wlh hameeda take garani duk yanda nake bukace da itah saita ce wai itah ta gaji nikuma narasa dalilin gajiyar tunda bawani aiki takeba
amman kuwa taban mamaki haydar ashe wayewar tata batada wani amfani mata yanzu dasuke tarairayar maza”” uhum kaga muje inrakaka gida indawo dan yunwa nakeji ah ah karakani kamar wani karamin yaro jeka abunka saimun hade anjima”” motar driver ce tafito tana bayan mota yahangi farin hijabinta kamar yatsaidasu saikuma yakyale
da fuskanta tana kallonsu sai kawai tadauke kanta gefe saida driver yaganshi y tsaya yallaba barka da safiya yauwa barka ina zuwa haka???yace wlh maryam zankai makaranta”yadan kalli inda take basu take kalloba yayi murmushi yace k adawo lfy yace Allah yasa sannan yawuce haydar yabi motar da kallo
harsuka kule yasauke ajiyan zuciya aransa yace dama mom makaranta tasakata bansanibah.. yamaida kallonsa wajen fadil yace kaganta ko yace naganta amman da alama zatayi daukan kai dama wannan ce kuma kace yar kauyece??yadan harareshi
tozan maka karyane yanzun ne tazama haka kuma wlh fadil duk abunda kasan inaso ajikin diya mace babu abunda tarasa abu dayane rashin ilmin addini bansanibah koyanzu ta iyah karatu dan nasan mom bazata barta hakabah amman duk yanda nake son matata takasance wlh maryam harta zarta tunanina jiyafa wlh kasa barci nayi mutumina sukayi dariya gaba daya anan sukayi sallama fadil yayi gida
Aisha. Ibraheem
[10:41AM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
65
Bangarensu ya nufah ko kallon kofar dakinta baiyibah yawuce nashi yayi wanka yacenja kaya sannan yafita zuwa bangaren mom saman diner yatarar da itah da yanbiyu yagaisheta shima yazauna yafara hadawa kansa abunda zaici tea yafara sha yakalli mom””yace ina bakin get dani da fadil sainaga anwuce da maryam a motah
bata kalleshiba tace ah saikuma akayime??yadanyi murmushi mara sauti jin yarda tayi maganar yace bakomai kawai nayi tambayane”tace tona baka amsa ” yasake kurban tea mom wace karanta takeyine??? tace badamuwar ka bane kasani yayi dan jim har saida gabansa yafadi yadauka zai samu dan sassauci wajen mom tayanda bazaisha wahalaba wajen sawokan maryam
kamar tasan tunanin da yake tace nasan kana tunanin yanda zaka kasance da yata idan kamanta bari intuna maka kada kakus kurah inganka tare da itah gaisuwace bazan hanakubah amman banason kana shisshigemata
yace amma… hannu ta daga masa nasan iyah kace matarkace ko????yanzu kasan dahaka ai tsallakewa kayi kabarta tare da wata matar taka akalla koda saudayane ka iyah tambayar ta amman tunda kake katabacewa ina take???? bar ganin ina sassata maka wannan kam babu shassauci kafita daga idona mikewa tayi taja hannun yanbiyu suka hausama
aje kofin tea din yayi yadafe kansa dayake sarawa lallai ya aikata babban kuskure kuma zaigane kurensa kamar yanda tafada ko ayanzuma yafara gane hakan yanzu yazanyi???? gaba daya sai yaji bayajincin abincin mikewa yayi yadaukarwa hameeda yawuce dan yasan tunjiya bataci komaiba
ahankali yaturah kofar dakinta tana zaune saman gado taci kuka harta gode Allah idanuwanta sunyi sutu sutu yakawarda kansa daga gareta ya aje mata abincin yajuya saida yakai kofah yadan waigo kigama abunda zakiyi kishiga cikin gida za a gyara gidan nan baiji mezata cebah yafita
angyara gidan yayi fes komai anshare an wanke mai datti dakansa yaje kasuwa yasiyo mata kayan abinci da komai nabukata dakinsa yakoma jin barci yana damunsa yadan kwanta kafin la asar koda yafarka har hudu tagota agurguje yayi wanka yayi sallah yashirya yafito falo zaune yasameta
yace kindafa mana abinci?? bata tanka masaba abun yabashi haushi yafita kawai yayi bangaren mom koda yaje bata cikin falon yayi hanyar kichin yasamu abinci yazubo yadawo saman diner yanaci yana danna wayarsa harya gama baiji motsin mom ba yasha ruwa yana shirin fita saigata tashigo ashema bata bangaren tana wajen dad
yadan sosa kai mom ina wuni” tace lafiya qalau haydar aina dauka kayi fushi banga kazo cin abinciba yadanyi dariya ah ah wazaiyi fushi da mamarsa yarki ce kikace inbarmaki kuma nabarta aishikenan
tace kahutama kanka yace hmm ina yan biyu suke bangansu bah”” tazauna saman kujerah wlh suntafi islamiyya da antynsu””dama abunda yakeson ji kenan yasamu waje yazauna suna dan fira da mom yana fada mata maganar fara aikinsa tayi masa fatan alhairi zuwa biyar da zabi saigasu sundawo mairo tana sanye da kayan makarantar ruwan omo hijabinta har kasa
takalleshi ina wuni””yace lfy qalau tamaida kallonta wajen mom tace barka da hutawa mom”tace yauwa maryam ya karatun tace alhamdu lillah mom yau akwai labari wlh ankawo mana wani malami gaskiya yanada tsanani yanzufah yahanamu hausa gaba daya sai labarci
yau yanbiyu sunyi kuren shan duka””mom tay dariya to aisu basu iyabah adan lallabaman yarana husaina tace mom ni yunwa nakeji “”tokucire hijabin idan antynku tashirya saikuci tare dakinta tanufah tace mom baridai indibo masu nibanajin yunwa
saida tacire kayan tasanya nagida sannan tafito bata sake kallon inda haydar yakebah tadibo masu abincin tabasu tayi hanyar dakinta suka bita ta waigo kuje wajen mom tabaku haddata nakeson biyawa kunji kuje anjima zanbaku sweet suka koma husaina kam kuka takama bazataci abincinba
haydar ne ya lallashesu kuci idan kuka gama kuzo muje insiya maku sweet sunata murna sukaci sannan yadaukesu kowacce da hannu daya sunatayiwa mom bye bye tace idan kukasha kuragoman husaina ta make kafada
basu suka dawoba saida akafara kiran magrib yana ajesu yayi masallaci
Aisha. Ibraheem
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [12:51PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
56
Bayan kwana hudu mairo ce zaune cikin falo tan kallo tare da yan biyu mom ce. tazo tazauna tace kallo kukeyine? mairo takalleta eh mom wlh nakagara inga karshen kaset din nan””
mom tace yaushe zakije karbo dunku nanki yaufa sati biyu dakika kai dinkin””tadan bata fuska wlh mom nibanason zuwa wajen mai dinkin nan saiyayi ta jana da surutu wai sona yake kuma nafada mashi inada aure amman yaki yarda””
mom tayi dan jim lallai yakamata tahana mairo fitah tunda har wasu sunfara cewa sunasonta kada haiydar yadawo yaji hakan tasan akwai rigima amman maza da fitina suke duk hijabinda mairo take sakawa bataso tasakawa mairo takunkumi har mutanen gidan sufara. zargin wani abu””
tanisa shikenan bari insa driver ya karbo maki”” tayi murmushi nagode mom yauwa mom dama inaso intambayeki inaso inje wajen innah wlh ranar nayimata alkawarin zandawo””tayi shiru tana kallon mom”” tomeyasa tun ranar baki sanar danibah
saita dauka nifa nahanaki zuwa””yanzu bar wannan kallo kije kishirya idan driver yadawo yakaiki dan na aikeshi kasuwa to tace sannan tamike hanyar kichin tayi mom tace ina kuma zaki kikabi hanyar kichin”” mom zanyiwa inna falfesun hantane naga tana sonshi sosai”” kai kawai tagyada mata
dama tasan mom bata rabo da hanta a firij dan dady bayacin jelof saida hanta haka tadibi yar daidai yanda take bukata ta wanketa saida tanika kayan miyanta daidai yanda take bukata saita soya mai sannan tasaka kayan miyan tadan juyasu tasaka kayan dandano
da kayan kamshi sannan tazubah hantar ciki tarufe”” ta yanka albasa irin yankannan mai fadi tare da karass tawanke tazubah sannan tadan matsa lemun tsami kadan tarufe sannan tayi dakinta
wanka tashiga. bayan tafito tashirya fauda kawai tasaka sai manbaki tasaka kayanta atamfane riga da siket siket din rafa hudu akai masa yayi masifar karban jikinta rigar tayi mata das ajiki takama gashinta tatufke baya yanda kota daura dankwali babu wanda zaigani
tadaura dankwalinta sannan tafito mom tana zaune cikin falo tabita da kallo ganin kyan da tayi tatabbata duk haiydar yaganta saiya gigice amman kuma bazata taba yarda yasamu maryam da saukibah saita nuna masa itah ma tanada gata tunda yaje yamanta da itah ko maganarta bayasonyi
tagyada kai nasan kuka ma saikayi kafin inyarda maryam tasakar maka fuska koda taduba hantar ta nuna tubus sai kamshi yake tashi mom ta kwala mata kirah ta amsa tace idan dayawa kikayi kidan sammo mani”” tace mom zai isah ai tazubawa innah sannan tazuba wa mom tafito takawo mata takoma daki tadauko hijabin ta tasaka aikuwa yan biyu suna gani sukahau kuka sai anje dasu hakan yasa tace tosu dauko hijabinsu suka ruga da gudu mom tace kinga tafiyarki kafin su fito idan sukaje damun innah zasuyi da fitina
Aisha……………….
[2:07PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
57
Tana shirin fita wani kyakkyawan saurayi yayi sallama yashigo cikin fara arsa yana sanye cikin kananun kaya mom tace lala wanake gani kamar muhd”” yayi murmushi nine mom saman daya kujeran falon yazauna saida yaduka sannan yagaishe ta amsa
mutanen turai ankammala karatun kenan?? insha Allah mom kudai tayamu addu”a tace aikasan addu”a dolene yaushe kasauka?? yadanyi murmushi yana kallon inda mairo take dazun nan wlh amman banshigobah bangarena naje nahuta tukun ina yan biyu
daidai shigo warsu husaina tana kuka mom tace lfy kike kuka hassana tace wai bataga ijabintaba ilin nawa shine take kaka”kudai da rigima kuke wlh driver ne yayi sallama yabawa mom sakon zaifita tace tsaya dan Allah kakai maryam wajen innah to yace sannan yafita takalli yan biyun kudauko wani ko intafi
husaina tace nibazaniba itah ma hasana tace tafasa mom tace kije kawai maryam muna gaishesu”‘kokallo inda yake batayibah tace mom saina dawo tana zuwa tashiga mota driver yaja sai gidan yana ajeta tadau kulan bata shiga shashen subah kaitsaye bangaren innah tanufah
tanata kwada sallama amman taji shiru saitace kilanta barci take afalon ma babu kowa saitaji kaman muryan innah tana kiran ruwa adaki dagudunta tashiga dakin tatararda innah bakinta duk yabushe tanata kiran ruwa dasauri tadawo falo tadibo mata ruwa takoma saida tadan dago kanta tabata ruwan aikam tayita kwankwada’
tamaida itah ta kwantar taji jikin innah yayi zafi hijabin ta tacire. tadibo ruwa tasamu wani dan kyalle tasakashi tana daddanawa innah jikinta nan take zafin jikin yasauka”” tadauki rob din tamurza ahannu tana matsa mata kafafuwanta ba jimawa barci yayi awon gaba da itah
sai bayan la asar tafarka har mairo tayi sallah tana zaune tanayi mata fiffita ganin tana zufah ahankali tabude idon ta saitaji kafafuwan sundaina yimata zugi kamar dazu ta kalli mairo tana murmushi tace samun ruwa abuta zanyi alwala tace to sannan tamike zuwa bayi tasaka mata ruwa tazo tarikata har tolet din sannan tafito
saida tagama alwalar takirata tarikata suka dawo falon dakin tashinfida mata sallaya tayi sallah bayan tagama tadauko flat tazubah mata felfesun hantar tabata innah kam saidai flat tazube mata ragowar tacinye
babu wanda yasan innah batada lfy saidare da Alhj auwal yazo gaisheta yasamu mairo””ta gaishe shi saita komawarta falo ya amsa sannan yakalli innah yace wannan kuma wacece?? innah tace wai maryam wlh yar gidan safiyace tadaukota tayi mata rainon yan biyu yace k aikuwa yanzu naga driven gidan yana bakin get yana jiranta
yarinyar akwai kirki aiyau badan Allah yakawo taba dasaidai kutarar da gawata yace subhanallah innah yakike fadar haka?? aidolene dan nan yanzu saboda Allah kanada mata biyu amman arasa wacce zata rika zuwa dakin nan akai akai kunsan halin tsufa yauciwo gobe lafiya
saidai kawai idan sungama abinci suba mai aiki takawoman ina dalili tonidai ko abincin banaso dan ni bayar yunwa bace””yi hakuri innah yanzu menene yafaru??? anan takwashe komai tafada masa yace kiyi hakuri insha Allah zan nemomaki yar aiki tadinga kula dake yayita bata hakuri yadade adakin sannan yatafi
innah takira mairo taje tace kigyara kije driven ku yazo daukarki””‘tace toh mikewa tayi tafita zuwa waje tace idan kaje kacewa mom innah ba lafiya bazan samu damar dawowa yauba bakowa wajen ta yace shikenan maryam
takoma warta ciki innah tace ah ah yakuma kika dawo kokinyi mantuwane kina gudun indauka inkaru dake””
Aisha. Ibraheem
[5:54PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
58
Tayi murmushi ah innah kinsan kuma kayana ba irin nakibane kokin dauka saidai kiyita ajiya”” tasamu waje tazauna”” yanaga kinzauna yanacen yana jiranki “aiyatafi innah nace aiyafada mata bazan dawoba bakida lfy kuma babu kowa wajenki
tanisah kina ganin maman taki zataji dadi naga bataso kiyi nesa da itah nan ma murmushi tayi ai kuma nafada mata dalilina nasan bazata damubah ainan ma gidane nidai innah yimun tatsuniya kinsan fah agida anaman tatsuniya ke gaki bakida ko kayan kallo balantana mutun yadebe kewa””
to bari inmaki wata tatsuniya”” tagyara zama inajinki innah.da kishiya da kishiya uhum innah inajinki taci gaba itah dayan kishiyar ita akeso dayan kuma ba asonta kowacce tanada ya daya”” sai akatara taki maiyawa akabaiwa yarda ba aso akace takai daji akabata igiya duk inda igiyar tatsaya. to anan zata zube takin”” inajinki
tadauki takin nan tafara tafiya saiga hadariya taso yayi bakinkirin hartakai gunda zata zube taki sai akasoma ruwa”taga wani dan madaidaicin gida saita shige”taga wata yar tsohuwa tayi mata sallama tace dan Allah aikoni akayi kawo taki sai ruwa yatareni kozan samu wajen da zanfake yar tsohuwa tace bakomai yarinya ga dakicen ki kwanta
taje daki tayi kwanciyarta sai safe tafarka saiga tsohuwa tazo tagaisheta tace kidauki kwano kije rafi kidibo ruwa duk abunda kika gani arafin kidauko tace toh tadauka tatafi saita samu kayan miya masu yawa bayan tadibo ruwa saita dauko data koma tasamu shinkafah maya ta uku saita samu nama dadai sauran kayan girki takawowa
tsohuwa sai tsohuwar tace toki daura girki tace to tayi abinci tsohuwar tace kidiba kici nima kizuboman duk tayi haka tace kibawa karena kuma tadiba tabashi tace kicika wancen kwanon kirufe kikai bayan dakin nan tayi yanda tsohuwa tace bayan tadawo tsohuwa tace to idan dare yayi zamuyi baki
idan kinji muna magana kada kifito tace toh bayan sun kwanta cen cikin dare saigasu kutub kutub suka kwankwasa kofa suna rera waka kutumbule tasoooo kutumbule tasoooo ga bakinki sun zaka gaisheki””yar tsohuwa tace kutumbule tayi kwana kutunbule tayi kwana aikin duniya ya wahal sheta””sai sukace kutumbu cacca da kudi kutumbu cacca da kuddi suka zube mata kudi masu yawa
sannan suka zagaya bayan gida suka cinye abincin suka tafi washe gari tsohuwa tahada mata dukiyarta tadorata saman doki taci ado maikyau takoma cikin gari tunkafin takai gida labari ya iske dandan sarki nan take ya aikoda fadawa aka nema masa aurenta aikam matarda akaso itah ma tace sai yarta taje tasamo arziki
itama tadau takin nan takama hanya tana kaiwa inda wacce ba aso tazube takin itah ma tazube ganin anfara ruwa saita shiga gidan babuko sallama tana ganin yar tsohuwa tawuceta zuwa daki tayi kwanciyarta dasafe saiga tsohuwa tace tashi kidebo ruwa tace inye kehar kin isah kisani diban ruwa angaya maki ninasabah da wahalane
kedai dakika saba kije kidibo tagama masifarta tatashi taje tadibo ruwa taga kayan miya tadauko komaidai hartayi maya uku saitsohuwa tace kidaura girki tace waike wace irin tsohuwace tunda kika ganni da kayan miya aikinsan abunda zanyi
bayan tagama girkin tazubama kanta taci sannan tazubawa tsohuwar kokoshi batayibah ta hanama karen kuma tsohuwa tace kidiba cikin wancen kwanon kikai bayan gida sannan indare yayi zakiyi baki koda kinjisu kada kifito tace wlh saina fito kunjimin tsohuwa yar bakin ciki
tadibi abincin takai bayan gida dare nayi saigasu sunzo suka fara waka kutumbule taso kutumbule taso ga bakinki sun zaka gaisheki””yar tsohuwa tace kutum bule tayi kwana..takatseta wane irin nayi kwana idona biyu””dariya saida mairo takai kasa harda hawaye tace innah toyasuka kaya amman gaskiya takwabsawa tsohuwar nan
innah tayi murmushi mikewa tayi tafito yartsohuwa takulle gidan ta samarine kyawawa tace haba ga samari kyawawa shegiyar tsohuwa tanaso tayiman bakinciki suka zagata bayan gidan suna firah tana dariya suka cinye abincin sannan suka kwalkwale mata idanu suka tafi
sati daya bata dawoba sai uwarta tabiyo sahu cen nesa tahangota tana dariya tace umm lallai kinsamu dukiya kin manta dani bayan nina maki hanya kika zonan itah yar uwarki data samu takoma gida kekuma kinanan kinyi bulbul abunki kinama ganina sai dariya kikemun saida takai ta isko ta babu ido kuma ta mutu
itah ma nan tafadi ta mutu kunkurus takan kusu dabadan gizoba danayi karya koyanzuma karyar ce nashirya mairo kam tana ta gimtse dariya saida aka gama data fara dariya harda hawaye ai gwai wlh innah gwanda da aka kwal kwale idon
Aisha. Ibraheem
[6:32PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
59
Tace innah karamun wata tace to yar innah tashi tayi tadibo rob ta murza ahannu tafara yimata tausa “”tace wani.saurayine yanada kanwa su kawai iyayensu suka haifa. kullum idan zaije daji saiyace kanwarsa takulle
gida kada tabude saiyayi waka idan yadawo saiyakwankwasa kofah yace bude daki tasallah bude daki nayi dare walakin shirwa yafi namaciji kyawo tasallah dakin daurah kinyi rawa””tace inbude daki amadu in bude daki kadawo saita bude dakin yashiga
ana haka a she wata kurah tagani takuma hadiye yawu akanta saida tabari dare yayi kafin amadu yadawo taje dakin ta kwankwasa bu e yaki da chayya bu e yaki nayi daye wayakin chiywa yafi na ma i i chawo da chayya dakin auya kinyi yawa “”taji shiru
shine taje wajen wani boka tace yabata maganin yamin baki yabata yace idan taje saman hanya komai tagani kada taci tace toh tana cakar tafiya saita gawani nama mai maiko sai kamshi yake tashi tahadiye kwadayinta tawuce
saikuma tadawo tace waya i ayi bali inchinye wannan sannan indoyah da itah tadawo tacinye sannan taje gidan amman yamin bakinta nanan saita koma wajen malamin yasake bata wani washe gari da dare saita koma
tana zuwa tayi waka kamar amadu saita bude mata kofa kurah ta hadiyeta.koda amadu yadawo baisame taba saiya hakikance lallai wani nadam dawane yacinyeta aikam yaje yakwashe duk ruwan garin inda dabbobi keshan ruwa
yana nan zaune bakin hanya saiga zaki yace suzaki suzaki ina za a?? saiyace zani bare kudu shanruwa”yace ruwan barekudu sun kare danaga maci yar leleta dana bashi ruwanai yasha zaki yace banciba wallai banciba tuf kaga abincin shafe tuf kaga abincin rana tuf daga danciki sai tumbinatuf saifa harawar wake tuf
sai amadu yabashi ruwa yasha haka yayi tayi har aka kai kan ku …………rah. sai………….tace……….tana magana saicen tabude ido saitayi dib saboda dadin tausarda mairo take mata ganin tayi barci mairo tayi mata rufah sannan tadauro alwala tayi addu”a tatofa mata itah ma tayi saita kwanta
sai asubah tatasheta sukayi sallah tasake komawa saisafe koda tafarka har ankawo abun kari daga gidan mom saida tayi wanka sannan taci tana ma innah dariya ke innah daga maki tausa sai barci baki karasaman tatsuniyar ba
innah tayi dariya ai wlh idan kinaman tausa wani barci mai dadi yake dibana dama kinji ance barci waka raina yace na kwance””todama inajinsa kuma ga tausa airabona da inyi barci mai dadi harna manta””
tace tonidai innah karasamun tatsuni…. bata rufe bakibah saiga sallamar gwaggo aikam nan take jikin mairo yafara rawa duk tatsure kamar tasaki fitsari awando tana ganinta ta daure fuska””to muna fuka algunguma uwar sanabe nan kuma aka lallabo
mairo kanta yana kasa batace komaibah banda hawaye innah tace ke hure dake dawa??? tace innah dawa nake bayan wannan kidahumar yarinyar tanuna mairo nan take annurin fuskar innah yagushe tace ke dakata banason shakiyyanci mekuma tayi maki daga zuwanki??
idan dai kinzone danki cimata mutunci toga hanya nan koma inda kika fito dama zuwa kikayi ganina tonaji sauki Allah anfana”gwaggo kam baki tasaki ganin inda inna take korarta akanwannna banzar yarinyar
taballawa mairo harara sannan tazauna mairo tamike tafitah innah tace ina kuma zakije maryam zauna abunki idan itah taji bazata iyah zamaba takoma inda tafito cikin dari dari takoma tazauna amman idanunta basu kai wajen gwaggoba suna kasa dan tasan idan suka hada ido akwai tsaraban harara
gwaggo tagaisheda innah ciki ciki take amsawa tayi mamaki sosai abunda innah ko yannen tama bata taba yarda suyi mata fada yaukuma itah takeyi mata fadan um lallai yinin ranardai haka tayishi dukmasu zuwa ganin innah ma sunlurah dahakan saida mairo tayi kwana hudu wajen innah sannan takoma gida dan zata fara zuwa makaranta gobe
Aisha. Ibraheem
[6:57PM, 11/21/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
60
kwance take saman kujerah abun duniya duk yabi yadameta rabon datasa haiydar a idonta yau sati biyu kullum baya dawowa saitayi barci watarana ma acen yake barci kuma koda take tashi saidai taga ya ajemata kudi yayi tafiyarsa
batasan tanason haiydar ba saiyanzu tanaji azuciyarta zata iyah komai akansa tayi sabo da jikinsa fiye da komai yawan tunaninsa datake haryasa tadan soma rama kwana biyu ko kofar hotel din bata fitah ba tana wannan tunanin saiga kiran wayar alhj hamza
kamar bazata daukaba saikuma tadauka takara akunne yace hlo bebyna kina ina kwana biyu najiki shiru???tadan fata fuska kamar yana ganinta inah gida mana ;; yace dan Allah kisameni dakina wlh kwana biyu amatse nake kuma kinsan idan bakebah bana iyah kwanciya dakowa”
tadan mus kuta toganinan zuwa mikewa tayi tayi wanka tashirya tafita sai hotel dinsa kaitsaye dakinsa tanufah bawani tsoro taturah kofa yana zaune cikin falon dagashi sai gajeren wando ba riga. yasaki katon tunbinsa kamar randa
yana ganinta yabude hannuwa alamar tazo saida tayi taku daya biyu saita tsaya chak”” yace lfy kika tsaya babyna. wlh amatse nake kizo kawai mu more rayuwarmu konawa kikeso zan baki kinsan ni kudi ba matsalata bane zo mana
ko motsibatayibah daga inda take ganin batada niyar zuwa yasa ya aje lemunda yakesha yataso zuwa inta take yana shirin rungumarta tamatsa tsaya haka alhj ya isheka haka’dakarfi tayi maganar kabarni dan Allah
inason tarayyarmu ta datse daga yau banason kasake nuna kasanni har abada duk wata tarayya damukayi dakai abaya inaso tazama tarihi tamkarma amafarki mukayita;;yayi mata duban rashin fahimta meyasa zakice haka beby????
kinsan bazan iyah mu”amala dakowaba bayanke banada wata wacce nake kulawa
kidaina wannan maganar idan kudinda nake bakine suka maki kadan zan kara maki wasu yarungumota takwace kanta daga gareshi sannan tagaurah mashi mari natsaneka natsaneka macuci azzalumi wanda baisan darajar aureba
kabataman rayuwa abaya bazana taba yarda kahanani sauran damar datake gabanaba tatubah ada banason mijina shiyasa nake biye maka amman yanzu inson mijina danhaka ina fada maka kafitah hanyata kada kasake nuna kasanni ko ahanya muka hadu kanuna kasanni wlh saina tona maka asiri takoma dagudu tana kuka
anan tabarshi rike da kunci yabita da kallo yashafo inda tamareshi yayi murmushi yarinya bakisan waye alhj hamza ba nikika mara??? wlh saina nuna maki kin aikata babban kuskure bazan taba barinkibah har abada kuma nadau alkawarin sainayin sanadin mutuwar aurenki dakike takama dashi yacije lebe dani kike zancen
yana nan yanakai kawo cikin falon yacika yayi fam yau wlh saiya nunawa hameeda kurenta tabar ganin yazubah mata ido tanayin abunda taga dama. ahankali taturah kofar tashiga cikin sauri taruga tafada jikinsa tana kuka ya haiydar ina sonka meyasa katafi kabarni tureta yayi yawanka mata mari jikake fyuuu fyuuuuu
saida taduke yanunata da yatsa idanun nan sunyi jajir kaman gauta yace gidan ubanwa kikajeee,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,??
Aisha. Ibraheem
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [4:10PM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭 YAR SADAKA!!!💭
66
duk yanda haydar yayi tsammani abun zaizo masa dasauki saiyaga bahaka bane yau tsawon sati biyu dadaworsa amman banda gaisuwa babu abunda yake hadashi da maryam ko kallon arziki bataimasa balantana takaisu ga magana yayi matukar fitah hayyacinsa
gashi bayaso yafada halaka domin yakai iyah makurah wajen sha awa yaudai kam yayankewa kansa shawarar saidai ayita takare shiya gaji yanaso yasan matsayinshi yasan sarai mom bazata taba barinsa da maryam ba yasan tym dinda take zuwa islamiyya
yayi fkng daidai inda zaiganta yanayi yana kallon agogo dayaji mutsi saiya duba bakin get cen bajimawa saigata tazo batasan da mutunba tana kawowa yabude kofar yajawo hannunta tafada saman jikinsa zatayi ihu yasa hannu yarufe mata baki
kada kiman ihu “”tadan bata fuska tomeye haka zaka wani chakumoman jiki”” yace magana zamuyi dake shigo sosai saida tadanja masa rai kamar bazata shigoba tace toka matsa inzauna”” yayi murmushi sannan yamatsa tazauna amman fuskanta bata kallon inda yake glass din motr yarufe tayanda babu wanda zai gansu koyaji mesuke fada
yakalleta yanda tawani dauke kai kamar taga dodo” yasakeyin murmushi maryam nikike gudu ko????shiru tayi batace komaibah yaci gaba nibansan mena tare makibah kwata kwata bakya kulani tsakanina dake sai gaisuwa karfa kimanta ke matatace
taballa masa harar saikuma akayi yaya dan ina matarka yanzu kasan da haka kadaiji abunda mom tace shekaranjiya kada kakuskura tagan mu tare dakai””idanuwansa sun kada sunyi ja itah abun ma saiya bata tsoro yace mom Allah ce ina Allah ya halatamun ke amatsayin matata
dan me ina kallonki kuma ina bukatarki amman amun halin karfi kawai dan ansan banida wanda zai shigarmun itah kam abun ma dariya yabata yanda yake ta masifah tace yanzu kasan da haka ina aikanada mata koka manta matar socefa
nida katafi kabarni anan bansan kowaba bayan kai amman kayi tafiyarka baka taba tunanin wanne hali nake cikiba kuma wanne hali zanshiga shekararka hudu baka kasar nan yanzu mezaka ceman nina hakurah da kai aituni kamar yanda mom tace incireka daka raina dama cen ni bana sonka
cikin kaduwa yadago kai yana kallonta maganarta tayi mummunan firgitashi tamkar faduwar aradu yajita yace maryam da bakinki kike cewa bakyasona akan laifinda na aikata maki wanda bacikin sanina nayi hakanba kinkuwasan hukuncin matarda take gudun mijinta
Allah subhanahu wa ta ala yana cewa acikin suratun nisa”i bismillahir rahmanir rahem
Arrijalu kauwamuna alannisa”i bina fadalallahu ba dahum ala ba adin wabina anfaku min amwalihim fassalihatun kanitatun hafizatin lilgaibi bima hafizallahu. zuwa karshen aya nasan kinsani amman bari infassara miki
bana bukata malam kabarni intafi gida mom tasan yanzu ake tashin mu
yanzu maryam zaki yarda mala”kun rahma su tsine maki???? kin manta da hadisin manzon Allah inda yakecewa
manzon Allah yanacewa iza da a rajulu inmaratahu ila farashiha falam ta atiha la anathal mala ikatu hata tusbiha
idan namiji yakirah matarsa zuwaga shinfidarsa batazomasaba mala iku zasuyita la antarta har gari yawaye haba maryam nasan bazakiso kikasance daidaga cikin subah kituna nifah mijinkine zakiyarda kisabaman akan wani dalili dazaki iyah yafeman
manzon Allah yanacewa laukunta amri ahada am yusjidu li ahadin la amartul mar ata anyusjida lizaujiha
daza a amurci wani yayiwa wani sujada lallai da an umurci mata tayiwa mijinta sujada duk wannan yana nuna kugane munada daraja awajenku baidace mijinki yanada bukata akankiba kidinga guje masa
ta ballah masa harar yanzu kasan da haka??? ina kaika manta dokokina daka take ina matsayin matarka idan kamanta intuna maka “”yasunkuyar da kai amman ainace kiyi hakuri ko????
Aisha. Ibraheem
[4:50PM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
67
Ahakan ake baiwa mutun hakuri yanzu da lalurar kanka tatashi toni bana ra ayinka cikin inuwata danhaka kafita daga rayuwata kamar yanda kasa kafa katake dokokinda aka gindaya maka
na hakkina dayake kanka nima haka zansa kafa intaka naka dokokin kawai danni bakasha wahala wajen aurena ba shiyasa kawofintar dani amman itah daka kashe kudi ainaga hardaukanta kayi kukabar kasar saita fashe dakuka harda sarkewa
gaba daya yaji wani iri jikinsa duk yayi sanyi yace haba maryam yazaki fadi hakan wlh maryam ina sonki fiye dayanda nakeson kaina””banajin akwai wata diya mace dazanso bayanki plz kikarbi kokon barana kuma dan Allah kidaina cewa infita rayuwarki kada kimanta saboda Allah yahadamu tunkafin muzo duniya nayi tattaki har garinku
kisani Allah ya halicceki saboni danine wlh babu wani mahalukinda ya isah yarabani da matata ina sonta kuma yanzu nake da bukatarta yatada motarsa kawai cikin sauri taje bude kofah amman taki buduwa kuka tafashe dashi tana dukansa yabude amman ko ajikinsa yayiwa maigadi hon yabude masa get kawai yahau hanya
ihu take tana kiran mom amman kamarma baijinta duka da yakushi yashashi saiyayi kamarma baijiba batasaniba tabinsama datakeyi tana kara takulo sha awar sane gaba daya baya cikin hayyacinsa kaitsaye bakin wani gida yayi hon maigadi yabude masa yakunna kan motarsa
gidan daka ganinshi sabon gidane yatsayarda motar yafito sannan yazagaya gefenta yabude mata yace fito “wlh nibazan fitobah saikamai dani gida mekakawoni nan inyi maka””baikoma kantaba kawai yadauketa chak yace hakkina zan karba inga kuma wanda zaihanani
ihu takama tana dukan kirjinsa yace yarinya gwandama kibada kai bori yahau dan wlh saina kashe kishina idan baki bari nayi da hankaliba injimaki ciwo tayanda mom din zata gane tabani matata
yana bude kofah yawuce karamin wajene ciki da falo da tolet dakin bakine daman shikawai yagyara yazuba gado da kujeru saboda wannan ranar yayi wannan tanadin kaitsaye daki yanufah da itah tana zillewa ya azata saman gado kawai yafada kanta kuka take tana rokonsa yabarta banaso ya haiydar kayiwa Allah kabarni intafi gida
amman kamar kara turashi takeyi””ganin hijabinta yana takurah masa yacire hijabin yayi cilli dashi yafara aika mata da shakonni tako ina wajen cire riga tace itah batasan haka nanba aikuwa yace wlh koki bari incereta da lalama ko inyagata inyaso kisan abunda zaki fadawa mom
dakyar ya iyah cire rigar aikuwa saida tayage yasa hannu yaballe brezian ta tasaka hannu tadafe nonuwanta wani shegen kallo yakeyiwa kirjinta hannu yasaka yarike hannayenta yayi baya dasu
yadanke yafara tsotsan bakinta babu halinkuka daga nan yakoma kan dukiyar fulaninta kuka kawai take tana rokonsa yatashi nan take tajawo zanen gadon tarufe jikinta taci gaba da kuka tadauka yakyaleta ashe kayanshi ya cire kawai ya yaye zanen yaxuge wandonta
plz ya haydar kada kamun fady banaso kakyaleni shikam goga baisan tanayiba hannunta tasaka tarufe gabanta ganin abunda yake shirin aikatawa haiydar hankalinsa yayi kololuwar tashi jikinsa har rawa yake kamar baitaba ganin macebah
hannayen nata yajaye zuwa sama yarikesu bakinsa yanakan dukiyar madara yanasha da kafafuwansa yasa yabude mata kafafu ahankali yafara shigarta amman ina babu hanyar shiga zafi da radadi susukasaka mairo tafarayi masa Allah ya isah
saikiran mom take ganin idan yamatsa yi ahankali bazai samu hanyaba hakan yasa yadanna dakarfi wata kara tasaki daganan baki yayi shiru haiydar jiyayi duniya yake sama yake ko kasa yake tamkar yana yawo asararin samaniya baitabajin sa cikin ni ima irin wannan ba lallai yayarda mata sunada wata bayya
shikanshi yakasa sanin wani yanayi yake suma yayi kokuma mutuwa dadi kan dadi har kunnensa saida yamotsa yatabbatar wa kansa aduniya babu abunda yafi wannan dadi ko mahaukaci yadandana saiyayi sambatu
mairo baki yamutu sai haweaye kawai dayake fitah ta idonta tsawon awa biyu amman haiydar baisaurara mataba saida yayi sau biyu sannan yabarta gefenta yakoma yakwanta yana lasar baki yana murmushi
yadaga hannunsa sama Allah nagode maka dakayiman kyauta da wannan ni imar hakika wannan kawai ya isheni jindadin duniya Allah nadoge da ni imarka agareni yajuyo fuskarsa tayanda zaiganta haryanzu kuka take amman mara sauti saiyaji tabashi tausayi mikewa yayi yashiga tolet yayi wanka sannan yahada mata ruwa itah ma
yanazuwa yasunkuceta saicikin ruwan zafin wata irin ukubah taji ta kankameshi wayyo zan mutu wlh yau saina fadawa mom macuci kawai ai wannan cutace dan kawai kaga banida gata”” hannu yasaka yarufe mata baki bayason tana furta hakan
saida yagasata sosai sannan yabarta tayi wankan tsarki yafita key dinsa yadauka yafita baifi minti shabiyarba yadawo yatarar bata fitoba yadauki kayanta yakai mata tolet din sannan yafito
Aisha. Ibraheem
[5:45PM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
68
Saida ya kwatanci tagama kimtsawa sannan yakoma ganin bata fitoba yadaukota saman gadon ya ajeta yadauko ruwa da maganin dayazo dasu yabata tasha hardana zazzabi yahada mata
haryanzu batadaina kukaba yakalleta ya kwantarda murya yanzu maryam akan abunda namaki shine kiketa bannar hawayenki??? abun nanfa baharamun bane halat dinane dankuma nanemi hakkina shine zaki dinga kuka harki jawowa kanki zazzabi
maryam nikaina banji dadin abunda naimakibah amman wlh inasonki kada kidauka dan abunda yake jikinki yasaka nafadi hakan kece irin matarda nake mafarkin mallaka bandamubah danke bakyasona nasan ahankali zankoya maki soyayya ta
amman banason kina furta cewa bakyasona wlh raina yanayiman kuna idan naji kinfurta hakan kuma kiyi hakuri akan abunda nayi maki nakasa rike kainane ya nisah bantabayin zinaba kuma bana sha awarta tun ina saurayina shiyasa nayankewa kaina sha wara in kusanceki dan gudun fadawa halaka
amman tunda naga hakan baiyi maki dadibah insha Allah nahakurah bazan sake neman kibah. nayarda da duk abunda Allah yakaddaromani amman kisa aranki idan nashiga wani hali kece shila koda kuwa neman matane bazan bari sha awa ta kashenibah yana fadin hakan yace kitaso in maidaki gida yamike hannunsa tariko
kayi hakuri ya haydar wlh bazanso kashiga wani hali akainabah dani daduk abunda na mallaka mallakinkane jikina da komai nawa nakane menene zan hana maka bayan kuma Allah ya halattamaka shi abunda nakejin tsoro idan mom tagane zatace narainata
tamun magana akanka amman saida nashige maka saita fashe dakuka dawowa yayi yadurkusa yarungumeta yana bubbugata ahankali kada kidamu bazata ganeba kinji aikinsan dubararda zakimata””
tashi muje kinga magriba tayi magungunan dana baki zasu taimaka maki sosai bazata gano mekike cikibah yadagota daga kafadarsa amman takasa hada ido dashi yace plz amman daga yau bazaki sake gudunaba. kaita gyada masa
yayi murmushi sannan inaso dan Allah idan nazo da bukatata maryam kada kigujeni kece kawai madafata ayanzu banason doguwar tambaya ki amince da haka””tayi shiru yace plz maryam kiyarda dani””
shikenan ya haydar amman wlh zafi sosai kamar zan mutu”” yi hakuri bazan sake yimaki dazafiba kinji tashi muje yadauko mata hijabinta tasaka yadauketa har cikin motah haryanzu bata yarda sun hada idobah shikam sai faman murmushi yake yana kallonta
ya ajeta sannan yazagaya yazauna yatada motar maigadi yabude masa get yafita yana tafiya yana kallonta yana murmushi harsuka kai gida yayi fkng yace indaukeki ko tayi maza tace ah ah wlh barni in lallaba idan wani ya gammufah
ahankali take takawa tana cije lebe yafito cikin mota yana kallonta yana murmushi aransa yace dole kijaman aji kinsan abunda kika tanada na ni ima itah hameeda datasan batada wata mamorah ai itah ma take nemana
kai ammanfa ko anci goro ansha bauri na wahala kafin insamu wannan ni imar hartakai bangaren mom taci sa a kuwa tana wajen sallar magrib kawai tashige warta daki tanada alwalarta danhaka tashinfida sallaya tayi sallah
tadauko kur ani tana karatu gabanta sai faduwa yake wace karya zata shirgawa mom tayarda har bayan sallan isha i mom tasauko yayi daidai da zuwan haydar tare take da yanbiyu haydar yagaisheta ta amsa
tace dama kai nake nema haydar tundazu banga maryam ta dawoba lfy hankalina duk ya tashi wlh yadan waro ido kamar ya firgita yace yau meyasa bataje islamiyya dayan biyu bane???? tace wlh sune sukace bazasubah amman maryam bata taba kaiwa iwar hakaba bata dawoba yace mom kuma kindubah dakinta bata nan
tace nadubah kafin magrib amman bangantaba yace tokiduba mana yanzu kota dawo yasamu kujerah yayi zamansa kamar baisan komaiba”” au wato zama zakayi alhalin bangantaba wai wannan wace irin kiyayyace kakeyiwa yarinyar nan
shikenan zauna nibari inje nemanta tunda nitanada mahimmanci agareni””mikewa yayi yihakuri mom kefah kikace indaina shigewa yarki idan natada hankalina kice nafaye zakewa bari induba dakinta idan batanan inje islamiyyar su
tare sukaje dakinta tana zaune tana karatun kur ani saida mom tasauke ajiyan zuciya afili tace maryam ina kika tsaya tadago fuska tana murmushi mom ina malaminda nace maki ankawo mana yahanamu hausa
shine amiran ajinmu tamun magana in karata karatu dan nace tabari malamin yafita ashe yajimu shine yarikemu saida aka fara magrib yasallamemu inata sauri nasan zaki nemeni gashi akwai duhu banlurah da rami gaba naba nafada ciki duk na koje
haydar yakafeta da idanuwa jin yanda ta iyah shero karya nan take ahankali yasaukarda ajiyar zuciya yaso tadago suhada ido amman taki””mom tace ayya Allah yatsare gaba amman kidaina yin abu idan ankafa maku doka kanajina
kikama mutuncin kanki tace insha Allah mom zan kiyaye mom tajuya sannan tawatsa masa harara lafiya kayiwa mutane tsaye wuce daganan yadan sosa kai yanzu kuma laifin me nayi mom dazu kince banma damubah kuma nadamun ana korata yafita tabishi da baya mairo tadaga kai tana kallon bayanshi tayi murmushi
kur aninta ta aje takoma saman gado takwanta duk da zuginda takeji baihanata sakin murmushiba waiyau itah ce takwanta gado daya da haydar kuma ba a mafarrkibah agaskiya wannan itah ce ranar farincikinta bazan taba mantawa da wannan ranabar
Aisha. Ibraheem
[6:28PM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
69
Tasake lumshe ido ina sonka sosai haydar dina tajawo filo ta rungume wani barcine yadauketa duk da tanajin yunwa”” haydar kam baki har kunne duk farinciki ya dabaibayeshi kaman wanda akaiwa albishir da aljanna
mom dai talurah yawan murmushin nashi yayi yawa tace waikai lafiyarka kuwa kanata faman murmushi kaidaya yace mom bakomai wlh yamike bari inshiga gida yau inada dutyn dare fadil bayajin dadi tabishi da to kaitsaye bangarensa yanufah
yasamu hameeda zaune gefenta yazauna yace ina abincina batareda ya kalletaba””tace wanne abincin nikaina kawai nagirka mawa ainaga wajen mom kakeci shiyasa””yayi kwafa kinsanfa nagaji da abunda kikemun yaushe zantule kayan abinci kinbarsu harsun fara lalacewa saidai kawai kidafa indomie kici nikuma ko oho
tokai banda abunka aikasan ban iyah girkibah”” ya mike haka kikaceko kuma bazaki koyawaba dakyau ai jibine meetn din family wlh zan fadawa dad asan yanda za ayi idan gida zaki koma kikoma sai ankoya maki sannan kidawo
nikam wlh banci ribar aurenki ba ankawoman ke fanko sannan kuma komai baki iyah ba baki iyah taray rayar mijibah babu ruwanki da abunda nakeso dawanda banaso kuka tafashe dashi nikake kirah fanko haydar???
ah nace maki fankon ko karya nayi bahakan kikeba dankinga bantabayi maki maganaba wlh ni angama cutata tunfarko kowa aka hadashi da kamilallar mace amman ni aka hadani da watsatstsa wadda tagama yakewa wasu sukaci sannan takawoman ragi wlh anyi hasara
ya isheka haka haydar barganin inasonka zaka fake da wannan kaciman mutunci aikaimadin dan iskanne idan bahakaba ya a kai kagane ni yar iskace alhalin bakataba kusantar wata mace ba bayanni
yayi mata wani mugun kallo nizaki rainawa hankali kada kimantafa ni likitane akwai wani abunda zaki boyeman kidaina ganin laifina wlh natsaneki tun farko akan halinki kuma nasake tabbatarda hakan yakalleta sama da kasa bakida abunda zan gani yanzu yaburgeni ajikinki yayi tsaki fanko kawai
gefenta yaratsa yabarta nan tana kuka harya kimtsa yafito ko kallon inda take baiyibah yafita yadau motarsa yayi hosptl kuka take kamar ranta zaifita wlh yau bazan kwana gidan nanba shi harya isha yakirani fanko tayi daki tajawo gyalenta tayafa hartakai bakin kofar fitah saikuma tayi tsaye zuciyarta tace gaskiyafa yafada kedin fankoce zaki iyah tuna namiji nawa yakwanta dake kafinma kiyi aure????
zaki iyah tuna ciki nawa kika zubar kafin kiyi aure???? kada kiga laifin haydar danya fadi haka cendin ma dakikaga yakyaleki asirine ke dawainiya dashi kuma yanzu yakare shawara daya tunda haryanzu aikinda akaimaki baikuma kamashibah
kilallaba kuzauna lafiya tunkafin yayi maki kishiya”” kinsan sarai babu namijinda zai iyah zama dake dankuwa jikinki yabude tanisa lallaine nikaina bazan iyah kirga namijinda muka kwanta dashiba jiki asabule tayarda gyalen takoma saman kujerah tafada
tadafe kanta tana kuka wayyo ni hameeda yanzu yazanyi idan ma naje gida ince meyakawoni babu wanda yasan abunda nake aikata muddin naje gida nasan za a tursasa haiydar yafadi mena masa idan kuwa yafada kashina yabushe
abunda kawai yafi indinga yimasa girkin koba dadi insamu muzauna lfy rayuwace dai nariga nabata tawa tunda nakasa kai budurcina dakin mijina wanda kuma shine tinkahon duk wata mace dakuma darajarta
taci gaba da kukanta. ganin baida rana tamike zuwa dakinta tayi shirin kwanciya takwanta tunanine fal cikin ranta sai sake sake takeyi yanzu wace hanya yadace inbullo masa baya kwana dani balantana insamu hanyarda za aimasa aiki kamar yanda akai masa shekarun baya
gashi baya wasa da addu”o i akoda yaushe kai idan harbansamu aikin nan yakamashibah akwai aiki ja agabana nalurah kiyayyata kamar yawa take karawa azuciyarsa da wannan tunanin barci yayi awon gaba da itah
har tsawon sati daya haydar baisake neman maryam ba bawai baya bukatabah ah ah kwata kwata taki yardama su hadu balantana tayarda dashi gashi kuma yanada bukata fiye data kwanan baya
yaukam bakin islamiyyar su yatsaya tana fitoba yakirata gabanta sai dukan uku uku yake bata fatan susake maimaita ta ranar amman yazatayi hakan tashiga motar yakulle sannan yajuyo yana fuskan tarta yace haka mukayi dake maryam???
batace komaibah meyasa kikeson wahaldanine duk nabi na susuce kamar wani mahaukaci idan kinsan bazan samubah kisanar dani indebe raina ga mata nan dayawa agari cikin sauri tadago kanta
tana kallonsa yadaga mata girah kwarai kuwa idan kebazaki baniba inje in nema dakudina a clup kudi sun kauda komai”” hannu tasa tarufe masa baki yasakarwa hannun kiss wani irin dadi taji yashiga jininta tasaukarda kanta
yace kinyarda muje tunkafin dare yayi kaita gyada masa amman dan Allah kada kaman da karfi yace nayarda bazanyibah ahanhali zanyi harkema zakiji dadin da nakeji kunyace takamata tarufe fuskanta yana dariya yaja motar suka lolaya
sai gidan sa yayi hon maigadi yabude masa suka wuce yaukam da kafarta ta taka harcikin dakin duk da tanajin tsoro amman itah kanta tanaso jikinsa yadinga gogar nata dan dadinda takeji bama gaskiya bane
Aisha. Ibraheem
[7:38PM, 11/22/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
70
Suna shiga dakin tayi tsayinta bakin kofah saida yadawo yajawo hannunta sauka zauna saman gado yasa hannu yacire hijabin nata sai kamewa take ahankali yafurta mata ni kunyar nan taki tana nema tacutar dani mikewa yayi shima yacire kayan jikinshi yakoma sai gajeren wandon sa kaman kasa tabude tashiga dan kunya
yahaye saman gadonya jawota jikinsa yafara sakar mata kiss cikin salon soyayya yake tafiyar dakomai gaba daya yariketarwa wa mairo da kwakwalwa salon soyayyarsa dabance ahankali yafurta mata akunne plz kisaki jikinki kidinga yimun abunda nake maki kinji
hakan yasa tabiye masa duk da tanajin tsoro sun lulaya duniyar ma aurah yaukam bataji wani zafi sosaibah dan ahankali yamata duk da yaji wajen yagame kamar ma baitaba shigar shibah saida suka gama lubayya nikaina nayi mamaki irin salonda haydar yakeyiwa maryam na soyayya nace um ni Aisha ashedai haydar ya iyah soyayya haka
itah kanta mairon tabani mamaki yanda tasaki jikinta tare sukayi wanka suka kimtsa yana rike da hannunta suka fito yakalleta kinga yanzu aimunyi sauri mom bazata ganeba tayi murmushi kawai
yace ammanfa yau bby kinshayar dani zuma waikema kinji abunda naji kuwa taboye fuskanta tana dariya nidai banaso kaibakajin kunya. yace kunyar me zanji dani da matata yabude mata tashiga sannan yazagaya yashiga akabude masa get saida yafara tafiya yajuyo yana kallonta
agaskiya maryam banga laifin wadan da suke bawa matansu mota ko gida ba idan sukajisu cikin ni ima nikaina nakusa ince nabaki raina gaba daya””itah kam dariya kawai take masa yace waike bakiji abunda naji bane???? kinsan Allah aduniya banga abunda yafishi dadiba shiba sugaba shiba zumabah duk yafisu dandano
nikam nazama shalele wannan kam aisaina manta da mom dina dariya saida tayi hawaye nidai banaso wlh kanasa indinga jinkunyarka”” yadan zaro ido nadaina ina fada maki abunda najine amman tunda bakyaso ambari daidai sunkai gida zata fito yariko mata hannu saida ya manna mata kiss sannan yace tnx dear takwace hannunta tadau jakar makarantar ta tayi cikin gida
mom bata kawo komai arantaba ganin batayi darebah tundaga ranar haydar yasamu wajen hutawarsa kullum daya kwatanci takusa dawowa makaranta zaije yadaukota suje suci soyayyar su yamaidata gida mom kuwa komai bata ganobah
tafiya tayi nisah soyayyar haydar da maryam kamar zasu hadiye kansu kusan ma ince sunzama daya duk wani bugu nazuciyar maryam haydar ne shima haka yahakikance da jin dadin kwanciya da matarsa kwata kwata yamanta da rikichinda zai biyo baya muddin akagane yana tareda itah wace amsa zaibasu kokadan bayason dad yasan maryam matarsace
harzuwa yanzu bayan mom sai fadil babu wanda yasan matarsace maryam kam tagama yarda da haydar tasallama masa kanta da gangarjikinta”” tsayin wata uku dasukayi suna tare babu abunda tasani bayan soyayyar haydar
abangaren kasim kuwa yanacen ingila amman zuciyarsa tunaninsa mafarkinsa suna wajen maryam dinsa yakudiri aniyar sanarda family dinsu yasamu matar aure kuma maryam muddin bazasu yarda ya auretaba yasan yayi bankwana da farinciki har abadah
bangaren muhd ma haka shidai kawai tana burgeshi gata batada hatsaniya yanayiwa kansa fatan samun mata kamarta yanajin sonta aransa amman kokadan baiyi niyar sanarda itah ba ganin yanzu take ss 1
yabarwa zuciyarsa zaici gaba da rainon sonta harta gama scndry aranar zaibata gift tareda tayin soyayyarsa idan yazauna baya tunanin komai sai daddadan muryanta mai matukar taushi akantane yake zuwa bangaren mom hirah dan kawai yaganta
kamar kullum yauma suna zaune dashi da haydar waje daya maryam tana kusa da mom suna kallo suna taba fira
muhd yana satar kallonta saiyaga tana murmushi shima yasakar mata murmushi yadan kalli gefenda haydar yake yalurah da irin kallonda haydar yake mata itah madin saiyaga tana mayarwa haydar murmushi kodai sunason junane???? kenan yarigani furta mata yana sonta?? gabansane yafadi yayi sauri kawarda tunaninsa
anya zanyarda wani yarabani dake maryam ba gaskiya bane nasan bazakiso kowaba bayan ni yasake kallon inda take haryanzu junan susuke kallo nan take yaji wani abu yadaki zuciyarshi mikewa yayi yace mom nizan wuce saida safe tace harzaka tafi yadan kalli inda maryam take suma shisuke kallo yahuro iska tabaki eh mom zanyi wani abune mukwana lfy
yaba haydar hannu suka gaisa saida yasake kallon inda take sannan yafita zuciyarshi tana suya suma basu dadebah mom tayi daki saida yarakata hardaki sukadanyi soyayya sannan yawuce bangarensu washe gari harkarfe tara mairo bata fito ba mom tanata tashinta amman taki tashi
tasake komawa tana tambayarta waike yau lafiya kike kinsanfa zakije sch ammankinyi kwancinki ahankali tace mom wlh banda lafiya””tace kodai yunwace maryam bari inkawo maki abinci kikarya tafita bata jima dafitaba tadawo
Aisha. Ibraheem
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [1:16AM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
71
Dauke da tea da abinci cikin flat ta aje kasa taje saman gadon tajaye bargonda tarufah dashi tariko hannunta zafi taji raurau”” innalillahi maryam tun yaushe bakida lfy amman kikasa sanardani tunyaushe ne bakida lfy
dakyar take magana mom wlh cikin darene zazzabi yataso man ayya sannu kinji bari kici abinci zakisamu sauki tarikota ta kaita tolet. tataimaka mata tawanke bakinta tarikota zuwa bakin gadon tamika mata tea din tasha saida tashanye duka
saizuciyanta takama tashi dagudu tayi hanyar tolet tunkafin takai tafara kela amai shaaaaaa bakakkautawa mom dagudu taje inda take tariketa tanayi mata sannu saida tagama tadaga kai mom tadibo ruwa tabata takuskure bakinta tamaida itah takwantar
takoma tana share wajen bata gamaba wani aman yatasoma mairo tatashi dagudu tashiga tolet tana amai mom hankalinta yatashi ganin yanda jikin maryam yayi sanyi kafin kace me gaba daya takwamtse kamar ba itah ba mom wayarta tadauko ta lalubo nmbr haydar
yana asiviti ringin daya yadauka asalamu alaikum””wa alaikas salam haydar kana ina???yaji muryanta kaman da damuwa yace mom ina hospital wlh meyake faruwa naji muryanki sai a hankali
inafa lfy haydar maryam ba lafiya gashi nan duk ta zube man wlh ni hankalina yatashi dan Allah kazo kada yar mutane tamutu wlh bakaga yanda takomaba kayi maza kuma kazo da kayan aiki dan amai take tayi
gaban haydar ne yafadi jin mom ta ambaci amai yace to ganinan zuwa mom cikin sauri yafito yadauki abun awo allurai da ruwa yafita yanata sauri bakin kofah yahadu da fadil zaishigo office nashi saura kadan ma sudan hade. yace haydar lfy kaketa sauri haka????
wlh fadil maryam ce ba lafiya yanzun nan mom take sanardani dan Allah kakula da marasa lafiya ina zuwa harda dangudu yake hadawa baimajirah mezaicebah fadil yabishi da kallo ganin yanda haydar ya firgice kaman sabuwar hauka yagirgiza kai Allah yasauwake yawuce
gudun da yakeyi kaman zai tashi sama gaba daya bayacikin hayyacinsa yadafe kansa idan. kuwa zarginsa gaskiyane ya shiga uku taya zai sanarda mom kuma dasu dad yasan yana cikin tsaka mai wuya zufah ne yaketo masa. tako ina agaggauce yakai gida yadauki kayansa dasauri yashiga bangaren mom
yasameta cikin falo tanakai kawo yace tana ina tace tana dakinta kaitsaye dakin yanufah kodah yaje tana tolet tana amai dasauri ya aje kayan hannunsa yakarasa inda take yarikota yanayi mata sannu dakyar ta daga kanta yace kingama kaita daga masa
yace sannu taso muje yarikota yakaita saman gadon yace ina zuwa yafita wajen mom yace mom taimakamun da tea dan Allah tace toh dasauri taje tahado tea din tabashi yakoma dakin yamika mata tea din ta girgiza kai ya haydar bazan iyah shaba dakabarshi yace to bari inmaki allurah zakiji sauki yadauko sirinji yaja ruwan allurah yadan rungumotah yayi mata
Aisha. Ibraheem
[8:20AM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
72
Ya kwantar da itah yasaka mata karin ruwa bajimawa barci yadauketa yayi zugum yana kwallonta yama kasa fitah tome zaicewa mom??? mikewa yayi ganin barcinta yayi nisah yafito. dakin jiki asanyaye mom tana ganinshi tataso tana tambayarsa lfy???
yaje saman kujerah yazauna yakalli mom nayi mata allurah nasaka mata karin ruwa aciki nasaka allurar barci data tsaida amai kuma tasamu barci insha Allah koda zata farka zata dawo normal””
takoma tazauna hankalina bazai kwanta ba haydar yarinya tana amai kamar maishigar ciki aidole hankalina yatashi ta kasan ido haydar yake kallonta kirjinsa sai dakan uku uku yake zufah kawai yake karyo masa
tace meyake damuntane???yayi shiru yana dan sosa kai yana kallonta kasa kasa “” ah ah ya ina tambayarka kana wani noke noke idan wani abu yake damun yar mutane kafadamn mana kada yar mutane tamutu da ciwo
kafadaman.. mom aishine.. tace shine me haiydar kafahimtar dani yanaga saizufah kake??? yace mom cikine da itah zaiyi wata uku!!! ciki!!!!! kirjinta tabuga haydar sake fada inji kako aunata sosai cikifah haidar innalillahi wa inna ilaihir rajiun
haydar dan Allah kafadaman gaskiya dagaske kake ko wasa gaba daya haydar yatsure ganin yanda mom hankalinta yatashi sai tsumuiniya yake kamar wanda yayi karya yakasa ko zama daidai mom kuwa tatsureshi da ido
maganafa nake maka.. ah mom cikine wlh innah lillahi wa innah ialaihir rajiun menene yake shirin faruwa wlh bana barinta fitah ko ina a inakuma maryam zata samu ciki” mom kiyi hakuri dan Allah hakuri name haiydar da aurenta na hanaka matarka ace inwayi gari inganta da ciki haba haydar
mom ai..saikuma yayi shiru “aime haiydar???? mom ciki nane mom tazaro ido saura kadan tafado daga saman kujerah jin abunda haydar yafada saita fara tafa hannu yanzu haydar saboda Allah duk yanda nake kafa kafa da yarinyar nan saida ka lallaba kayi mata ciki
haba biri yayi kama da mutun nidama ince rawar kanda kakeyi gidan nan tayi yawa kace kasan sherinda kakeyi kaje ka kalailaye yarinya da dadin baki amman haydar baka kyautamunba kahaifi yaro da cikinka amman yanuna yafika wayo
amman bakomai kanunaman matar kace bazanga laifin maryam ba dan nasan duk aikin kane amman kasani katanadi abunda zaka fadawa dadynka da sauran yan uwanka da kuma matarka da gwaggo wlh babu ruwana awannan tafiya nacire hannu na
yadan shafo zufa mom.. rufeman baki shasha sha kawai kasan rayuwar yarinyar kajefah amatsala muddin gwaggonka tasan wannan lamarin tunfarko daka fadi matar kace nasan duk hatsaniyarda za ayi zatazo dasauki nibabu abunda yadaman dubara tarage taka kuma kaine zakayi jinyar matar ka babu hannuna
yadan sauke ajiyan zuciya mom kiyi hakuri akullum zance banida wanda zai fuskanceni arayuwa sama dake nasan har abada kece maijin tausayina kece kikasan damuwata fiye dakowa kuma kezaki bani mafita akan duk abunda yake damuwata
tayi murmushi idan kuwa hakane meyasa baka sanardani lokacinda zaka aikata wannan aika aikarba nikainakeji da maryam bayan haka aini nafi kowa murnar naganku atare
yanisah wlh mom nakasa rike kainane inacikin mawuyacin haline banason fallasa sirrin gidana kuma inacikin bukata shedan haryanamun huduba azuciyata gudun karna kaiga aikata sabo yasa kawai na nemi maryam amman dan Allah kiyi hakuri
Aisha. Ibraheem
[8:58AM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
78
Hmm kadaina bani hakuri haydar dan bakaman komaiba dakai da matarka ban isah inmaka katanga da itah ba cendin ma danasan kanada bukatarta dana baka matarka yanzun ma gata nan ahannunka amman abunda zan fada maka shine
katanadi amsoshin tambayoyin da alhj zaimaka dakuma gwaggonka kasan duk daren dadewa dole sugane idan adah anboye masu yanzu kuwa ciki shizai bayyana kansa ni karama da hakan tafaru ko maryam zata samu yancin ta nasandai duk tsiya baza ace kasaketabah
amman fah akwai tarin kalubale agabanku dankuwa gwaggo bata kaunar maryam kokusa idn tazo gidan nan bakaga irin abunda take mataba babu ranarda zatazo batareda tasakata kukabah nasan fin hakama idan taji wannan lbr
haydar yadago kai yakalli mom yadan yamutsa fuska meyasa baki taba fadaman hakaba??? wlh ni dagake sai dad kune kawai zan iyah yarda kutaba maryam batareda nayi maganaba bazan dauki cin mutuncin matata ba idan kuwa hakane wlh sai inrama ga yarta nasan labari dole yasameta
ah ah yaushe zakayi haka haydar kasan duk family din nan sunfi sonka saboda kafi sauran hankali dakuma ilimin addini banaso kabata alwalarka kawai kazubama sarautar Allah ido muga yanda zaiyi sama sama sukaji kaman ana magana dasauri yamike zuwa dakin yatarar ruwan harsun kusa karewa gefenta yazauna yadauki kanta yadorah saman cinyarsa yana shafa gashinta ahankali yanayi mata sannu
bata wani jimaba barci yakuma daukarta damacen maganin barcin basakinta yayibah ciwone yatasheta haydar yakurah mata ido yana murmushi ashe nima inada rabon ganin jinini ta dalilinki Allah gwanin iko ta dalilin auren zumunci nagudu ashe arzikinane yayi kirana
yalumshe ido yasake kallonta takara masa kyau amman kuma tadan rame kusan ranar anan yawuni bamaganar komawa wajen aiki mom tayi tayi dashi tunda yacire mata karin ruwan kuma barci take yatafi yace ah ah koda yatafi hankalinsa bazai taba kwanciyaba
dole yasaka ta kyaleshi da akai azahar yaje yayi sallah yadawo ba itah ta farkabah saida yadawo sallar la asar yana zaune gefenta kusadabango yayi baya da kansa yajingina kanta yana saman cinyarsa yakiro hannu wanta amman ba itah yake kalloba yana kallon silin dakin ne
tunani ne fal cikin ransa tana motsawa yadan zaburah yakallota kintashe ahankalita bude idonta suka sauka tar akansa saiga hawaye suna fitah ta idonta “”lafiya kike kuka maryam dakyar ta iyah buda baki ina sonka ya Haydar banaso in mutu inbarka saita fashe da kuka maisauti
tarungumo kugunsa”” plz meyasa zaki fadi hakan insha Allah bazaki mutubah saimun haihu munyi jikoki da yawa keharma mu aurarda jikan kidaina fadar hakan kinanan tare da haidar dinki kinji yayimata kiss agoshi
ya haydar to menene yake damuna????yayi murmushi tashi inyi maki wanka idan kikai sallah kikaci abinci sai in sanar dake kinji tashi yayi daga kan gadon yadauketa sai tolet saida yayi mata brosh yayi mata wanka yadaukota shiya shiryata yasaka mata kaya marasa nauyi yakwantar da itah
inazuwa kalbi ta gyada kanta yasakar mata murmushi sannan yafitah mom tana zaune da yanbiyu suna ganinsa suka taso suna ya haydar yadaukesu yakarasa wajen mom yazauna mom mekike ganin yakamata adafawa wannan yarinyar???
aina dafa mata taliya gatacen da fate kuma nayi mata danta malele kasan sumasu ciki akwai kwadayi shiyasa nayi mata ko asamu abunda zata iyah ci cikinsu yace k mom bari mugani yaje kichin din yadauko yakai mata taliya da faten yakoma yadauko danta malele
yanata yatsinar fuska wannan abu mutun zaici yana shiga ya ajemata kafin ma yayi magana tace wannan zanci cewa da dantamalele yazaro ido wannan fah kalbi tabdi bakyajin zai lalata maki ciki kidaici wannan ko wannan dama dama
tayatsina fuska cikin shagwaba nidai wannan nakeso ya haiydar ah ah dakata kada kiman kuka zanbaki
Aisha. Ibraheem
[4:33PM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
79
Yadauko danta malelen yana bata abaki tanaci daya kalleta tayi murmushi shikam jiyake kaman yayi amai wannan abu zaiyarda yasakawa cikinsa yana bata tanacinyewa saurah kadan tace ya haydar akara yaji..ido yazaro waje yaji kuma kalbina duk wannan dake cikifah
shima cikin shagwaba yayi maganar.. tamarairaice fuska nidai akarah yace bakya tsoron basir ne kinsanfa yaji yanada matukar illah ” to ai ya haydar sau dayane kawai yakwallawa hassana kirah saigata tazo da gudu dama mom ce tahanasu shiga
tace dani yaya yadafa kanta maza kije wajen mom kice nace tabawa anty yaji zata kara tace to tajuya da gudu saiga husaina dani yaya”” yayi murmushi oyah kekuma jeki kisamo mata ruwa tace to itah ma tafita
hassanace tafara bada yajin tayi tsayenta saiga husaina da ruwa tamika masa itah ma tayi tsaye sunata kallon maryam”” mom ce takwalo masu kirah suka fita da gudu yabisu da kallo yana murmushi yaji ta zanbada maiyawa sannan takarasa cinyewa sai suwar yaji takeyi tace bani ruwa insha ya haydar kai ya girgiza mata
abunda yake haifarwa mutane da ciwon zuciya dakuma zafin kirji kenan””idan kaci abu maiyaji kadau ruwah kasha sannan kuma kidaina cin abu maiyaji idan kinajin yunwa shiyake jawo ulcer ina fatar kingane
niban wani ganeba tafada kirjinsa ta lumshe ido yarungumo abarsa saida sukayi tsayin mintuna talatin ahaka sannan yabata ruwa tasha sumadin kadan gudun kartayi amai bakuma tayibah ansamu yatsaya ganin ankusa magrib yace bari intashi inje inyi wanka hannunsa tarike ina zaka kabarni baka fadaman meke damunaba
yadan bude ido au wlh nina manta yakoma yazaune hannunsa yasaka yashafo cikin ta yarada mata akunne ajiyatace kwance cikin nan kishirya rainon bebynmu kunya taji takamata tarufe fuskanta da hannuwa tana murmushi
agefe guda kuma kirjinta sai dukan uku uku yake tasan sarai duk abunda kefaruwa haydar bayaso kowa yasan alakarta dashi toyanzu yakenan gata da cikinsa tasan kulba dade sai komai ya bayyana itah dai tasan tana tsoron fitinar gwaggo data hameeda amman bata shakkar susan cikin hydar ne dan itah tana sonshi
abu daya kawai tasani shine soyayyar haydar bayan wannan duk abunda za a tambayeta bata sanibah yayi murmushi tunanin me kikeyi kalbina????tace bakomai jeka kayi wankanka yace bazanibah saikin budeman fuskanki nagani
um um bazan budeba wlh ni kunya nakeji”shikenan bari inzauna dama bakiso intafi jin yana alamar zaunawa yasa tabude fuskanta amman ta kulle idonta gam tace toh gashi nabude ya haydar yayi murmushi
yadan duka ya sumbaci labbanta sannan yawuce saina dawo kikularmun da kanki dakuma bebyn mu bakunya haryakai falo yana magana suka hada ido da mom yadan sosa kai yana kallon kasa mom tacinye nizanje inyi wanka kafin akirah sallah kai kawai tadaga masa sannan yafita
mairo wani dadine yake ziyar tarta bata taba hango rayuwarta ahakaba da itah da abun sonta hannu tasa tashafo lafaffen cikinta wai yanzu dane acikin nan nima zanzama mama tayi murmushi maidan sauti takoma takwanta sallamar mom taji tashigo da yan biyu aikam takulle idonta dan itah batasan dawanne idoma zata kalli mom ba dan tasan cikine da itah
mom tayi murmushi dama tasan hakan saman kujerah tazauna takirah sunanta murya na rawa ta amsa kada kibata hawayenki kinsan dai abunda kike dauke dashi danhaka banason dogon tunani kikularmun da lafiyar jikana nasan kinajin kunyane akan abunda yafaru
daman ninasan haydar bazai iyah barinkibah duk kuwa dabarata nasan saiya bullo ta inda bazan ganebah keda kanki bazaki kai kanki wajen saba saidai shiyaja ra ayinki dan haka nikidaina jin kunyata ba laifi kuka aikatabah dagake harshi kusan ma ince nice mai laifin dana hanashi matarsa
alhalin kuma halas dinsace yanzu yakikejin jikin naki???? dakyar ta iyah magana mom da sauki”” to Allah yakara sauki kinji yata Allah kuma yaraba lafiya acen kasan makoshinta ta amsa da ameeen
tomezakici anjima???? mom idan da sauran dantamalele shizanci’ ah ah babu amman inada garin masara zantuka maki wani “”ngd mom”bari intashi kisamu kihuta
ina maibaku hakuri sakamakon jina dabakuyiba da safe wlh banda lfy yanzuma hudu kawai nayi kuyi hakuri dasu nagode
Aisha Ibraheeem
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [6:04PM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
75
Kuyi hakuri da kurenda nasamu garin insaka 73 nasaka 78 sorry all
*******************************************
to mom tana fitah mairo tasake rungume filo kai amman naji dadin mom bata dauki abunda zafibah yanzu nasan zanfi samun kulawa agunsa fiye da da jin amfara kiran magrib yasa ta mike duk da haryanzu batajin karfin jikinta
ta dafa bango harban daki tayo alwala tashin fida sallaya tagabatarda sallah bata daga nan ba harsaida akai isha i bajimawa saiga haydar yashigo da saurinsa yayi hanyar dakinta yasameta saman sallaya yasaukarda ajiyan zuciya afili
wlh yanacen hankalinsa yana nan yaduka inda take yajikin kalbina” tadago kai naji sauki saidai wlh bakina banajin dadinsa sosai”zaman dirshan yayi saman kafet din yajawota jikinshi kiyi hakuri yanayine insha Allah zaki dawo normal kinji
yanzu inane kemaki ciwo?? kaita girgiza bako ina amman yunwa nakeji”aidole kiji yunwa kirasa mezaki sakawa cikinki sai wannan abu bari inga idan akwai abinci inbabu inje in nemomaki yana shirin mikewa saiga mom ta kawo mata
mairo sai kokari take tatashi akan cinyarsa amman yasa hannu yadafeta da hannu daya ya amshi abun yace mungode mom da dawainiya damu””tayi murmushi kawai tajuya ai kusan ma saitace tafisu murna da samun wannan cikin sosai tanaso taga jinin danta haydar
bawai danbatada jikabah tunda yayyensa da kanensa duk sun haihu nasa kawai take muradin gani dan batasan irin murnarda zatayibah ranar da akacemata mairo ta haihu Allah yanuna mata wannan rana yan biyu kam sunason zuwa wajen antynsu amman mom tahana saboda haydar yana nan manne da abarsa
mom tana fitah tadan harareshi da wasa kaga nifah banason haka meyasane bakada kunya gaban mom din ma bazakaji kunyabah idan kai bakajin kunyarta aini inaji “”yayi murmushi yaja hancinta harsaida tasaki karar shagwaba ya haydar zafi
yace ohh sorry namanta bakida lafiya tashi inbaki abincin kici yabuda ftl din saiya waro ido menene kuma haka dazufa shikikaci?toni shikawai nake sha awanci shikenan tana rungume cikin jikinsa yana bata ahankali tanaci saura kadan tacinye sukaji ankwan kwasa kofah
haydar yariketa gam yaki sakinta tana kokarin kwacewa yaki sakinta yace shigo aikam takai masa cizo dasauri yasaketa takoma samangado ta kwanta daidai muhd yaturo kofah ba mairo ba hatta haydar saida gabansa yafadi Allah yasoni da wannan yaron yasamemu haka yakenan
yasaki fara a broth kace kana nan kanajinya” afili yafadi haka amman azuciyarsa jiyayi kaman yashake haydar ganin zakewarsa tayi yawa yana nema yayi masa katanga da maryam saman kujerah yazauna suka gaisa da haydar sannan yakalli inda take sister yajikin
tace da sauki””yace to Allah yakara sauki meyake damunta halan yayi maganar yana kallon haydar shima din shiyake kallo aransa yace tokaikuma meyadameka da abunda yake damunta kaidai zuwa kayi ganinta kuma mungode amman afili saiyayi murmushi yana kallon inda take yace maleria ce
yadan kada kai amman dai anyi mata allurah ko wlh duk nashiga damuwa da ciwo nan nata shikanshi baisan sanda hakan yafito bakinshiba””haydar yadan zaro ido jin maganarsa akufule yace anmata
muhd yasan dazuciya haydar yafadi hakan amman baidamubah duk da baiso bakinsa yafurta hakan ba”” tashi yayi yakarasa inda take yaduka kasa kasa yakeyin magana yakamata aje asiviti maryam kada tsiwon nan yacikarfinki naga duk kin rame
aikam haydar wani bakinciki yaji ya tokareshi yataso da sauri zuwa inda muhd din yake kaga menene damuwarka dasaitaje asiviti kaidai zuwa kayi ganinta to mungode kana iyah tafiya fuskar nan tasa kamar an aiko masa da mala ikan mutuwa babu sauran annuri afuskansa
Aisha Ibraheem
[7:16PM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
76
Muhd ya kalleshi da mamaki karara afuskansa bangane infitaba haydar??? akan wanne dalili zakace infitah naga dani dakai duk ganinta mukazoyi dan haka kayi abunda yakawoka inyi abunda yakawoni
cikin daga murya haydar yace malam zakewar takafa tasomayin waya menene ruwanka dahar zakazo kana damun mutane da tambaya mairo kam kuka tafasa masa dasauri yaduka yana tambayarta lfy shima muhd dukawa yayi zairiko hannunta haydar yatureshi baimasan sanda yadaga hannu ya gaurah masa maribah ya nunashi da yatsa kaiii wlh kashiga hankalinka agabana zaka tabata????
muhd yaturo ido cikin mamaki nika marah haydar???? ah din am mareka kaje kafadawa duk ubanda zaka fadama” yazo ya rama maka” hmm balaifin ka bane dan kawai tana karkashin mamanka bashine zai hanani ince inasontaba ada banyi niyar sanarda itah ba saita gama makaranta amman ayanzu nafadi gabanka yajuya wajen da mairo take tanata faman kuka
yace maryam ina sonki kin zama bugun zuciyata bazan taba iyah rayuwa babukeba haydar gaba daya hankalinsa yafita jikinsa jiyakema zai iyah kashe muhd ayanzu yataso masa sai gaurah masa mari yake shikuma bakinsa baidaina cewa ilove u maryam fadi yake da karfi mairo ganin abun yazama fada ta kwalla karah wanda yajawo hankalin mom dagudu tashigo dakin
ganin abunda yake faruwa yasa tayi cikinsu haydar sakeshi wlh menene kukeyi haka kamar mahaukata??? mekuma yahadaku fada” muhd yace mom kyaleshi ya kalli inda haydar yake yanata faman ciccika wlh summa tallahi kaji rantsuwa daya kota halinkaka saina auri maryam!!!!
muzubah dani dakai sainaga wanda zaici nasaran samun zuciyarta yanakaiwa nan dazancensa yawuce fuuuuuuuu haydar ma yabi bayanshi mom ce tajawoshi da karfi kada kakus kurah haydar komawa yayi saman kujerah ya zauna sai kuka
ainikam haydar dariya yabani zafin kishin nashima na dabanne”” cikin fada mom tafara magana haydar meyake damunkane ina iliminka da natsuwarka take zaka tsaya kana fada da dan uwanka???? yadago jajayen idanuwansa yana kallonta mom bakiji meyace ba???? hannuntafa yarika akanmene bazan mareshibah
wlh kadan ma yagani wlh zan iyah kasheshi akan maryam ke shaidace akaina banayarda wani yarabi duk wani abunda nakeso shiharya isah dama batun yaubah naga take takensa ” yiman shiru haydar kakosan kalubalenda yake gabanka wannan fitinarda ka lalube bamusamu munfitah ba zaka jajibo mana wata yakakeso inyi yanzu idan yaje yafadawa mamansa ????
nadauka kasauya daga bakin kishinka ashe yana nan daram to maza kaima kabar dakin nan gashinan kunsaka yarinya saikuka take tanacikin ciwo kuna nema kusakata cikin wata masifah”” amman”banason jinkomai kafitah kawai””
mikewa yayi daga kan kujerar yayi hanyar waje idanuwansa rufe suke baya ganin komai koda yashiga gidah hameeda tana masa magana ko kallonta baiyibah yafada dakinsa yasaka key saman gado yafada yana huci
saida yafitah sannan mom tamatsa wajen mairo ta dafata maryam kidaina kukan nan hakanan dan Allah nasan da muhd yasan akwai aure tsakaninki da haydar bazai taba furta hakanba nima tuni naso ingano hakan agame dashi ganin yanda yake yawan zama gida nan saikuma nakawar
kiyi hakuri wannan abu dakikaga haydar yayi kadan ne wlh lallai nayarda bakaramin so haydar yake makibah nice mahaifiyarsa kuma ninasan halinsa fiye da komai saboda tsananin kishin sa karatu ma baiyarda yaje makaranta daya da yan gidan nan ba islamiyya kanta baguda sukayibah
tun yana yaronsa muddin akasiya masa abun wasa idan haryana mutuwar sonsa to bazai yarda yaga wani da irinshiba idan kuwa yagani to dole wancen yayi hasaran nashi nadauka dayaje karatu india yasauya halinshi ganin baicika damuwa dakomaibah koyanuna zafinsa akan hameeda
saiyau nadada tabbatarda kece kalar matarda haydar yake nema inaso inja hankalinki kikiyaye dayiwa wani magana idan harbashine yayardar makibah wannan fushi dakikaga yayi ba muhd ba harke kanki yashafa dasauri mairo tadago idanuwanta dasuka cika da hawaye tana kallon mom
tagyada kanta kwarai kuwa kekanki saikin fuskanci fushinsa saidai zanyi kokarin ganin baishafi lafiyarkibah kikula sosai””‘kuka mairo ta fashe dashi
Aisha. Ibraheeem
[7:57PM, 11/23/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
77
mom toni menene laifina???? mom tagirgiza kai bakida laifi maryam amman kekike ganin haka dani dake shi haydar bazai taba tunanin hakan ba salon nashi kishin kenan kiyi hakuri nasan kema kina sonsa amman kidinga rufe dakinki kafin yahuce dan nasan wlh saiya dawo kobayan na kwantane kuma idan harya sameki tobansan mezai yankebah
dan baya cikin hayyacinsa”” kiyi hakuri kinji daina kukan nan kinsan ba lafiyane dakebah tashare hawayen ta mom tamike tamata saida safe tafita””tana fitah ta tashi takulle kofan takoma takwanta wani shabon kukane yakubce mata agaskiya itah kam haydar yabata tsoro wannan wanne irin kishine dan uwankama baka raga masaba to idan kuma yaji zancen kasim kumafah hannu tasa tatoshe bakinta
ganin kukanta ya tsananta kada mom taji dama mom itah takeda girki tayi bangaren alhj””haydar tunda yashiga daki yaketa juyi kamar mahaukaci har zufah yake babu abunda idonsa yake ganar masa sai hannunta da muhd yake kokarin tabawa zumbur kamar an mintsineshi ya diro daga saman gado
yabude dakin yafito baidamu da dare yayibah yayi bangaren mom babu maganar sallama dakin mairo yaje yakwankwasa cikin barci taji ana kwankwasa mata kofah tadan motsa tace waye? yace nine haydar kitaso kibudeman harta taso saikuma tatunada maganar mom datace kemafa fushin zai shafeki””
komawa tayi ta zauna jikinta sai rawa yake ya tsananta bugun kofar kamar hauka bazaki taso kibudeman bane????kuka take ya haydar kayi hakuri wlh nibansan komai akaibah dan Allah kada kamun wani abu..
aiyau saikin fadaman menene tsakaninki da wannan dan iskan yaron ganin batada niyar bude kofar yasa yafara bankarta da karfi hartana gyangyadi mairo mikewa tayi tana layi dan kukanda tayi yajawo mata ciwon kai bango tadafa zuwa cikin tolet din kafin takai da kullewa jiri yakwasheta gakuma santsin tayis
tayi luw tafadi Allah yasa ba aciki tafadibah baya tayi tafadi “”nan take numfashinta yadauke mom cikin barci taji kaman ana bankar kofah mikewa tayi dasauri tazare jikinta daga jikin alh ta dauro zani tanufi bangarenta da sauri dandama cikin zullumi ta kwanta tana kawowa haydar yana samun sa ar balla sakatar cikin sauri ya danna dakin kaman kububuwa yayita warar ido cikin dakin baigantaba daidai shigowar mom
fincikoshi tayi ta gaurah masa mari saida yaduke “wai haydar yaushe ka lalace haka kishi haukane????kasan yarinyar nan batada lafiya amman kana nema kasakata cikin matsala wlh idan kasa tsiya saika saketa sai inga karyar kishi
haydar mutuwar tsaye yayi jin furucin mom akansa wlh dayasaki maryam kara tasa bindiga ta harbeshi mom juyawa tayi tana neman maryam amman bata gantaba cen tahango kafarta cikin tolet da sauri takarasa inda take tatallafota dakyar takawota saman gado takoma waje dasauri tadibo ruwa
koda tazo haydar yayi kan maryam yana jijjigata mom tatureshi sannan ta yayyafa mata ruwa taja doguwar ajiyar zuciya tabude idonta saitaga mom tarungumeta tana kuka mom wlh nayi mafarkin ya haydar yazo zai kasheni dan Allah kice yayi hakuri wlh baruwana bansan komaibah
jikinta yayi raurau sai rawar dari takeyi hakoranta suna gabgab mom tace kyaleshi babu abunda zaiyi maki kinji tadago idanuwanta takalleshi yana tsaye haryanzu kamar bishiya ta ballah masa harar kabaceman dagani”jiki asanyaye yajuya yafita
saida mom tasamu tayi barci sannan tafita taja mata kofar dakin yana nan jingine da bango hawayene suketabin kumatunsa tace mekake jirah banace kabaceman da ganibah yanzu saboda Allah haydar bazakaji hakuribah yanzu ga irinta nan idan kuma sokake dan cikin yazube aishikenan
dasauri yadago kai yakalleta tadaure fuska kafita gidan nan kuma Allah idan nasake ganin kafarka saina sassabamaka wuce nace jiki asabule yawuce saida yafita takulle kofar shashenta sannan tayi bangaren dad tana kawowa zaifito yace safiya daga inakike ? naji hayaniya kamar gidan nan
Aisha. Ibraheem
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [6:43AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
97
Kokadan bata bari yagano tana cikin damuwaba tare suka karasa cin. abincin sannan yamike bari ingaida mom kaita daga masa yafito yasamu mom saman diner dayan biyu suna karyawa shima yazauna ya gaisheta ta amsa yan biyu suka gaisheshi ya amsa
yakalli mom waiyau lfy naga kamar ranki abace yace ?? tayi murmushi bakomai haydar ina hameeda??? yadan mere baki nima bansanibah danba gida ta kwanabah watakil takoma gidan su nasan dai duk abunsu yauzasu kai karata tunda yau ake meetn suje su fada wlh babu wanda ya isah yasakani inrabu da maryam
saidai itah tayita zama gidan nasu”” mom tanisah itah harma tamanta dayau ake meetn lallai yau akwai rikici amman bata nuna masaba tace shikenan Allah yakaimu”” mom kinsan kasim yadawo jiya???? Allah ah wlh yakirani da dare suna sauka kace yau meetn harda manyan baki ah wlh bari inje wajen fadil
tace shikenan saika dawo saida yakoma wajen mairo yatarar harta koma barci yadade tare da itah kafin yafito yayi wajen fadin karfe biyu daidai dukkan wani familyn gidan ya hallara kwai da kwarkata harda innah
bayan anbude taro da addu a Alhj auwal yafara yimasu bayani akan abunda yatarasu kamar yanda sukeyi ga zumunci kuma ga warare matsaloli kowa yace babu matsalar data taso wan nan karon
gwaggo tayi saurin karbewa wlh akwai matsala babba bama karamaba gaba daya hankalinsu yakoma kanta alhj auwal yace matsala tame??? tace kafin nan inaso afara turah direbah yadauko maiyiwa safiya raino”” tsitt akai falon alhj auwal yace hure itah kuma daba cikin danginmu takebah menene ruwanta tace aikuwa duk itah ce muna fukar kukalli goshin hameeda yanda tasa akaimata duka haka duk hankalinsu yakoma wajen hameeda data soma zubarda hawaye
kawai yaya kasa adaukota zanfijin dadin gayamuku komai”” alhj yagyada kai ya kalli haydar yace jeka dauko min maiyi maku raino… ah ah kul ka aiki wannan wlh zaice tagudune saidai ka aiki dahir ko muh seen. ya gyda kai ya kalli muh”seen jeka da sauri kadauko mana itah yace toh yamike haydar zuciyarshi sai tafasa takeyi wannan wane tozarcine take nema taimasa
waje yayi jigum kasim kam murna yake dan za a kawota yauyayi niyar warware masu burin ransa muhd ma haka yanada wannan kudirin danharya sanarda mahaifiyarsa cikin minti ashirin suka dawo shine agaba tana bayansa kafin ma tazauna gwaggo tayi kukan kurah ta fige hijabin dayake jikinta fuskanta takauce tana kuka tasa hannu tarufe jikinta kukalla kugani cikine jikinta
kasim kusan suma yayi awajen muhd kam tsaye yamike bakinsa yana rawa ganin abunda idonsa yanuna masa innalillahi wa innah ilaihir rajiun” shine abunda kowa yake fada banda mom dan itah kam bataga abunyiwa sallal lamibah
gwaggo ta danhareta kasa gata nan nema take tabata mana suna daganan tafada masu duk abunda yafaru da abunda mom taimata wajen yayi tsit”alhj auwal yayi gyaran murya yakalleta yarinya hakika yanda nake ganinki da natsuwa da tunani bantaba tsammanin haka daga garekibah duk da nasan halin samari yanzu
ya nisa amman kifadaman waye yamaki wannan cikin saboda musamu mu warware maki matsala yayi shiru yana saurarenta gaba daya hankalin kowa yana kanta itah kawai ake saurare gwaggo ta daka mata tsawa waidan ubanki badake akebah ana tambayarki ubanwaye yamaki ciki
muryar haydar sukaji da karfi yace ciki nane!!!!!!!!!!!!!!!!!!! tashin hankali alhj abubakar baisan sanda yakai tsayeba yakalleshi watt haydar sake maimaitawa inji????? yakallishi kwarai dad cikina ne!!!!!
Aisha. Ibraheeem
[7:08AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
98
Innalillahi wa innah ialihir rajiun shine abunda kowa yake furtawa innah kanta mutuwar zaune tayi tana kallon mairo lallai kuwa dolene haydar ya auri mairo tunda yabata mata rayuwa wannan abun taketa sakawa azuciyarta gwaggo tana tafa hannu tace lallai haydar kace babanzaba kake dukan mun ya akan wannan yar iskar kace tana baka kana danawa shiyasa kadaure mata gindi
alh abubakar komawa yayi yazauna yadafe kansa menene wannan haydar ya aikata da iliminshi da tunaninshi idan sonta yakeyi aidayafada nimai aurah masa itah ne wlh”” muhd kam jiyayi kaman yashake haydar dama yasan nane mata dayake abunda sukeyi kenan amman yacuceni yacuci uwar yayana
kasim kam harda hawaye ganin tabun da haydar yayiwa wacce yafiso sama da komai gwaggo takatse masu tunani yanzu kai haydar da matarka dan matatttar zuciya irin taka kakoma kana biyar mairaino tunda muke adanginmu babu wanda yataba aikata abun kunya tajuya wajen mairo kekuma kinji kunyar duniya saurah ta lahirah kuma Alllah bazaki haife mana wannan cikin gidan nan ba mairo kuka take kamar ranta zaifita haydar mikewa yayi yafara takawa zuwa inda take hankalin kowa yakoma kansa yatsuguna kusa da itah yadago kanta
suka hada ido yasakar mata murmushi kidaina kuka kinji nafi ganin kyanki idan kina dariya yasa dan yatsansa yagoge mata hawaye yace pls kidaina bannar hawayenki abanza wlh kukanki yana bataman rai yajawota jikinsa yana lallashi gaba daya kowa suyake kallo baki bude iskancin nasuma haryakai haka itah kam mom murmushi take dankuwa haydar yayi mata daidai
gwaggo tahau tafa hannu laha ilah menake shirin gani haydar da hankalinka gaban iyyayenka da kakarka kake wannan iskancin tunkanayi aboye yanzu abunda kayi ma kadai bai ishekaba kayi mata cikin shege …. bata karasaba yafara magana wai mekike nufi nine shegen ko???? kinata cewa cikin shege kenan nine shegen dan wannan kam dan halas ne wlh
kundun ubanka gidan ubanwa yazama halas yace matata ce ido hameeda tazaro da sauri hawayenta sukacigaba da zuba dasauri dasauri gaba daya suka hada baki matarka???? gwaggo tace gidan ubanwa tazama matarka fadaman nidai bansan sanda aka daurah maka aure da itah ba shidai baice komaibah sai bubbugan bayanta yake alamar lallashi. alhj auwal ya kalleshi yakirah sunan sa ya amsa yace kawarware mana kai haydar kace ciki nakane kuma matar kace alhalin mudai bamusan sanda akadaurah maka aure da itah ba
yayi minti biyu ahaka sannan yagyara zaman sa yana fuskantarsu hannunsa yana rike da hannunta yanisah ina farawa da neman afuwarku akan abunda zan fada watakil yayi maku dadi watakil sabanin haka”yanisah yadaga fuska yakalli mom””datake murmushi yace abunda yafaru babu wanda yasani daga mom sai fadil sune kawai sukasan komai sukasan maryam matatace
lokacinda kuka yanke hukuncin hadani aure da hameeda agaskiya banasonta!!! hameedace tadago da sauri tana kallonsa baidamubah yacigaba dalili kuwa halinta sam ni baiyimunn bah duk da tana yar uwata amman batada dabi un da nakeso matarda zan aureh ace tanadashi karamar maganamah sallah kanta bata dami hameeda ba
taya kuke ganin zata iyah yiwa yarana tarbiyya!??? duk da haka banfadawa kowa banasontabah sai mom da fadil sune suketa tausata akan inyi hakuri indau kaddara danni amatsayin mummunan kaddara nadauki wannan auren tunda akasaka ranar bikin mu sai hameeda takoyi dabi ar zuwa dakina kuma batayin sallama datazo zata fadaman saman jikina
Aisha. Ibraheem
[7:37AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
99
Wannan abun yana konaman rai nayita mata nasiha amman kamar kara turata nake wannan dalilin yasaka nasanarda mom zansameku infada maku banasonta amman mom tahanani nace to agaskiya bazan iyah cigaba da zama anan garin ba dan mundun hameeda bazata daina shigarmun dakibah wlh zanmata rashin mutunci nafada mata komai take nema tajirah tukun adaurah aure zamanta adakina hadarine gareni amman takiji shine momtasanarda dad zanje katsina wajen gwaggo na
alhalin kuma bacen zanjebah natambayi fadil yafadaman sunan wani kauye dayake nesa da nan intafi shine yace inje funtuwa garin maiyi masu aiki hakan kuwa akayi nadau hanya saidai rabon samun farincikina ashe akan hanyata yake saina sauka akauyensu mairo bawai dan nasan garinba inajin amfadi sunan garin naji ina sha awar zama garin mahaifinta nafara haduwa dashi shine yakaini gidansa yabani masauki daganan yacigaba da basu labarin duk abunda yafaru dayanda mahaifinta yakeyiwa yayansa harkawowa ga mairo ya nisah kunji abunda yafaru
gwaggo kusan suma tayi awajen jin wai mairo kishiyar yartace gaske taji tatsaneta bagairah ba dalili kowa yayi tsit kasim kam kuka yake hihihin sundauka kukan tausayin mairo ne basusan kukan anyimasa katangane da itah ba muhd kam kasa natsuwa yayi kuma baiga laifin abunda haydar yayi masabah kodah shine zaiyima fiye da haka gwaggo jirah kawai take ayanke hukunci amman su alhj sunyi shiru kowa da abunda yake sakawa aransa
gwaggo tace kunyi shiru wanne hukunci zaku yanke akai kunsandai yata bazata zauna da kishiyaba tunda sauran ma basuda itah kuma yataka dokar gidan nan tunda ai itay yafara aurah
innah ce tadaga hannu sama tace alhamdulillah amman naji dadin wannan labarin haydar meyasa tuni baka fadaba aidani ba a wahalmun da maryam dina hakaba babu wani hukunci daza a yanke aimagana takare matar sace kuma wlh dole abarsa da abarsa aini tuni banason irin auren nan dakukeyi kubar kowa ya auri wacce yakeso idan mutun adangi yagani yanaso abashi idan kuma awaje yagani abashi amman daga yau nina kashe wannan
wlh nadade inayiwa haydar kwadayin mairo inama ace yana sonta ya aureta kobashibah daidaga cikin jikokina wani yace yanasonta wlh kullum da abun nake kwana ina tashi ashedai bansan kishiyatacebah takalli mairo taso nan kinji ashe dama kinsan kishiyarki kikewa hidima duk da haka nasakar maki mijin dankinfini chanchanta dashi gaba daya wajen aka kwashe da dariya banda hameeda da gwaggo
taso kinji maryam haydar yakalleta yana murmushi itah ma shitake kallo yalumshe ido yabude tamayar masa da murmushin mikewa tayi yatashi yadauko mata hijabinta yasa mata sannan suka jerah wajen innah kusa da kafafuwan innah tazauna innah tadorah kanta saman cinyarta
tana shafar kanta takallesu kuma abunda nakeso kuyi shine inaso dagayau afara shirin biki dankuwa sai anyi wani bikin danni saina taka. rawa abikin nan bantabajin dadi irin naranar yaubah takalli haydar kaikuma kagyara gidan ka rana itah yau matanka sukoma cen yagyada kai innah aini gidana dama agyare yake kayane kawai babu aciki
tace to Alhamdulillah maganar yar uwarka kuma kayita hakuri kaji haydar matane saida hakuri insha Allah zakaci ribar wannan hakurin gwaggo ce tamike lallai yau kun nunamun iyakata to wlh yata bazata komabah
kawai danson kai ainaga kowacce itah kadai take zaune sai yata za ahada da qamayamaya. aibashine kawai autan mazabah yasakarmun ya wlh kunsan ko ayanzu hameeda tafita gari saita samun dubun haydar kawai dan yana dan uwanta saiya fake da wannan yacima yata mutunci
kawai tafashe da kuka aida yayankune bazaku taba bari yayimasu kishiyabah kuma alhamdulillah koyanzu kasuwa tawatse dankoli yaci ribah yata kudi aka saka aka aurota amman wannan kumafah YAR SADAKA!!! ce
Aisha. Ibraheem
[8:34AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
100
Taja hannun hameeda kizo muje wlh bake ba wannan kaddararren auren tanajan hameeda hameeda tana togewa dan itah kam duk da haka tanason mijinta sai kuka take tana kiran sunansa shikam dauke kansama yayi daga wajenda suke. haka gwaggo tafita da itah takirah wayar muh”seen tace yazo yakaisu gida maza
saida yafadawa dad yace tashi kakaita indai hurece babu wanda ya isah yasakata ta sauraremu idan tagaji dakanta zata dawo da itah mikewa yayi yayiwa haydar congrt sannan yafita alhj yayi gyaran. murya haydar kajidai abunda innah tace danhaka saika fara shirye shirye
innah takarbe kuma wlh dolene kahada mata lefe nagani nafada idan kuwa bahakaba zanriketa aguna kobanza nafika sonta yayi murmushi innah kenan za a hadamata ciki harda mota sabuda dal da nairah miliyan daya amatsayin tukuicina sauran bayani sairanarda Allah yasauketa lafiya innah kudai tayani addu a tahaifoman yan biyu
innah saida ta rangada guda saiba maryam dinaba harda karin miliyan daya haydar??? yayi dan murmushi yasafo sumar kansa innah harma da tukuicin zuciyata kasakasa yake kallon mairo wadda kunya duk ta rufeta wani dadi takeji itah ma yanzu tashiga cikin sahunmasu yanci tarokam yawatse cikin jindadi duk sungama shirya meza ayi abikin nikam nace biki da ciki hehehheh
kursum tana nan manne da maryam tunda taji matar yayan tace damacen tana sonta kamar yanda mom take sonta motar haydar mairo tashiga suka koma gida tafiya yake yana murmushi yacije lebe amman wlh naji dadin wannan abun kinga komai yazo cikin sauki gwandama dahakan yafaru kinga zuciyoyin mu sun samu sauki yajawo wayarsa yakirah fadil yana dauka yace kai mutumina komaifa ya warware rana itah yau zan zama ango
fadil yace ango kuma wani auren zakayi yakalli gefenda mairo take wayaketa aure yanada kamar maryam mutumina aiyanzu daga wajen meetn nake komai ya warware ansan yanzu matatace gobema zanbar kasar nan inje hadomata lefe
kai amman ina tayaka murna mutumina kaga kunhuta dawani boye boye”wlh kuwa saidai munhade sukai sallama ya aje wayar kinsan me kuwa ??? um um saika fada wlh jinake kamar anyimun albishir da aljanna tayi dariya haba dai yace wlh kedai bari kawai
mom kanta bakaramin dadi tajibah muhd yasamu haydar yabashi hakuri akan abunda yafaru rashin sanine yace bakomai aiyasan dayasani dabaifurta hakanbah kasim ma yasakawa zuciyarsa dangana tunwuri kafin takaishi ga aikata zunubi
washe gari kuwa haydar yabar kasar kwanansa hudu yadawo da kayan lefen mairo kamar hauka idan kagansu zaka dauka lefen mace biyarne akwati ashirin da hudu kowanne kayandasuke ciki bana wasa bane sun hadu iyah haduwa haydar yasan kalar kayanda mairo zata saka sukarbeta sosai komai dayasaya acikin kayan yanada takalmansa da mayafinsa agogo da jakarsa dakuma sharka banda fasion gasunan kamar za abuda wani babban kanti anfara biki kamar za a aurarda wata sabuwar amarya bangaren mom tahau gyaran maryam danso takeyi takoma tamkar budurwa tasha zanen lalli da kitso kanana kanana saida yahada diner biyu
ya gaiyaci abokansa dayawa har wadan da sukai makaranta india da abokan aikinsu yakara gyara gidan haydar bangaren maryam yasa kaya innah saida tayimata set kayan dubai mom kam daga saudia tasa akayomata odar su. dad ma yayi mata kaf kayanta babu wanda akasiya akasar nan mairo takoma kamar wata tauraruwa su kursum ma ba a barsu abayabah saida suka kawo gudun muwa akara gyarawa yayansu amarya
ranar asabar takama ranarda za a kaita saida sukayi wata diner ta musamman abokan ango yan uwa da da makota wajen yayi masifar kayatuwa murna biyu ta aurensa dakuma murna cikinda yake jikinta haydar harda rawa waishida yace bai iyah rawabah saida fadil yayita tsokanarsa innah ma yau saida ta taka dan harda masu kidan kwarya tadauko abunda bata tabayibah
karfe tara daidai akashirya mairo cikin wani material maidankaran kyau tayi kyau harta gaji aka kaita wajen dady yayi mata huduba mom ma tayi mata momharda kuka tayi rabuwa da mairo itah kanta mairo kuka take kamar ranta zaifita dakyar aka banbareta jikin mom akafitah da itah har haydar yakawo motoci harda innah wajen kai mairo lallai innah bakaramin so takeyiwa mairobah ankaita gidansa kwaton gida nagaban kwatance to damadai da itah da haydar ne babu wata damuwa mutane sai santin kayan dakinta suke kafin goma kowa ya watse tana shirin zuwa wanka dan zafi takeji saiga hayaniyar haydar da abokansa abun itah haryasoma bata dariya wai kenan siyen baki sukazo kamar budurwa
suka zauna akabude taro da addua daganan sukai masu fatan alhairi yarakasu sannan yakulle gidah yadawo yace amarsu ta ango tana dariya tace uwar mata dai ina fama da ciki dugugu dugugu kace wai amarya
yana cire babbar rigarsa yace wlh kinfima amarya awajena danhaka kima yarda duk abunda zakice madai kice amman ni nasan haka kinga tashi muyo alwala tace kuma dai saida sukai alwala sukayi raka a biyu yayi mata addua kamardai yanda akeyi yagabato masu da naman kaza gasassa da madara suka ciyarda kansu tare sukai wanka sannan suka lulaya duniyar ma aurata haydar kam yakasa banbance ranarda yafara saninta da yau saiyake ganinma kamar yauce dankuwa yasha zuma sauran zancen nashine
haka rayuwar aurensu tacigaba dakasancewa haydar yakoma aiki amman kullum suna manne dawaya idan kuma yana gida suna tare amfara shirin bikin fadil da Aisha humairah sati maizuwa yanzukam haydar yayi wuyar gani dansun fara hidimar biki agefe guda cikin maryam yashiga wata na takwass amman idan kaganshi zaka dauka yanzu zata haihu
Aisha. Ibraheem
[6:42PM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
001
Duk wata kulawa tana samu sosai wajen haydar ranar asabar aka daurah auren fadin da Aisha humairah akan sadaki dubu hamsim ranar kam fadil baki harkunne haydar sai tsiya yake masa yana cewa yaudai kaima zaka dandana kaji abunda mukeji
sati daya da bikin fadil haydar yaje garinsu mairo amman tafiyar dai rana yayi itah kanta batasan yajebah dan ankammala ginindayasa aimasa gidakam ya hadu ya amsa sunansa komai anyi yasa anzubah kayan daki akowanne bangare bangaren innah dukyafi girma sai bangaren. hardo kusa yake dana innah sukuma nasu gwaggo da iyya waje daya yake zokaga murna akofar gidan kuma dama anbuda katon shago haydar yacikashi da kaya kala kala wadan da yasan ba a samunsu anan sai anje zariya yadamkawa halliru sannan yace yanaso yadauki nauyin kula da innah da hardo murna kamar me harda kuka su gwaggo kam sun aje makaman yakinsu ganin wannan hidima da haydar yayi masu aranar yabaro kauyen koda yadawo gidama har ansoma kiran magrib masallaci yawuce kaitsaye saida akai isha i yadawo
kwata kwata baisanarda mairo ina yajeba
bangaren gwaggo kuwa tagaji da tijarar hameeda hakan yasa ta tattarota tamaidota dakinta saida aka gyara mata bangarenta ta tare dad saida yayi masu nasiha akan zaman hakuri sannan haydar yaraba masu kwana kuma daidai gwargwado yana kwatanta adalci abu daya kawaine baiyarda dashiba yahada shinfida dai da hameeda alhamdulillah suna zaman lafiya
watanta daya dadawowa gidan mairo takama nakudah kuma gashi haydar baya gida nakuda take zangu zangu babu kowa dan mom taso yamaidota amman yace ah ah shikam yanada bukatar matarsa saidai idan tahaihu yakaita saigashi nakudar takamata da rana kuma haydar bayanan
kuka take tana kwalawa hameeda kirah tayi neman wayar ta bata gantaba hameeda tazo wucewa saitaji kaman tana kiranta dasauri takaraso tana kallonta saikuma ta sheke da dariyar mugunta”lallai yau aikinsu zaiyi kyau” dan Allah sister kitaimaka kikiraman ya haydar wlh mutuwa zanyi
kai alhamdulillah wlh dama zaki mutu dake da abunda kika haifa dayafi komai sauki kinga kin taimakaman nasamu narabu dake kinsan bazaki iyah haihuwaba ubanwa yasakaki kika kwanta da miji badaike dadi. aureba dan Allah kitaimakaman zan mutu saikuka take tana murkususu hameeda kallonta take tana dariya yarinya alkadarinki ya karye nibarima kigani komawa tayi taja kofah tarufe tayi sashenta
takunna duma kuma takai karshen murya gaba daya gidan yarude bakajin motsin komai sai taunar cingam take abunta tasan tagama da matsalar mairo haydar boka yace yasan yanda zaiyi mata dashi ya manta duk wani abunda ta aikata ya zaimada suyayyar mairo takoma agareta zata sameshi ahannu fiye da shekarun baya
yana zaune asiviti duk yaji jikinsa sai ahankali gabansa saifaduwa yake yaso yadaure amman yakasa hakan yasaka yadauko key kawai yayo gida tunda yanufo unguwar yaji tashin kida agidan sa yaso yaje bangaren hameeda yace takashe harzai shiga saiyajuya zuwa bangaren mairo yasamu dakin akulle
ina kuma maryam tatafi wayarsa yajawo yakirata saiyaji ringin cikin dakinta sauri yayi zuwa bangarensa yadauko wani key yabude cikin falo yasameta harta suma ga yaranan ta haifah guda uku biyu maza daya mace sai tsandara ihu suke baikoma takansuba mairo yafara girgiza amman ko numfashi batayi
ciccibota yayi dasauri zuwa cikin motar ya ajeta sannan yakoma yasamu zannuwa yanade jariran yadauko mahaifar yasaka amota yajata zuwa asiviti tunkafin yakai yakirah fadil haydar duk yafita hayyacinsa kamar wani tababbe
nantake akaturata saman gadon zuwa cikin daki akabata taimakon gaggawa haydar saikuka yake yama kasa mezaiyi sauran likitoci suka dauki yaran akagyarasu akamasu wanka fadil ne yakirah gida yasanar saiga mom da maman zulai hardasu dad kowa yadau yaran saiya zubarda hawaye gayara kyawawa amman mahaifiyarsu ba lafiya
Aisha. Ibraheem
[7:24PM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
002
Harsu kursum sunzo nan take asiviti tacika da mutane yandubiya sai koke koke akeyi duk yanda likitoci sukaso ganin sun shawo kan lamarin amman sunkasa ko motsi batayi haydar kam idonsa yayi ja saboda kuka
fadil kansa saida yazubarda hawaye duk wani maisom mairo bazai iyah hada ido da itah ba”” saikusan magrib hameeda takoma dakin mairo bata sametaba tace nashiga uku kaddai haydar yadawo dasauri tasauko kasa wajen maigadi tana tambayarsa yace mata ah shine yazo yadauki madam””
tace kaganshi da yara???? yace ah ah itah kawai naga yadauko cikin sauri takoma cikin gida tajawo mayafinta sai asivitin tanashiga takama kuka kamar gaske saifaduwa take ana riketa tace yanzu mundade muna neman haihuwa gashi Allah yabamu kuma haka abu yakasance
maman zulaitace sai hakuri hameeda fatanmudai Allah yabata lafiya sukuma yaran Allah yarayasu”chak kukanta yatsaya takalli maman zulai banganeba waita haihun ne??? maman zulaitashare hawaye ah tahaihu yan uku ne kuma lafiyarsu kawau itah ce ba lafiya
gaban hameeda yabada rass anya kunnuwanta gaskiya sukejiyo mata to kenan bokan nan yayi mata karya dayace dazaran tahaihu zaituro aljannu su tsotse jinin yaron itah kuma zai turo mata arne””ganin tana shirin sakin layi yasaka tayi saurin kawarda abun
takalleta ina ya haydar dinyake???? tace yana ciki wajenta nan tayi gumda baki tabuga tagumi yautaga samu taga rashi yanzu duk yan kudadenta datake takama dasu sune takwashe tabayar wajenyin wannan aikin amman kuma gashi aiki baiyibah
amman kuwa bokan nan yacuceni saida takaikaici idon mutane tazare jikinta bata zame ko inaba sai wajen boka afusace taje wajensa yana ganinta yakwashe da dariya muguwa kin dawo””tasamu waje tazauna boka nifah wannan aikin banga komaiba kace za a shanye jinin yaran nan gashinan harguda uku tahaifah amman sunanan kalau alhalin bahaka mukai dakaibah
saida yakwashe dawata mahaukaciyar dariya yace naturasu kamar dai yanda nafada maki amman sunkasa zuwa kusa da yaran dalili kuwa lokacinda tanada cikinsu mijinki yana karanta ayatul kursiyuu da lakadja akum yana lofawa aruwan zanzam yana bata tanasha babu yanda za ayi asiri yakamasu ko aljani bai isah yamatsa kusa dasubah
mahaifiyarsu kawai mukaci nasara akanta dan batada tsarkine itah ma dama nafada maki aikin nan akwai hadari cikinsa kuma akwai wahala. idan da aljanin yakone akanki zairama amman duk da haka kada kidamu kisani kinyi adashe waje mai kyau kikoma gida kikwanta duk sauran bayani nawane puhahahahaha yakece da dariyar kamar muryan jaki jiki na rawa hameeda tabaro wajen boka da murna cikin ranta
Kwanan mairo uku sannan tafar fado babu um babu umm um batasan waye akantaba batada wani kuzari saidai kawai tarika bin mutane da kallo kafin kace me tasake komawa barci yara kam saidai akasoma basu madara dan ganin halinda mahaifiyarsu take ciki
batayin tsayin mintuna ashirin afarke kullum zaka sameta tana barci kuma nafitar hankali tana wani gurnani kamar zakanya.fadil ne yabada shawara shidai yaga aikin yakici yaki cinyewa maizai hana afitah da itah waje haka kuwa haydar da mom suka shirya zuwa babban asivitin india akadorata saman na ura sudai basuga wani ciwo atattare da itah ba
amman abu saidada gaba yakeyi haydar haka zaizauna yatasata gaba yayita kuka kamar karamin yaro tun momy tana lallashinsa har itah ma saitakama kukan mairo gaba daya tarame bata cin komai saida arika bata abinci ta hanci kassa duk sun fito mata ganin hakan haydar yasiyo kasat din kira a dadan karamin redio danshi yafara zargin kodai aikin anjanune ranarda yasaka mata kira a ranar tana farkawa tadauki redio tabuga da bango yayi tara tara kanta tabuga saman glass dinda ake ajemagunguna
hayadar dasauri yariketa amman nema take tafi karfinsa mom ce tadanna abunkiran ma aikata hauka tataso kuma zangu zangu duk inda taga glass saita fasama kanta likitoci sunfi goma suka riketa sannan akasamu akaimata allurar barci ahankali takoma barci yanda taimajikinta jina jina shikanshi haydar yajimu garin riketa haydar zaune yafadi yanata rusar kuka
nimadai bansan sanda hawaye suka zubomanba 😭😭😭😭😭
Aisha. Ibraheemh
[6:51PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [8:48AM, 11/27/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
90
AZZANNU ZANBIN WALAU KANA HAKKUN haka zato zunubine koda yazamo gaskiya yar uwata ina kirah agareki daki daina abunda kikamun kin aikata zunubine tunda nake novel wlh bantaba kallan wani littafibah waidan insaci abunda yake ciki
hasalima rabonda na karanta littafi indai ba a whatsapp ba wlh anyi shekara uku banma tabajin sunan wannan littafin dakika fadaba wai mijin aro
najima ace shine nai copy book dinkike??? kokuma kekikayishi???? menene dangartakarki da wacce tayishi inaso inja hanklinki kisani abunda kikai baida kyau manzon Allah sallahu Alaihi Wasallam yana ce wa
minhusnul islamir mar’i tarkuhu malaya anihi yanadaga kyawon musuluncin mutun shibar abunda baidameshiba bake kadaiba ina kirah gaduk wani mai niyar yinhakan watarana kusani duk abunda baidami mutunba yadaina saka kansa
nasan hassadace kawai lallai Allah yayi gaskiya dayacewa manzon Allah acikin suratul falak ayar karshe BISIMILLAHIRRAHMANIR RAHEEM wamin sharrin hasidin izah hasadan “”kanemi tsarin Allah ga mai hassada yayinda yayi hassadar wa iyazubillah tonima ina neman tsarin Allah daga duk wani maihassada
jan hali agareki kisani hassada dabi ar yahudawace bada’ibar kwarai bace bazai shiga aljannaba wanda yakasance ynada koda kwatankwacin kwayar zarrane na hassada acikin ransa hakika nikin bataman kai sosai wlh amman yanzu raina tass yake nabarki da wanda yayi fitowar rana da gushewarta jama a kawai mucigaba da gashiiiiiiiiiiiiiiiiiiiii
*******************************************
Tace nifah kunya nakeji wlh”yadan dungureta akafada wlh idan kikasa tsiya agabansu zan rumgumeki sai inga yanda zakiyi ta kwalalo ido rufan asiri dan Allah natubah muje kawai nasan zaka iyah bakin kofar wucewa ciki yatsaya yace kije kisanar dasu ganinan shigowa tace waikai kamar bako kazo mushiga
kaiya girgiza mata baidace ba ai maryam yanada kyau saina nemi izzni kafin inshiga kinmanta ayar kur ani inda take karantar damu akan mahimmancin wannan Allah madaukakin sarki yanacewa acikin littafinsa mai tsarki
bissmillahir rahmanir raheem
ya ayyuhal lazina amanu latadhulu buyutan gairah buyutukum hatta tas ta anisu watusallimu………. harzuwa karshen aya””
to malam yaya haydar kaida mutun yayi abun kadan kaja masa hadisi bari ina zuwa yayi murmushi yauwa kokefa saida tayi sallama tashiga haka kuwa gwanda dabasu shiga tareba gwaggo ansaki shabaibai kaman silifas tana zaune tanacin waina taduka tagaisheta ta amsa sannan taje dakin iyya tagaisheta saitayi dakinsu tagaida innah tace waizaishigo yagaisheku””
gwaggo takarbe jiman ja irah bazaki fadamana tun jiyaba yanzu haka zaishigo gida duk datti danyakoma gaba yace iyayenki kazamaine ko??? itah dai batace komaiba dan kofar innah chaf take kofarsune da datti innah tamiko mata tabarma tashinfida sannan tajuya dasauri gwaggo akadau tsintsiya aka shassare inda zaigani tasaka hijab
tasameshi yana waya da fadil tayi tsaye saida yagama tace to muje tana gaba yana bayanta sukai sallama tare innah ce ta amsa gwaggo kam bakinta yaki rufuwa yanda taga haiydar shekarun baya baiyi kyau hakaba yanzu taga yakara gogewa yayi haske sai kyafta ido take kamar wanda yayi karya gaban mai gari
yazauna saman tabarma yatankwashe kafarsa yagaishesu suka amsa yadade duke awajen sannan yamike kudine yazaro rafa rafa yan dari biyar biyar ya aje gaban innah ”innah tace haba kaikuwa haydar ayihaka kaida kake bako kuma wlh mundai gode duk wadan nan kaya dakuka kwaso ai abun yayi yawa
ah ah innah bakomai albarkarku muke nema”da addu arku” ai addu a muna nan munayi maku itah amman kadauka mungode gwaggo ce tabuga salati” innalillahi yaunaga jaraba ance kidauka amman saikin tsayayin wani sanabe ansandai ke mabukaciyace danbakida su shikuma harsun mashi yawa neman maraba yake dasu idan zaki dauka kidauka ta kalli haydar kai yaro mikoman nan wayaki arziki angode dai
Aisha. Ibraheem
[9:42AM, 11/27/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
91
Haydar mikewa yayi yayi masu sallama yakama hanyar waje innah harda dan guntun hawayenta kokadan bataji dadin irin abunda gwaggo tayiba menene haka gaban bakoma saika saida hali Allah ya kyauta mikewa tayi tashigewarta daki mairo dai tana tsaye gwaggo tataso dasauri har zanenta yana faduwa zata dauki kudin sai rigenge suke da iyyah daidai shigowar malam yabisu da kallo duk da baisan abunda sukaibah daganinsu akwai alamar tambaya
yakalli mairo yace ina innah ki?? tace tana daki yace wannan kudinfa??? tadan share hawaye ya haydar ne yabasu;; yadan kalleta sosai tomenene abun kuka kuma.anyi wani abunne??? tace ah ah sannan tajuya waje yaduka yadau kudin sannan yakwallawa innah kirah tafito duk da tayi kokarin boye damuwarta saida yagano
lafiya dai shatu??? bakomai malam yanisah hakan dai kikace toya za abaki abu kibarshi nan???? tace ah ah malam kadauka kayi hidima dasu tajuya daki gwaggo tabuga kaida kasa wlh saidai abamu kasonmu sannan naki kibar masa mubamu yardaba wlh haka akeyi ke idan bakida bukata mumunadashi ko tsire masiye da kudin ehee innah dai bata cemasu chas ba malam kuwa baikoma kansubah yayi shigewarsa daki gwaggo sai masifah take inda take shiga batanan take fitaba
mairo kofar dakin su tasamu haydar tunda yaga ta dade yasan abunda yasa kanta yana kasa tayi shigewarta daki yacire takallim yabita saman kujerah tazauna yadade tsaye kafin shima yazauna yadago kanta hawayene kwance afuskanta yasa hankicip dinsa yagoge mata haba maryam menene kuma abun zubarda hawaye dan Allah kidaina yiman bannar hawayenki akan wannan kada kidamu kanki dama ninasan halinsu batun yauba babu abunda halliru baisanar danibah nasan innah tana hakuri da zama dasu amman kada maganardasukayi tadameki kinji wlh banason ganinki cikin damuwa
koki saki ranki konima inyi kuka yalamgwashe kai kamar zaiyi kukan saigata tayi dariya yaja mata hanci kokefah nema kike kawai kiwahaldani yakalli agogon hannunsa yauwa kinga yanzu shabiyu tayi bari inje innemi halliru muje yawo kinga kayan nan kisamu kibudesu kubawa kowa nashi duk yanda kikayi hakan yayi daidai
amman akwai shaddodo suna nan iri daya kada kitabasu gobe nakeso rabasu masallaci tace yanzu tafiya zakayi kabarni????? yayi murmushi idan kuma tare zamu saiki taso dajifah zamuje kizauna warki kihuta kinga akwai masu zuwa ganinki idan sukazo akace kuma bakyanan fa??? shikenan yayana adawo lafiya saida yasunbaceta sannan yafita
tadade zaune sannan tatashi tawatse kayan tafara rabawa kowanne saida tabashi nashi hatta makota yara kuwa akaita raba masu sweet su gwaggo baki harkunne sukam gobema akara duk da malam yayi masu halin karfi da kudin amman bakomai sunsan kafin yakoma aizaikara masu wasu
labarin zuwan mairo harya kai kunne larai saikuwa gata tazo da danta harta yayeshi habibu yaron yayi wayo sosai matar halliruma tazo da takwaran haydar yinin ranar kam sunsa firah saidare suka koma yauma batasake ganin haydar ba sai dare sannan suka wuce dakinsu
da asubah bayn sunje sallah da akagama haydar yasanarda hardo dashi da halliru sukaje daukan shaddodin haka akaita bawa mutane daidai tare da kudin dinki dubu biyu kowa sai murna yake bakamar hardo saiyakeji kamar dansane yake wannan hidimar
washe gari akasakewa masallacin sabon fenti aka gyarashi yakoma kamar sabo haka dai sukacigaba da zama cikin jindadi dakansa yaje kasuwa yayo siyayar kayan abinci da riso da jarkar kalanzir kullum mairo idan taimasa girki saitakaiwa innah
su gwaggo har ruguguwa ake wajen sidin kwano abunma haryabaka haushi””haydar baitaba saran haka mairo ta iyah girkibah sai yanzu tare sukecin abincin da halliru suyita buga santi
Aisha. Ibraheem
[10:15AM, 11/27/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
92
Saiyanzu gwaggo talurah dacikin dayake jikin mairo baki dada yamutu dakullum saitayi tsegumi watansu daya da sati uku suka fara shirin komawa gidah duk wani shirinda zasuyi sungamashi
haydar yanunawa halliru yanda zairika ciro kudi katon fili yasiya bayan gidan su mairo yadauko masu aiki daga zaria yanuna masu yanda za ayi ginin amman baifadawa kowa nawayebah halliru kawai yasani yangarikam basuji dadin komawar haydar ba dansuna karuwa sosai dashi
ranarda zasuje gida mairo harda kuka itah tana zullumin abunda zata tarar gashi yanzu cikinta yashiga wata na biyar yafito kwas ko makaho ya lalaba yasan akwai ciki batasan kuma wani tashin hankali zatashigaba shikuwa haydar baya kawo komai aransa danyanzu yaji dadin zamansa yayi kiba yayi fari kamar wanda yaje kasar waje tunda suka fara tafiya babu wanda yacewa wani uffan kowa da bikin zuciyarsu shikam haydar tunanin zasuyi nesa da itah itah kuma tunaninta ranarda zatayi arba da gwaggo taganta daciki
daidai kofar gidansu yayi hon maigadi yabude masa yashiga yana tsaida motarsa mairo tafito dasauri danbataso kowa yaganta tanashiga tafada jikin mom tana murna lalala maryam kece kika koma haka lallai garinku akwai dadin zama
mom wlh nayi missing dinki sosai ina yan biyuna???? tayi murmushi suna makaranta wlh kebakinyafe karatubah ke dadi aure tarufe fuskanta mom kenan” ya kuka baro mutanen gidan lfy qalau wlh suna gaishaku
muna masawa waiku saikukaje kukasamu wajen zama saidai waya masuyin wata saigaku harda sati uku sama ”tadan muskuta mom niyanzu ina zullumi idan akagane tare muka dawo da yaya haydar”” kwantarda hankalinki ainasanar dasu zaidawo nace yabiya yadaukoki amman kirika yawo da hijab dan cikinki yafito nibansan abunda zaifaru anan gababa
Allah yasadai komai yazoda sauki mairo kam gabanta saidukan tara tara yake tamike mom bari inje inyi wanka inyi sallah wlh nagaji tana shiga daki tarage kayanta tayi wanka da sallah takwanta da sallamarsa yashiga bangarensu bakowa afalon ya aje kayanshi dakin hameeda yashiga tana kwance tana waya takauda fuskanta
yana nan tsaye saida tagama tasauko daga saman gado tana kallonsa kasa da sama sannu maitafiya wai saboda Allah katafi wani waje tsayin wata biyu batare da matar kabah nifah wlh hakurina yakare katunafah inada lafiya kuma kasan ina bukatar ka atare dani
kasan hakkokina dasuke kanka amman kahaura katafi kabarni!yace ah ah dakinsake tunaman inaganin namanta””tonima bansanibah amman nasan kasani kuma kasan Allah yana kallonka yaushe rabon kakwanta dani tun muna india wlh nagaji zansanarda su dad abunda ake ciki dansu kwatarmun hakkina amman bazan iyah ba wlh
yarungume hannuwansa yana kallonta lallaikuwa dakin kyauta kiyi hanzarin sanar dasu dan Allah bari kiji nibazan iyah hada jikina dakebah kawai inje inkwasarwa kaina cuta ido tazaro cuta kamarya ya haydar???
Aisha. Ibraheem
[6:52PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [8:17AM, 11/26/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
85
Hannun sa tariko tana kuka yakuma juyowa yaduka dan Allah kidaina wannan kukan wlh harcikin raina nakejin kukanki pls kidaina kukan haka ya isah zan dau mataki kinji””
kai ta girgiza masa nibashiba dan Allah kayi hakuri kada kacemata komai nasan dad ranar yayi magana akai dan mom tamun magana akan indaina kula matarka kayi hakuri wannan kaddaratace
bansan ranarda zanfita daga cikin taba.kasaurareni ya haydar indai akainane banaso kasake nuna bacin ranka koda kuwa gabankane matarka zata dakeni naji nadauka amman kada kasake dukanta akaina wannan bawai yanci kake kwatarmun bah
kanasone karuguje zumincinku nikuma bazanso hakanba dan Allah kataimaka man.yajawo ta jikinsa yana lallashinta shikenan my luv zan kwatanta inga ko zan iyah amman kinsan bazan iyah gani anacimaki mutunci ba in nada hannuwana ina kallo amanafa akabani ke kuma inasonki idan akatabaki tamkar antaba zuciyata ne
tadago kanta takalleshi murmushi tayi saida hakoranta suka bayyana yasa hannu yagoge mata hawaye tace aduk lokacinda naji kana furta wadan nan da dadan kalaman akaina nakan hakikance babu wata macen da tafini dace aduniya
nayarda nice mace mai sa a aduniya da Allah yayiman katari da samun kyakkyawan saurayi ajin karshe ga kyau ga ilimi wannan shine kadai burina aduniya ganin na mallaki zuciyarka da gangar jikinka,, indai nine kisa aranki kinsamu tunima nagama sallama maki kaina
tasake murmushi Allah ko ido ya lumshe alamar eh ta rausatar da kai ina alfahari dajin wannan zancen nayarda na amince idan za a lissafa maiyawan sa a aduniya tonizan kasance ta daya
Allah ko matata murmushi tayi taboye fuskanta cikin kirjinsa yarungumeta nima haka matata nasan nafi kowane namiji dace aduniya da kowane namiji zaihango abunda nahango tattare dake dakuwa babu wanda zai yarda ki kubce masa nagodema Allah babu wanda yahango hakan akauyenku saida babana yabanike naga kayana
tayi murmushi au wai yaya ina fadil??? koyatafine ya salam wlh kwata kwata namanta dashi kinsan idan ina tare dake nakan manta komai da kowa sainaga kamar ina yawone awata duniyarda babu kowa dagani saike
tazame jikinta daga nashi tasakar masa kiss agefen kumatunsa to yayana tashi kaje dan Allah yadan rausayardakai yace bai isheniba cikin shagwaba yayi maganar taja gefen kumatunsa cikin wasa kaje kawai idan wan nan ne saika gaji dashi
da gaske???? girah ta daga masa yayi dan tsalle yeeee yataba ashedai nakusa zama dan lele yana dan taka rawa yafita dariya saida takai kasa haryafita yasake lekowa da sauri ta bakin kofah yace luv u muah tace mee 2 sannan yawuce tayi murmushi takoma tajingina Allah nagode maka daka dasa soyayyata azuciyar mijina Allah kabarmu tare. kashiga tsakaninmu da mahassada nidai nace ameeen
yana fitah yadan hurah iska abakinsa yasa hannu yana shafa dan shajensa alama kenan yayi rashin gaskiya fadil yatareshi da tsarabar harara yana dariya yakara inda yake afuwan mutumina bandadebah aiko””
um lallai baka dadeba ai yanzuma kashiga gidan kaidaga zuwa lallashi saika maida waje kazauna aisaika fadaman soyayya zakuyi insani ni inkara gaba
Aisha. Ibraheem
[8:52AM, 11/26/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
86
Habadai abokina wace irin soyayya kuma Allah lallashinta kawai natsaya hannu fadil yasaka yashafo janbakinda yake saman kumatunsa ya nuna masa wannan duk hakurinne???? kaga malam ainasanka sarai akan abunda kakeso
mayena kai nizakacewa wai lallashi kayi bayan kuma ga alama nan nagani basaika fadaba kawaidai kashanyani malam kace dai inyi hakuri kawai”” anki abaka hakurin aini bansan labbanta sunlikemun akumatuba yajawo dan yatsan fadil yagoge ga rigarsa banyarda koda jambakin matata yatsaya ajikinkabah
kaima idan kayi zuciya kayi aure yana maganar yana dariyar keta””kwantar malam albishirinka???? yace menene zaka wani ceman albishir ni idan dai bacemun zakayi zansake samun.maryam fiye da yanzu ba shine kawai albishirin da zakayi yaburgeni
shikenan tunda bakaso bari narike abuna”yayi murmushi haba abokina aikai nadabanne manta kawai fadaman,,bazan fadaba yakai masa dukan wasa kardai kace maganar tatsaya??? yayi murmushi sosaima kaga nima nahuta da gorinka”” yadafashi wannan wace mai sa arce tayi dace da santalelen saurayi kamarka gaskiya ina tayata murna
yakalleshi ta kasan ido yace Aisha humairah mai babban suna Aisha adon yammata ga hakuri ga ilimi rashin son abun duniya kawaici dasanin yakamata Aisha kyakkyawa mai alkunya ai ina fada maka sunciri tuta duk mai suna Aisha akwai hakuri kamar ruwa
hahahahahaha wayyo cikina dariya saida haydar yakai kasa lallai abokina kashiga layi waitunkafin kasan dadin abun kake wannan yabo to inama kadandana ainasan saikace maza kada sukarah auren mace wadda ba tada suna Aisha
fadil yayi dariya sosaima kaga kuwa duk wanda yahaifi yarsa saiyasaka mata sunan Aisha barima kaji wakarda akaimata momyna Aisha humairah kakata Aisha humairah matata Aisha humairah kowacce Aisha humairah inyamutu ba akonashi”” ni inason Aisha humairah kuma nace Aisha humairah inna mutu ba a konani
hahahahah kai fadil wan nan waka kacedai mufarazuwa studio dankuwa zamuyi kudi sosai naga alama kanka yanaja amman da anlaba dani da wakar tafi dadi nima saina rerawa maryam dina waka
haba malam badai kamar tawaba kaga malam idan kanason soyayya kanemi yarinya mai suna Aisha ina fadamaka komai kake nema kasamu””haydar yahade fuska kaga malam kaidai kowa yarike tashi nikam babu macenda tafi matata iyah soyayya idan kuwa haka sauran mata suke to tabbas sunan maryam yaciri tuta
hmm kaidai bakasan sirrin ba shiyasa bari saika shigo hannu sannan kabani. labari na Aisha indo ”yakai masa duka wlh idan zaka bata mata suna nima daga yau mairo yankirah taka “”ah ah kada kabatamun suna andaina na indo au sorry namanta ne yakanne ido daya
yakai masa dukan wasa yagoce yana dariya kaga muje dan Allah inyo siyayya. k muje kaga ankusa magrib kace tafiyar tananan jibi????insha Allah zamuje mu soye son ranmu” fadil yace soyayya duk wadda kukayi yanzu aihar ansamu ribah. soyayya kuma tayaushe
Aisha. Ibraheem
[9:27AM, 11/26/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
87
Kake ganiko??? ai wlh ni kullum ganinta nake kamar yanzu nabareta cikin leda kullum dal nake ganinta. hahaha kaidai kawai kace kasan dadin mata kawai””eh ko hakan kace aibakayi laifibah
harsuka kai banki saida yaciro kudi sannan suka wuce kasuwa basu wani dadeba suka dawo bangaren mom yakai kayan sannan suka wuce masallaci tare da fadil basu dawo gidaba sai bayan isha i saida yashiga gidan yayiwa maryam yajiki suka dan taba firah sannan yayi masu sallama yafitah
washe gari tare da maryam yaje sukayu sauran siyayyar wannan karon kam da motarsa zaije. duk wani shiri yagamashi mom ce tasanarda dad an turah haydar wani asiviti kaduna zaiyi tsayin wata biyu kafin yadawo shikam haydar ko ajikinsa danshi aikin ma baidameshiba zai iyah ajeshi saboda kula da maryam bayada wata damuwa muddin yana tare da maryam dinsa
dan kudinda yake dasu sun isheshi rayuwa dashi da yayansa da matarsa dan ba kananan kudi yasamo a india ba kuma gashi yasaka hannun jari wajen guda goma yanzun ma arzikinsa yafara bunkasa danba karamar riba suke samubah akamfaninsu dashi da fadil suka hada hannun jarin
washe gari karfe takwas suka dau hanya maman zulai dai mom cemata tayi mairo zataje ganin gida shiyasa haydar zairage mata hanya zuwa kaduni saita karasa dakanta tunda tasan hanya
tunda suka fara lafiya tafara gyangyadi yace karfa kimun yanda kikamun sanda muka fara zuwa garin nan yanzu kuwa mufasa tafiyar nan””tayakuna fuska wlh barci nakeji.tojirah yakantar mata da kujeran takwanta barcinta tacigaba dashi
shikuma yana tuki yana kallonta yana murmushi bata farkabah saida suka kusa kaiwa gida baifi minti ashirinba danharsunkai Zaria suna kaiwa tafara murmushi yayi fkng daidai kofar gidan yara sun dabai baye mota suga waye aciki zata fita yariko hannunta kada kimanta da alkawari wlh yau ina bukatar abun dakyarma zan iyah hakurah zuwa dare
tayi murmushi ai bazan barkaba yayana nikaina ina bukatar kasancewa tare dakai saida ta manna masa kiss sannan tabude kofah tafita tagyara mayafinta tabdi wai kallo yakoma sama kunga yanda akai tururuwa ana kallon mairo gani sukema kamar bayar kasar nan bace kamar irin yan india mairo tayi kiba tayi haske dan cikinta dayasoma fitowa yakara fitoda kyanta
duk da ciwonda tayi kwana biyu tasoma maida jikinta cikin fara a take gaida tsofaffin da suka tsaye wajen tayi cikin gida haidar yabuda bt din mota yafitoda sweet kala kala dayawa yasoma rabawa yaran wadansu su karba sau biyu wadansu su ruga sukirah wadan da basanan
wasu har kannensu suke daukowa wanda baimasan komaiba sumika hannunshi abashi idan sun kauce sukarbe su hada da nasu gaba daya aka maida kofar gidan kamar kasuwa labarin zuwan haydar harya game gari
halliru ne yafara karasowa wajen haydar da murnarsa suka yi musa baha yaja hannunsa muje gidana kahuta”yace au kace kayi aure kaima?? yace harta haihu nayi maka takwara ai””haydar yace dana sani aidanayiwa takwarana tsaraba
suna dariya sukawuce sauran yaran sukayi cikin gida wajen mairo tana shiga gidan innah ce tafara ganinta tace mairo yaukune agarin namu tayi murmushi innah ina wuni”lfya qlau
Aisha. Ibraheem
[10:21AM, 11/26/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
88
Su gwaggo sukayo wuf jin an anbaci sunan mairo lalaikuwa mairon ce gwaggo dasauri takaraso wajenta tana yakunar fuska to baki mukayi”tayi murmushi taduka tagaisheta ta amsa sannan tagaida iyya ta amsa
ummah tace ya kika baro mutanen gidan da mijinki tace qalau suke suna gaisheku aitarema muke dashi””ah kice manyan bakine agarin namu amman shine kika barshi waje bari indauko maki mabudin dakinku amman sai anshareshi dan nasan yasha kurah shekarah biyar aiba wasaba
gwaggo ta mere baki shekara biyar kam amman babu ko kazantar daki nidai wannan auren banga ribarsaba da anan ne aidayanzu takaida yaya biyu ga sa anninta nan da yayansu amman itah shiru wayasanima ko acendin bangaren masu aiki take maigidan ma baisan da zaman taba
taya zata samu wani ciki bayan koshinfida ba ahadawa da maigida ni wlh wannan auren bana kaunarshi dan banga ribar saba”” hardo ne yayi sallama yashigo gidan yacewa yaran tome kuke jirah kufitah mana suka fita suna waigen mairo
taduka tagaida hardo ya amsa yace yahanya kunzo lfy tace lafiya lau baba yace.ina haydar naji ance tare kukazo amman nazo banganshiba”tace baba nima anan nabarshi nashigo gida”yace tokunanan lafiya daiko tace kalau baba
gwaggo tace malam kaga muna magana amman kashigo bakace komaibah shin wai aurah masa itah akai danyatasata gaba koya maida itah yar aiki danni banyarda wannan gayen zai iyah kwanciya koda gado daya da wannan ba amman tabi ta manne masa kagani batama zuwa ganinmu sai anshekare.
itah idan uwarta batayi maganaba mu zamuyi albarkacin hakkin makotaka dayan uwantakar musulunci” hardo yayi murmushi yace tomunji munkuma gode da wannan shawara taki amman ni banga abun kamawaba waike kenan kullum magana daya haryanzu kinki kisakawa kanki dangana akan wannan auren
insha Allahu wannan auren alhairini kamar yanda nasaka araina idankuma bazaki daina hassadaba kezatakai tabaro yajuya wajen innah kinga shatu kaita daki tahuta bari inje inga haydar din
tace to malam adawo lfy tawuce daki shima yafita mairo tabi bayan innah gwaggo tahau bakinta lallai malam dole kaiman cin mutunci akan nayi magana kakwatarwa yarka yanci ai wannan basiyen mutunci bane amman bakomai nagode da wannan cin mutuncin takaba kanta tayi daki fuuuuuuuuuuu
sudai su mairo basuce komaibah haydar baisake dawowa wajenba sai bayan isha”i yanacen tareda halliru sai lokacin hardo yaganshi dasuka fito masallaci yaduka yagaisheshi “”kai haydar haka akeyi kazo da motar ka kabarta nan kasan halin yarah basajin magana kada sumaka barna
yayi murmushi bakomai abba munsameku lfy??? qalau wlh ya kasuwanci”” alhamdulillah sundade suna gaisawa sannan sukayi sallama.saida halliru yarakashi har kofan dakin sannan yashiga gida yakirah masa mairon da fitila tazo masu
Aisha. Ibraheem
[11:01AM, 11/26/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
89
Tadaga ta daidai saitin fuskansa tayi dariya ashe dai zanganka dan gari daga zuwa kayi tafiyarka tun dazu aka ajeimaka abinci amman bawanda yasan inda kake””yayi murmushi kema kinsan ina tare da yayan mu bari ashigo da kayan nan inkulle motar tace toh tashiga dakin ta aje fitilan halliru ne yashigarda tsarabar tare da haydar sauran aka kaidakin inna
sannan yakulle motar yasaka mata tanfol halliru yace toyanzu zamuje dandaline kabude ido kokwanciya zakayi???? yashafa sumarsa ah kam wlh nakwashi gajiya barni dai inje inkwanta saigoben kagaida uwar gida kuma kashafaman kan takwarana sukayi saida safe yakoma ciki
koda yaje mairo har anlotse karamin gado yayi murmushi bari kikeyi yarinya yafito yasamu kuwa ancika masu kaya da ruwa yadiba yaje yayo wanka kasancewar ana zafi
yatada itah tashi malama kiyi wanka kinsan fah wlh bazan iyah hakurah ba idan kuma sokike kauyen nan ajimu to bisimillah tayi kaman batajishiba saman dagon yahau yajawota jikinshi yafara sumbatarta tanajinsa amman tayi shiru kaman batajibah
saida taga abun yayi yawa itah ma tafara maida martani kafin kace me soyayya tayi dadi sukaci gaba da faranta ranjunansu saida suka darji juna sannan sukaje sukai wanka yarumgume matarsa saida safe nima gashi sai faman hamma nake nakoma saman kujerah nakwantarda hakarkarina
bansake farkawa sai safe lokacin harsunyi wanka sundau nakuti shaddace suka saka iri daya ko mairo batasan da dinkinba shikawai yayisu kala biyar kowanne kala daya kuma yasaimasu komai kalar kayan shida takalmansa ta agogo da hula
itah kuma takalmanta da jaka da mayafinta da sarka bayan sungama kimtsawa yazubah mata ido haddarta riga doguwace tasha dinkin wuta sama tamatseta harzuwa kugunta kasa kuma tabude tayi das da itah kamar dan saboda itah akai kayan sai kallonta yake yana lumshe ido
wani kyau take karamsa kamar ba maironda aka kawomasaba tana gefen gado yabuga tagumi yana tsaki wai anhadashi da jaraba ashe itah ce. zata zame masa hasken idaniya sunan wani littafi na HAUWA JABO
lallai yayarda da ake cewa sa a tafi gata na taskar BEBEELO.tabbas yayarda da hakan maryam tazama sa arsa dayaci karo da itah amman gatanda iyayensa sukai masa baizama haske agareshibah
ayanzu yatabbatarda Alhairi danko ne sunan littafin UMMI AISHA”” hausawa sukace baya faduwa kasa banza”kuma yayarta ya amince akoda yaushe yana murna da kasancewarta matarsa yayi murmushi ya lakuci hancinta maryam ke tawace hakanda yafada yasa natunoda sunan littafin MAMAN SHAKUR. ke tawace
Tayi murmushi tariko hannunsa kaima nawane yayana ina matukar alfahari dakai kasani nadade ina DAKON SON KA.. na KAUSAR HASSAN..nayardarwa zuciyata banida kamarka tunkafin kace kana sona nadade dayarda dakai naba zuciyata amanar kula da ruhinka kaine JAGORAN RAYUWATA na taskar Aisha ibraheem
kazama haske agareeni kullum burina dayane inkasance akullum ina kyautata maka saidai kuma haryanzu bansamu yancin yinhakanba idanuwantane suka kawo kwalla yace NO dan Allah kada kibatamun kwalliya. barima kigani yakamata insayi wannan kwalliyar yabuda akwatin kayansu yadauko wani karamin kwali yabuda saida mairo tazaro ido
wata dankareriyar wayace iphone kamfanin tecno sukayita kai agaskiya wayar dahadu kuma kamar yasani kalar shaddarta wayyo dadi wani dadine yakume mairo saida tarungumeshi yace saiki fara aiki da itah kuma wannan wayar babu ruwanta darashin babu savice akusa
nima irin tace amman karamar taki dan baidace inrika abunda yafi naki tsadabah””tayi masa hararar wasa kai yaya to aikuma niban iyah ba kasan bakowace waya nake tabawaba ta mom ce kawai saikuma ta kawayena. kada kidamu zandinga koyamaki aibabu wuya kinga mushiga mugaida su gwaggo tare suka jero………………
Aisha. Ibraheem
[6:52PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [1:51PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
78
Takalleshi eh dani da maryam ne tabar yanbiyu saikuka sukeyi “”yajuya tabi bayanshi sannan takulle kofar yace aikece nace maki kidinga zuwa dasu nan muna kwana tare””tabata fuska haba alhj nikam bazan yarda yayana suna kwana gunda muke kwanaba
aiwan nan shine farko wajen ruguje tarbiyar yayanmu masuyin hakama ina ganin wautarsu yarone bakasan lokacinda zai iyah farkawa kana kwance da babansa shima rayuwarda kukeyi sannu ahankali zaifara kwadayinta
aini dayaro yahaurah shekara uku nadaina kwana tare dashi balantana su husaina dasuka shiga shekara biyar kuma kana gani sunada surutu sosai ”yarikota yikuri uwar gida nima wasa kawai nayi muje dai mukwanta yana rike da hannunta harsuka hausaman gado nace ashe dai har su dad an iya soyayya wink
washe gari mom koda tasamu mairo tayi amai duk ta fita hayyacinta wayarta tadauko takirah fadil”” yana shirin zuwa asiviti yaga kiran yadauka assalamu alaikum mom wslm fadil kana ina dan Allah yace ina gida yanzu zanfita meyake faruwane????
balokacin bayani dan Allah idan kanada kayan aiki agida kazo dasu maryam ce batada lfy “”yace mom haydar fa??? idan bazaka zobah inkaita asiviti kawai cikin daga murya tayi maganar takashe wayarta gefen maryam tazauna tadafe kanta yarinya kamar tamutu saboda masifar haydar baifi minti biyar ba saigashi yashigo dama yasaba shiga gidan tanajin sallamarsa tafito tace muje kaganta tare suka shiga dakin
shikanshi yafirgita ganin yanda takoma babata lokaci yace inazuwa yafita baijimaba yadawo da abun karin ruwa yasaka mata tare da allurai aciki harda allurar barci bajimawa tayi barci yasauke ajiyan zuciya yakalli mom yace mom meyake damunta?????
tanisa cikine da itah saida fadil yakwalalo ido yace to ina haydar yake???? tace kadaina yiman maganar haydar wlh yabataman rai anan takwashe komai tafada masa shima kansa yadafa yana fadar innalillahi yanzu mom yana ina????
nasanar masa tunjiya dana korashi baidawobah yajinjina kai mom kiyi hakuri kinsan haka haydar yake gaskiya nayarda bakaramin so haydar yakewa maryam bah insha Allah zansameshi inmasa magana agaskiya banji dadin faruwar hakanba yanzu gashi yana nema yasaka matar sa cikin damuwa..
yadade suna magana sannan yamike yace mom zanwuce wajen aiki idan ruwan yakare saiki cire mata idan tafarka taci abinci anjima andawo indubah ta mom tayi masa godiya sannan yatafi wayar tace tayi kara tadauka saitaga nmbar kursum tadauka
hello mom ina kwana tace lfy qalau ya gidan da maigidana tace kalau mom anmaki kishiya”” mom tayi murmushi masha Allah yaushe???? tace jiya da dare wlh”” to Allah yaraya tace ameeen ashe mom kinason kishiya mom tace nasamu yar aikin gidana dai bakishiyaba sukayi dariya sannan suka sallama
mom ce takirah dad tafada masa yace kice dai infara kai toshi anhaifaman mata maijini ajika sukayi dariya tace dadin abundai da tsohuwar zuma ake magani yayi dariya yace banda wannan zumar kam”” haka kace tosaikaga wanda zaimaka girki yau”*ah ah uwargida aike ta dabance
sukayi dariya sannan sukayi sallama saida ruwan suka kare mom tacire mata bata farkabah saibayan azahar jikikam alhamdulillah taji sauki mom takaita tolet tayi wanka tayi sallah sannan taci abinci mom tace sannu maryam yanzu meyake maki ciwo???’kai tagirgiza mata itah damuwarta daya taga haydar
Aisha. Ibraheem
[3:00PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
79
Batajin akwai abunda zaiyi taji batason ganinsa tanason tambayar mom ina yake kuma tana tsoron kada mom tayi mata fada zuwa dare saiga kiran zulaihat tahaihu itah ma mace zokaga murna wajen is”hak dayake tunda tayi haihuwar fari abu baizo daraiba bata sake samun wani cikinba sai yanzu
su Aisha da na ima suke kan layi asiya kuma haryanzu shiru farida ma tasake haihuwa namiji habib fiddausi ma haka mace da khadiya mace fiddausi kausar yar khadija fatima zainab namijine tahaifa lirwan sunansa family dai saicika yakeyi kuma suna zamansu lafiya
haydar baisake marmarin shiga gidan ba sai bayan kwana uku amman muhd kullum saiyaje kuma mom bata hanashi ganin maryam ba saidai maryam din daya shigo saita kama kuka tace yafita dole yake fitah badan yasobah kokadan bayajin dadin kukanta harcikin ransa yakejin kukan yaudai haydar anhuce bayan la asar yashigo mom tana zaune cikin falo yayi sallama
ta amsa babu yabo ba fallasa yasamu kasan yazauna yatankwashe kafafuwansa kansa yana kasa yace mom ina wuni tace lfy qalau sarkin kishi harka hucene???? yayi murmushi yadan sosa kai mom kiyi hakuri da abunda yafaru wlh nakasa rike kainane shiyasa gaba daya nafita hayyacina
mom tanisah banda abinka haydar aibaidace laifin muhd yashafi maryam ba itah ina ruwanta???’kaine da bakar zuciya wlh kabataman rai ranar sosai yanzu daka kashe yar mutane aida sai inga ta karyar kishi””
mom daina danganta mutuwa da maryam dan Allah amman banji dadi dakika kirah fadil alhalin ina gida yaje yasameni yanatamun masifa baisan abunda zuciyata take cikibah yanaso yasake dadamun wani”
aigaskiya yafada maka idan kana rage kishin nan kama rage “”insha Allah mom amman gaskiya kiyiwa muhd shamaki da matata agaskiya bazan daukaba “”waikai haydar banda abunka matar kacefah duk wani abunda zaiyi ga banza tunda bata sonsa kaga haukace kawai yake””dukda haka mom aja masa kunne kinsan yanda zaki masa katanga da itah tunkafin inyi aika aika” yana kaiwa nan yamike yayi hanyar dakinta mom tabishi da kallo tana girgiza kai Allah yarage maka wannan kishin
ahankali yaturah kofar yashiga da sallamarsa tana kwance saman gado idanuwanta suna kallon sama amman talulaya duniyar tunani yau kwana uku bata saka haydar a idon taba tanason ganinsa batamasan yashigobah saida yazauna gefenta taji antabata sannan tazaburah tatashi zaune ganin haydar yasa tasauke ajiyan zuciya
sannan. ta duke kanta yasake matsowa yadago fuskanta saiyaga tana hawaye rumgumeta yayi yana lallashi plz kidaina kuka kinji kalbina “” mekuma yafaru kiyi hakuri akan abunda naimaki wlh kishine yaturani kiyafeman ” shiru tayi yadan dago fuskanta kinyi hakuri???
nibakaman komaiba ya haydar laifinka daya kauraceman da kayi shinkokasan zuciyata tana nunfasawane tare da taka??? rayuwata tana cigaba da wanzuwane tasanadin tattalinka muddin baka tare dani duk wani tubali daka gina na rayuwata zai rushe
tamaida kanta takwantar akirjinsa ciwonda yake jikina baya damuna sama da rashinka kwana ukun nan danayi bangankabah na kwammace acikin kabarina nayisu naso mutuwa ta riskeni kafin kasameni meyasa kamun haka tasake fashewa da kuka
yasake kankameta kiyi hakuri kinji maryam insha Allah hakan bazai kuma faruwaba wannan ma kaddarane”” nasanda kaddara amman dason ranka kasan bazaka iyah cigaba da kula danibah tunfarko meyasa kakoyawa gangar jikina tarayya dakai”” kasan bazaka dorebah meyasa baka barni ayanda nasaba rayuwataba”‘ ninagaji wlh kana wahalda zuciya dayawa”
bakinta yarufe plz kidaina fadar haka kinji wlh bazan sakebah nayarda kowanne hukuncine kiyankeman”” amman ina maibaki hakuri nikaina nashiga damuwarda kika shia fiyema da taki inason jina akusadake akoda yaushe bana fatar wani abu yanisantar dani daga gareki wannan abu daya faru kaddarace dama Allah yaruboto hakan saiya faru amman inajan hankalinki Allah yabaki wani irin miji mai tsananin kishi banyarda wani yasamu abunda na mallakaba
muddin nina fara mallakarsa banason wani yasamu irinsa musamman ke”” kinzama wani haske azuciyata banajin zan yarda wani yarabo koda inda kike ki fahimceni inasonki sosai” tasake kankameshe”” yayi murmushi alama tanuna anhakurah tadago fuskanta dama ashe kina sona??? dariya tayi takai masa dukan wasa
yagoce plz kiss me in my lips jst 2 kawai bada yawaba””tayi murmushi to rufe idonka sannan yace angama kalbina yarufe idonsa. tasakar masa kiss har guda uku na hudune tayi masa maidan tsayi ahankali yabude idonsa yarungumotah
bantambayeki yajikinba da bebyna?? ta rausayarda kai munji sauki sosai amman muna tattare da kewarka”” yashafo cikinta. maryam taimako nake nema” name kenan ya haydar”” yasake jawota jikinsa zansamune?????
Aisha. Ibraheem
[3:42PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
80
Sosai makuwa indai inada halinyin abun mezai hana” yadan rage murya abun nake kwadayi wlh duk amatse nake kwana uku fah ai nayi kokari ataimakaman dan Allah””nasan mom bazata bari infitah dakebah amman kisan dabarar da zakimana mudan fitah koda sau biyune indan leka kindai gane””
jikinta tajaye waime yasa kaibakada kunya kuma kana ganin haryanzu jikina sai ahankali”” nasani amman nasan zaki iyah taimakona ta wannan hanyar dan bazakiso inshiga wani halibah”mikewa tayi tana turo baki tayi hanyar waje yabita dasauri yana kiranta ina harta fitah yadafe kansa
agaskiya ina bukace dake meyasa zakiman haka nasan mom bazata banike yanzubah tunda tasan abunda zanyi””tashi yayi yabi bayanta koda yaje tana kusa da mom tana kumburi “”mom takalleshi tace mekuma kayi mata da zuwanka”” yawaro ido banyi mata komaibah aiga tanan ki tambayeta
cikin zuciyarsa yace lallai yarnan kinaso kijawoman jafa i wlh ko acikin gidan nan ne saina korarda sha awata aigidan mune””mom takalleta gayamun meya maki maryam”” saida takalleshi sannan takalli mom tace wai mom dannace masa ina sha awan shan ice cream yakaini dakaina daganan insha iska nakwana biyu kwance shine yace wai bazaije danibah saidai yaje yasiyoman
mom takalleshi saboda mene bazakaje da itah ba???? yace mom kina ganifah yaron cikine da itah banaso tana yawo ta wahalmun da beby”” ta harareshi to sarkin son yaya to wlh saikaje da itah jeki dauko hijabinki inga inda zaka fitah gidan nan batare da itah ba
yabata fuska nidai mom zaki kwabsaman wlh tace kaci gidanku tosaidai kafasa tafiyar gaba daya mairo tamike saida tamasa gwalo sannan tayi daki bajimawa tadawo tare da hijab anan tasakashi tafita mom tace idan akasha arikowa yan biyu tace toh mom abaya yabiya kamar yayi kuka saida yafita sannan yayi ihu yayi tsallen dadi
dasauri yakasa inda take yabude mata mota tashiga tunda yatada motar sukabar gidan taketa masa dariya”tace ya haydar harnaga ka tsure halan kadauka mezancewa mom yayi murmushi yakalleta wlh nadauka zaki fada matane harnaji kirjina yanata buga watayi dariya ai wlh kaban dariya sosai ashedai komaza sunada tsoro yayi murmushi todakumafah mezai hana amman kada kidauka wai komai mukejin tsoro ah ah ai tsoro sai mata
yadaga mata girah Allah muma bamuda wani tsoro yauwa ya haydar zanje suna gidan sister jibifah””babu inda zakije Allah”” kai yayana kowafah zaije”yakalleta ta kasan ido yace hardani????? la bancebah aiku maza baku zuwa taron suna naji ance harda dj za ayifah gidan sister zulai”
ohh kice rawa kikeso kije kiyi tobazakibah saina gani””tariko hannunsa daidai yayi hon kofar gidan maigadi yabude masa yana kawo gaisuwa ya amsa masa sannan yakunna kan motarsa ciki yayi fkng yazagayo yadauketa kamar karamar yarinya
tazagayoda hannunta saman wuyansa harsuka shiga cikin gidan baidireta ko inaba sai saman gado yawuce wajen drowa yacire kayansa yadawo kusa da itah yazauna suka kurawa juna ido natsayin lokaci mairo ce tahurah masa iska yalumshe idonsa sannan yajawota jikinsa daganan wasa tasauya
sun darji soyayya son ransu haydar yasake tabbatarwa kansa bayan mairo babu abunda yafi soyuwa dashi aduniya yayarda itah ce linzamin zuciyarsa itah kanta haydar yashayar da itah zumar mai wuyar fada bayan komai ya lafa yajawota jikinshi yana zubah mata godiya””
banda murmushi babu abunda takeyi yace kinga kada dare yayi muje muyi wanka shiyadauketa har bandaki sukai wanka tare suka fito suka shirya yace yanzu mufara biyawa asiyi ice creem ko””tadaga masa girah yace kinsan wani abu kuwa
ah ah saika fada yace nafarayi mana shirye shirye zuwa garinku wani ihun dadi tayi sannan ta kankameshi””yace kijirah mana bari murna yarnan da sharadifah”” tarausayarda kai fadi sharadin inji””yauwa zan dauki hutu asiviti tunda ga fadil nan zamuyi wata daya acen amman wlh dakinmu zamu sauka banyarda kikoma cikin gidaba
fuska tabata kai yayana yanzu dan bamuda kunya saimu kwana daki daya??? ido yazaro ah tomekike nufi ai abba dayabanike badan intasaki gaba ina kallonkibah kamar madubi yashafo sumar kansa yabanike dan inyi ehem ehem kindai gane””kuma gashi har anci ribah yanuna cikinta
takai masa dukan wasa yagoce yana dariya kokinga laifina kemafa yanzu kinsan dadin harka yarinay wlh ba magar wasa idan harbaki yarda waje daya zamu zaunabah saidai afasa tafiyar” shikenan nayarda yazanyi tunda inason zuwa””
yauwa kokefah amman kuma wlh idan mukaje kikaki zuwa narantse maki kwana biyu zamuyi incewa abba zamu dawo” kaidai son mugunta aikuma nace nayarda muje nidai yace yauwa zanhole nikam kafin mudawo garin nan itah dai batace masa komaibah harsuka fito saida suka biya yayi mata shopin harda ice cream mai yawa sannan suka koma gida yanayin fkng yace
ammanfa kin iyah wayo yanzu kinga munsoye mom bata ganebah dan Allah gobema kice gwaba kikeso tana dariya tafito tace ankidin shima fitowa yayi yace aitaimakona zakiyi suna dago kansu tar akan muhd gabansa sai dukan uku uku yake ganin abarsonsa cikin nisha di tareda haydar
Aisha. Ibraheem
[4:23PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
81
Me maryam take nufi tafison haydar dani kome??? ni idan naje dakin kuka take man amman gashi haydar har fitah sukayi yawo kuma idan sabone yadace ace dani tayi sabo tunda kafin haydar yadawo tar yasamemu
yadago idanuwansa dasukayi ja yazubasu akan fuskar mairo bakinta tamera tabita gefensa tawuce shima haydar baikoma kansabah yarabashi yawuce sukabarshi nan tsaye tare sukayi sallama cikin falon mom haydar baisamu damar karasa sallamar shibah ganin hameeda tayi zumbur ganinsu tare da mairo
kafin mairo tasamu wajen zama hameeda ta dauketa da mari”gidan ubanwa kikaje da mijina??? kafin tarufe bakinta haydar dasauri ya karaso inda take shima yadauketa da mari yace gidan ubanki naje da itah yar iskar yarinya haka kurum zaki mareta datayimaki me
gyalenta tacire tadaure da kugu wlh yau sainaci ubanta cikin gidan nan koni danake matarka bakataba daukata katafi dani yawoba tayi cikin mairo datake dafe da kunci ta karbe ledar hannunta ta watsa matasu ga jiki dahauta da duka mairo kam dukewa tayi tana kuka
haydar yayo cikinta yana fallah mata mari waike wace irin dabbace marar hankali zakihau yar mutane da duka dan kawai nafita da itah motar ta ubankice”” naji motar bata ubana bace amma ai motar yaya nace kuma mijina dan haka babu wata kazama yar raino data isah tarabi mijina batareda na fitar mata da jinibah
wlh sainayi sanadin mutuwarki yar iska diyar talakawa tayi cikinta haydar yasake fincikota ya wurgata saman kujerah mom ce taji hayaniya tasauko kasa da sauri ganin abunda yake faruwa tabuga salati hameeda lafiyarki kike sa insa da mijinki
menene yake faruwa wanda bazaki fadaman ba. tana kuka tace mom jibifah kiga shine yadauki wannan yar iskar yarinyar suka fitah yawo kuma suka dawo suna dariya tunda suka shiga motah ina ganinsu shine yabude mata motah nida nake matarsa baitaba fitah dani yawoba tunda muka dawo kasar nan yamaidani dani da banza duk daya
waikuma dan na mareta har zai mareni akan wannan diyar maciyatan yar raino mom tazaro ido mari kuma hameeda??? yayo cikinta mom tarikeshi haydar kaga wuce masallaci “”mom kibarni nasaita mata hankali nadauketa din ta isah ne shiyasa kebakida wannan damar kisani kikara sani natsaneki banasonki kekanki kinsan kakabaman ke kawai akayi banza kawai
wai haydar ba magana nake makabah kafitah kawai yana hararar ta yaduka yakwashe kayanda tazubar na maryam yariko hannunta harcikin daki ya aje mata kayan yazaunar da itah saman gado pls maryam kidaina kuka kinji komai zaizo karshe insha Allah batace komaibah tace kaje masallaci kada karasa jam i yace shikenan nagode yatashi yafita kokallon inda take baiyibah yafita bangaren yanufi bangarensu
mom tazaunar da itah saman kujerah tace ina hankalinki yake da tunaninki hameeda yanzu gashi kinja kunyiwa kanku tone tone komai naduniya dan hakurine baidace kina daukar abuda za fibah kishi ba hauka bane kuma dakika gansu tare nina aikesu susiyowa yan biyu ice cream
kinsan tamkar yar uwarsa yadauketa danshine yazo da itah daga garinsu yakawota nan kuma kafin abashi itah amana akadamka masa kina ganin yadace yayarda amanarda akabashi yarinyar nan ko lafiya batada itah amman zaki hauta da duka kisan halin mijinki mana duk abunda yake tsakaninku dakanki zaki warwareshi batareda kowa yajikubah
ina gujemaki fushin haydar yanzu gashi kinja haryakaida marinki kiyi hakuri kinji kuma insha Allah zanyi masa fada yadaina irin abunda yake maki tashi tayi daga saman kujerah tafita fuuuuuuuuu batajirah mom tagama nasihar da zatayi mataba
tana shiga gida ta lalabo nmbr gwaggo tana dauka tafashe da kuka gwaggo tana zaune tamike tana tambayar lfy hameeda kike kuka???? gwaggo wlh nagaji da zama gidan nan kisa kawai ya haydar yasakeni”” innalillahi ke wace irin jakace kina cikin daula zakice asakeki kanki daya kuwa?????
wlh momy ina cikin tashin hankali tunda muka dawo india gaba daya haydar yajuyaman baya kinsn dama baya sona kullum cikin wulakanci yakeman idan nayi abinci bayaci kullum saidai yaje wajen mom dinsa yaci yanzu kuma abunma yawuce nan yau harda daukar wannan yar matsiyatan maimasu raino yakaita shopping
gwaggo tabuga kirji shopping fa kikace badai wannan shigiyar yarinyar ba???? itah wlh momy nikuma shine namareta””kimmun daidai wlh inda nice saina lakada mata shegen duka samun waje dantaga kwana biyu nadaina zuwa gidan badan kowa nabar zuwa gidan ba saidan ke kada aga nacika zarya. ace wata kirsa nake koyamaki amman wlh zan sameta sainaji idan gidan na ubantane
Aisha Ibraheeem
[6:22PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
82
Kwantar da hankalinki kin mari banza inga ubanda zairama mata yar matsiyata kawai tasake fashewa da kuka gwaggo tace yanzu akan wannan banzar kike bannar hawayenki har kina cewa wai ince yasakeki??? momy bahaka bane marina fa yayi akan namareta haryana cewa wai kakaba masa ni akayi
gwaggo tace marikuma??? marinki kikace yayi kuma agabanta??? ah wlh momy marinda yamun yayi guda goma innalillahi wa inna ilaihir rajiun kice zaman bauta kike agidansa jaka na aurah masa halan dazaiyita dukanki akaan wata yar talakawa to ina uwar tasa take????
tana gani agabanta ya mareni amman kuma hakuri takama bashi “” saida gwaggo tacika baki tazubar jar uban nan gani nan zuwa yausai ansanar dani idan jaka na aurah masa kishare hawayen ki ganinan tafe. takashe wayar tanata sababi da zage zage
taziri gyalenta sannan takirah wayar muh”sen kirah daya yadauka yakara akunnensa tare da sallama bata amsa sallamarba tace masa kana ina????yace momy hanyar zuwa masallaci baima karasaba tace maza kazo ina nemanka”da mamaki yace komenene mom amman kina bari inyi sallah har antayarfa shikenan da ansallame kazo ina jiranka yace toh sannan takashe wayar taci gaba da ciccika sai zage zage take har makotah ana jinta
malam ne yayi sallama yashigo yasaki baki yana kallonta lafiya kuma hjy kiketa tada jijiyoyin wuya kekadai babu kowa dawa kike fada???? dawa nake banda wadan cen debabbun albarkar na aura masu yata sun maida itah jaka yanzu gidan zanje inji dalilinda yasa zaimaidaman ya jaka yadinga dukanta kamar baisan ciwontabah
malam yayi murmushi wai akanwa kike wannan zancen badai gidan yayanki zakiba???? shifah wlh sainaji dalilinda yasa yake dukan mun ya idan su sunajin tsoron sa nibanajin tsoronsa “” malam yayi murmushi to amman kina bari har gobe yanzu nasan baidade da dawo wa gidaba
wlh bazan bari har gobeba idan nabari aizasuga kamar bandamubah”” nidai inaganin dakinbi komai ahankali watakil laifitamasa kinama iyah yarda da maganar yarki???? tobazan yardaba duk shekarunda akayi tataba kirana tace yadaketa sai yanzu danhaka bazan karyata yatabah ”shikenan mudai namu idone yakaba kansa yashiga cikin daki. taci gaba da masifarta
tuntanayi harta gaji takoma tazauna muh”seen baishigo gidan ba sai 8;30 cikin falo yasameta yanayin sallama tace kaikuma ka kauta tundazu inazaman jiranka kashanyani muje yanzu kakaini gidan su haiydar
gidan su haydar kuma yayi tambayar da mamaki danbaitaba saran hakaba yakalleta kekuma mezakiyi gidan su haydar da dare??? ubanka zanyi nace ubanka zanje inyi gashicen cikin daki zaka kaine ko inje innemi adai daita???? yi hakuri mom muje yamike tabi bayansa
yabude mata tashiga shima yashiga yatada motar baice mata uffan ba harsuka kai gidan yayi hon maigadi yabude masa yashiga yayi fkng tun kafin yatsaida motar tabude murfin tafito tayi hanyar bangaren alhj bakin bangaren mom tayi cikibis da haydar
gabansa yafadi badai hameeda gwaggo. takirah ba lallai tatokano masifa yaduka gwaggo ina wuni to tabbatacce ina ruwanka daya na wuni??? wato na aura maka ya kazo kana dukanta ga baiwa nakawo maka”” gwaggo mekuma akai mata
uwarka akaimata nace uwarka akai mata harnizaka tambaya me akaimata balaifinka bane uwarkace tadaure maka gindi bari inje inda take dan itah ce daidai dani bakaibah tawuce fuuuuuuuuuuuuuu anan tabarshi duke tunda take maganar kansa yana kasa saiyanzu yadago
Aisha. Ibraheem
[7:01PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
83
muh”seen yada fashi yadaga kai ya kalleshi yamike yabashi hannu suka gaisa yace kayi hakuri haydar duk da bansan menene yafarubah amman nasan hameeda ce batada gaskiya kasan halin momy bata ganin laifin hameeda kodakan
ina yawan sanarda itah illar sangartarda yaro yanzu ga irinta nan yarinya tataso babu wata cikakkar tarbiyya wlh ninamaga kokarinka dakake iyah zama da itah wlh danine da tuni na korata saidai duk abunda zai faru yafaru wlh kodatake kanwa ni kwata kwata bata gabada dabi un ta haushi suka bani hatta itah kanta
tana shiga bangaren alhj tasameshi da mom da maman zulai””bako sallama tashiga falon maman zulai tace lfy hjy hure kika shigo kamar anjefoki??? ina ruwanki tsohuwar muna fuka ta nunasu da yatsa aiduk kanku muna fukaine wajen yayana nazo ko akwai mai magana” basuce komaibah suka maida kallonsu wajen alhj daya rike baki yana kallonta shikam yarasa wane irin haline da itah
yace hure zauna.. sannan tazauna yace menene yake faruwa???? tace yanzu saboda Allah yaya haydar yarasa wazai daka sai kanwarsa kuma matarsa akan wata banza mairaino mom tace kafin yamareta ai itah tafara marin… alhj yadaga mata hannu alamar tayi shiru
yadauki wayarsa yakirah haydar din yana tsaye da muh”seen yadauka yace kana ina??dad ina cikin gida toje kakira hameeda kutaho tare yace to dad sannan yakalli muh”seen kajiko abunda nake fada fada maka bari inkirata yayi hanyar bangaensu kwance yasameta saman kujerah tana taunar cingam wato tasan mugum abunda tayi dole taji dadi tana ganinsa tamike tsaye
wasu marin yazabga mata kyawawa guda biyu ya nunata da yatsa wannan shine tukuicin zaginda gwaggo tamun kuma kije dad yana kiranki kindade baki cewa gwaggo na marekibah harya juya saikuma yatsaya yawaigo idan kin haihu kada kifasa fadin irin zamanda mukayi dake nikuma wlh saina sanardasu duk baunda kike aikatawa kuma zanfada masu niba amatsayin budurwa aka kawoman kebah dan haka zankarah aure yana kaiwa nan dazancensa yafita
kara kaka kaka tayi aniyar fada masu irin zamanda suke dashi yadaina kusan tarta tsawon wata biyar amman kuma idan nafadamasu shima zaifada masu watakilma dad yace yasakeni to ribar menaci idan har akarabani da haydar????
jiki asabule tafita zuwa bangaren dad tayi sallama tashiga kanta yana kasa tasamu kusa da gwaggo tazauna haydar yana kusa da muh”seen dad yayi gyaran murya ya kirah sunanta tadago ta kalleshi yace mekika kirah kika fadawa mamanki????? tayi shiru takalli gwaggo takalli haydar
shikam harararta kawai yake ganin batada niyar magana gwaggo takaimata duka ba tambayarki akeyibah kifada masa kada kiji tsoron komai”tana in in na tace marina yayi”” dad yace dakika masa me???? takumayin shiru saida yasake maimaita tambayar
tace waidan kawai na daki maiyiwa mom raino” dad yace tomeyasa kika daketa???? takumayin shiru yadaka mata tsawa nace meyasa kika daketa???? abba tare nagansu da yaya haydar sunfita cikin mota”ya nisah sannan yakalli haydar yace kaikuma meyasa kamareta””yace dad dan kawai tagan mu tare mom cefah ta aiketa shine tace inkaita dan driver baya nan shine kawaifa dan taga munshigo gidan tadauke yarmutane da mari wai saita kasheta tawatsa mata kayanda muka siyowa mom kuma tahauta da duka shine nikuma na mareta saboda ina mata magana tadaina amman taki
shiru ne yabiyo baya dad ya kalli gwaggo tokinji abunda yafaru yanzu wanne hukunci kikaga yadace adauka????ni ba wannan ba yaya tace tunda suka dawo daga india baya kulata yafita harkarta idan yadaina sonta sai araba auren kowa yahuta. haiydar yace wlh danaji dadi dakun taimaka mani cikin zuciya yayi maganar
hameeda kam cikin sauri tadago kai tace nidai inason mijina muna zaman lfy”” dad yagyara zamansa yana murmushi gwaggo baki bude takalleta da mamaki”” labdi jam nizaki tozarta”” takalli dad shikenan nizan koma tunda haka
tace amman kisani nazone dan in kwatar maki yancinki amman tunda kin watsaman kasa a ido agaban wadan nan tanuna su mom kinkyauta kuma kada insake ganin kafarki kin kawoman kararsa koki kirani ta kalli muh”seen kaikuma tashi muje kakaini gida yayi masu saida safe tawuce yabi bayanta
wlh momy danasan wannan abun zai kawoki dabanzobah gashi nan yanzu tatozartaki ta karyata maganarki ba ashiga tsakanin mata da miji”” to malam idi naji ko wa azi zakaman???? idan shizakaman sai in nemo littafai kasaka lasifika kowa yaji
Aisha. Ibrraheem
[8:04PM, 11/24/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
84
Aibansan kafara wa azibah”” Allah yahuci zuciyarki mom tayi tsaki tabude motar tashiga shima yashiga yaja motar maigadi yabude masu gt suka fita
dad yayi masu nasiha suyi hakuri zaman aure hakuri akeyi dashi kowa yace zomu zauna yace zomu saba kai haydar kaine babba hankalinka da nata badayaba kasan mata ba hankaline dasubah koda ta girmeka zakaga hanklainka yafi nata
mu akasani da hakuri idan mutun bayakai zuciyarsa nesa baza aizaman lafiyaba kana ganin yan uwanka har yau babu wanda yataba kawo karar dan uwansa sai ku kuma wannan yazama nafarko na karshe kekuma idan yasake yimaki magana kibar abunda kike kikaki bari yakawo kararki sainayi mugn saba maki tashi ku baceman da gani mikewa tayi tana kuka tafita
haydar yaduka Allah yahuci zuciyarka insha Allah zankiyaye Allah yakara maka lfy yamike yayiwa maman zulai saida safe yamike ita ma mikewa tayi tadau abdul tayi masu saida safe tayi bangarenta
haydar bangaren mom yanufah bakin kofar yayi cikibis da muhd yayi masa kallon tuhuma shikuma yaraba ta gefensa yawuce”” cikin sauri yakarasa cikin falon yayi dakin mairo yasameta tana kuka dasauri yayi kanta yana tambayarta lfy
tayi banza dashi duk yabi ya susuce yanata tambayarta lfy haba maryam meyasa zaki shareni bakisan halinda nake cikibah kitaimaka kiyimun magana taci gaba da kukanta.. haba ya isah haka haba!!! yakike so inyi da rayuwata maryam dame zanji da kukanki koda kishin abunda akai maki yanzufah naga muhd yafita dakin nan
ganin batada niyar dainawa yasa yasassauta murya yazauna saman gadon yajawota jikinshi yana lallaminta hartasoma daina kuka waimeyasakaki kuka naga koda nabarki ba kuka kikeyibah wani abu yayi maki???
tashare hawaye ya haydar wlh nagaji kana ganin abunda matarka tamun sannan ga dan uwanka yadameni ni wlh nagaji zan sanardashi inada aure”ido ya zaro kisanar dashi kuma maryam baki hango abunda sanardashi din zai haifar???
bandamubah gwanda kowa yasani duk hkuncinda za a yanke ayankeshi ni wlh nagaji takara shigewa jikinsa yadan bubbuga bayanta alamar lallashi kiyi hakuri kada kisanardashi kinji dan Allah kikarah hakuri insha Allah gobe zamubar gidan nan kafin mudawo kinga kurah tadan lafa dakyar yasamu ta hakurah.
da safe kishirya saimunbiya kinyi siyayya sannan muwuce tace toh”saida yamatsa mata taci abinci sannan yafita yakoma bangarensu baisamu hameeda falon ba dama yasan bazai sametaba yahada kayansa duk abunda yake bukata har kudi
yakirah fadil yafada masa komai yace. bayanzu naso tafiyarba amman abun yadameni gwanda muje tasamu takarasa warware wa yace ah ah haydar kakwantar da hankalinka dagobe da jibi duk daya hankali kwance yafi kutafi a hargitse kuma kaga yanzu idan kashaidawa dad zaiyarda da maganar gwaggo cewa abunda kakewa hameeda gaskiyane
yajinjina kai shikenan fadil bari da safe zanfada mata mubari har ayi sunan yar kursum yace yauwa kokaifah sundade suna magana sannan sukai sallama haka kuwa akayi washe gari yafada mata tace bakomai dama tanason zuwa suna
kwana biyu akai suna yar kursum karima yar zulaihat saudat su gwaggo basuje sunaba yayane kawai suka tafi harda mairo ma taje duk da hameeda taje shiyasa kwata kwata bata saki jikintabah dari dari takeyi ganin duk abunda tadauka sai hameeda ta amshe waibatason zama kusa dayar talakawa abunda taci itah ma taci
adaddafe tabari akai la asar bata jirah driver ba tatari adaidaita sahu yamaidata gida kofar gida tahadu da haydar dashi da fadil suna maganar yana jingine jikin mota yataso dahanzari zaimata magana ta daga masa hannu tayi shigewarta gida
yajuya wajen fadil da mamaki fadil yace hmm tokaida mezakaimata waikai meyasa bakada fahimtane?? haba fadil kana ganifah dan adai daita tahau ina da motah amman takasa sanar dani inje indaukota” tanada wayane????
yace ah ah amman aibazata rasa wayarda zata ara takiranibah yace tasan nmbr kane kokun taba wayane???? nanma yace ah ah yace kadinga tunani kafin yanke hukunci kaidai nalurah dakai indai akan kishine baka aiki da iliminka yanzu kana ganinta ai hawayene a fuskanta dadukkan alamu akwai abunda akai mata
yanisah inazuwa dan Allah cikin gidan yashiga kaitsaye dakinta yanufah yasameta takifah kai tana kuka dasauri yakarasa yana tambayarta lfy??? haba ya haydar waime iyayena suka tarema matarka akullum cin mutuncinta baitsayawa akan kowa sai akan iyayena
duk abunda zatamun tamun nida tagani basaita sako iyayena ba sunacen suna neman abunda zasuci ana nan anazaginsu na tabbata da agarin mu yayiman aure bazai samu tukuicin zagibah bakinta yarufe kinga ni banason wannan maganar wazai aureki agarinku nafada maki sabodani Allah yayiki kiyi hakuri zanyi maganinta ya mike afusace……………
Aisha. Ibraheem
[6:52PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [7:33PM, 11/29/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
006
Taro yayi taro maijego sai shiga da fice take tsakanin cikin gida da wajen maigidanta haydar baki yaki rufuwa jinsa yake kamar ango baitaba lurah dakyan yayansaba saiyanzu dayaga mamansu cikin walwala anyi barin kudi kamar hauka duk wanda yazo bikin saiyakoma da kayan arziki anyi rabon darduma shaddodi atampopi leshi
kayan yara takalma hijabaiyya wayoyi kai agaskiya nikaina nayi mamaki barin kudinda akayi komai da aka raba yanada tambarin sunan yaran wani kuma pic nasu kowanne daban akaimasa nasa yaba yayyenta mashuna boza sabbi hul anci ansha sainama ake wucewa dasu zuku zuku ranar hardare babu wanda yarumtsa
washe gari su mom suka koma shikam haydar yace yana nan tare da matarsa saida yayi sati daya sannan yakoma gida idan kaga haydar yanzu zakasan yana cikin jindadi yanasauka yakwaso pic din da suka dauka wajen suna da mamansu da yaran da kayanda aka rarraba yasamu hameeda tana zaune cikin falonta yayi sallama ta amsa da sakin fuska gabanta yazube mata pics din
bakaramin rudani tashigaba ganin abunda yake gabanta ido tazaro ya haydar wai dama…. tawarkene???? da in in na tayi maganar yasaka hannu cikin aljihunsa yana mata kallon gefen ido yace aigashi kingani “” nakawo makine kitabbatar da haka duk wani wanda bayasona da karuwa kuma bayason abunda nakeso nima bana sonsa
yana kaiwa nan dazancensa yawuceta yana murmushi dama yayi hakanne ya tabbatarda abunda yakeson sani kuma yagane dasa hannunta”” yana fita tadauko pic din tana dubawa tadafe kanta nashiga uku kaddai haydar yagano nice nayi wannan aikin??? zama baiganoniba
dole inkoma wajen boka duk da banida kudi yanzu wlh ko arone sainayi mayafinta kawai tadauka tahau mota sai wajen boka bakaramin tashin hankali tashigaba samun labarin aiboka yahaukace tuni jiki bakwari tadawo gida komai yahargitse mata lallai akwai babbar matsala
alhj hamza ne agaban boka bayan yagama shaida masa dalilin zuwansa yanisah ni komaine wlh kayi boka duka narasa gane meyake faruwa tuni namatsa mata tarabu da mijinta in aureta amman tace wai tanason mijinta tunda narabu da itah harkokina saijada baya suke
komainawa ya tabarbare kuma bansan garinsubah bansan inda takebah nmber ta damuke waya da itah tunda tatafi tasauya layi kataimaka mani dan Allah boka.. wata tsawa yadaka mashi kaiiiiiiiii ba afadan Allah anan wajen
tuba nake boka tuba nake” yakece da dariya hahahahahahahh ainafada maka muddin karabu da itah tokomainaka zaitafi tauraruwarta tanada karfi dan haka hanya dayace kayi gaggawa dawowa da itah cikin rayuwarka
taya boka yarinyarda bansan inda zansametaba???? hahahahah akwai hanya mana ninasan yanda za ayi kasameta tana cikin garin nan dasauri alhj hamza yakalleshi kwarai kuwa kuma aiki akanta bazaiyi wuyaba dan asake take bata damu da addua ba danhaka aiki akanta saukine dashi kamar shan ruwa puhahahahahah
yadaga hannu sama yana wasu sanbatu saiga wata kwalba dawani abu yana motsi ciki yamika masa kaga wannan zuciyar tace aciki kariketa dakyau kakasance kana yawo da itah duk inda kake dakayi bukatarta
Aisha. Ibraheem
[8:06PM, 11/29/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
007
Toka kalli wannan kwalbar kakairah sunanta sau uku duk inda take koda abayan duniya take saitazo wajenka kaikoda tsakiyar darene saita zo inda kake yana murmushin mugunta yakarbi kwalbar yana jujjuyawa yana murna hakika yasamu aunda yakeso da wannan zaisamu hameeda tadawo gareshi
yakalli boka yakece da dariya boka nawane kudinka??? yace dubu dari uku yayi dariya ankarah maka za abaka miliyan daya”” nan take ya aje masa kudin yana godiya yakoma gida cike da murna da farinciki sabon gidansa yawuce ganin har dare yayi yayi wanka yayi sallolinda baiyiba naranar amman buga buga danshi kanshi baisan abunda yake karantawabah
dan ba wani cikakken ilimine dashiba yana kwance saman gado yayi shiru yana tunanin zancen boka tashi yayi dasauri yadauko kwalbar ya kalla yakirah hameeda hameeda hameeda yakece da dariya hahahahhahahahahh
tana kwance cikin dakinta kamar anmintsileta tashi tayi tahau yamutsar loka saida tayamutse kayan kaf sannan tagano sim din tana ganinshi tasauke ajiyar zuciya dasauri tasakashi awayan takirah nmber sa yana ganin kiran yaki dauka wai saiyaja mata aji kamar tayi kuka
dan Allah kadauka my lov i need help zan iyah mutuwa wlh idan bangankaba saikirah take amman yaki dauka saida tayi kirah goma sannan yadauka kafinma yayi magana saida yaja aji tanata magana yayatsina fuska ya akayi???? my lov kana ina dan Allah???? yadanyi murmushi ina ruwanki da inda nake bakince infitah hanyarkibah
dan Allah kayi hakuri kasan bisa kuskure nafadi hakan wlh nasan bankyautaba amman kayi hakuri da abunda naimaka kataimaki rayuwata kafadaman ina zan sameka sauran bayanin sainazo”yadanyi jim sannan yace kibari saigobe yanzu dare yayi” ah ah dan Allah kada kamun haka wlh ko a india kake saina kawo kaina kataimakeni idan bangankaba zan iyah rasa raina””wani dadi yajie
kisameni abakin rest hotel yanzun zanzo indaukeki tace toh ganinan zuwa jikinta har rawa yake takashe wayar tadauki hijabinta babba tayi hanyar waje batasamu kowa awajebah tashiga motarta tayi hanyar wajen koda taje tasameshi tsaye jikin motarsa tana fitowa dagudu tafada jikinsa tana sakar masa kiss
shima yamayar mata yaja hannunta cikin motarsa sundade manne dajuna sannan takoma cikin motar ta yana gaba tana binsa har gidanshi agurguje suka gama abunda zasuyi takoma gida saida takoma takejin haushin kanta mekuma yakaita wajen alhj hamza duk da tana bukatar namiji amman tayi bankwana da zina meyasa yanzu ta aikata takasa bawa kanta wannan amsar
tundaga ranar saiya zama kullum yakirah ta tajikin kwalba saitaje gareshi saidai idan tadawo gida tayita kuka dan itah yanzu tun mutuwar boka komai yakwance mata tayi nadamar duk wani abunda ta aikata amman yanzu tasamu kanta dumu dumu dason alhj hamza da aurenta kuma tana gudun duk wani abunda zaibata masa rai
yanzu takoma ruwa tsundum rashin ilimin addini dakuma aiki dashi shine abunda yake damun hameeda koda tatubah tunda batasan yanda zata bautawa Allah ba zaiyi wuya tashiryu
abun ma yayi nisah yanzu harkwana takeyi cen idan taje tun haydar baiganoba harya gano tadaina kwana gidah lallai abun hameeda saigaba gaba yakeyi wato idon da yasaka mata baisa tayi hankalibah saidaima taci gaba da abunda takeyi
washe gari da yamma yashiga bangarenta tana kwance yayi tsaye akanta saida yagama natsarinta sannan yakarasa inda take yakirah sunanta ta amsa amman bata dago daga kwancen da takeba
Aisha. Ibraheem
[8:34PM, 11/29/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
008
Shima baidamubah yaci gaba ina kike zuwa kwanan nan harkike kwana bagidaba???? kaitsaye tace masa inda ka aikeni dasauri yakallo inda take mekike nufi da hakan kina nufin ina mijinki ban isah insan inda kike zuwabah????
tayi shewa wai mijina tobari kaji nituni nayi fatali da igiyoyin aurenka idan ma bakasaniba kasani kana wani ikirarin kai mijinane amman kakasa bani hakkokina dasuke kanka ciyarwa da sayarwa aiba sune kawai hakkinaba ko anfada maka nibanda sha awane danhaka karkasake shiga sabgata kabarni inje innemo inda za a biyaman bukatata
hannu yasaka yajawota daga saman kujerah yafara gaurah mata mari harsheda bakinta yafara zubarda jini duk wannan abun dayake faruwa akan idon gwaggo duk taji maganganunsu yadaga hannu yamareta gwaggo tarike hannu ta zabga masa mari
dan iskan yaro dama ashe duk abunda hameeda take sanar dani akanka gaskiyane yanzu dama zargin matarka kake ta sunna??? ninasan hameeda bazata taba aikata wani abu makamancin abunda kake mata fataba yar uwar taka lallai haydar bansan kiyayyar dakakewa yata yakai hakabah
duk nagano take takenka sokake tagaji tabar gidan ka to wlh zama daram duk akan waccen banzar matar taka yar talakawa yar sadaka wacce iyayenta suka rasa yarda zasuyi da itah suka jajubah maka kake fifitata akan yar uwar ka
tozanje insanarda uban naka inyaso yasan matakinda zaidauka dannikam bazan yarda kana tozartamun yaba takalli hameeda kiyi hakuri ainasan dole dai yaji maganar ubansa idan niya rainani tawuce fuuuuuuuuuuuuuu
haydar yana nan rike da kunci tana fita yadauke hameeda dawani marin cikin daga murya yace nibana barin bashi yarinya kuma daidai nake daku yaja tsaki yafitah hameeda tanata kuka dankuwa tasha mari
gwaggo kaitsaye gidansu haydar taje batasamu dadyba tayi bangaren mom tana zaune tana koyawa yan biyu karatu saigata kamar wacce akajefo safiyya wajenki nazo” mom tanisa wajena Allah yasadai lafiya amman kekuwa kina zuwa babu ko sallama
mutanen arziki wadanda suka gaji arziki su akeyiwa sallama ba irinkibah dakika haifi shaidanin yaro wai harni haydar zai kalli idona yaciman mutunci duk abunda haydar yakeyiwa yata yaunagani da idona bawai wani yafadaman ba sakone nabaki kifadawa yaya wlh yasan yanda zaiyi danni bazanyarda atozartamun yaba
mom tayi murmushi takalleta hure kenan kina iyah zuwa kisameshi idan yadawo dannikam bazan fada masa komaibah”” taci gaba da abunda take gwaggo baki bude um lallai banga laifin haydar ba yayi gadone kuma hausawa sunce wuce gado sai andaure zandawo insameki
tawuce tana ciccika aikuwa dadare saida tadawo tasanarda dad karya da gaskiya aikam dad ransa yabaci yakirah haydar haydar yana zuwa yaduka yagaisheshi dad yadaukeshi da mari damakai mutumin banzane bansanibah????
duk irin abunda nake fadamaka bakaji ina iliminka yaje da tunaninka suntashi abanza menene ribarka nadukan mace kuma kanwarka danbakasonta sai akace jaka muka aurah maka wlh bakataba bataman rai irin nayauba
haydar idan nakumajin wani abu yataso daga wajenka kokuma kasake dukan matarka wlh banyafemakabah cikin sauri yadago kai yana kallon dad yamaida kallonsa wajen gwaggo datake murmushi jindadin hukuncin da dad yayankewa haydar
mom kam kokallan inda suke batayibah tayi kamarma batasan sunayibah dad saifada yake masa sannan yafara hadawa da nasiha saidayaga jikin haydar yayi sanyi sannan yasallameshi yayi masu saida safe yawuce afusace yakai gida dan wannan marin yajishi kaitsaye bangarensa yanufah yafara cire kayan jikinsa kamshin turarenta yaji yana dososi yajuyo inda yaji kamshin
tana sanye cikin wani less maishegen kyau tazubo sumanta saman bayanta fuskannan tarrr kamar farin wata saikyalli take
kuyi sorry wlh kwanakin nan banda ishashshen chaji
Aisha. Ibraheem
[6:52PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [6:43AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
97
Kokadan bata bari yagano tana cikin damuwaba tare suka karasa cin. abincin sannan yamike bari ingaida mom kaita daga masa yafito yasamu mom saman diner dayan biyu suna karyawa shima yazauna ya gaisheta ta amsa yan biyu suka gaisheshi ya amsa
yakalli mom waiyau lfy naga kamar ranki abace yace ?? tayi murmushi bakomai haydar ina hameeda??? yadan mere baki nima bansanibah danba gida ta kwanabah watakil takoma gidan su nasan dai duk abunsu yauzasu kai karata tunda yau ake meetn suje su fada wlh babu wanda ya isah yasakani inrabu da maryam
saidai itah tayita zama gidan nasu”” mom tanisah itah harma tamanta dayau ake meetn lallai yau akwai rikici amman bata nuna masaba tace shikenan Allah yakaimu”” mom kinsan kasim yadawo jiya???? Allah ah wlh yakirani da dare suna sauka kace yau meetn harda manyan baki ah wlh bari inje wajen fadil
tace shikenan saika dawo saida yakoma wajen mairo yatarar harta koma barci yadade tare da itah kafin yafito yayi wajen fadin karfe biyu daidai dukkan wani familyn gidan ya hallara kwai da kwarkata harda innah
bayan anbude taro da addu a Alhj auwal yafara yimasu bayani akan abunda yatarasu kamar yanda sukeyi ga zumunci kuma ga warare matsaloli kowa yace babu matsalar data taso wan nan karon
gwaggo tayi saurin karbewa wlh akwai matsala babba bama karamaba gaba daya hankalinsu yakoma kanta alhj auwal yace matsala tame??? tace kafin nan inaso afara turah direbah yadauko maiyiwa safiya raino”” tsitt akai falon alhj auwal yace hure itah kuma daba cikin danginmu takebah menene ruwanta tace aikuwa duk itah ce muna fukar kukalli goshin hameeda yanda tasa akaimata duka haka duk hankalinsu yakoma wajen hameeda data soma zubarda hawaye
kawai yaya kasa adaukota zanfijin dadin gayamuku komai”” alhj yagyada kai ya kalli haydar yace jeka dauko min maiyi maku raino… ah ah kul ka aiki wannan wlh zaice tagudune saidai ka aiki dahir ko muh seen. ya gyda kai ya kalli muh”seen jeka da sauri kadauko mana itah yace toh yamike haydar zuciyarshi sai tafasa takeyi wannan wane tozarcine take nema taimasa
waje yayi jigum kasim kam murna yake dan za a kawota yauyayi niyar warware masu burin ransa muhd ma haka yanada wannan kudirin danharya sanarda mahaifiyarsa cikin minti ashirin suka dawo shine agaba tana bayansa kafin ma tazauna gwaggo tayi kukan kurah ta fige hijabin dayake jikinta fuskanta takauce tana kuka tasa hannu tarufe jikinta kukalla kugani cikine jikinta
kasim kusan suma yayi awajen muhd kam tsaye yamike bakinsa yana rawa ganin abunda idonsa yanuna masa innalillahi wa innah ilaihir rajiun” shine abunda kowa yake fada banda mom dan itah kam bataga abunyiwa sallal lamibah
gwaggo ta danhareta kasa gata nan nema take tabata mana suna daganan tafada masu duk abunda yafaru da abunda mom taimata wajen yayi tsit”alhj auwal yayi gyaran murya yakalleta yarinya hakika yanda nake ganinki da natsuwa da tunani bantaba tsammanin haka daga garekibah duk da nasan halin samari yanzu
ya nisa amman kifadaman waye yamaki wannan cikin saboda musamu mu warware maki matsala yayi shiru yana saurarenta gaba daya hankalin kowa yana kanta itah kawai ake saurare gwaggo ta daka mata tsawa waidan ubanki badake akebah ana tambayarki ubanwaye yamaki ciki
muryar haydar sukaji da karfi yace ciki nane!!!!!!!!!!!!!!!!!!! tashin hankali alhj abubakar baisan sanda yakai tsayeba yakalleshi watt haydar sake maimaitawa inji????? yakallishi kwarai dad cikina ne!!!!!
Aisha. Ibraheeem
[7:08AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
98
Innalillahi wa innah ialihir rajiun shine abunda kowa yake furtawa innah kanta mutuwar zaune tayi tana kallon mairo lallai kuwa dolene haydar ya auri mairo tunda yabata mata rayuwa wannan abun taketa sakawa azuciyarta gwaggo tana tafa hannu tace lallai haydar kace babanzaba kake dukan mun ya akan wannan yar iskar kace tana baka kana danawa shiyasa kadaure mata gindi
alh abubakar komawa yayi yazauna yadafe kansa menene wannan haydar ya aikata da iliminshi da tunaninshi idan sonta yakeyi aidayafada nimai aurah masa itah ne wlh”” muhd kam jiyayi kaman yashake haydar dama yasan nane mata dayake abunda sukeyi kenan amman yacuceni yacuci uwar yayana
kasim kam harda hawaye ganin tabun da haydar yayiwa wacce yafiso sama da komai gwaggo takatse masu tunani yanzu kai haydar da matarka dan matatttar zuciya irin taka kakoma kana biyar mairaino tunda muke adanginmu babu wanda yataba aikata abun kunya tajuya wajen mairo kekuma kinji kunyar duniya saurah ta lahirah kuma Alllah bazaki haife mana wannan cikin gidan nan ba mairo kuka take kamar ranta zaifita haydar mikewa yayi yafara takawa zuwa inda take hankalin kowa yakoma kansa yatsuguna kusa da itah yadago kanta
suka hada ido yasakar mata murmushi kidaina kuka kinji nafi ganin kyanki idan kina dariya yasa dan yatsansa yagoge mata hawaye yace pls kidaina bannar hawayenki abanza wlh kukanki yana bataman rai yajawota jikinsa yana lallashi gaba daya kowa suyake kallo baki bude iskancin nasuma haryakai haka itah kam mom murmushi take dankuwa haydar yayi mata daidai
gwaggo tahau tafa hannu laha ilah menake shirin gani haydar da hankalinka gaban iyyayenka da kakarka kake wannan iskancin tunkanayi aboye yanzu abunda kayi ma kadai bai ishekaba kayi mata cikin shege …. bata karasaba yafara magana wai mekike nufi nine shegen ko???? kinata cewa cikin shege kenan nine shegen dan wannan kam dan halas ne wlh
kundun ubanka gidan ubanwa yazama halas yace matata ce ido hameeda tazaro da sauri hawayenta sukacigaba da zuba dasauri dasauri gaba daya suka hada baki matarka???? gwaggo tace gidan ubanwa tazama matarka fadaman nidai bansan sanda aka daurah maka aure da itah ba shidai baice komaibah sai bubbugan bayanta yake alamar lallashi. alhj auwal ya kalleshi yakirah sunan sa ya amsa yace kawarware mana kai haydar kace ciki nakane kuma matar kace alhalin mudai bamusan sanda akadaurah maka aure da itah ba
yayi minti biyu ahaka sannan yagyara zaman sa yana fuskantarsu hannunsa yana rike da hannunta yanisah ina farawa da neman afuwarku akan abunda zan fada watakil yayi maku dadi watakil sabanin haka”yanisah yadaga fuska yakalli mom””datake murmushi yace abunda yafaru babu wanda yasani daga mom sai fadil sune kawai sukasan komai sukasan maryam matatace
lokacinda kuka yanke hukuncin hadani aure da hameeda agaskiya banasonta!!! hameedace tadago da sauri tana kallonsa baidamubah yacigaba dalili kuwa halinta sam ni baiyimunn bah duk da tana yar uwata amman batada dabi un da nakeso matarda zan aureh ace tanadashi karamar maganamah sallah kanta bata dami hameeda ba
taya kuke ganin zata iyah yiwa yarana tarbiyya!??? duk da haka banfadawa kowa banasontabah sai mom da fadil sune suketa tausata akan inyi hakuri indau kaddara danni amatsayin mummunan kaddara nadauki wannan auren tunda akasaka ranar bikin mu sai hameeda takoyi dabi ar zuwa dakina kuma batayin sallama datazo zata fadaman saman jikina
Aisha. Ibraheem
[7:37AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
99
Wannan abun yana konaman rai nayita mata nasiha amman kamar kara turata nake wannan dalilin yasaka nasanarda mom zansameku infada maku banasonta amman mom tahanani nace to agaskiya bazan iyah cigaba da zama anan garin ba dan mundun hameeda bazata daina shigarmun dakibah wlh zanmata rashin mutunci nafada mata komai take nema tajirah tukun adaurah aure zamanta adakina hadarine gareni amman takiji shine momtasanarda dad zanje katsina wajen gwaggo na
alhalin kuma bacen zanjebah natambayi fadil yafadaman sunan wani kauye dayake nesa da nan intafi shine yace inje funtuwa garin maiyi masu aiki hakan kuwa akayi nadau hanya saidai rabon samun farincikina ashe akan hanyata yake saina sauka akauyensu mairo bawai dan nasan garinba inajin amfadi sunan garin naji ina sha awar zama garin mahaifinta nafara haduwa dashi shine yakaini gidansa yabani masauki daganan yacigaba da basu labarin duk abunda yafaru dayanda mahaifinta yakeyiwa yayansa harkawowa ga mairo ya nisah kunji abunda yafaru
gwaggo kusan suma tayi awajen jin wai mairo kishiyar yartace gaske taji tatsaneta bagairah ba dalili kowa yayi tsit kasim kam kuka yake hihihin sundauka kukan tausayin mairo ne basusan kukan anyimasa katangane da itah ba muhd kam kasa natsuwa yayi kuma baiga laifin abunda haydar yayi masabah kodah shine zaiyima fiye da haka gwaggo jirah kawai take ayanke hukunci amman su alhj sunyi shiru kowa da abunda yake sakawa aransa
gwaggo tace kunyi shiru wanne hukunci zaku yanke akai kunsandai yata bazata zauna da kishiyaba tunda sauran ma basuda itah kuma yataka dokar gidan nan tunda ai itay yafara aurah
innah ce tadaga hannu sama tace alhamdulillah amman naji dadin wannan labarin haydar meyasa tuni baka fadaba aidani ba a wahalmun da maryam dina hakaba babu wani hukunci daza a yanke aimagana takare matar sace kuma wlh dole abarsa da abarsa aini tuni banason irin auren nan dakukeyi kubar kowa ya auri wacce yakeso idan mutun adangi yagani yanaso abashi idan kuma awaje yagani abashi amman daga yau nina kashe wannan
wlh nadade inayiwa haydar kwadayin mairo inama ace yana sonta ya aureta kobashibah daidaga cikin jikokina wani yace yanasonta wlh kullum da abun nake kwana ina tashi ashedai bansan kishiyatacebah takalli mairo taso nan kinji ashe dama kinsan kishiyarki kikewa hidima duk da haka nasakar maki mijin dankinfini chanchanta dashi gaba daya wajen aka kwashe da dariya banda hameeda da gwaggo
taso kinji maryam haydar yakalleta yana murmushi itah ma shitake kallo yalumshe ido yabude tamayar masa da murmushin mikewa tayi yatashi yadauko mata hijabinta yasa mata sannan suka jerah wajen innah kusa da kafafuwan innah tazauna innah tadorah kanta saman cinyarta
tana shafar kanta takallesu kuma abunda nakeso kuyi shine inaso dagayau afara shirin biki dankuwa sai anyi wani bikin danni saina taka. rawa abikin nan bantabajin dadi irin naranar yaubah takalli haydar kaikuma kagyara gidan ka rana itah yau matanka sukoma cen yagyada kai innah aini gidana dama agyare yake kayane kawai babu aciki
tace to Alhamdulillah maganar yar uwarka kuma kayita hakuri kaji haydar matane saida hakuri insha Allah zakaci ribar wannan hakurin gwaggo ce tamike lallai yau kun nunamun iyakata to wlh yata bazata komabah
kawai danson kai ainaga kowacce itah kadai take zaune sai yata za ahada da qamayamaya. aibashine kawai autan mazabah yasakarmun ya wlh kunsan ko ayanzu hameeda tafita gari saita samun dubun haydar kawai dan yana dan uwanta saiya fake da wannan yacima yata mutunci
kawai tafashe da kuka aida yayankune bazaku taba bari yayimasu kishiyabah kuma alhamdulillah koyanzu kasuwa tawatse dankoli yaci ribah yata kudi aka saka aka aurota amman wannan kumafah YAR SADAKA!!! ce
Aisha. Ibraheem
[8:34AM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
100
Taja hannun hameeda kizo muje wlh bake ba wannan kaddararren auren tanajan hameeda hameeda tana togewa dan itah kam duk da haka tanason mijinta sai kuka take tana kiran sunansa shikam dauke kansama yayi daga wajenda suke. haka gwaggo tafita da itah takirah wayar muh”seen tace yazo yakaisu gida maza
saida yafadawa dad yace tashi kakaita indai hurece babu wanda ya isah yasakata ta sauraremu idan tagaji dakanta zata dawo da itah mikewa yayi yayiwa haydar congrt sannan yafita alhj yayi gyaran. murya haydar kajidai abunda innah tace danhaka saika fara shirye shirye
innah takarbe kuma wlh dolene kahada mata lefe nagani nafada idan kuwa bahakaba zanriketa aguna kobanza nafika sonta yayi murmushi innah kenan za a hadamata ciki harda mota sabuda dal da nairah miliyan daya amatsayin tukuicina sauran bayani sairanarda Allah yasauketa lafiya innah kudai tayani addu a tahaifoman yan biyu
innah saida ta rangada guda saiba maryam dinaba harda karin miliyan daya haydar??? yayi dan murmushi yasafo sumar kansa innah harma da tukuicin zuciyata kasakasa yake kallon mairo wadda kunya duk ta rufeta wani dadi takeji itah ma yanzu tashiga cikin sahunmasu yanci tarokam yawatse cikin jindadi duk sungama shirya meza ayi abikin nikam nace biki da ciki hehehheh
kursum tana nan manne da maryam tunda taji matar yayan tace damacen tana sonta kamar yanda mom take sonta motar haydar mairo tashiga suka koma gida tafiya yake yana murmushi yacije lebe amman wlh naji dadin wannan abun kinga komai yazo cikin sauki gwandama dahakan yafaru kinga zuciyoyin mu sun samu sauki yajawo wayarsa yakirah fadil yana dauka yace kai mutumina komaifa ya warware rana itah yau zan zama ango
fadil yace ango kuma wani auren zakayi yakalli gefenda mairo take wayaketa aure yanada kamar maryam mutumina aiyanzu daga wajen meetn nake komai ya warware ansan yanzu matatace gobema zanbar kasar nan inje hadomata lefe
kai amman ina tayaka murna mutumina kaga kunhuta dawani boye boye”wlh kuwa saidai munhade sukai sallama ya aje wayar kinsan me kuwa ??? um um saika fada wlh jinake kamar anyimun albishir da aljanna tayi dariya haba dai yace wlh kedai bari kawai
mom kanta bakaramin dadi tajibah muhd yasamu haydar yabashi hakuri akan abunda yafaru rashin sanine yace bakomai aiyasan dayasani dabaifurta hakanbah kasim ma yasakawa zuciyarsa dangana tunwuri kafin takaishi ga aikata zunubi
washe gari kuwa haydar yabar kasar kwanansa hudu yadawo da kayan lefen mairo kamar hauka idan kagansu zaka dauka lefen mace biyarne akwati ashirin da hudu kowanne kayandasuke ciki bana wasa bane sun hadu iyah haduwa haydar yasan kalar kayanda mairo zata saka sukarbeta sosai komai dayasaya acikin kayan yanada takalmansa da mayafinsa agogo da jakarsa dakuma sharka banda fasion gasunan kamar za abuda wani babban kanti anfara biki kamar za a aurarda wata sabuwar amarya bangaren mom tahau gyaran maryam danso takeyi takoma tamkar budurwa tasha zanen lalli da kitso kanana kanana saida yahada diner biyu
ya gaiyaci abokansa dayawa har wadan da sukai makaranta india da abokan aikinsu yakara gyara gidan haydar bangaren maryam yasa kaya innah saida tayimata set kayan dubai mom kam daga saudia tasa akayomata odar su. dad ma yayi mata kaf kayanta babu wanda akasiya akasar nan mairo takoma kamar wata tauraruwa su kursum ma ba a barsu abayabah saida suka kawo gudun muwa akara gyarawa yayansu amarya
ranar asabar takama ranarda za a kaita saida sukayi wata diner ta musamman abokan ango yan uwa da da makota wajen yayi masifar kayatuwa murna biyu ta aurensa dakuma murna cikinda yake jikinta haydar harda rawa waishida yace bai iyah rawabah saida fadil yayita tsokanarsa innah ma yau saida ta taka dan harda masu kidan kwarya tadauko abunda bata tabayibah
karfe tara daidai akashirya mairo cikin wani material maidankaran kyau tayi kyau harta gaji aka kaita wajen dady yayi mata huduba mom ma tayi mata momharda kuka tayi rabuwa da mairo itah kanta mairo kuka take kamar ranta zaifita dakyar aka banbareta jikin mom akafitah da itah har haydar yakawo motoci harda innah wajen kai mairo lallai innah bakaramin so takeyiwa mairobah ankaita gidansa kwaton gida nagaban kwatance to damadai da itah da haydar ne babu wata damuwa mutane sai santin kayan dakinta suke kafin goma kowa ya watse tana shirin zuwa wanka dan zafi takeji saiga hayaniyar haydar da abokansa abun itah haryasoma bata dariya wai kenan siyen baki sukazo kamar budurwa
suka zauna akabude taro da addua daganan sukai masu fatan alhairi yarakasu sannan yakulle gidah yadawo yace amarsu ta ango tana dariya tace uwar mata dai ina fama da ciki dugugu dugugu kace wai amarya
yana cire babbar rigarsa yace wlh kinfima amarya awajena danhaka kima yarda duk abunda zakice madai kice amman ni nasan haka kinga tashi muyo alwala tace kuma dai saida sukai alwala sukayi raka a biyu yayi mata addua kamardai yanda akeyi yagabato masu da naman kaza gasassa da madara suka ciyarda kansu tare sukai wanka sannan suka lulaya duniyar ma aurata haydar kam yakasa banbance ranarda yafara saninta da yau saiyake ganinma kamar yauce dankuwa yasha zuma sauran zancen nashine
haka rayuwar aurensu tacigaba dakasancewa haydar yakoma aiki amman kullum suna manne dawaya idan kuma yana gida suna tare amfara shirin bikin fadil da Aisha humairah sati maizuwa yanzukam haydar yayi wuyar gani dansun fara hidimar biki agefe guda cikin maryam yashiga wata na takwass amman idan kaganshi zaka dauka yanzu zata haihu
Aisha. Ibraheem
[6:42PM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
001
Duk wata kulawa tana samu sosai wajen haydar ranar asabar aka daurah auren fadin da Aisha humairah akan sadaki dubu hamsim ranar kam fadil baki harkunne haydar sai tsiya yake masa yana cewa yaudai kaima zaka dandana kaji abunda mukeji
sati daya da bikin fadil haydar yaje garinsu mairo amman tafiyar dai rana yayi itah kanta batasan yajebah dan ankammala ginindayasa aimasa gidakam ya hadu ya amsa sunansa komai anyi yasa anzubah kayan daki akowanne bangare bangaren innah dukyafi girma sai bangaren. hardo kusa yake dana innah sukuma nasu gwaggo da iyya waje daya yake zokaga murna akofar gidan kuma dama anbuda katon shago haydar yacikashi da kaya kala kala wadan da yasan ba a samunsu anan sai anje zariya yadamkawa halliru sannan yace yanaso yadauki nauyin kula da innah da hardo murna kamar me harda kuka su gwaggo kam sun aje makaman yakinsu ganin wannan hidima da haydar yayi masu aranar yabaro kauyen koda yadawo gidama har ansoma kiran magrib masallaci yawuce kaitsaye saida akai isha i yadawo
kwata kwata baisanarda mairo ina yajeba
bangaren gwaggo kuwa tagaji da tijarar hameeda hakan yasa ta tattarota tamaidota dakinta saida aka gyara mata bangarenta ta tare dad saida yayi masu nasiha akan zaman hakuri sannan haydar yaraba masu kwana kuma daidai gwargwado yana kwatanta adalci abu daya kawaine baiyarda dashiba yahada shinfida dai da hameeda alhamdulillah suna zaman lafiya
watanta daya dadawowa gidan mairo takama nakudah kuma gashi haydar baya gida nakuda take zangu zangu babu kowa dan mom taso yamaidota amman yace ah ah shikam yanada bukatar matarsa saidai idan tahaihu yakaita saigashi nakudar takamata da rana kuma haydar bayanan
kuka take tana kwalawa hameeda kirah tayi neman wayar ta bata gantaba hameeda tazo wucewa saitaji kaman tana kiranta dasauri takaraso tana kallonta saikuma ta sheke da dariyar mugunta”lallai yau aikinsu zaiyi kyau” dan Allah sister kitaimaka kikiraman ya haydar wlh mutuwa zanyi
kai alhamdulillah wlh dama zaki mutu dake da abunda kika haifa dayafi komai sauki kinga kin taimakaman nasamu narabu dake kinsan bazaki iyah haihuwaba ubanwa yasakaki kika kwanta da miji badaike dadi. aureba dan Allah kitaimakaman zan mutu saikuka take tana murkususu hameeda kallonta take tana dariya yarinya alkadarinki ya karye nibarima kigani komawa tayi taja kofah tarufe tayi sashenta
takunna duma kuma takai karshen murya gaba daya gidan yarude bakajin motsin komai sai taunar cingam take abunta tasan tagama da matsalar mairo haydar boka yace yasan yanda zaiyi mata dashi ya manta duk wani abunda ta aikata ya zaimada suyayyar mairo takoma agareta zata sameshi ahannu fiye da shekarun baya
yana zaune asiviti duk yaji jikinsa sai ahankali gabansa saifaduwa yake yaso yadaure amman yakasa hakan yasaka yadauko key kawai yayo gida tunda yanufo unguwar yaji tashin kida agidan sa yaso yaje bangaren hameeda yace takashe harzai shiga saiyajuya zuwa bangaren mairo yasamu dakin akulle
ina kuma maryam tatafi wayarsa yajawo yakirata saiyaji ringin cikin dakinta sauri yayi zuwa bangarensa yadauko wani key yabude cikin falo yasameta harta suma ga yaranan ta haifah guda uku biyu maza daya mace sai tsandara ihu suke baikoma takansuba mairo yafara girgiza amman ko numfashi batayi
ciccibota yayi dasauri zuwa cikin motar ya ajeta sannan yakoma yasamu zannuwa yanade jariran yadauko mahaifar yasaka amota yajata zuwa asiviti tunkafin yakai yakirah fadil haydar duk yafita hayyacinsa kamar wani tababbe
nantake akaturata saman gadon zuwa cikin daki akabata taimakon gaggawa haydar saikuka yake yama kasa mezaiyi sauran likitoci suka dauki yaran akagyarasu akamasu wanka fadil ne yakirah gida yasanar saiga mom da maman zulai hardasu dad kowa yadau yaran saiya zubarda hawaye gayara kyawawa amman mahaifiyarsu ba lafiya
Aisha. Ibraheem
[7:24PM, 11/28/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
002
Harsu kursum sunzo nan take asiviti tacika da mutane yandubiya sai koke koke akeyi duk yanda likitoci sukaso ganin sun shawo kan lamarin amman sunkasa ko motsi batayi haydar kam idonsa yayi ja saboda kuka
fadil kansa saida yazubarda hawaye duk wani maisom mairo bazai iyah hada ido da itah ba”” saikusan magrib hameeda takoma dakin mairo bata sametaba tace nashiga uku kaddai haydar yadawo dasauri tasauko kasa wajen maigadi tana tambayarsa yace mata ah shine yazo yadauki madam””
tace kaganshi da yara???? yace ah ah itah kawai naga yadauko cikin sauri takoma cikin gida tajawo mayafinta sai asivitin tanashiga takama kuka kamar gaske saifaduwa take ana riketa tace yanzu mundade muna neman haihuwa gashi Allah yabamu kuma haka abu yakasance
maman zulaitace sai hakuri hameeda fatanmudai Allah yabata lafiya sukuma yaran Allah yarayasu”chak kukanta yatsaya takalli maman zulai banganeba waita haihun ne??? maman zulaitashare hawaye ah tahaihu yan uku ne kuma lafiyarsu kawau itah ce ba lafiya
gaban hameeda yabada rass anya kunnuwanta gaskiya sukejiyo mata to kenan bokan nan yayi mata karya dayace dazaran tahaihu zaituro aljannu su tsotse jinin yaron itah kuma zai turo mata arne””ganin tana shirin sakin layi yasaka tayi saurin kawarda abun
takalleta ina ya haydar dinyake???? tace yana ciki wajenta nan tayi gumda baki tabuga tagumi yautaga samu taga rashi yanzu duk yan kudadenta datake takama dasu sune takwashe tabayar wajenyin wannan aikin amman kuma gashi aiki baiyibah
amman kuwa bokan nan yacuceni saida takaikaici idon mutane tazare jikinta bata zame ko inaba sai wajen boka afusace taje wajensa yana ganinta yakwashe da dariya muguwa kin dawo””tasamu waje tazauna boka nifah wannan aikin banga komaiba kace za a shanye jinin yaran nan gashinan harguda uku tahaifah amman sunanan kalau alhalin bahaka mukai dakaibah
saida yakwashe dawata mahaukaciyar dariya yace naturasu kamar dai yanda nafada maki amman sunkasa zuwa kusa da yaran dalili kuwa lokacinda tanada cikinsu mijinki yana karanta ayatul kursiyuu da lakadja akum yana lofawa aruwan zanzam yana bata tanasha babu yanda za ayi asiri yakamasu ko aljani bai isah yamatsa kusa dasubah
mahaifiyarsu kawai mukaci nasara akanta dan batada tsarkine itah ma dama nafada maki aikin nan akwai hadari cikinsa kuma akwai wahala. idan da aljanin yakone akanki zairama amman duk da haka kada kidamu kisani kinyi adashe waje mai kyau kikoma gida kikwanta duk sauran bayani nawane puhahahahaha yakece da dariyar kamar muryan jaki jiki na rawa hameeda tabaro wajen boka da murna cikin ranta
Kwanan mairo uku sannan tafar fado babu um babu umm um batasan waye akantaba batada wani kuzari saidai kawai tarika bin mutane da kallo kafin kace me tasake komawa barci yara kam saidai akasoma basu madara dan ganin halinda mahaifiyarsu take ciki
batayin tsayin mintuna ashirin afarke kullum zaka sameta tana barci kuma nafitar hankali tana wani gurnani kamar zakanya.fadil ne yabada shawara shidai yaga aikin yakici yaki cinyewa maizai hana afitah da itah waje haka kuwa haydar da mom suka shirya zuwa babban asivitin india akadorata saman na ura sudai basuga wani ciwo atattare da itah ba
amman abu saidada gaba yakeyi haydar haka zaizauna yatasata gaba yayita kuka kamar karamin yaro tun momy tana lallashinsa har itah ma saitakama kukan mairo gaba daya tarame bata cin komai saida arika bata abinci ta hanci kassa duk sun fito mata ganin hakan haydar yasiyo kasat din kira a dadan karamin redio danshi yafara zargin kodai aikin anjanune ranarda yasaka mata kira a ranar tana farkawa tadauki redio tabuga da bango yayi tara tara kanta tabuga saman glass dinda ake ajemagunguna
hayadar dasauri yariketa amman nema take tafi karfinsa mom ce tadanna abunkiran ma aikata hauka tataso kuma zangu zangu duk inda taga glass saita fasama kanta likitoci sunfi goma suka riketa sannan akasamu akaimata allurar barci ahankali takoma barci yanda taimajikinta jina jina shikanshi haydar yajimu garin riketa haydar zaune yafadi yanata rusar kuka
nimadai bansan sanda hawaye suka zubomanba 😭😭😭😭😭
Aisha. Ibraheem
[6:52PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [11:08PM, 11/29/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
009
Tana sagale da ikram akafadanta suna hada ido tasakar masa wani shu umin murmushi nan take yasu suce hannunsa yasaka yamurza idonsa dashi anashi tsammanin gizo take masa wanda tasabayimasa kullum tayi murmushi sannan takarasa kusah tashi tadorah ikram saman gado tafara tayashi cire kayan kana mamakin ganinane????
baice komaibah taci gaba dazun nan yaya halliru yakawoni waiyanaso yabaka mamakine shiyasa sukaki sanardakai zandawo yakaji daka ganni???? wani ihun dadi yyi yadauketa chak yana juyawa da itah cikin dakin yasakar mata kiss akumatu wlh naji dadi sosai
kamar dama sunsan inada bukatarki aini nama yanke shawaran jibi zanje cen mutare tunda innah tarikeman ke tun satinda yawuce naso zuwa aikine yayi yawa shiyasa ina hassan da husaini
tari farr da ido suna daki bari indaukosu da kasan fa bazan iyah rikosu su ukubah yana dariya tomuje inrika maki tare suka jera har bangarenta shiyadau husaini itah hassan suka dawo bangarenshi tataimaka mashi yayi wanka yaran dama sunyi barci sukuma suka shige bargon soyayyar sauran karatun nimadai bansaniba amman kunsan yau haydar akwai maganar hana makota barci
tundaga ranar yafita sabgar hameeda babu ruwanshi da itah duk abunda take yasaka mata na mujiya mairo ma babu ruwanta da itah dankuwa tagano bata kaunarta tana zuwa wajen mom akai akai dawajen yan uwan haydar duk tana zuwa
yanbiyu sunada wata biyar sunyi wayo abusu idan kagansu kamar sunyi shekara daya dama andauko mata yar raino tana kula da yayan haydar yamaida itah makaranta amman ss1 dole aka sakata tare suke zuwa sch din da maiyimata raino
*******************************************
falon cike yake da mutane kaf family din babu wanda baizobah sunyi jugum gaba daya idanuwansu sunakan gwaggo dataketa rusar kuka kamar karamar yarinya kowa yayi jugum yana kallonta innah tace wai hure menene haka kintaramu nan kince akwai magana amman munzo kuma kintasamu gaba kina kuka menene dalili
idan bakida abun fada kowa yatashi yayi tafiyarsa munada ayyukanyi agaban mu”” nan ma gwaggo shiru tayi saida Alhj auwal yayi magana sannan ta face majina tashare hawaye takalli kowa nadakin taga itah ake kallo tajuya kallonta wajen hameeda takawarda kai batareda ta kalli haydar ba takirah sunansa ya amsa tace ina umurtar ka dakayi gaggawar sakin hameeda kuma saki uku!!!!!! dam dam gaban hameeda yabuga dajin kalamin gwaggo itah da bakinta takecewa asakeni
gaba daya wajen akabi gwaggo da kallo baki bude hardai malam mijinta dakuma haydar yana in in na yace saboda me zansaketa gwaggo???? tadaga murya bashawarar ka nake nemaba umurni nabaka idan harna chanchanci kamun biyayya amatsayina na kanwar babanka
haydar yadago kansa yakalli alhj auwal yadaga masa kai alamar yayi yanda tace sannan yakalli dad dinsa shima haka yajuya wajen mom itah ma haka taimasa saida yayi dan jim sannan yace hameeda kiyi hakuri bazan iyah ketare wannan ba amman banyi niyar rabuwa dakebah har abada nasakeki saki biyu
dakarfi gwaggo tace uku nakeso kaimata haydar tsinanna la a nanna wacce batasan annabi yazobah Allah ya isah tsakanina dake hameeda banyafe maki nono na dakikashaba shegiya maibakin hali daman hausawa sunce kadaiga mutun wlh kincuceni kuka tacigaba dayi gaba daya wajen sunshiga rudani jin kalaman gwaggo duk tasanyasu aduhu meyasa taketa cinewa hameeda hartana cewa bata yafe mata nononta data shaba
Aisha. Ibraheem
[3:58PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
010
Innah takirah sunan ta ta amsa tanisa menene ribarki nacewa baki yafemata nononki dakikashaba laifin me tamaki???gwaggo tasake face majina ta kalli innah tace kunsan aduniyar nan babu wacce nafiso sama da hameeda kuma kunsan bazan yimata karyabah
nasamu lbrin wai ana ganinta tana yawo da wani alhj suna zuwa gidan sa nikuma da labari yazoman sainaki yarda ina zargin cewa haydar ne kawai yakeso yabata mata suna na watsarda abun saikuma jiya nakuma samun labari wannan dalilin yasaka nadauko mayafina dan inzo inciwa haydar mutunci nakirah muh”seen yazo yakaini shine yace aiki yamasa yawa inbari harsai anjima nikuma naga nawa kardare yayi ashedai darabon sainaga abunda zaitayarman da hankali
nafito natari dan achaba muna cikin tafiya kamar ance inwaiga saina hangota jikin wani katon mutun saurah kadan infado daga saman adaidaita suka wucemu nacewa dan adaidaita yabi wannan motar suna gaba munabin bayansu harsuka kai hotel tare suka fito data fito shine tasaka nikaf tayanda babu wanda zaiganeta
dasaurina nabiyo bayansu kodan achaban banbiya kudinsaba abakin dakinda suka shiga natsaya inaji tashin muryoyinsu ta kusurwar kofah na rega gabana sai bal bal yake bantaba dauka iskancin ta yakai hakabah alhj hamza yana cire kaya wai my luv meyasa kika zabi muzo nan dagidana
tacire dan kwalinda yake kanta tace saboda yafi sirri a unguwarku ranar nahadu da fadil abokin hydar kuma kasan idan yaganni zai iyah sanardashi shiyasa kawai nace maka muzo nan dan nasan baya zuwanan kuma babu wanda zaigammu anan” yayi murmushi yazauna kusa da itah
hameeda aikece tunyaushe nace maki kikaso auren ki nizan aureki amman kinki”” tadan kalleshi bawai banyarda bane ah ah kasan auren zumuncine akaimana duk da shi bayasona amman bazai taba gigin sakinabah dankuwa yana gudun bacin ran iyayensa kuma kasan koda nafadi hakan momy na bazata taba yardaba aini tuni naso ya sauwakeman amman yaki
taja tsaki ni wlh banason inbuda ido inganshi dashi har matarsa ” yanisah to wanne mataki kika dauka”‘ tayarfa hannu wanne mataki kuma kwanaki kudina nakashe wlh naje wajen boka dan kawai inga bayan matarsa da yayansa shidin mai saukine amman kuma aiki kamar zai yi saidaga baya nasamu labarin tawarke sumul
shidin kuma ko zakaimasa magani aikin banza kayi dan asiri baya kamashi saboda yawan addu o inda yake baya wasa kokadan tamaido ta kallonta wajensa amman maizai hana kayo hayar yandaba su kasheshi baki gwaggo tarufe tazaro ido jin wannan baran barama ta hameeda
yanisah ah ah hameeda kisan kaidai nigaskiya bantabayin hakanba””taja tsaki ashekai baka cika dan iskabah menene aibu basai mutubaba daga baya kaga idan bazakayi hakanba bazaka taba samunaba dankuwa babu yanda za ayi yasakeni aruwan sanyi” yanisah akwai yanda za ayi
tasake kallonsa taya kenan???? zansa akamashi mukulleshi inda babu wanda yasani mudina gana masa azaba daga karshe mufada masa kudirinmu nasan tunda baya sonki aruwan sanyi zai sakeki tayi dariya kai amman kasamo shawara mai sauki nikaina banason akasheshi dan ina sonsa wlh amman kanada wannan dabarar meyasa tuntuni bakayi mana itah ba?
to aiyanzu gata kinga darefa yasomayi acigaba dagashi kawai anan suka fara tsotsan junansu harsuka koma zindir haihuwar uwarsu narufe idona dakyar nabaro hotel din nakama hanya jikina kamar waccce aka daka kuka kawai nakeyi naja kafafuwana zuwa bakin titi bansamu dan adaidaitaba nasan yagaji dajirana yatafi
Aisha. Ibraheem
[4:22PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
011
Natari wani dan adaidaita nafada masa inda zaikaini yakawoni gida koda nakai gida zazzabine yarufeni sai magrib muh”” seen yazo yatarar banida lafiya shine nasanar dashi yakirah kowa yafada masa inada magana kowa yataru tashare hawayenta
takalli hameeda wadda zufah yaketa keto mata kamar ruwa takasa ko daga kai balle takalli inda take mairo kam duk ta tsure jin wannan labarin haidar saikallon hameeda yake tace to hameeda kinsamu abunda kikeso daga haydar gashi nan yasauwake maki aruwan sanyi kuma kisani yaudin nan zaki bar masa gidansa
kuma ko allurah banyarda kidauka acikin gidan nan ba tundaga kayan daki har kayan sakawa danbabu nerarki aciki abunda kawai kika saya wajen yawon karuwancinki shine dole kidauka kuma kada kafarki takuskurah kije gidana kokuma gidan yan uwana
innah ce takatseta bakida hujja hure saboda me zaki yanke mata wannan hukunci maitsauri haka munsandai hameeda tabbas bata kyautaba kuma batayo halin yan gidan nan ba itah ce kawai tafitah bare acikin mu
gwaggo tace wlh inna zamanta acikin gidan nan yakare idan dai niyar kice wlh banyarda hameeda takaracin arzikinmubah wlh da inada ikon tare mata nunfashi wlh datuni natareshi tamutu kowa yahuta dabakin iri
saiyanzu alhj auwal yanisah gaba daya maganganun hure sun saka jikin kowa sanyi duk abunda hameeda tayi saikuma sukejin tausayinta jin tsatstsauran matakinda gwaggo tadaukar mata hameeda kam saikuka take
hure agaskiya banji dadin wannan danyen hukunci dakika zartarba yakamata kiyi aiki da hankali itah dai wannan ya yarmuce kuma balaifi bane danke tamaki laifi kice zatabar gidanki kuskurene tayi amman kiyi hakuri maaganar tabar gidan kima baitasobah wlh yaya babu gurbinda hameeda zata zauna agidana bama gidan kaba nibanyarda tazauna ko inabah
takalli inda take kimaza kitashi kibar mana gida bakar daga maibakin hali wlh kincuci kanki da kanki kuma zakiyi nadamar marar amfani arayuwarki”tana kuka tafara bata hakuri momy dan Allah kiyi hakuri wlh aikin shedanne dan Allah kada kikoreni idan kika koreni ina zanje banida kowah aduniya bayanku kune iyayena
gwaggoce takatseta ke dakata nadaina maki wannan kara kije kinemi iyayenka amman niba mahaifiyarki bace!!!!! dam dam gabanta yafadi saiyanzu malam yayi magana haba hure duk da ni ba abakin komai nakebah indai akan yarkine amman baikamata kina cewa taje tanemi wasu iyayenba ba ason yanke hukunci cikin fushi
gwaggo ta daga murya wlh wannan ba yata bace!!!!! saikuma tafashe da kuka hameeda tazaro ido jin furucin gwaggo innah tadaka mata tsawa wannan wane irin shirmene kikeyi kina rantsuwa akan karya dan kawai tabata maki rai
tadago raunannun idanuwanta takalli innah wlh tallahi innah wannan bayata bace shegiyace!!!!!!!!!!!!! innalillahi wa inna ilaihir rajiun” kowa nawajen hankalinsa yatashi bakamar hameeda nikaina birona fadi yayi akan tsananin firgita tonidai tambayata anan ya akai hameeda tazama shegiya???? kuma meyasa gwaggo tarantse cewa bayarta bace uhum saidai munji daga gareta munshare kunnuwanmu muna saurare
Aisha. Ibraheem
[6:53PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [11:08PM, 11/29/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
009
Tana sagale da ikram akafadanta suna hada ido tasakar masa wani shu umin murmushi nan take yasu suce hannunsa yasaka yamurza idonsa dashi anashi tsammanin gizo take masa wanda tasabayimasa kullum tayi murmushi sannan takarasa kusah tashi tadorah ikram saman gado tafara tayashi cire kayan kana mamakin ganinane????
baice komaibah taci gaba dazun nan yaya halliru yakawoni waiyanaso yabaka mamakine shiyasa sukaki sanardakai zandawo yakaji daka ganni???? wani ihun dadi yyi yadauketa chak yana juyawa da itah cikin dakin yasakar mata kiss akumatu wlh naji dadi sosai
kamar dama sunsan inada bukatarki aini nama yanke shawaran jibi zanje cen mutare tunda innah tarikeman ke tun satinda yawuce naso zuwa aikine yayi yawa shiyasa ina hassan da husaini
tari farr da ido suna daki bari indaukosu da kasan fa bazan iyah rikosu su ukubah yana dariya tomuje inrika maki tare suka jera har bangarenta shiyadau husaini itah hassan suka dawo bangarenshi tataimaka mashi yayi wanka yaran dama sunyi barci sukuma suka shige bargon soyayyar sauran karatun nimadai bansaniba amman kunsan yau haydar akwai maganar hana makota barci
tundaga ranar yafita sabgar hameeda babu ruwanshi da itah duk abunda take yasaka mata na mujiya mairo ma babu ruwanta da itah dankuwa tagano bata kaunarta tana zuwa wajen mom akai akai dawajen yan uwan haydar duk tana zuwa
yanbiyu sunada wata biyar sunyi wayo abusu idan kagansu kamar sunyi shekara daya dama andauko mata yar raino tana kula da yayan haydar yamaida itah makaranta amman ss1 dole aka sakata tare suke zuwa sch din da maiyimata raino
*******************************************
falon cike yake da mutane kaf family din babu wanda baizobah sunyi jugum gaba daya idanuwansu sunakan gwaggo dataketa rusar kuka kamar karamar yarinya kowa yayi jugum yana kallonta innah tace wai hure menene haka kintaramu nan kince akwai magana amman munzo kuma kintasamu gaba kina kuka menene dalili
idan bakida abun fada kowa yatashi yayi tafiyarsa munada ayyukanyi agaban mu”” nan ma gwaggo shiru tayi saida Alhj auwal yayi magana sannan ta face majina tashare hawaye takalli kowa nadakin taga itah ake kallo tajuya kallonta wajen hameeda takawarda kai batareda ta kalli haydar ba takirah sunansa ya amsa tace ina umurtar ka dakayi gaggawar sakin hameeda kuma saki uku!!!!!! dam dam gaban hameeda yabuga dajin kalamin gwaggo itah da bakinta takecewa asakeni
gaba daya wajen akabi gwaggo da kallo baki bude hardai malam mijinta dakuma haydar yana in in na yace saboda me zansaketa gwaggo???? tadaga murya bashawarar ka nake nemaba umurni nabaka idan harna chanchanci kamun biyayya amatsayina na kanwar babanka
haydar yadago kansa yakalli alhj auwal yadaga masa kai alamar yayi yanda tace sannan yakalli dad dinsa shima haka yajuya wajen mom itah ma haka taimasa saida yayi dan jim sannan yace hameeda kiyi hakuri bazan iyah ketare wannan ba amman banyi niyar rabuwa dakebah har abada nasakeki saki biyu
dakarfi gwaggo tace uku nakeso kaimata haydar tsinanna la a nanna wacce batasan annabi yazobah Allah ya isah tsakanina dake hameeda banyafe maki nono na dakikashaba shegiya maibakin hali daman hausawa sunce kadaiga mutun wlh kincuceni kuka tacigaba dayi gaba daya wajen sunshiga rudani jin kalaman gwaggo duk tasanyasu aduhu meyasa taketa cinewa hameeda hartana cewa bata yafe mata nononta data shaba
Aisha. Ibraheem
[3:58PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
010
Innah takirah sunan ta ta amsa tanisa menene ribarki nacewa baki yafemata nononki dakikashaba laifin me tamaki???gwaggo tasake face majina ta kalli innah tace kunsan aduniyar nan babu wacce nafiso sama da hameeda kuma kunsan bazan yimata karyabah
nasamu lbrin wai ana ganinta tana yawo da wani alhj suna zuwa gidan sa nikuma da labari yazoman sainaki yarda ina zargin cewa haydar ne kawai yakeso yabata mata suna na watsarda abun saikuma jiya nakuma samun labari wannan dalilin yasaka nadauko mayafina dan inzo inciwa haydar mutunci nakirah muh”seen yazo yakaini shine yace aiki yamasa yawa inbari harsai anjima nikuma naga nawa kardare yayi ashedai darabon sainaga abunda zaitayarman da hankali
nafito natari dan achaba muna cikin tafiya kamar ance inwaiga saina hangota jikin wani katon mutun saurah kadan infado daga saman adaidaita suka wucemu nacewa dan adaidaita yabi wannan motar suna gaba munabin bayansu harsuka kai hotel tare suka fito data fito shine tasaka nikaf tayanda babu wanda zaiganeta
dasaurina nabiyo bayansu kodan achaban banbiya kudinsaba abakin dakinda suka shiga natsaya inaji tashin muryoyinsu ta kusurwar kofah na rega gabana sai bal bal yake bantaba dauka iskancin ta yakai hakabah alhj hamza yana cire kaya wai my luv meyasa kika zabi muzo nan dagidana
tacire dan kwalinda yake kanta tace saboda yafi sirri a unguwarku ranar nahadu da fadil abokin hydar kuma kasan idan yaganni zai iyah sanardashi shiyasa kawai nace maka muzo nan dan nasan baya zuwanan kuma babu wanda zaigammu anan” yayi murmushi yazauna kusa da itah
hameeda aikece tunyaushe nace maki kikaso auren ki nizan aureki amman kinki”” tadan kalleshi bawai banyarda bane ah ah kasan auren zumuncine akaimana duk da shi bayasona amman bazai taba gigin sakinabah dankuwa yana gudun bacin ran iyayensa kuma kasan koda nafadi hakan momy na bazata taba yardaba aini tuni naso ya sauwakeman amman yaki
taja tsaki ni wlh banason inbuda ido inganshi dashi har matarsa ” yanisah to wanne mataki kika dauka”‘ tayarfa hannu wanne mataki kuma kwanaki kudina nakashe wlh naje wajen boka dan kawai inga bayan matarsa da yayansa shidin mai saukine amman kuma aiki kamar zai yi saidaga baya nasamu labarin tawarke sumul
shidin kuma ko zakaimasa magani aikin banza kayi dan asiri baya kamashi saboda yawan addu o inda yake baya wasa kokadan tamaido ta kallonta wajensa amman maizai hana kayo hayar yandaba su kasheshi baki gwaggo tarufe tazaro ido jin wannan baran barama ta hameeda
yanisah ah ah hameeda kisan kaidai nigaskiya bantabayin hakanba””taja tsaki ashekai baka cika dan iskabah menene aibu basai mutubaba daga baya kaga idan bazakayi hakanba bazaka taba samunaba dankuwa babu yanda za ayi yasakeni aruwan sanyi” yanisah akwai yanda za ayi
tasake kallonsa taya kenan???? zansa akamashi mukulleshi inda babu wanda yasani mudina gana masa azaba daga karshe mufada masa kudirinmu nasan tunda baya sonki aruwan sanyi zai sakeki tayi dariya kai amman kasamo shawara mai sauki nikaina banason akasheshi dan ina sonsa wlh amman kanada wannan dabarar meyasa tuntuni bakayi mana itah ba?
to aiyanzu gata kinga darefa yasomayi acigaba dagashi kawai anan suka fara tsotsan junansu harsuka koma zindir haihuwar uwarsu narufe idona dakyar nabaro hotel din nakama hanya jikina kamar waccce aka daka kuka kawai nakeyi naja kafafuwana zuwa bakin titi bansamu dan adaidaitaba nasan yagaji dajirana yatafi
Aisha. Ibraheem
[4:22PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
011
Natari wani dan adaidaita nafada masa inda zaikaini yakawoni gida koda nakai gida zazzabine yarufeni sai magrib muh”” seen yazo yatarar banida lafiya shine nasanar dashi yakirah kowa yafada masa inada magana kowa yataru tashare hawayenta
takalli hameeda wadda zufah yaketa keto mata kamar ruwa takasa ko daga kai balle takalli inda take mairo kam duk ta tsure jin wannan labarin haidar saikallon hameeda yake tace to hameeda kinsamu abunda kikeso daga haydar gashi nan yasauwake maki aruwan sanyi kuma kisani yaudin nan zaki bar masa gidansa
kuma ko allurah banyarda kidauka acikin gidan nan ba tundaga kayan daki har kayan sakawa danbabu nerarki aciki abunda kawai kika saya wajen yawon karuwancinki shine dole kidauka kuma kada kafarki takuskurah kije gidana kokuma gidan yan uwana
innah ce takatseta bakida hujja hure saboda me zaki yanke mata wannan hukunci maitsauri haka munsandai hameeda tabbas bata kyautaba kuma batayo halin yan gidan nan ba itah ce kawai tafitah bare acikin mu
gwaggo tace wlh inna zamanta acikin gidan nan yakare idan dai niyar kice wlh banyarda hameeda takaracin arzikinmubah wlh da inada ikon tare mata nunfashi wlh datuni natareshi tamutu kowa yahuta dabakin iri
saiyanzu alhj auwal yanisah gaba daya maganganun hure sun saka jikin kowa sanyi duk abunda hameeda tayi saikuma sukejin tausayinta jin tsatstsauran matakinda gwaggo tadaukar mata hameeda kam saikuka take
hure agaskiya banji dadin wannan danyen hukunci dakika zartarba yakamata kiyi aiki da hankali itah dai wannan ya yarmuce kuma balaifi bane danke tamaki laifi kice zatabar gidanki kuskurene tayi amman kiyi hakuri maaganar tabar gidan kima baitasobah wlh yaya babu gurbinda hameeda zata zauna agidana bama gidan kaba nibanyarda tazauna ko inabah
takalli inda take kimaza kitashi kibar mana gida bakar daga maibakin hali wlh kincuci kanki da kanki kuma zakiyi nadamar marar amfani arayuwarki”tana kuka tafara bata hakuri momy dan Allah kiyi hakuri wlh aikin shedanne dan Allah kada kikoreni idan kika koreni ina zanje banida kowah aduniya bayanku kune iyayena
gwaggoce takatseta ke dakata nadaina maki wannan kara kije kinemi iyayenka amman niba mahaifiyarki bace!!!!! dam dam gabanta yafadi saiyanzu malam yayi magana haba hure duk da ni ba abakin komai nakebah indai akan yarkine amman baikamata kina cewa taje tanemi wasu iyayenba ba ason yanke hukunci cikin fushi
gwaggo ta daga murya wlh wannan ba yata bace!!!!! saikuma tafashe da kuka hameeda tazaro ido jin furucin gwaggo innah tadaka mata tsawa wannan wane irin shirmene kikeyi kina rantsuwa akan karya dan kawai tabata maki rai
tadago raunannun idanuwanta takalli innah wlh tallahi innah wannan bayata bace shegiyace!!!!!!!!!!!!! innalillahi wa inna ilaihir rajiun” kowa nawajen hankalinsa yatashi bakamar hameeda nikaina birona fadi yayi akan tsananin firgita tonidai tambayata anan ya akai hameeda tazama shegiya???? kuma meyasa gwaggo tarantse cewa bayarta bace uhum saidai munji daga gareta munshare kunnuwanmu muna saurare
Aisha. Ibraheem
[6:53PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [6:35PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
012
Innah tasake katsa mata tsawa waike wace irin uwace da ba aimata laifi kan laifi daya zaki rika kiran yarki shegiya kehaka akai maki aiduk abunda hameeda ta aikata balaifin kowa bane sai naki dankece kika maida rayuwarta haka kika sangartata
danhaka dole kiyi kuka akan rainonda kikaimata banason jinkinsake kiran yarki da wannan sunan tana kuka tace innah bawai karya nayibah kuma ba kazafi naimatabah wlh ba yata bace nasan zakuyi mamakin jin wannan zancen daga bakina nasan idan baniba babu wanda yasan wannan sirrin nabarshi azuciyata kuma na binneshi bantaba sanarda kowaba
tanisah. kuyi hakuri akan abunda nayi kuma kuyafeman musamman mijina tashare hawaye tana kallon malam kamardai yanda kuka sani malam matafiyine baicika zama agaribah bayan na haifi muh seen bansake samun cikibah nikuma ina mutuwar son ya mace idan naga yayan yan uwana mata sai inta rayawa araina inama nima inada mace amman Allah baibanibah
nasan Allah yayi hakan ne saboda yasan bazan iyah bata tarbiyyabah saida muh seen yayi shekara goma sannan nasamu ciki cikin yana matukar bani wahala fiye dazaton kowa amman bandamuba inata rokon Allah yasa macece zan haifa bayan wata tara natashi da nakuda kuma gashi mijina bayanan muh”seen ne yakiraman kawata sa ade itah takaini asiviti cikin motar ta bayan ankaini dakin haihuwa nasha wahala sosai sannan nahaihu mace amman batazo daraiba”tashare hawaye tunda naji haka naita kuka likitanda take dubani tayita bani hakuri baiwar Allah kiyi hakuri haka Allah yakaddara maki kuma hakika mahaifarki tasamu matsala bazaki sake samun haihuwaba kuka yaci karfina
inata kuka tayita bani hakuri anan nake fadamata ina mutuwar son ya mace da dayane nake dashi yanzu shikenan banda mace tayi shiru nadan wani lokaci sannan tadan kalla gefena taga bakowa tace zan iyah taimakonki wata mata tahaihu yanzu. tare aka kawoku amman tayi tafiyarta tabar yar zanyi musaya sai inkai taki acen dasauri nace inaso wlh hakan kuwa tadauki yata matatta takai tadaukoman waccen wadda uwarta tagudu
takawoman na amsa ina kuka na sumbaceta tace to amman fa kada kisanarda kowa dan nataimaka maki idan akasamu labari za a koreni nataimaka makine dan naga kinason mace kuma nasan bazaki cutarda itah ba nashare hawayena nace nayi maki wannan alkawarin bazan fadawa kowaba kuma zanriketa amana inata murna nabar sirrin cikin raina mukai musayar nmbar tundaga ranar nacire sim din na aje dangudun kada maiyar tadawo takirani tace inbada yar
da aka sallameni nadawo gida dayata kwana uku da haihuwar malam yadawo kokadan banason kowa yazo kusa da itah ranar suna akasakamata suna hameeda daganan naci gaba da shayarda itah nayarda inrasa farincikina indai akan hameeda ne waini innuna mata gata ashe sangartarda itah danayi babbar illace gashi yanda tamun sakayya dama hausawa sunce barewa bata gudu yarta tayi rarrafe duk yanda naso tunda hameeda tayo halin uwarta dolene tayi yawon karuwanci kinji asalin lbrinki
jikin kowa yayi sanyi dajin wannan labarin kowa yayi jugum gaskiya akwai alamar tambaya wanda bakowa zaisaniba duk wanda yaganta zaiyita tunanin wata biyo malam ko hure dankuwa bata kama dayan gidan kaf
Aisha. Ibraheem
[6:58PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
013
Dan Allah malam kayi hakuri akan wannan abu danayi kuma ina neman afuwarku nasan na aikata babban kuskure”malam yanisah nidai indai tawaje nane babu komai wlh amman fa gaskiya abunda kikai baki kyautaba sam sam
daganan dakin yayi tsit kowa da abunda yake sakawa aransa bakajin komai sai tashin kukan hameeda tashi tayi takoma kusa da gwaggo kanta yana kasa mom nagode da irin rikonda kikaman tamkar ke kika haifeni hakika wannan kawai ya isah insan niba kowa bace kuma nayi nadamar abunda nadade ina aikatawa meyasa baki sanardani asalinaba tun farko daban kasance mai aikata irin abunda mahaifiyata takasance tana aikatawaba
nasan karancin ilimin addinine yake damuna da inada ilimin addini nasan dabazanyi wannan abuba kugafarceni dan Allah takalli haydar dan Allah ya haydar kayi hakuri akan abunda naimaka tun farkon aurenmu nasan nayimaka wulakanci sosai narabaka da iyayenka da matarka natsawon shekara hudu daganan tabasu labarin abunda taimasa a india tanisah wlh nayi nadama sosai kuma hakan yasamo asaline akan kiyayyarda kake nunaman
tajuya wajen mairo dan Allah sister kiyafeman akan abubuwanda naimaki dawanda kika sani dawadanda baki sanibah maryam tace wlh bakomai nibakiman komaibah sister takalli haydar yayana kaima kayafe mata yanisah bakomai nayafe mata duniya da lahirah
tamaida kallonta wajen gwaggo mom duk kalamanki banji haushin subah amman naji zafin kalma daya dakikace baki yafeman nononki danashafa. ba inaso kidubi girman Allah kiyafeman yazama amatsayin sadaka!!!malam yace hameeda anyafe maki kinji daina kuka ai bakida laifi itah ce babbar mai laifi
tasake kallon gwaggo sannan taduke kai momy inaso kiman taimako daya dan Allah kinunaman mahaifiyata idan ma tana raye idan tamutuma insani amman inason sanin iyayena koda batahanyar sunnah suka samenibah
kukane yaci karfinta. gwaggo tanisah agaskiya nibansan iyayenkibah amman bari ingwada nmber doc din kozan sameta tadauko wayarta talalubo nober tayita ringin amman ba a daukabah tasake kirah nan ma haka saida tayi kirah uku sannan akadauka daya bangaren akafarayin sallama gwaggo ta amsa
tace dan Allah ina magana da doc khadija ce??? tace eh itah ce gwaggo tanisah Alhamdulillah nasan baki ganenibah nice matarda kika taba baiwa kyautar ya shekaru ashirin da bakwai dasuka wuce dasauri tace hurairah ko???? gwaggo tace eh yanzu kina ina????
ta katseta dan Allah kiman kwatancen gidan ki ganinan zuwa yanzu gwaggo takalli su innah innah tace tome kike jirah kifada mata mana” tanisah ina tudun wada idan kika kawo kice agwada maki gidan Alhj auwal ko karamin yaro kika tambaya zainuna maki tace to nagode ganinan zuwa dasauri tayi magana tana katse wayar takamo wata nmber jikinta haryana rawa takara akunne tafara ringin
matar tana kishingide jikin kujerah daka ganta kaga alamar hutu atare da itah tana sanye dawasu kaya masu kyau na manyan mata ga kayan ciye ciye nan agabanta amman hankalinta baya jikinta kwata kwata
Aisha. Ibraheem
[7:52PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
014
Talulaya duniyar tunani har wayar tatsinke akasake kirah sannan tafarga ganin sunan doc khadija yasa tadauka bakinta haryana sassarfa wajen magana doc ansameta?? daya bangaren aka amsa eh nasameta yanzun nan takirani
kisameni gidana yanzu saimuje tace toh ganinan zuwa takashe wayar takamo nmber maigidanta tana fara ringin aka yadauka gimbiyata barka da warka..alhj kadawo gida ansamu matarda aka baiwa yarmu dasauri yamike da gaske ganinan zuwa yakashe wayar
yataso dasauri yayi sallama da abokinsa yaja motarsa saigida cikin falo yasameta tsaye suka juwo yabude mata motar tashiga shima yazagaya yazauna sukahau hanya. sai gidan doc khadija awaje suka sameta tana jiransu tashiga bayan motar tagai shesu tafada masa sunan unguwar. da sunan maigidan yace kice gidan abokina ainasanshi sosai wlh abokin kasuwancina ne
suna isah kofar gidan yayi hon maigadi yabude masu kofah suka shiga shine yanuna masu falonda suke meetn din kaitsaye suka kutsa kai ciki.alhj auwal yana ganinsa yamike da fara arsa Alhj isah kaine agidan namu shiru yayi ganinsa tare da wasu kuma da alama tare suke idanunta tarr akan hameeda duk wanda yakalli matarda tashigo tabbas bazai rabata da hameeda ba
gwaggo tamike yauwa ga doc din nan tazo takalli hameeda kinga wacce tabani ke nan tayi nuni da itah dasauri hajiyan takarasa. tarungume hameeda tana kuka” alh isah yasamu waje yazauna itah kuka hameeda kuka saida suka dade ahaka sannan tajuyo wajen alhj isah tace kaga yarmu shima hawayen yakeyi yace taso yata ba musu kuwa hameeda taje gunda yake taduka yasafo kanta yana murmushi
duk dakin su akebi da kallo bakamar haydar alhj auwal yace waidama abokina wannan yar takace??? yanisah kwarai kuwa itah ce kawai jinina aduniya yashare hawaye Allah nagode maka dakanunaman jinina
hameeda tafashe da kuka ashedai itah ba shegiya bace kamar yanda gwaggo tace takalli abban ta takuma juya wajen maman ta ummah meyasa kika yardani bayan kin haifeni laifin menayimaki dakika yardani alhalin bansan abunda duniya takunsaba
tafashe da kuka itah ma hajiyar tafashe da kuka kiyi hakuri yata nasan bankyauta makibah amman babu yanda zanyi saboda batahanyar aure muka samekibah dam dam gaban hameeda yafadi chakwakiya kenan
taci gaba nidai sunan kubrah sunan mahaifina abubakar sunan mahaifiyata fatima mu biyu ne wajen iyayenmu dani da yayana bashir babana babban malamine nibayar nan kasar bace asalina yar sudan ce. mukadawo gombe da zama arayuwar babana bayason yarsa tawuce scn dry batareda yayi mata aurebah
kasancewar mamata yar bokoce itah kuma tanuna masa tanason inyi karatu dakyar babana yayarda amman yace bazanje wata kasaba dakyar aka yarda yabarni inje kano”taci gaba ranarda zanzo babana saida yayiman nasiha akan insan irin mutanenda zanyi mu amala dasu kada inzubarda kimata ta ya mace amakaranta
ina kuka nabar iyayena tunda nafara karatu bana wasa banada kawaye kodaya danni banyarda dakowaba ina shekara tabiyu nahadu da isah amakaranta yanuna yana sona amman nibana kulashi kullum saiyamun magana tun inashareshi saina fada soyayyarsa tsundum hakan yasa nafara kulashi mukakama soyayya kamar muhade junan mu isah yanada hankali kuma yanada ilimi addini
illarsa daya duk abokansa yan iskane basuda aikin komai saina neman mata kullum yana masu wa azi sudaina bakyau amman kamar kara turasu yake watarana suna zaune sai usher yace guys wlh ni abunda isah yakemana yana bataman rai
shamsu yace barshi waimu zainunawa takawa damunyi abu yadamemu da kala Allahu kala rasulu todan me akayi matan badan mutaka suba ni wlh biyar ma idan zan samu zantaka insha dadina”‘ osy yace hahah wlh dazaku yarda damun tsula masa tsiya suka taba suna shewa shegen gari mekasamo mana yajawosu sukai maganar sirri aikam suka kama dariya harda buga kafa lallai kasamo dabara nasan yanzuma yanacen wajen ta bari mumaza kafin yazo
suka dau lemu suka zubah masa maganin suka mayar a fijij din dakin minti biyar kuwa saigashi yashigo da sallama suka amsa masa yace ashe kunanan inacen ina nemanku suka kalli juna suka gimtse muna nan muna hutawa yabasu hannu suka
gaisa yazube saman katifar dakin zuwa mintota yamike kunga anfara kirah muje sallah babu musu kuwa suka mike sukai alwala suka wuce masallaci saida akayi isha i suka dawo suna shiga dakin yayi wajen frig yabuda lemu daya kawai yasamu babu ruwa kuma kishi yakeji babu wata tantama yasha abunsa saida
yashanye yake tambayar nawaye basu koma kansaba dariya sukeyi ciki ciki
Aisha. Ibraheem
[8:20PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
015
Yasake tambaya osy yace tunda kashanye magana takare basaikadamu kanka dasanin kona wayeba yadaga kafada alamar shikenan yayarda gorar yakoma saman katifar yafadi jagwab
suka kalli juna suka kyaf ta ido zuwa mintuna ashirin isah yafarajin wani yanayi najikinsa yadafe kansa shamsu yajawo wayarsa yakirah budurwarsa suka fara firar batsa isah yana jinsu dan hansfree yasaka sailumshe ido yake yana budewa saiya samu kansa dajintsikar jikinsa tana tashi tunyana daurewa harya fara nishi wata irin sha awa ce tataso masa suna ganin haka suka sheke da dariya
osy yamike kutashi muje clup guys yakalli wajenda isah yake yana dariyar keta kozaka bimune kaima kadana munga kaima yau kana cikin halin sha awa ya cije lefe hannunsa yana dafe da mararsa yace ah ah ina neman tsarin Allah daga aikata zina dan Allah kudaina yiman maganarta kuma ina neman maku shiriya
shamsu yayi dariya suka taba yace mungode amman fa kasani babu makawa kaima saika aikata abunda kake gudu dankuwa lemunda kasha munsa maka magani aciki kuma dole saikayi tarayya da mace komai ustazancinka idan ma zakataso muje kataso wasu hawaye yaji suna bin fuskarsa meyasa zakuman haka shamsu?? amman wlh kuncutar dani
menene ribarku idan kuka sakani na aikata zunubi???suna dariya suka fitah mudai muntafi idan kaji bazaka iyah ba kasamemu a clup muna daki mailamba 7 sukayi ficewarsu anan suka barshi yanata murkususu yarasa yazaiyi abunda baitaba yibah duk yanda yaso yadaure amman hakan ya gagara wayarsa yajawo ganin shedatai tana neman barin jikinsa yakirah nmber kubrah tana kwance adakinsu tana karatu taji kirn wayar dasauri tadauka da sallama
saitaji muryansa sai ahankali cikin sauri tace isah lafiya yace banda lafiya kubrah dan Allah kisameni dakin mu yanzu ” takalli agogo isah dare yayifah””yacije bakinsa dan Allah kitaimaka kizo wlh zan iyah mutuwa “”wata kara yasaki nan take hankalinsa yatashi mikewa tayi tadauki hijabinta tafito.
tahau dan adaidaidai ta zuwa bakin makarantarsu itah inda take zama ba kusa da makaranta bane sune suke zaune kusa da makaranta kaitsaye dakinsu tanufah tun akofah takejin kukansa dasauri takarasa cikin dakin haryanzu yana dafe da mararsa
lafiya isah meyake damunka dakyar yake magana kubrah kitaimakaman dan Allah”wanne taimako zanyi maka isah ina abokanka???? suka barka nan??? yasake cije baki danshi kawai yasan abunda yakeji kubrah suna clup yau sun cuceni sun cuci rayuwata dakyar yasamu yafada mata abunda sukai masa
bakaramin rudani tashigaba yanzu daka kirani toni wane taimako zanyi maka???? yace kubrah nasan kece kawai zaki taimakaman insamu ingusarda wannan lalurah dasauri taja baya tana girgiza kai inah bazai yuwuba isah da wanne ido zan kalli iyayena agaskiya bazan iyah cin amanar iyayenabah
shima kukan yake kubrah kitaimakeni wlh zan iyah rasa raina kekanki kinsan ba halina bane wannan kaddarace kitaimakeni yaci gaba dakuka haryanzu bata daina jada bayaba inah agaskiya bazan taba aikata wannan mummunan aikinba kayi hakuri isah nasan kanasona kuma nasan ba halinka bane amman bazan iyah ba inajin tsoron mahaliccina
juyawa tayi tafita dagudu tana kuka kubrah dan Allah kada kitafi kibarni cikin wannan halin kitaimakeni tana jinsa amman taki juyowa wata kara yasaki nan take yasuma
Aisha. Ibraheem
[6:53PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [11:33PM, 11/30/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
016
Hartayi nisah saitaji kuma bazata iyah barinsa cikin wannan halinbah dasauri najuyo zuwa dakin na tarar yasuma nayita neman ruwan bansamubah saina shiga tolet dinsu acen nasamu sun boye ruwa nadauko daya nadawo jikina sairawa yake
na yayyafa masa yasaukarda ajiyar zuciya sannu ahankali yabuda idonsa dakyar ya iya kiran sunana nima ina kuka na amsa yacije lebe kitaimaki rayuwata kikaini clup wajen su osy wlh bayanda zanyi da rayuwata sunriga suncutardani
ido nazaro jin wannan zancen yasake maimaitawa kitaimakeni kikaini kubrah;;kai nagirgiza ah ah isah bazan yarda kaje clup ba banason rayuwarka tafada cikin hadari duk da inajin tsoro amman bazan iyah hanaka aikata hakan akainaba naruntse ido wasu zafafan hawaye suka zuboma”yagirgiza kai ah ah kubrah nasan dagayau shikenan kada inbata maki rayuwa kikaini dai clup din idanuna naruntse sannan natube hijabin jikina narungumeshi daganan duk almari yasauya duk dagani harshi kuka muke sanin abunda muke aikatawa bawai zafin abunne yasakani kukaba zafin dawanne ido zan kalli mahaliccina dakuma iyayena
nasha matukar wahalaa dagani harshi musamman shima dayagaji amman kuma maganin baisakeshiba karshe dai haka muka suma awajen sanyin asubane yafarfado dashi. yana kallona yadauke kansa yafashe da kuka yana buga kansa da bango kukansane yatasheni nikaina bana iyah daga kodan yatsa nima sainakama kuka
mundade ahaka sannan nayi karfin halin yunkurawa nakasa shine yataimaka yakaini tolet dinsu nakimtsa kaina nayi wanka zazzabine yatasoman gashi ko tafiya banayi dankuwa yamun illah sosai ajikina shima yayi wanka ina zaune ina kuka yatada sallah yana kuka yana rokon gafarar Allah abokansa dama a clup suke kwana
gashima washe gari babu sch karfe bakwai nafita dakin yarakani nasamu. adaidaita yakaini gida saida naje sannan nagasa kaina nasiyo magani nasha sannan nakwanta””bajimawa barci yadaukeni””aranar isah yakwashe kayanshi yabarmasu dakin yakama wani dakin nesa dasu tundaga ranar baisake kulawa kansubah ko hanya suka hada saidai yakauce duk yanda sukaso sushirya yaki sunyita bashi hakuri amman isah yaki hakurah kasancewar sunsan babanshi mai kudine kuma wajensa suke samun yan kudin kashi
tunda hakan tafaru saikomai nasu yatsaya suka daina neman matanda sukeyi komai yayi sanyi kunsan saida kudi ake iskanci idan babu dole abari koda hannuna wlh isah baisake rikawaba sai inyi wata daya bansakashi a idobah kalu bale gareku yan uwana yanada kyau mutun yasan irin abokanan da zai rikayi kungadai abunda yafaru da isah Allah yakara shirya mana zuriyarmu
dankuwa damun hadu babu abunda mukeyi sai aikin kuka nashiga tashin hankali ganin watana uku banga al adatabah bakaramin rudani nashigaba hakan yasa nakirah isah nasanar dashi innalillahi wa inna ilaihir rajiun itah ce kawai kalmarda yake furtawa tare da zubowar hawaye nice mai karfin guywar bashi hakuri
dakyar nasamu yadaina kukan naje asiviti aka aunani inadaciki wata uku dama ninasan hakan zaikasance nashaidawa isah ranar kamar yakashe kansa haka yayita buga kansa da bango yana kuka ..kasan kafarsa naduke nima kukan nake isah kayi hakuri wannan KADDARAR MUCE sunan littafin sister yakamata muyi imani da kaddara haka Allah yarubuto mana nima nacigana da kuka
dukanmu bamu yarda muzubarda cikin ba dangudun aikata kisan kai haka nayita rainon cikin batareda kowa yasanibah dama bana yawo da gyale kuma cikin saiya shige cikin jikina koda nacire hijab bazaka taba ganowaba saidai kirjina ya cicciko nayi mazaunai
kuma nayi haske cikin yanada wata tara nakama nakuda dakaina nakai kaina asiviti bansanarda isah ba
Aisha. Ibraheem
[5:33PM, 12/1/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
017
Cikin ikon Allah nasauka lfy ahannun doc khadija saida nabari tafita ina kwance kusa da jaririyar saitunani nakeyi yanzu idan harnaje da wannan ya gidan mu dawanne ido zan kalli iyayena nayita kuka nikadai wata zuciya tabani shawarar intafi inbarta bantsayayin wani nazaribah namike jikina bakwari nasumbaci goshinta hawayena suka zuba akan fuskanta
saitsala ihu take kaman tasan abunda nake shirinyi ina tafiya ina waigenta harna bar asivitin batareda wani yaga fitowatabah nadawo gida ina zaune tunani yadameni abunda nayiwa yata bankyautaba aiba laifinta bane kuma nima kaddarace duk da inason kawarda tunanin akanta amman abun yagarara idan narufe idona itah kawai nake gani hakan yasa nakasa sukuni nakoma asivitin amman bansametabah
wajen doc khadija naje ina kuka tana ganina daman taganeni amman kuma saitacemun wlh tabawa wata yata amman bari takirah ta awaya taji koda takirah nmber tajita akashe tayita bani hakuri akan kada intona mata asiri za a iyah korarta bayanda zanyi haka nadawo gida jiki bakwari nacigaba da kula da kaina
isah baisan ma nahaihubah. watana biyu da haihuwa muka kammala karatun mu zankoma garin iyayena aranar nasanar dashi nahaihu amman abun baizo daraiba ya amshi adres din gidan mu muka rabu muna kewar junanmu tunda nakoma gida banda aiki kullum saina tunani samarina kaf babu wanda nake kulawa dankuwa nasan koda nayi aure mezankaiwa mijina amatsayina na wacce tazubarda kimarta
abangaren isah kuwa saidai muyi waya amman haryanzu yakasa turowa kuma ninakasa cewa yaturo ana haka babana yace wani yaturo iyayensa neman aurena kumashi yabashi dankuwa yagaji da zubaman ido kuka kam nasashi kamar me bandamu da sanin sunan kowayebah bankuma taba ganin shibah har aka daurah man aure dashi sairanarda aka kaini naga ashe isah ne.
munyi zaman soyayya da fahimtar juna saidai abunda yake damun mu dayane rashin haihuwa tsawon shekarunda mukayi ko bari bantaba yibah kullum nakan shige daki inyita kuka saidaga baya nasanarda isah yarda nahaifah bata rasubah nafada masa yanda abun yafaru baiji dadibah
wannan dalilin yasa muka baro gombe zuwa kano badan komaibah saboda neman yarmu ko Allah zaisa muganta iyayen mu kansu sunsan da labarin saidai kuma komai kaddarane kuma rubutacce babu yanda zasuyi babu ranarda zamu kwanta batareda tunanin yarmubah ina rayawa araina yanzu kotana raye kokuma tarasu idan tana raye aiyanzu ta isah aure watakil ma harta hayayyafa takai karshen labarin tana share hawayee
Aisha. Ibraheem
[5:54PM, 12/1/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
018
Kowa nawajen kuka yakeyi bakamar mairo jitake kamar itah ce wannan abun yasama hameeda kuka take kamar ranta zaifita tace mamana nayi aure amman banhaihubah lbrin rayuwata baida wani sha awar jiga kowa hakika nayi dace da iyaye dasuka rikeni tamkar susuka haifeni suka fifitani akan dan cikinsu
saidai kawayen sunyiman hudubar shaidan wadda tarinjaye ta iyayena sune suka jefah rayuwata cikin hadari da halin rayuwa ina maineman afuwarku banyi tir dakasancewata bayar sunnaba wannan yazama kaddarata dama komai arubuce yake taci gaba da kuka kowa wajen yayi tsit alhj auwal yayi gyaran murya yakalli haydar yakirah sunansa yadago asanyaye shikanshi tausayin hameeda yakeyi kuma ashirye yake daya gyara zamansu
na am abba yanisah inaso kadubi girman Allah kamaida matarka dakinta kadaiji abunda yafaru duk aikin shedanne ina fatar komai yawuce shiru yayi sannan yamaida kallonsa wajen mairo tayi murmushi tadaga masa kai alamar yayarda hameeda ce tayi magana inaso inyi magana abba
yace munajinki hameeda tanisah nagode da kaunarda kuka nunaman duk da nakasance bacikin tsatsonkubah duk abunda naimaku bakudamubah kunaso inkoma acikin danginku saidai kuyi hakuri nahakurah da auren ya haydar kada kuyiman tilas akan komawa gidan sa bazan iyah yimaku musubah dan kunchanchan ci inbi umurninku saidai koda zan kara aure anan gaba inaso saina samu ilimin addini dayanda zanyi zaman aure
sannan inaso in samu mijinda yakesona nake sonsa ina fatar zaku karbi maganata” kowa yayarda da maganar hameeda sukaimata fatan alhairi daganan akaiyiwa juna godiya gwaggo sai kuka ganin take shikenan anrabata da hameeda dankuwa tanasonta kamar ranta suna kuka suka rabu tabi iyayenta ko kayanta basu tsaya daukabah sukai hanyar gida saida suka sauke doc khadija suka wuce gidan su
wai Aljannar duniya ashe su gwaggo karyar arxiki sukeyi mahaifin hameeda yanada kudi naban mamaki dakuma kwatance ai hameeda baki tasaki ganin tsaruwar gidan nasu tamkar aturai komai yimata akeyi saitarasa wanda yafisonta tsakanin mamanta da babanta sunkirah yan uwa sun sanar dasu anga hameeda
suntayasu murna sosai alhj isah harda walima yahada ta musamman saboda yarsa ranar walima saida tagayyato su gwaggo haydar ma yaje da mairo da yayansu sukansu dasukaga irin daularda hameeda take ciki saida suka girgiza
hameeda kam tayi sanyi dukiyar sam bata dametaba tafarazuwa islamiyya damacen tasauka amman duk ta manta yanzukam karatu take bawasa sannan idan tadawo gida kuma akwai malaminda yake mata sauran littafai. tadinka hijabai manya manya da nikaf idan kaga hameeda saita baka sha awa rayuwarta ta chanja kwata kwata.
alhj hamzane zaune cikin gidan sa nahutawa.yanzu yadawo daga tafiyarda yayi tsawon wata daya yajawo yar kwalbarsa yana murmushi yakalli kwalbar yakirah sunan hameeda sau uku yamayar ya aje yayi kishingide yana jiranta
Aisha. Ibraheem
[6:53PM, 10/22/2016] My Lovly Kawa: [7:37PM, 12/1/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
019
Takabbarta sallar la asar cikin natsuwa tafara sallah harta kammala ra aka a hudu ta sallamae tadaga hannu tana kai kukanta wajen Allah yayafe mata kurakuranta aduk sanda tatuna da irin rayuwarda tayi abaya takanyi kuka tayi tir dahalinta saidai kuma idan tatuna Allah gafurur raheem ne takanji sanyi aranta tadade tana mai kaskantar da kanta wajen Allah sannan tashafa addu arta idanuwanta suna mai kwaranyarda kwallar
tadauko kur aninta tafara karantawa tsayin mintuna talatin yana zaman jiranta amman shiru hakan yasaka yasake dauko kwalbar yasake kiran sunanta dakarfi har sau uku yajirah amman still dai babu alamarta yadauko wayarta yakirah saiyajita kashe yasake dauko kwalbar yana kiranta daya gana biyu tayi bindiga tafashe abunda yake ciki yabi iska
ido alhj hamza yazaro menene yake faruwar da wannan kwalbar baida wata cikakkar amsa hakan yasa yatashi da hanzari yayiwa dajin da bokansa yake cinke dankuwa yasan akwai matsala tunkafin yakaida zaunawa yafara korah masa jawabi sannan yasamu wajen zama
bokan ya turkune fuska tunda naganka nasan babu lafiya amman ya akai kwalbar tafashe bari mugani yadauko madubin tsafinsa yafara sambatu yana shafa madubi kaiiiiiiiiiii wata zaburah bokan yayi wadda ta haddasa tsakewar madubin tsafinsa
nan take hantar cikin alhj hamza tamotsa kutumar ubah wlh aiki ya warware alhj hamza yace kamarya boka toyanzu menene abunyi???? yagirgiza kansa ai wani babban lamari nagani hameeda tana zagaye da wani haske mai matukar kariya agareta yanzu duk wani surkulle namu dayake jikinta natsayin shekaru goma ya warware
babu kuma wani aiki wanda zamu aika mata yanzu yasameta alhj hamza yakatseshi haba boka yanzu da akwai abunda zai gagareka???? kwarai kuwa bamu iyah yiwa ma abota hasken goshi sihiri duk wani maiyawan ibada da salloli dayawan addu oi yanayin azkar aljannun mu koda kusa dashi sukaje zasu kone atake
ya musmuta kamar yayi kuka amman boka ya akai hakan tafaru bayan kace yimata aiki abune maisauki??? adah nafadi hakan amman ayanzu wlh tafi karfina kana iya zuwa duk wajen bokanda za kaje amman nikam wannan aikin bazan iyah ba alhj hamza jiki bakwari yabar wajen boka kasa komawa yayi gida haka yayita bin bokayensa amman maganar dayace daga karshe yasamu wani bokan yabashi wani kwalli yace yasaka kwallin yakwanta kwana da tunanin ta acikin zuciyarshi to zaiyi mafarkinta muddin takwanta kwana
zasu hadu acikin mafarki shikenan zata dawo gareshi har abadah idan kuma bata kwantaba tabbas zai haukace yayi masa godiya maitarin yawa dankuwa shiyasan duk yakwanta kwana saiyayi mafarkin hameeda suna aikata alfasha wannan kuwa baidameshiba dajin furucin hauka da farinciki yadawo gidah
karfe goma yadauko kwallinsa yasaka sannan yakwanta da tunanin rayuwarsu tabaya da hameeda shiyariga yayi yakinin hameeda matarshi ce babu kuma wanda ya isah yarabashi da itah sai mutuwa duk matansa basa burgeshi sama da hameeda baya samun gamsuwa matukar batare da hameeda yakebah yayi murmushi tunowa da kalaman boka ba shakka gobe warhaka yana nan tare da annurinsa
kuma yakudiri aniyar har abada bazai bari ta kubce masabah yajawo filo yaci gaba da barcinsa
Aisha. Ibraheem
[8:12PM, 12/1/2015] gentle ladyyy💃🏻: 💭YAR SADAKA!!!💭
020
Tunranar da hameeda tadawo gidan su batada lokacin kwanciya kullum cikin sallolin dare take tanakai kukanta wajen Allah yauma kamar kullum haka takwana saida akai asubah haske yafito sannan takishingida tana lazimi harbarci yadauketa
*******************************************
akwana atashi babu wuya gashi har maryam ta yaye yayanta yanzu tana dauke dawani cikin suna yawan zuwa garinsu mairo da itah da maigidanta haydar rayuwa tayi dadi inda muhd yayi aure matarshi rukayya kasim kuwa ya auri fatima kanwar fadil matar fadil Aisha tahaihu namiji akasamasa haydar
su hardo yanzu sana arda suke takarbesu akullum sukayi sallah sunayiwa haydar addua yasa yagama daduniya lafiya hameeda takan kawo masu ziyara hargidansu kursum suma sukanzo gidansu yanzu hameeda tazama malama amman kuma abu dayane taki tsaida miji tayi aure dan itah tsoron auren ma take
alhj shamsu yasamu alhj isah akanyanaso yatur sagir yafara soyayya da hameeda koda hakan zaisa alhj isah yayafe masa abunda yayi masa wanda tasanadinsa suka samu hameeda dakyar yayarda dahakan cikin sa a kuwa sagir yana ganin hameeda yaji yana sonta shima yataba aure matarsa tarasu tabarshi daya daya khadija
itah kanta hameeda taji yamata duk da haryanzu akwai sauran son haydar acikin zuciyarta amman tasan yanzu anriga anzama yan uwan juna sati biyu kawai akasaka akai aure biki bam yayi biki yangidansu haydar kaf babu wanda baijeba aranarne kuma akayi walimar haddace akur ani da hameeda tayi tasamu kyaututtuka dadama mairo kam tareda itah akakai hameeda dakin mijinta saidai suyi masu fatan samun zaman lafiya rayuwa kenan
sagir ne zaune saman kujerah hameeda tana gefensu likita yagama yan rubece rubucenda zaiyi yadago yana murmushi yamika masa hannu suka gaisa ina tayaka murna matarka tanada juna biyu kuma yaya biyune kwance amahaifarta yamika masa takarda da hoton sagir baki harkunne bakamar hameeda data rufe ido wai kunya agaban likitan yafara sakar mata kiss
wayarsa yajawo yafara kiran su mom dinta yafada masu yakirah su haydar yafada masu sannan mamanshi da dad dinshi kowa murna yake yana mata fatan sauka lafiya yayiwa doc godiya chak yadaukota tana zillewa ganin mutane saikallonsu ake ammanshi ko ajikinsa saida yajingineta cikin mota yalakuci hancinta aikinsan Allah dagayau bakebayin tafiya dankuwa bazaki wahalmun da yayanaba tayi murmushi yazagawo bari muje musha ice cream
sunakan hanya sukaci karo dawani waje mutane cinjim babu ko hanyar wucewa wani mahaukacine zindir haihuwar uwarsa yarasunata jifansa sagir ne yafito yana tsawatar masu kamar ance hameeda kalla tazaro ido ahankali tace alhj hamza haka Allah yayi dakai jitayi jikinta yana rawa. ganin sagir yayi kusa dashi tafito dasauri tana kwala masa sagir kirah yanajiyo muryarta yayi ido hudu da itah yaruga dagudu yana kaiwa saman titi motah takwasheshi ko shurawa baiyibah wata kara hameeda tasaki taduke tana kuka dasauri sagir yadawo wajenta yana tambayar lafiya tace muje gida nidai banason ganin wannan abun yadauketa cikin motar suka wuce kokallon inda yake batayibah mutane suntaru wajen suna kallo harsukakai gida hameeda batadaina kukaba yinin ranar sukuku tayini harzuwa dare sagir yakasa gane kanta
suna kwance saman gado amman hankalinta bayajikinta yajawota jikinshi waimeyake faruwa hameeda daa ganin alhaj hamza duk kinbi kindami kanki abunda yawuce aiyawuce banason kina tunawa dashi dasauri tajaye jikinta taga kirjinsa tana kallonsa dama kasan abunda yafaru??? ido yalumshe mata alamar eh yace nasan komai matata danhaka kidaina damun kanki nidazuciya daya nakesonki banatuna abunda yawuce kema inaso dagayau kidaina tuna komai inba yayanaba yashafa cikinta cikin dariya ta makalkaleshi daganan wasa yasauya nidai saina fito najamasu kofah
ALHAMDULILLAH inagodiya ga Allah dayabani ikon karasa wannan labarin inda nayi kuskure Allah kayafeman Allah yasa mutane zasu amfana da darasin dake cikin wannan labarin Allah yasa mufikarfin zukatanmu
SADAUKARWA
Nasadaukarda wannan littafin ga yan uwana kuma masoyan wannan littafin kaihardama wadanda basasona nidai ina sonku saboda ku yan uwanane almuslim ahul muslim daga karshe ina miko godiyata gawadanda suka karfafa man guywa dan intoshe kunnuwana daga masu sukata godiya agareku
taku har kullum
Aisha. Ibraheem
08069067379