Monthly Archives: March 2017

[7:12PM, 1/31/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Page 1-2

     By

Gentle Lady💃🏽

Dasunan Allah mai rahma maijinkai”” dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki maikowa mai komai ina kara godiya ga Allah subhanahu wata ala “” Wanda yabani ikon fara wannan labarin Allah yasa jama a zasu amfana da fadakar wardake cikinsa
Hakika komai kaga yasamu bawa mukaddarine daga Allah Amman kuma akwai sanadi wannan labarin kirkirarren labarine nayishi domin tsokaci dawadansu abubuwa dasuke faruwa acikin al umma””
Wacce wannan labarin yaxo daidai darayuwarta saita tuba tadaina domin ganin makomar Wanda yake kwatankwacin irin halintaa Allah yasa mudace Ameen
Wannan labarin narubutashine ra ayin kaina danhaka Wanda yaji zai iyah karantawa banhanashiba saidai kuma akiyaye karwani ya sarrafamun shitawata hanyaa idan kunne yaji gangar jiki tatsirah

*BISMILLAH*

***********************

 Gabadaya unguwar cinkushe take da manyan motoci sai kaikawo sukeyi alamu sun nuna wani mihimnin buki akeyi na wani kasurgumin maikudii Dan la akari da yawan motocin dasuketa karakaina hakazalika masu tsadar gaske kaima kasan ba bikin”” fukara”u bane
Bakin kofar gidan tacika makill da maroka dakuma masu kidaa”” ahakan nasamu tattakawa zuwa kofar gidan duk da dakyar nasamu nakai wajen asheni banga jama a ba dankuwa cikin gidan tamkar anabikin nadin sarautane”” 
Sai rarraba ido nakeyi domin samun hanyar shiga wannan katafaren gidan ginane namusamman maihawa hudu anyimasa fentiii da farin fentiii maishegen kyau da shekiii wannan gidan kusan yafi kowanne gida kyau dakuma tsari gabadaya ya haskaka unguwar anayiwa gidan nan lakabida farin gidaa!! Tofa Allah yasa abunda yakecikinsafarine🠽򢠊

Kutsa kaina nayi Cikin gidan kofar shigama abar adubace””nagama zagayena nikam banga alamar matar gidan ba”” dankuwa irin wannan gidan yakamata ace matar gidan ta banbantaa dayanbukiii ajikinta kadai za agane””
Nayi zugum inabinsu dakallo nace tomezaihana insaurari firarsu watakil nagane matar gidan aciki🤔 wannna shawarar nayarda da itah nafarabi lungu dasako ina saurare abun takaici abun bakinciki duk inda nawulga zancensu kusan dayane kishiyaaa!!!!
Waimenene illar kishiyane??? Kumata kunada abun mamaki idan mijinku ya aureku yace zaikara aure kuyita fitinaa toyakenan idankuma keza a aura??? Itakuma matarsa taceme??? Yakamata zuwa yanxu mata sugane Susan kalar kishinda zasuyi kuyi koyi da matan Manzon Allah (S A W) suma sunada kishi saidai nasu sunayinsane abisa tsari kowacce tanarigengen wajen kyautata masa domin tasamu matsayi fiye Dana dayar
Amman wasufa saboda tsabar bala.i da masifa daga ranarda yasoma maganar kara aure tofa ya ballowa kansa likii zatadaina wanka tabar dafamasa abincii wata hatta gadonta baxata barshi yakwantaba dazaran yace yimun kaza tace bazanyiba kajecen wajen amaryarka taimaka tabar yayanta acikin wahala waifa a irintata wautar waita naso tazubawa mijin haushine shikuwa dayafita iyawa saiyabuge iskanta yayima dadai duniya kamarma baisan da zamantaba sai idan tayi masifar tagababuci kuma biki yanata karatowa sai afara yangyare gyare waidaga bayakenan sadaka da bajawara bayan kinzubarda girmanki kimarki darajarki 
Bari nabaku wani sirri wlh idan mijinki zaiyi aure kika kwantarda hankalinki zakici arziki komai kikeso zaiyimaki domin yataushi zuciyarki kuma zai rika tambayarki menene kikeso haka zalika komai zaiyiwa amaryar zairika neman sha wararki”” sabanin idan kikasoma fitina zaiyibanza dake duk wuyartadai kece akasa bazaki hanashi auren ba
Saikiyi ba1 ba 2. Darajarki dayake gani kinbata bazaisake yarda dakeba kuma koda amaryar tashigo gidan akatada fitina kodakuwa kece mai gaskiya bazai yardaba zaice aiyaga take takenki tunkamin yayi aure kiketa fitina tosaidai kiyi abunda zakiyi matadai matar sace matsayinku daya awajesa uwargida kinga mutuncinki yaragu
Idan kikacigaba da fitina karshenta yasakeki yazauna da amaryarsa wagari yawaya???? Hakan yana faruwa sosai acikin al.umma 
Iyayena mata iyayen gobe mukula mukiyaye kishii ba haukabane!!!
Nafara biyar lungu dasako cen saman hawa na uku nayi katari da matar gidan “” sosai nafirgita daganinta sam bazaka taba cewa matar gidan bace”” irin matan nan ne wadan da mazajensu suke dakudi amman idan kagansu bazaka siyesu kwandalaba duk kayanda suke siyamasu basa sakawa idan kagansu mai aikinsuma tafisu daraja amman fa idan zasuje gidan bukii kokuwa zasuje unguwa zakadauka basason taka kasa saboda tsabar tsafta”” 
Abokananta dasuke gefenta dayar tace wai lubabatu mezaihana kitashi kiyi wanka gidan nanfa yanbiki sunfara cikashi kosokike araina class nakii

           Wacce take gefenta nadama tace hajiya larai kibarta hakan mana”” dame zataji dakishiyarda akai mata kokuma da kwachakwaimar kwalliya?? Kinsan Allah danice kotaron biki bazanyiba
Wata tace habadai hajiya larai aiyanzu andaina wannan yayin idan za akawomaka kishiya kahana kanka jindadin rayuwa yanxu kissa akeyi kikwantarda kai tamkar mumina ni wlh mijina yayi aure saina gasawa amaryar gyada ahannunta
Suka kwashe da dariya haryanzu uwargidan uwar iko batayi maganaba””” 

       Larai tace hajiya sadiya kenan ashe wacce tsautsayi yasaka tashigo gonarki zatafi gwammacewa kwana akabarintaa” suka sake shekewa da dariya”” amman banda itah””
Haba kukuwa banda abinku ai kishiya abokiyar zamace menene abunkishin??? Abunda akasaba bakifa badainawa za ayiba nisam banajin kodar akan auren nan 

Hajia lubabatu ce mai wannan maganar””
Hajia larai tarike haba lallai hajiya kodayake wannan bashine nafarkoba bakyada jinkomai nikam wlh bazan sakewa mijina fuskaba dahar zaiyi sha awar karawani auren”” tirkashi ranarkuwa dahakan tafaru wlh sai yayi zaton aturu aka kwantoni dan zankoma masa mahaukaciyar karfi dayajii 
Wannan karon harda hajiya lubabatu wajen dariya wata matashiyar budurwace tabude kofarda sallama””” sukabita dakallo babu wanda ya amsa tafara kallon mutanen dasuke cikin dakin daga bisani tadauke kanta kamar taga kashi

       Hajiya lubabatu ce ta daka mata tsawa ke wacce irin shashashar yarinyace labila???? Zakishigo wamutane daki haka bakiganin bakine dani??? Baki tatabe nagansu mana mom kuma ainayi sallama “” takai karshen maganar tanasake wurgamasu mugun kallo ta murguda bakiii

           Kinyi sallama gidanwa mu kuramene dabamujiba”” ta kwabe fuska to tayazakuji bayan kuna tazuba shegen surutu wanda bazai kareku dakomai ba”” 

        Ido lubabatu tazaro sukam su hajia larai inda sabo yaci acesun saba dahalin labeela”” tace labila waiyaushe kikazama tsagera nifa mahaifiyarkice kinamun magana tarashin da a
Tasake mere baki”” tacee malamai niku gyara zanduba jakata “” tayi maganar tana rike kunkumi afusace hajia lubabatu tasauko daniyar dukanta su hajiya sadiya sukariiketa haba hajia baidace kidaketaba ai labila karamar yarinyace kuruciya ce take damunta
Kotakansu batabiba tahauduba jakarta”” tadauko sannan takallesu daibayan daya tace naji kuruciya tana damuna amman karani saudubu daku sakarkarun mataa mstw tsaki taja tafita tabar dakin 
        Gabadaya dakin yayi tsit bakajin motsin komai saina saukewar ajiyar zuciyarasu” labila karamar yarinya amman kullum tasamesu agidan saita soka masu miyagun maganganu
Dasauri tasauko kasan tana rike dajakarta”” sai kutsawa takeyi cikin taron mutane ranta yayi matukar kuna bataso mahaifiyarta tana hulda da wadan nan matan saboda dukansu babu Allah azuciyarsu amman mahaifiyarta batada wasu shakikan abokai bayansu 

          Wayarta tajawo takamo wata nomber tadanna kirah babu jimawa akadauka”” tayi sallama ya amsa dad dan Allah katuro driver yamiyar dani bazan iyah zama anandinba!!
Ajiyar zuciya yasaukar yace saboda menene labila bazakijirah akawo antyn takiba cikin sauri tagirgiza kai no dady”” dagabaya zandawo inganta yanzu akwai muhimmancin tafiyar tawa gobe munada harda a islamiyya”” amman inshaa Allah idan komai ya daidaita zandawo naga mom din kafin lokacin tazama yargida da murmushi afuskarta tafurta hakan shima murmushi yayi badamuwa labelaa yanzun bari nakirashi yazo amman nayi kewarki yata gashi zaki tafii amman bamudan zantaba”‘
Tashafo gefen fuskarta bakomai dady zansake zuwa saimuyi firanko?? Yace yauwa yata kikasance cikin amincin Allah
Tasaki sassanyan murmushi tace kaima haka”” inasonka babana yace nima inasonkii tace bye yace ok bye taciro wayar akunnenta takuramata ido Allah sarki babana”” Allah. Yasa kayi dacen mata Allah yasa daka wannan auren kasamu kwanciyar hankali wasu sirarun hawayene suka sauko mata tasa gefen mayafinta tashare sake matsawa tayi saboda cinkoson mutane ga shi ankusa la asar”” batawani jimaba driver yazo bayan sungaisa tashige motar suka kama hanyar kano

Aisha✍🏼

[12:15AM, 2/1/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Page 3-4

     By

Gentle lady💃🏽

Sai bayan fitar” labila sannan hajiya lubabatu tasamu tashiga wanka ganin duk jikin kawayen nata yayi sanyi da maganganun da labilar tafadamasu yarinya tamkar banice nahaifeta ba sam bataganin mutuncina

Tayi kwabaa
Batajima dashiga wankaba tafito tasheka kwalliya tamkar wacce zataje gasar sarauniyar kyau” ta chanchade cikin wani tsadadden bugaggen less dan ubansu akalla kudinsa zasukai dubu dari da hamsin””

              Tasaka sarkar diamond hannunta yasha awarwaraye na gwal”” nantake tasoma shekii tashi sukayi dukansu suka fara zaga gidan duk indasuka wurga sai anjinjinawa kwalliyarta nikuwa araina nace wato yangulma kikewa kwalliya illai kuwa kwalliya tabiya kudin sabulu dankuwa tayankesu kowacce takoma gidansu tana Allahummar zukuni””
Wani abun saigidan manya bakuga yanda akasoma fitowa dakayan ciye ciyeba bikin gidan masu kudi ko ba agayyacekaba kaje kodakuwa ba asakarmaka fuskaba kakwaso gara”” 

           Dankuwa yanda akacika gidan kaima dagani kasan wadansu abincin kawaine yakaisu “” babujimawa akafara fitoda dakwalen kajiii dakuma babba kakkun raguna masu maiko”” anyimasu gashi Na musamman sunsha shafen barkono saizubarda mai sukeyi saikuma lemuna namanyan mutane wanidinma bantaba ganin irinshiba
Kowa kaganshi rabonsa yake yaga”” masu DJ ne sukafara sakin kidaa bayan suncika tunbinsu””” hajiya lubabatu ce tafara takarawa cikin murna kaikace ba itah za ayiwa kishiyaba babuwanda bata burgeba wasuma sunata rokon Allah yabasu uwargida maihalinta Sam batadauki kishi abakin komaiba 
Kai ranarfa tasha rawa nikam nace jikinki zaiyi ciwo kuwa””duk wannan bidirinda akeyi banga ma mallakin gidanba””  
Yinin ranarfa sunchashe son ransu DJ yakwashi kudii wadanda akaita masu likidasu kasan biki na kusoshin yan duniya wadanda sukarika 
Shigar hajiya lubabu goma kowacce shigarkuma saiwanda yaganie komai kuma kalar kayan” anzuba hotona”” magrib tana kawojiki kowa yafara haramar barin gidan”” daki suka sake kowama”” suna nan kowadai saifadin albarkacin bakinsa yakeyi
Karfe takwas mukafarajin dirar motocin amaryaa”” sunata rangada gudaa”” akashigo da itah”” zuwa bangaren uwargida sukashiga da sallama ta amsa dasakin fuska marabanku lale marhabin kuzazzauna mana””

       Daga kawayenta harmasu kawo Amarya bakisake suke kallonta sambatada bakinciki taja hannun amaryar tace zo Kanwata kizauna nan”” cikin jinkunya”” tazauna kanta yanakasa ayanda akebata labarin matarsa babu ruwanta ashema tafiyanda akabata labari””

       Take tamike tafara jidomasu kayan makulashe dakuma kayan sha”” da gasassun naman kajie”” bayan sungaisa sukace ga amanar kanwarkinan munkawo maki 

      Duk dakowa yana shaidunki bakida wata illah Dan Allah kiyi hakuri dahalin kuruciyarta dan kingirmeta nesa bakusaba idan tayi badaidaiba kiyimata fada””

     Tayi murmushi aibakomai abokin zama dadine dashi tadafa kafadarta”” Kanwata nandin kidauka gidane komai yashigemaki duhu karkiji shakkar komai kisanardani nikuma zanwayarmaki dakai
Allah yasa nandin gidan zamankine Allah kuma yasa ace karada akayi Allah yabamu zaman lafiya”” gabadaya aka amsa da amin”” 

     Mikewa sukayi tace yabazaku taba koda ruwabane ai anzama daya nibazanji dadi idankuka kicin komaiba nima idan nazowajenku tareda Kanwata aibazakuji dadiba idan nakishan koda ruwane
Sukace tayi hakuri akoshe suke ganin tamatsa yasaka sukadan kurba lemun”” tareda itah akafita zuwa bangaren Amarya “”” harkuryar dakin tazaunarda itah yanganin daki Duk suncika dakin”” sunfara tabe tabe”” hajiya lubu tasoma miyarmata”” dakayanda akasoma turewa tadade taredasu sannan tayimasu sallama takoma wajen kawayenta indasuma sunsoma haramar komawa gidan mazajensu”””
Tahadamasu shatara Na arziki tarakasu kowacce takama hanyar gidanta”” bangarenta takoma”” hawa na uku shine Nata nabiyu na Amarya maigidan shine hawana karshe”” 
Idanzakije bangarensa Mahayar Na ura zakishiga kidanna zuwa sama bàsàikin wahalda kanki wajen taka matakalaba
Tanashiga bangarenta tarage kayan jikinta tahaye saman makeken gadonta tasoma sharar barciii hardà minsharii hankalinta kwancee saijuyi takeyi sànyin Ac yanashigarta tako ina”””

Gabadaya gidan anwatse kowayatafi yana yabon lubabatu da kyawawan halayenta”” karfe shadaya motarsa tashigo gidan”” bayan driver yayi fkng yayi saurin fitowa yabudemàsaa kofaa
Yafito”” yacewa driver n ina” habu driver dubamun kagani nayita kiran”” wayarsa batashiga labila kuma bata dauki wayarba
Yadan gurfana dasaurii yayi hanyar dakinsu yanakwala masa kirah haryasoma barcii yaji anakiransa firgigit yamike yafito dasaurii taresuka koma wajen alhajin””

Aisha✍🏼

[6:10PM, 2/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA*☠

Chapter 5

       By

Gentle Lady💃🏽

Dukawa yayi yace yallabai andawo lafiya??

Qalau habu tundazu nake neman layinka Amman inajinsa akashe”” 

    Ah yallabai wayarne batada chaji wlh” haba habu yanzu duk wadatacciyar wutar nan da ake sakowa kuma ga gen Amman asamu wayarka babu chaji??? Duk kacinye chajin wajen shiriritaccen cheating dakukeyi kaidai koyaushe maganata dakai akan rashin wayane

    Yasosa kansa yallabai ayi hakuri kuskurene baza asakeba”” murmushi yayi yace hakan kake fada dai kullum”” ya labilar kun isah gidan lafiya ko????
Kai yagyada ah yallabai kafin magrib nihar najuyo tabada sakoma akawo maka”” yana murmushi yace to daukomun”” 

Dasauri yakoma cikin dakin yadauko key yabude motarda yaje da itah wata katuwar kulace dakuma leda”” yakarba “”

            Sukai masa saida safe yawuce cikin gidan kaitsaye hawa nahudu yadosa nikuwa ina biye dashi huhuhu ashe banga komaiba saboda wannan yafi sauran kyau nesa bakusaba 
Komai gashinan gwanin sha awa” tundaga flowers da kujerun dakin da center Capet” green color ne mai haske” sai makeken TV n bango” saikuma babban agogon bango”” 

Sai fream da ke dauke da ayatul kursiyyu dayan amanarrasulu gudan lakadja akum”” sai wadansu masu addu.o 
Sosai tsarin yaburgeni”” kularda take hannunsa ya aje yakarasa kuryar dakin”” kayan jikinsa yarage yashiga yawatsa ruwa yafito jallabiya yazura yafeshe jikinsa da turare yafito kular yabuda danbun kaxane”” sai babbar ledar gasassun kajine gashin gida harda diminsu kansa yadafe shisam yama manta bairikowa Amarya kazaba shikullum cikin mantawa yake”” yayi murmushi labilaa kenan”” mikewa yayi yabude fridge yadauko madarar yoghurt yasauko zuwa bangaren hajia lubabatu da sallama yashiga tayi daidai sai kwasar barcinta takeyi”” ledar hannunsa ya aje yakarasa saman gadon yakura mata ido murmushi yayi yashafo fuskarta shikawai yasan abunda yace azuciyarsa ahankali yasoma tashinta ta ture hannunsa cikin alamun mai barcii kuma yanamata dadi yace maman laby kitashi kokinyi sallah??? Cikin barci tace ah nayifa alhaji harkadawo???
Yace gashi kinyi barci bazaki rakani gun kanwar takiba murmushi tayi wlh nagaji alhaji baxan iyah zuwa ko inaba saida safe tasake juya kwanciya

Murmushi yasakeyi
Yaja bargo yarufemata jikinta yafito zuwa bangaren Amarya Yanashiga daddadan kamshi yadaki hancinsa yalumshe ido sannan yabude ahankali yafurta Alhamdulillahi ala ni imati”

Yataka harcikin dakinta tana zaune tsakiyar gado yadine sanye ajikinta “” dashikuma akarufe mata kanta dashi””
Ahankali yataka yazauna saman gadon yayimata sallama ta amsa ahankali”” hannunsa yasaka yadage mayafinda akaimata rufadashi

 

 Murmushi tasakarmasa takanne ido daya”” wani dadi yaji yamamayeshi yana tunanin zaihuta sosai ajikin habiba dantunkafin ya aureta yagano macece mai yawan sha awa shine dalilinda yasaka hartarabu damijinta Wanda tafara aura””
Mayafin yasaukar yace Amarya bakya laifi”” koda kinkashe Dan masu gida” tayimasa fari”” da ido”” yasaki fara a tashi muyi sallah mugodewa Allah”” mikewa” tayi daga kan gadon tashiga tayi alwala tafito tasamu yashimpida abar sallah yanagaba yajasu sallah bayan sun idar yagabatar masu da kajin da labiba ta aikomasa dasu kitchen dinta yaje yadauko plate yajuye masu naman yakalleta yace bisimillah cikin jinkunya tace nakoshi 
Yace wasa kikeyi nasan bakici komaiba hidimar buki nima kaina yunwa nakeji kodai nabaki abakine?? Yayi maganar yana jawota tanarke ajikinsa tashagwabe murya nakoshi my love 
Yace nifa banyardaba kokadanne saikinci ahakan yadibo yanufo bakinta cikin kissa take karba harsaida yatabbatar takoshi shima yaci yasha madarar””

 sannan sukafara wasanni
Ganin kasan bazaimasuba sukakoma saman gado yatashi zaikashe masu wutar dakin koda yadawo yasameta sai munsharii takeyi abunyabashi mamaki matuka dagazuwa kashe wuta wane irin barcine zaidaukeka kuma ayanda takeyin barcin kamar tadade dafarashi”” baikawo komai aransaba duk da amatseyake yauyaso more Daren amarcinsa da Habiba jiki asanyaye yaja bargo yarufemata jikinta yamiyarda kayansa”” yakwanta gefenta ido yakuràmatà 
Kamar maison tunawani Abu”” munshariii takeyi tamkar gurnanin zakii yayita juyi Sam barci yaki daukansa”” haryasoma jantsaki karshedai mikewa yayi yakullemata kofar dakin yakoma bangarensa

Aisha✍🏼

[7:22PM, 2/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 6

     By

Gentle Lady💃🏽

Dashigarsa dakinsa bai tsaya ko inaba sai akan makeken gadonsa “” yazube tamkar gajiyayyen mutum wanda yayi tafiyar yini guda cur batareda ya hadiye kwayar hatsi acikin saba” gabadaya damuwa ta mamaye zuciyarsa
Take yafara sake sake acikin ransa” wai me wannan takenufine??? Kowacce matar dazan aurah salonta daban yake itakuma wannan natasalon yaudarar abarci zata fake?? Yayi kwaba bakomai komai daren dadewa aizankaigaci inhar tasan wata aibatasan wataba lallai inkere nayawo zabo nayawo babu shakka saisun hade
Inma makircine irin nasu namata zanganota idan yanzu tayi makircin barci saina gani idan darana zatayi hakan”” yayi tsaki maganar banzama yau Allah kadai yasan bururrukan dasuke cikin raina awannan Daren Amman komai yarushe nakoma tamkar wandama baitaba aureba “” ina amfanin dukiyata??? Kansa yadafe Wanda yaji yanayimasa barazana tamkar zairabe gida biyu saigashi yana kuka da idanuwansa hawaye wadansu sunabin wadansu””
Waini saiyaushe zansamu kwanciyar hankali??? Wacce irin rayuwace nakeyi?? Duk irin tarin dukiyarda nakeda itah nakasa samun abunda nakeso saboda duka matan bakin halinsu dayane kowacce zan aura sainaga salon cin amanarta yafigaban kwatance
      Yashafe dakiku arba in yanata kuka shikadai batareda mai rarrashinshiba daga bisani mararsa tasoma ciwo wanda wannan ciwon kusan yazame masa tamkar ibada yadade agun yana mirgina tareda addua sannu ahankali ciwon yasoma sauka tamkar yanda ruwa suke sauko wadaga sararin samaniya “” yana nan agun bai motsaba saida sanyin alfijir yasoma bugomasa yatashi””alokacin yaji jikinsa yakoma daidai tamkar wani Abu baisameshiba
Kaitsaye bandakinsa yashiga yawatsa ruwa sannan yadauro alwala yashinfida abar sallah yafara sallah”” 

Saida akayi kiran asalatu sannan yasauko da charbinsa ahannu yanufi bangaren lubabatu hawana uku kamar yanda yabarta da dadaren hakan yasameta saidai wannan karon zaninda yakejekinta tuni yakoma gefe tamkarma tunfarko batareda shidin takwantaba”””
Bayan under dayake saye ajikinta da tinbir zatakasance gashi tatara taiba sai kirjinta dasuke manya manya kowanne daya yayi girman kofin roba
Gefe da gefe nacikinta amurde yake alamar jindadi dakuma Hutu sunkwanta akan lafiyayyar fatar jikinta tamkar irin dika dikan matan yarbawa hakan take
Yaduka ahankali yadauki zanen yarufamata ajikinta daga bisani yasoma tashinsa ahankali”” yadade yana tashinsa sannan tabude idonta”” yace tashi kiyi sallah”” murmushi tayi tasake juya kwanciya tace hutunake “” batareda yace komaiba yawuce zuwa bangaren habiba cikin yanmintuna kalilan Na urar tasadashi da bangarenta dakin yashiga tanakwance takama filo tarungume kamar wacce tasamu jariri”” haryanzu lullube take ciikin zanen gadon”” yataka kusa da itah yasoma bubbugarta ahankali yanakiraan sunanta”” tasoma juyi cikin barcinta maidadi tasoma bude idonta ahankali tadorasu akan mijinta tasakarmasa murmushi maikamada tusar jaki”” tabude bakinta daniyar magana tuni yakawarka fuskarsa sakamakon wani mugun doyi dayafito acikin bakinta tamkar gawar mushe ya tunkari kofofin hancinsa” cikin sauri yajuya yayi taku biyu tareda toshe hanchin nasa sakamakon yankayan cikinsa dayaji suna hautsinawa cikin sauri yace sauri nake kitashi kiyi sallah”” baijirah Jin amsarda zatabashiba yayi waje haryacin tuntube
Sam habiba batakawo komai arantaba saitadauki hakan amatsayin yanasaurine karyarasa jam i saboda falalarda kecikin sallar asubah acikin jam”i

 
Shiru tayi nawani lokacin tana tunanin daren jiya”” Sam tamanta abunda yafaru tayi iya kokarinta kozata iya tuna abunda yafaru bayan hawansu akan gado damijinta Amman takasa tunawa datamatsà datunani saitaji kanta yasoma ciwo take tayi saurin fatattakar tunanin daga zuciyarta tamike tadaura zani takarasa bayin domintayi wanka
Shikuwa dafitarsa yasoma saurii haryana waigen dakinta haryanzu dayan hannunsa yanakan hancinsa yadadeshi kyam yace aransa waiii wannan wane irin warine naji tamkar rubabben mushe”” wannan warin daidai yake da aturmuya kanka acikin shadda wacce taikwana shida arufe itakuwa wannan dawanne kalar mangoge hakorah take amfani dashi kodai rashin wanke bakine??? Idankuwà hakane akwai matsala dankuwa bazan iyah kusan tartaba muddin inajin wannan doyin
Dawannan tunanin yasauka kasa yasoma tashin ma aikatan gidan domin wucewa masallaci dama al adarsa kenan bayazuwa masallaci sallar asuba batareda yatada dukan ma aikatan gidanbà wannan dabiar tashi tanamatukàr burge yaran gidan asanadin hakan drivernsa Sunday yakarbi addinin musulunci Wanda yanzu akekiransa da Abdullahi
Sosai halin maigidàn nasu yana burgesu basu kadaiba hatta makotansa Dan mutunne Wanda yasan hakkin makotàka sautari idansukàje masallaci inyaga ankusà tàda sallah wani makocinsa baishigoba dakansà yake zuwa ya bugamasa duk da shidinfa maikudine Amman Sam dukiiyarsà batasakashi yazama maigirman kaiba

Aisha✍🏼

[11:02PM, 2/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 7

    By

Gentle Lady💃🏽

Sautari talakawan anguwar suna matukar mamakinsa saidai shi Sam baidauki wai girmankai yadorawa kansaba girmankai Wanda mafiyawan masu kudi suka sakawa ransu” dazaran sunyi kudi zasufara daukar kai Sam sumanta da lokacinda suke fakiransu gabadaya abokanansu nabaya saidai idansuka wulgo cikin mota sudagamasu hannu wanikoma dagahannu bazaiyiba yama manta dayataba zama wata majalisa”” dazaran yaga Wanda yasani talaka saiya saki gilashin motarsa yakauda kai gefe tamkarma baiga mutumen ba
Wannan girman Kaine kuma duk Wanda yakedashi yasani yakama hanyar halakarsane saboda abunda kesauran halakarda bawa girman Kaine dagahakan zakafara hassada kanadaukar kanka wata tsiya bakaso wani yayi kudii kamarka kasani ko shaidan abunda yasakashi hassada girman Kaine haryakaishi ga fadawa halaka

. Allah yaciremana girman kai dakuma hassada acikin rayuwar mu Ameen”” saida yajirasu dukansu sukayi alwala sannan yawuce suma suka Mara masa baya “” zuwa masallacin unguwar
Babu nisa Dan gabangidansa kadan akagina masallacin Ku San babu kwadagar kowa wajen ginin shine yadauki nauyin komai masallacinda aka kawatashi ko acikin manyan unguwanni saikayi dakyar kafin kasamu mai kyansa”” Dan asalin wajen wata tsohuwar ginace akazagaye korufin kwano babu akarosheta akagina wannan masallacin Wanda fankoki da ac kamar suyi magana idan kashiga kamar karka fito sannan gatarin littafai nan idan kanason karantawa”” bayan an idarda sallah”” yakoma gefe yasoma karatu inda sauran ma aikatan wajen sukasoma karatun zuwa adanjima sukafita zuwa wajen aikinsu””
Dai daikun jama ar wajen suka soma fita ahankali haske yanagama wartsakewa shima yatashi yakarasa wajen liman sukai musabaha sannan yafita zuwa gidansa tun a hanya suketa gaisawa da makotansa haryakai gidan dashigarsa yasamu ma aikatan gidan sungama aiki shikawai suke jirah bayan sungaisa yawuce cikin gida sukuma sukawuce
Dayake yauranar lahadine babu aiki duk da yakeshidin dankasuwane yanada campani masu yawan gaske Amman yanayin tsarinsa tamkar aikin gomnaty dashi da ma aikatansa 

 Basazuwa aiki asabar da lahadi acewarsa takasance ranar Hutu gakowa saboda idan sukaje takwas nasafe basa tashi sai karfe takwas darabi 
Ranar lahadi da asabar taxama ranar Hutu kowanne magidanci yafuskanci iyalansa yaji damuwarsu”” idankuma marar aurene yaje wajen budurwarsa idankuma yanada wata lalurah yayi koyayi ziyara”” musamman jumua dan ranar juma.a karfe hudu aketashi
Shikuma ranar asabar inhar yashiga gidansa bayafitowa bayan zuwa masallaci yanatare da matansa yakasance lokacinsune komai sukeso kosunada damuwa saisufadamasa duk da kafinsu kwanta kowanne darema suna ganinsa
Kaitsaye bangarensa yanufa yasakeyin wanka yakwanta kasancewar barcin jiya Yana nan a idonsa take barci yayi awon gaba dashi

           

Hajiya lubabatu ce tashigo dakin cikin takun kasaita balaifi yautayi kwalliya dass da itah fuskarta saifitarda sihirtaccen murmushi takeyi ahankali tataka zuwa saman gadon taxauna hannu tasaka tanashafo lallausar sumar kansa Wanda takwanta luf gwanin sha awa hakika tana matukar son mijinta dakuma kishinsa fiye da tunanin mai karatu hakaxalika tana mutuwar kaunarsa da begensa fiye da tunanin duk wani mai tunani taja gauron numfashi” atake talulaya wata duniyar daban
Sai farkawa yayi yasamu hajia lubabatu tasakashi gaba hannunta yanakan gashin kansa idanuwanta suna kallon saitin drawer yayi kuru yana kallonta daga bisani yasaka hannu yashafo fuskarta tadan zabura sannan tasaki murmushi hannu tasaka tajawo hannunsa daga kan fuskarta tace harkatashi ??? 
Murmushi yasakeyi akaro nabiyu yace ah tunanin mekikeyi??? Taware ido waini batunani nakeba 

Yace bayan Wanda nagani”” tayi murmushi ah ah alhaji wai shin inakabar Kanwata??? Tayi saurin kawarda zancen dawannan tambayar”” yace tanadaki tanabarci mana””
Cikin zolaya tace barcin gajiyako nasan halinka basauki jiya bakabarta tahutaba duk da take yarinya batasaba sosaiba

Yayi murmushi yace kinfara ko lubabatu yayi kyau inhar nakama ki akoma zakiyi bayani
Aransa kuma yace hmm inakikasani saida ta talemun kaza tacinye sannan tasoma barci kamar kasa yayi maganar yana mikewa daga kan gadon yashiga toilet domin watsaruwa

Aisha✍🏼

[12:44AM, 2/6/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*

Chapter 8

     By

Gentle Lady💃🏽

Tabishi da kallo dawani boyayyen murmushi Wanda itah kadaice tasan ma anarsa”” tana nan akan gadon haryafito yana daure da towel 
Yadauki comb yana taje sumar kansa”” saida tayi luf sannan yadauko turarukka yasoma fesawa ajikinsa”” yafesa akalla turare kala biyar sukahadu sukabada wani kalar kamshi na daban kaisaikace ma aiikatar turarece tayi ambaliya
Wata bugaggar shadda ja wacce taji aikin hannu da zare jinin kare maiduhu dinkin tazarcene daidai wandonsa bataja kasaba kamaryanda wandonsa baiwuce idon kafarsaba” 
Yadauko hukarsa kube maikalar kayansa hatta Zanen hular tamkar tarema aka kerasu”” yadaidaita tsayin hularsa sannan yajuyo wajen hajia lubabatu yasakar mata murmushi yace mujeko dannafarajin yunwa yayi maganar yanashafo cikinsa
Batareda tayi maganaba tamike sukajerah zuwa kasa kowannensu fara a kwance akan fuskarsa”” aka idar sa falon kasa yakeyin break saboda masu aikine sukeyin komai shiikuma bayason masu aiki suhau saman sa inhar ba matarsaba babu Wanda yataba shiga saman””
Kaitsaye saman dinner suka nufa yaja kujerah yazauna tadubeshi tace bari nakirah Kanwata ko batareda yakalletaba yace ok” 
Kaitsaye tasake hawa mahayar zuwa bangaren Habiba”” bakin kofar dakin tatsaya tana kwankwasawa cikin dakin akace waye shigo” taturah kofa habiba tana ganinta tasaki faraa danta shaidata tace Anty kece inakwana
Tamayar mata da martanin murmushinta tace lafiya qalau Amarya yakwanan amarci ya kuma bakunta?? Murmushi tayi kawai tadone kanta kasa””  
Hajia lubabatu tace hmm kunyata kikeji Amarya nifa antynkice kinga taso muje mukarya nasankema kinajin yunwa”” 
Batareda tace komaiba tamike hajia lubabatu tanagaba tanabayanta itakuwa saikada mazaunai takeyi kamkar randar ruwansha
Harsukakai kan dinner din itah ta gabatar masu da abincin sukaci sukai hamdala sannan suka koma cikin falon suka zauna sukasoma firah
Dama ankusa azahar bayan yayo sallah yasake dawowa falon alokacin duk basanan”” baijima daxamaba hajia lubabatu tafito tanaganinsa tawashe baki harkadawo yace ah wlh kusadashi tazauna
Yace inakuma habiba??? Tasake murmusawa tace banda abunka alhaji kasan kunya takeji bata sababa nidai nayafe hirar kakoma bangarenta zakufi sakewa kudarji amarcinku
Murmushin yake yayi yace hakane kuma kinkawo shawara mai kyau yamike yana gyara tsayuwar rigarsa yayi hanyar mahaya itakuma takoma bangarenta
Kofar dakinta yatsaya yana sake sake aransa karshedai kawai yayi kundun bala yaturah kofar tareda sallama tana zaune cikin katon falon tana kallo tadago cikin fara.a ta amsa masa” dannesa da itah yaxauna yana Dari Dari yace kallo kike???
Tace ah kanta yanakasa yace dakyau”” dagahakan baicekomaiba”” saidai yanata satar kallonta takasan ido haryana hadiyar yawu kafin cikar mintuna ashirin yaji baxai iyah dakatarda kansaba cikin kasalarlar murya yakirah sunanta ahankali ta amsa yayimata nuni akan tazo babu musu kuwa tataso
Al amaridai anan yasauya yafara aikamata da sakonni dayake yanayi yana kauce hancinsa dankarya shakomasa abunda yafi karfin Tunaninsa tsayin mintuna goma yasunkuceta zuwa kuryar dakin
Abun mamaki yana ajeta akan gadon yajitafara wani minshari arazane ya kwalalo ido cikin kaduwa yace barcin kuma???? Waimeke faruwane kodai yarinyar nan aljanun barcine da itah?? Kuma dantsabar shakiyanci ace barcin bayazuwa sai idan nazoda bukatata”??? tsaki yaja yamike akan dagon yafita abunshi zuwa bangarensa 
Saida akayi la asar yafito da mamaki yasameta cikin falon kasa da itah da wata kawarta”” kallo daya yamasu yadauke Kansa yawuce fuuuu tamkar kububuwa dansosai amaryar nan tasa tasoma batamasa rai jiyajiya dakawota jifa dazun barcitake haikam Amman gashi kawarta tazo tawartsake tamkar batayi barciba

 Anjima nasan mezanyi

Dawannan yakawarda tunanin yakarasa masallaci””
Habiba kam tacika da mamaki duk da bata nunawa kawarta dakwai wani abuba Amman tanacikin damuwa tarasa meke faruwa aduk lokacinda zaitara da itah batakoma sanin meke wakana saidai tafarka taganta itah kadai idan kuma tamatsawa kanta da tuna abunda yafaru saitaji kanta yasoma ciwo 
Har da dare taresukai dinner sukadan taba firah tayi masu saida” safe tayi bangarenta” batajima datafiyaba hajia lubabatu tamike tayi hamma”” tace nizan kwanta” alhaji saida safe”

             Shima yamike yace kenan duk kunwatse kunbarni””anan kamar tsinkàkken silifas”” bakomai muje inrakaki” tayi murmushi tayigaba”” yana bayanta saida yarakatà har bangarenta” saida takwanta sannan yarufemata kofa Yakoma bangarensa yayiwanka
 Yayi shirin kwanciya wannan karon kiranta yayi awaya tasameshi bangarensa””cikin shigar kayan barci masu sharara dukkan halittar jikinta ta bayyana” take Yakama zumudi jikinsa yasoma karkarwà tamkar zakinda yakwana biyar yanajin yunwa aganinku mezaifaru idanyayi arba da abinci
Ahankali ta takazuwa wajensa”” babuwani bata lokaci sukafara faranta ranjunansu”” kafin wani lokaci sunkai saman gado kamar almara saigashi tasoma barci
Ganin hakan yasa yaji haushi aransa yace kobarcin mutuwane bazai hakurabà saiya Kore kishinsà yanata”” kokarin biyan bukatarsa tasoma gurnani tanabude bakinta wani”” mugun doyi yana fitowa babu shiri yasa hannu daniyar rufemata bakiii yajikamar yataba wasu hakorah zagan zagan”” take Kuma zuciyarsa tasoma tashi

” 

 

Aisha✍🏼

[11:45AM, 2/7/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 9

      By

Gentle Lady💃🏽

Bazato kawai saiyafara jin amai”” dasauri yasauko zuwa bayin dakin dagudunsa yasoma kela amai tamkar zai amayarda kayan cikinsa yayi matukar galabaita”” take yazube acikin toilet din yana hakii tamkar wanda yayi gudun tsere da kartii goma””
Tsayin mintuna talatin yana wajen sannu ahankali yasoma samun natsuwa mikewa yayi yasakarwa wajen ruwa yawanke bakinsa sannan yafito kallo daya yamata yadauke kansa wasu hawayene suka sauko akan fuskarsa harzai wuce saikuma yadawo tareda saka hannu ya dade hancinsa zuwa saman gadon” yaja abun rufa yarufe mata jikinta sannan yawuce dasauri 
       Dayake akwai yalwatattun dakuna abangarensa tamkar wani babban gidane ahawan wani bangaren yashiga”” jiki sanyaye yakarasa bayin yayi wanka yadauro alwala domin koda yakwanta bazai iyah barciba 

Washe garin ranar Sam fuskarsa batada wani walwala dankuwa alal hakika wannan lamarin yasoma kaishi bango yanaji yanagani zai halaka kansa”” ko lunch dasukayi sama sama yaci daga bisani yamasu sallama yawuce ko rakiyar bainemaba dama dai yau rakiyar habibace Dan haryanzu hannunta yake
Saida akayi kwanaki uku cur kamar yarda addini yasimfida budurwa sati daya bajawara kwana uku Amman harzuwa wannan lokacin baisamu kwantawa da itah ba”” gashi hargirki yadawo akan hajiya lubabatu”” 

                Dadare suna zaune akan kujerah sunashan kayan itatuwa habiba tana barin gefensa nadama hajiya lubabatu tana barin hagu kokadan ayanzu bayajin warinta koda tabude bakinta”” aransa kuwa yana ayyana damacen muguntane bataso yakusanceta akwai abunda take sakawa ajikinta duk lokacinda tasan zaizo mata””” ahankade yake kallonta
Bayan sungama Shane yayi gyaran murya yasoma yimasu nasiha akan zamantakewar aure daga bisani yace kamardai yanda kukasani yaudai kwanana uku dakin Amarya danhaka yau za araba kwana kwana biyu kukeso ayi ko daya daya???
Hajiya lubabatu ce tayi saurin tarar numfashinsa tace maigida nidai kasan banda wata matsala amatsayina na antynta nidai nayafe nawa kwanakin nabaku watadaya kumore amarcinku

 

Jiyayi tamkar yafasa ihu

Dasauri yabude baki daniyar yin magana ta dakatàr dashi tahanyar rufe masa baki dahannunta tana girgiza kai cikin murmushi tace karkadamu basaika godemun ba nimaisonkace 
Inason duk wani farincikin ka ninasan amarcin nan bai ishekaba”” bazan cutuba harcikin raina nabar maku zuwa watadayan saika rabamana kwana
Gabadaya jikin habiba yayi sanyi son hajia lubabatu yashiga ranta lalai kowa da irin halinsa bata taba ganin macenda batadau kishiya abakin komaiba kamarta Allah yabarmu tare hajia
Al amarin alhaji kuwa sandarewa yayi awajen saboda kaduwa dajin furucin lubabatu anyakuwa tasan masifarda nake fuskanta??? 
Yanisa aransa batasaniba nasan datasani dabazataso incutuba”” yanda takesona fiye darayuwarta “” kuma haramun ne kasanarda matarka sirrin abunda ketsakaninka da dayar matarka dasaina fadamata”” yaja dogon nunfashi yace shikenan mungode hajiya yanayin yanda yayi maganar kaida ganinta kasan ba cikin dadin rai yayiba”””
Basuwani jimaba hajiya lubabatu tayimasu saida safe tawuce bangarenta”” shima hakan yasaka yamike zuwa dakinsa hakama habiba”” sosai yau taraya aranta zatafaranta ran maigidanta domin samun abunda yakeso
Bayan tayi wanka tashirya cikin shigar kayan barci farare masu sharara tafeshe jikinta da kalolin turarukka”” kaitsaye bangarensa tanufa
Tasameshi yayi shirin kwanciya yana ganinta gabansa yafadiii yaukuma meyakawota alhalin bankirataba ????
Batareda tanemi iso daga gareshiba tayi saurin fadawa jikinsa””” ’’kafin yayi kokarin tureta daga jikinsa hartafara aikamasa dasakonni tako ina””” 
Takesuka zube akan gadon tunbaya maida martani haryasoma maida mata da martani””” abukamar zaitafi ahakan sannu ahankali yasoma jin doyin tunyana daurewa tareda toshe hancinsa saiyaji abun kamarma karoshi akeyi kusamma doyin yafi nakoyaushe
Bashiri yahankadata gefe yamatsa baya dasaurii””” itakuwa alokacin hartayi barci abunta saitasake gyara kwanciya
Gefenda take yakuramata ido tamkar maison tunowani abun dagakarshe wanka yashiga koda yadawo baisametà dakinba tafita
Tsaki yayi damashi yasan komai takeyi dagangan takeyi kawai danyanason hakkinsa tana nema takasheshi indai Dan wannan ne bazansake nemantaba
Darenkuwa daciwon ciki yakwana”” tundaga ranar kullum idan sukatashi don su kwanta”” saikawai yarufe dakinsa kuma koda tabugàmà bazai budeba Amman Sam bayanuna komai idansuna tareda lubabatu ahakan har akacinye watadayan da hajiya tabasu

Aisha✍🏼

[3:02PM, 2/7/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*

Chapter 10

      By

Gentle Lady💃🏽

Alokacinne akaraba girki” yakoma hannun lubabatu”” 

Habiba Sam takasa gane wanne irin aurene tayi gatadai batadawata makusa wacce zatasa namiji yaji baya sonta” batada matsala tabangaren kishiya saidai tabangaren miji”” sosai yakesonta kafin auren ammankuma gashi tunda tashigo gidan komai yadargwaje tarasa gane kuma dalilin yinhakan gashi tanada tsananin bukata zuwa yanzu tarame tafige tafita hayyacinta””” 
Kwance take cikin falonta kasancewar yauma ranar hutuce yanagida Amman takasa fita domin ganinsa kawai zaisake tasomasa da bukatarta wacce tasan bazata samu maganintaba “” lallai tayarda akwai abunda yajefaruwa da itah cikinta taji yasoma juyawa tafara murkususu”” 
Tun tana kankujerah hartafado kasaa wata irin kara ta kwallah daidai shigowar hajiya lubabatu tazo kiranta suci abinci dasauri takarasa arude tadagota tana tambayar lafiya kafin tarufe bakinta jinine yasoma zubowa dakarfiii ta gabantaa”” 
Cikin tashin hankali lubabatu tace habiba dama bakida lafiyane???ina habiba tamatukar galabaita bata iyah kodaga kanta dasauri hajiya lubabatu ta kwantarda itah tafito dasauriii zuwa kasan 
A firgice tana kuka yana ganinta yamike yana tambayarta lafiya hajia??? Cikin kaduwa yaji meyafaru tace munshiga uku habibace ba lafiya 
Kafin tarufe bakinta tuni yahaurah saman baimabi takan na urarba tasaman benen yataka tuni hajiya lubabatu tabi bayansa koda suka karasa hartasuma ga jininan yanata malala”” gakuma wata karamar halitta wacce batawuce girma Dan kadan gareba”” take jikinsa yahau rawa duk da abunda yagani Amman hakan baisa yadamuba ya ciccibeta duk dajinin dasauri yasauko kasa hajiya lubabatu tana bayansu sai kuka takeyi
Tunkafin yafita yasoma kwalawa driver Kira”” dasauri yafito jinkiran jikinsa yanarawa Dan dagajin kiran yasan ba lafiyaba”” ganinshi damaidakinsa ahannu yasaka yabude masu Mota dama ashirye take”” akasakata taresuka dunguma har hajiya lubabatu zuwa hospital”” emergency akawuce da itah kaitsaye bakin kofa aka dakatar dasu aka hanasu shiga””” 
Dagashi har hajiya kaikawo sukeyi awajen kowanne kagani kasan yanacikin tashin hankali tsayin awanni biyu likitan yafito dasaurii alhji yatareshi “” saidai yadagamasa hannu yawuce haryana hadawa dagudu”” 
Zuwacen yadawo yashiga dakin”” ansake shude wasu awannin saigashi yafito 

Alhaji yatareshi tareda hajiya lubabatu harsuna hadabaki wajen tambayar yamaijikin???
Zufan kansa yashare yace kukwantarda hankalinku insha Allah zatasamu lafiya”” yanzudai muna bukatar jini cikin gaggawa”” kafinma yarufe bakinsa yace muje a auna idan nawa zaiyi”” hakan kuwa akayi saidai jininshi baiyiba
Adole akakirah yan uwanta mahaifiyarta “” dakuma yayyunta””” su ukune kowanne akadibi gorah biyu ajikinsa”” take akajonamata anasaka jini jinin yanafita”””
Harzuwa dare babuwani haske hakazalika sunkasa tsayarda zubar jinin”” yanda yakezuba zuba banawasaba hakan yasaka sukanemi Karin wani jinin”” duk dayana fita idan ansakamata”” 
Yan uwanta basuda wadataccen jinin gashi har andibi gorah biyu dagahakan baza sake dibaba”” gashi duka jininta ya tsiyaye”” hajiya lubabatu sai kuka take tace aduba konata zaiyi itakam bataso tarasa kanwarta
Likitan yatausaya mata sosai yace saidai hakuri hajiya ba adiban jinin mace”” cikin karaji ta chakumo wuyansa tace inaruwanka jininka konawa
Tasakeshi cikin kuka tahada hannuwanta gida biyu Dan Allah doctor kataimaka mana wlh koda zanrasa raina tasanadin dibar jinin nawa”” wlh nayarda Amman banaso kanwata tamutu
Jiki asanyaye yagyada kai ganin kowanawajen yazubamasa ido”” take aka auna jininta baidakomai”” akasoma diba anasakawa Habiba”””likitàn yafita mahaifinta dawani kaninsa sukabishi abaya”” zuwa office dinshi”” mahaifintane yasoma tambayarsà meyakedamuñ yarsa???

Yayishiru dagabisani yace barine tayi” cikin kaduwa mahaifinta yace barin lafiya watadaya da aurentafa??? Yajinjinà kai tareda turomasa takarda gabansa yace sakamàko yanuna tanashañ kwayoyin zubarda cikine babisa ka idaba shine yajawomàtà wannan matsalar
Kafin yarufe bakinsà alhaji yashigo dasauri yace doctor kataso jinin ya facce kusan taresukà mike dasauri zuwa dakin harsunà hadawa dagudu
Sannu ahankali tabude idonta takurawa gadonda hajiya lubabatu take kwance ido sirarun hawaye suka saukomata
Take tasoma Kalmar shahada”” idanuwanta sukai sama take Na urah tasoma kara”” daidai shigowar su doctor yakarasa wajentà yayi yan aune aunendà zaiyi yagirgizà kai
Yacire abun Karin jinin tareda Na hajiya lubabatu yarufe mata idonta yaja kallen yarufeta”” gabadaya dakin shisuke kallo Dan haryanzu basu fuskanci meyafaruba
Yajuyo dakallonsa wajen alhaji yace saidaifa kuyi hakuri Allah yakarbi abarshi””
Daga haka yajuya yafita hajiya lubabatu tasoma kururuwa tana wayyo itah tabani mahaifiyar habiba saman gadon lubabatu takoma tanabata hakuri suka rungume juna sunata kuka””” akarasa Wanda zai rarrashi waniii
Tsayin mintuna talatin mahaifin habiba dasauran yan uwa da sukazo dakyar akasamu su hajiya lubabatu sukai shiru
 Kanin Mahaifiyarta yakalli alhaji yace waimenene musabbabin ciwon nata””??? Kodama tadade batada lafiya??? 
Ciikin sanyin murya yace shima baisaniba yadaifàdamasu iyah abunda yasani ahakan”” mahaifinta yace sai asamo mota suwuce gida babu wani bata lokaci akadauki gawar zuwa gidan iyayenta””

Aisha✍🏼

[10:59PM, 2/7/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 11

      By

Gentle Lady💃🏽

Gabadaya gidan iyayen nata akanufa harda Alhji”” saidai dare yayi Dan lokacin andade dayin sallar isha I”” hakan yasa akaimata wanka aka suturtata” zatayi kwanan keso washe gari sai akaita gidanta na gaskiya

         Cikin Daren su labila sukasamu labari anasanarda itah tarabka salatiii kukane yakwace mata taruga cikin daki waisaiyaushe mom zatadaina kashewa dad matane??? 
Meyasa haryanzu nakasa sanardakowa abunda take aikatawa??? Ninasan koda nafadadin babu Wanda zaiyarda dani ganin irin yanda take nunarashin kishi akan matanda yake aurah
Ya Allah ka gaggauta tona mata asiri”” wasu hawayene suka sauko akan fuskarta tashare””” tundaga bangaren lubabatu har alhaji babu Wanda ya runtsa acikin Daren sai rarrashinta yakeyi washe gari labila abdulmajed da hajiya da kannen alhaji hafis da kubra suka kamo hanyar kaduna
Koda sukashigo kaduna bakwai darabi”” alokacin har anyimata sallah antafi Kaita makwancinta”” su hajiya gidan su habiba aka kaisu sukayiwa iyayenta gaisuwa””

 Harda hajiya lubabatu sukaje idanuwanta sunyi suntul saboda kuka kowayaganta saiya tausaya mata”” iyayenta Kansu basuyi kuka kamar yanda tayiba”” labila Kuwa dage take kallonta dankuwa tasan aikintane”” 

                Ahakan akayi zaman makoki akawatse “” Dan babanta yace bayason wani zama saidai kowa yabita da addua”” aranar kowa yawatse anayiwa habiba Neman gafarar Allah

        Kowa yazo gaisuwar dole yakoma dason lubabatu acikin ransa ba alfahariba ko mijinta baikaita nuna bakincikiba””

Ahakan akayita lallashin juna”” aranar sukadawo gidansu
Hajiya lubabatu harda karamar jinya tayi tarashin kanwarta adole alhaji yabar aikinsa yatsaya jinyarta”” su hajiya kwanansu hudu sukajuya suka koma””
Bayan satii daya darasuwarta yan uwanta sukazo gidan suka kwashe kayansu”” ranarma Ku San kukanda sukayi dasu da lubabatu tankar yafi naranar rasuwarta wata kanwar Innar habiba harcewa tayi da alhaji yanason yarta ai wlh databashi Dan sosai sunason lubabatu kamar yanda takesonsu””
Bayan sungama yan koke kokensu tarakasu sukawuce takoma cikin gida””tasheke dawata mahaukaciyar dariya””” tasoma tafawa lallai kimabashi yarki??? Aikuwa dakin yankarwa yarki ticket din zuwa lahira barganina ahakan bakar kunamaçeni🦂 “nidin damoce Amman nafi maciji hadarii
Babu wata wacce ta isah nayi kishi da itah ba ahaifetaba””” idankuwa tsautsayi ya saka wata tashigo gidan nan tabbas tasoma kididdigar ranar mutuwarta tasake shekewa da dariya tawuce saman 
*WADANSU SHEKARU BAYA*

 Alhaji adamu yunusa”” wani gawurtaccen maikudine kudikuma bana wasaba”” attajiri wanda yakrtashen kudi yanada mata biyu hajiya binta itace uwargida yayanta uku Usman hafis da kubrah”” sai Amarya hajiya hannatu yayanta biyu duk maza kabeer Ahmad”” Alhaji adamu irin mutanen nan ne wadanda sukeda kudi kamar hauka Amman ba agane hakan ajikinsu kokuma asuturansu domin bayaci kuma baya bawa iyalansa komai nagidan kwab kwab akedashi acewarsa aidukiya tattali take so” idan bahakaba tawargaje😂
Sam yan uwansa abun yanabasu haushi barinma hajiya hannatu dankuwa itah macece maison karya danuna isah
Abudayane bayawasa karatun yaransa danyafison kowanne yayi karatu yanemi nakansa dankar zuciyarsa tamace akan na mahaifinsa””
Usman tunda yatashi Sam dukiyar mahaifinsa bata burgeshi tunda yasoma karatu yamaida hankalinsa wajen karatu”” harya kammala degree dinsa fannin kasuwancii”” 
Alokacin babansu yabasu jari Usman da kabeer dankusan taresuka kammala karatu”” 

Usman yanada farinjini hakazalika akwaishi dason mutane babu ruwansa dashiga harkar dabata shafeshiba yanada wani aboki akaduna sunansa abdullahi shine kawai abokinsa baban abdullahi dankasuwane shima yakarfafamasu guiwa akan suyi karatunsu bangaren kasuwanci
  Alokacin da mahaifinsu yabasu kudi yanunawa mahaifiyarsa tasanya masa albarka ranar yakirah Abdul yasanardashi””
 Yace gobe zaizo kaduna hakan kuwa akayi mahaifin Abdul yahadashi damanyan yankasuwa yafara sana a
Cikin yan shekaru Allah yasakawa dukiyarsa albarka”” alokacinne hajiya binta tafara masa maganar aure”” damakuwa yadade yanason wata ameena wacce take tuyar awara alayin gidansu Abdul 

       Ameena marainiyaçe mahaifiyarta tarasu tuntana yarshekara hudu aduniya”” babu kalar wuyarda bataciba wajen matar ubanta huwaileDuka kuwa dayunwa dasuna kashi datuni sunkashe ameena
Mahaifinta yanasonta sosai Amman dagabaya da akaci karfinsa yakoma da itah dababu itah duk daya gashikuma itace kawai yarsa
Huwaile tasoma dauramata talle kuma baburuwanta nairah inhar tayi ciwon kai ajikinta Zata debe tashayi mata tsarki da attarugu tawanke mata daruwan zafiii
Azaba iri iri babuwaççe ameena batashaba”” tunlokacinda taga tasoma kirgan dangi saitafàra yimata awara tana toyawa alayinsu 
Dayake unguwar kowayasan mahaifiyàrtà babu Wanda yatabajinta tayi sa insa da makota bakamar huwaile ba harfada takeyi da kartii idansunçi bashinta basu biyaba babu ruwanta dawai itah matar aurece!!!

Aisha✍🏼

[12:27AM, 2/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 12

       By

Gentle Lady💃🏽

Malam garba kuwa dashi da babushi duk daya kobanza yana bala in tsoronta tunda ba banza tabarshiba”” 

Duk saurayinda yace yanason ameena har gigi yakaishi kofar gidansu huwaile ce zatafito tazageshi ta uwa ta uba”” hakan bazai ishetaba saita samu iyayensa tayi masu Tass kuma tace sujawa dansu kunne kartasake ganinshi kofar gidanta dayawa samari sunason ameena Amman balain huwaile suke gudu”” 

       Tunranarda Usman yaganta yaji takwanta masa arai barinma lokacinda Abdul yasanardashi ainahin tarihinta saiyaji babu matarda yakeso aduniya sama da itah”””
Lokacinda mahaifiyarsa tayimasa maganar aure saida yafara neman shawarar abdul akan yasanarda itah”” dariya yasoma yimasa yace zakafara wautar taku ta yayanfari tomenene dankafada mata kokunyarta kakeji”” 
Dariya yayi yace wacce irin kunya Abdul tunani nayi yarinyar nan bataSanniba kawai dai saninda tamun inazuwa cin awararta lokacinda nake karatu” atunaninka itah zatasoni??? Nifa banaso nacutarda itah
Abdul yasake kwashewa da dariya yace kwantarda hankalinka mutumina indai ameena ce wlh bakada damuwa kasan sarai itama kamar akan kayatake agidansu yanda aka azabeta nikam hakan yayima kaga huwaile Batasan da soyayyar kuba ballantana ta fatattakeka
Tare suka kwashe da dariya yace fatattakadai abokina aitasan wadanda zatayiwa hakan sudinma rainasu tayi kodayake hakan datayi alhairi ne agareni dayanxu banine zansamu wannan kyakkyawarba”” sosai Usman yarude akan sonta cikinwai ma bata kwalliya Dan huwaile batabari waidan kartasamu samari
Ranarda yasanarda mahaifiyarsa tafadawa alhaji adamu yayi murna sosai Amman kafin yanema masa auren saida ya tabbatarda kasuwancinsa dayanda yasamu riba sosai fiye dakudinda yabashi 
Bawani batalokaci yasanarda limamin unguwarsu dawasu abokansa sukaje kaduna sukanema masa auren ameena awajen mai unguwa
Saboda Usman yafadamasu komai akan matarsa””mai unguwa yaji dadi sosai yasa akakirah malam garba” agabansa akayi komai sunbada harda kayan nagani inaso dakuma kudin saka rana ahakan alhaji adamu yace asaka biki kusa kusa kumashi yaron yace basaitayi komaiba shizaimata kayan daki dakomai malam garba kam yayi murna duk dakasan zuciyarsa halbawa yakeyi shikawai yasan fitinarda zaihadu da itah agida”” mai unguwa yace totunda har hakane mezaihana adaurah auren ayanzuma idan ashirye kuke”” hakan bakaramin dadi yayiwa alhaji adamu ba babu bata lokaci yakirgo kudi dubu hamsin amatsayin sadakii
Goron saka rana shi akayita mikawa mutane mai unguwa shiyazama waliyin Amarya”” take akadaurah aure jama a suka shaida bayan yan gaishe gaishe”” alhaji adamu da tawagarsa suka kama hanyar kano cikin farinciki
Malam garba yanarike da sadakin ameena dagoro yatunkari kofar gidansa gabansa yanafaduwa”” yadade bakin kofar gidan dagabisani yashiga da sallama

          Ameena tana tsakar gidan tana darzar wankin huwaile da fa Iza ” ita kuma uwar ikon tana inuwa zaune tanayiwa fa Iza tsifar kaiii”” fa iza yartace Amman batareda malam tahaifetaba bayan tahaifetane tarabuda mahaifinta saita auri malam
Bagidan take zamaba saidai tanazuwa akai akai duk sanda tazokuwa kafin takoma komai ameena takemata duk dakuwa ameena tagirmeta””
malam yakalleta yadauke kansa aransa yace kinkusa hutawa da wahala ameena “” tunkafin yazauna huwaile tamike tanakallonsa yanda yake fara”a
Kujerah yaja yazauna yana mai fuskantar huwaile sannan yakwalowa ameenar Kira””

Huwaile tace haba malam yaxaka kirata bayankuma kana ganin wanki takeyi???
Cikin in inna yace ainaga ba wani abubane dannakirata badadewa zatayiba”” tace kaikasan wannan nidanakeso tagama dawuri tafita tuyar awara

            Cikin malam yahau hautsinawa jin furucinta lallaikuwa akwai aiki jajir”” takatsemasa tunaninsa tahanyar karbe kudin hannunsa tana jujjuyasu tanakallonsa
Sunahada ido yaji zawo tamkar zaizubomasa”” tajefomasa tambaya kudin waye wannan??? Yace eyin eyin”” takatsamasa tsawa batambayarka nakeba”” 

           Cikin kaduwa yace dama yarkice kinsan kwanaki kinacemun gashinan tagirma”” Amman”batada mabidi “” kinsan komai lokacine da”” katseshi tayi cikin karaji kamar mai magana da danta tace sai akayime??? Kafito kayimagana kadaina wani yan zagaye zagaye””
Saida yahade wasu yawu yace sadakin ameenà ne”” gakuma goro “” kafinma ya ajegoron tamike tafara liliyo ashar”” tawatsa masa kudin afuskarsa
Tace kayi gaggawar daukar sadakin nan kamiyar dasu inda suka fito nibantashi aurar da itah ba”” malam garba yashafo zufar goshinsa yace saidai kiyi hakurii Dan maigama tagama har andaurah auren
Wohoho inawuta tasakashi “” jitayi tamkar tarufeshi da Duka”” tace tabdijam wato Dan anunamun iyakata shine akaje waje aka kimtse magana tsofaffun munafukai dama ninadade dasanin duk yan unguwar nan munafukaine
Wato ana bakincikin yar tallarda nake doramata saida sukai kutunguilar samomata miji”” tonikuma sainaga wanne shafaffen damaine ya isah yashigo gidan nan yadauketa
Tallekuma yanzu akafara hartuwo tuwo zanfarà yimata tanazuwa kasuwa yan bakinçiki saidai su mutu kuma ko anki ko a anso ko anasonmu ko anakinmu dole aganmu akyale
Cikin sanyin murya yace kiyi hakuri nikainà badason raina akayi abunba aikin mai unguwane
Rufemun baki tsohon munafuki aikaine babban mailaifin kafadamun tareda mai unguwa kukayi cikinta dazaiñuñà maka iko akanta???

Aisha✍🏼

[9:46PM, 2/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 13

        By

Gentle Lady💃🏽

Yanisa bahaka bane kiyi hakuri abun duk baikai na tashin hankaliba”” tayi saurin gwatseshi tace awajen kaba ?? Wato malam dakai za ahada kai acimun mutunci a unguwar nan
Saboda banice nahaifi ameena ba?? Amman inda kara aitamkar nidince na haifeta tunda nake auren ubanta kuma bauta wacce hawalane banshaba tunyar nan tana tatsitsiya saiyanzu data girma za anunamun halin karfi bakomai aure ko aje ayi “” inazaune zatadawo tasameni taja hannun fa iza sukashige daki
Ameena kuwa tun lokacinda suke maganar tanaduke banda kuka babu abunda takeyi Sam abunda akemata agidan bayadamunta 
Sama da abunda akeyiwa mahaifinta !”tana tsaka da tunani taji yadafata”” tadago dahanzari takalleshi saita done kanta tacigaba da sharar kwallah”” 
Yanisa kiyi hakuri ameena ninasan amatsayina na uba bankare maki hakkin kiba dayake akaina”” inajin tsoron tambayar ubangijina agobe kiyama abisa amanarki datake hannuna nakasa riketa
Nikaina bansan yazanyiba alal Hakika inason ganin farincikin ki”” yasake jan ajiyar zuciya kiyi hakuri kuma kisa Allah aranki insha Allah zakiga sakamakon hakuri
Tagyada kanta nagode Abba inshaa Allah zancigaba da hakuri har lokacinda zanbar duniya Amman Abba auren nan idanhar inna bataso kawai abarshi kwanciyar hankalinka shine nawa banason abunda zai rika sakawa kanasamun sabani da itah””
Ya murmusa karkidamu ameena magana anriga da angama kizama cikin shiri aduk lokacinda mijinki yazo zakibishi”” Allah yabaku zaman lafiya”” inarokonki akan kizauna da mijinki lafiya da yan uwansa “” 

Tanisa nagode Abba”” kudin yamiko mata”” yace gakudinki”” kanta tasanne kasa alamar kunya”” tace Abba kadauka nabaka Kayi wata lalurar dasu”””
Yace haba ameena ina kikataba ganin anyi haka sadakin kinefa?? Tace bakomai wlh Abba””” yace shikenan Amman ninasan mezansiya maki dasu idan bukatar kudi tasameki saiki tambayeni”” tagyadamasa kai kawai”””anan yabarta yashige dakinsa itah kuma tacigaba dawankin datakeyi”””
Alhji adamu yakoma gida murna fal ransa”” alokacin Usman yanagida sosai yakagara mahaifinsa yadawo yaji ko ambashi ameena”” saiyasamu labarin harma andaurah aure wani dadine yakamashi tamkar yayi ihu””” dukawa yayi yayi sujjada yanamai godiya ga Allah dayabashi ameena””
Take yakirah Abdul yasanar dashi”” yatayashi murna”” nesa kadan”” dagidansu Abdul Usman yasiye gida Dan madaidaici mai dakuna biyu ajere”” kowanne daki daya dabayi sai falo daya dayake farkon shigowà saikuma bayin tsakar gida””sai kichin komai yasaka acikin gidan daidai gwargwado”” 
Yakuma tanadi kayan abincinda zasu bukata”” alokacinne yasanarda mahaifin Abdul yasamu mai unguwar yafadamasa Usman yanason abashi matar sa”” domin haryanzu huwaile batadaina doramata talleba””
Mai unguwa yaturah maidakinsa taje gidan tahado mata kayanta”” tatasota gaba ammanfa ansha rigima saida taji alamar za ahadata dayan sanda sannan tabarta”” matar mai unguwa babu laifi”” tagyara ameena daidai karfinta satinta daya agidan mai unguwa akace Usman yazo yadauki matarsa
Alokacin ameena tayi Dan kyau tayi yar kibarta daidai gwargwado””” ranar kuwa Usman sukaje tareda Abdul sukadaukota”” 
Alhamdulillah sunazamansu lafiya babu wata fitina”” saidai huwaile datake zuwa gidan takwashe mata kaya har abinci”” Amman Sam bata taba fadamasaba “” kodakuma abincin yakare dasauri tafadamasa bayacewa komai zaisiyo wani
Wataranane huwaile taje gidan harda mai baro Wanda za alodo kaya saboda tamiyardasu hajarta”” dankuwa har suturah takedauka”” barta ameena harta Usman dauka take”” aranar tayi rashin sa a kubrah kanwar Usman tanagidan”””
Dashigarta”” ameena tanazaune kotakanta batayiba kallon banza”” kawai tawa tsamata tawuce kuryar”” dakin””
Tasoma jido kaya”” tana ajiyewa bakin kofa”” daidai fitowar kubrah tace La Anty wanki zakiyine shine kokimun magana intaso intayaki bayankinsan kwance kawai n”” batakarasa rufe bakintaba saiga huwaile dazannuwan gado”” 
Sabbine hull maman Usman tasiyomata su jiya kubrah takawomata””” aikuwa kubrah damamaki takalleta tace wannan kuma wacce mahaukaciyarce?????
Sai alokacin huwaile tadago kai afusace tace uwarkice mahaukaciya yar iskar yarinyà”” aikuwa batama rufebakintaba kubrah tadauketa damari jikake tasss
Batagama mamakiba”” tasake dauketa dawani”” Marin tareda nunata dayatsa karki kuskurah wlh mahaifiyàtà bakalar zagi bace ki kiyaye harshenki
Sannan kisan kalar furucinda zakiyi agidan nan”” daganinki nasanke kowacece”” taduka tadauki kayan tawuce tagefenta hartana tureta sainagani idan ubankine yakesiyo kayan
Huwaile tanatsaye rike dakumàtu baki bude takasa cewa kala”” har kubrah tagama miyarda kayan”” itakuma ameena tamkar gunki takoma sai rarraba ido takeyi”””
Tadawo gabanta tareda kyasta yatsunta biyu”” daidai saitin fuskarta”” tace oya mekike jirah kama hanya kibar gidan nan tunkafin inrasa natsuwàta wlh inlakadamaki shegen dukanda yausaikin kwana agadon asiviti”” 
Hannunta dafe dakunci tawuce sumui sumui”” kubrah tadakamatà Tsawa Keee!!! saida tazaburah harsaida guntun zawo yazubo awandonta”””
Kubrah tace sauran idan bananan kisake wanko wannan jemammar kafartaki maikamada kashin shanuu kidawo gidan nan hmm wannan gargadine nakemaki Dan muddin nasamu labari hargidanki zansameki inlakadi banzaa tsohuwar banza wacce batasan Allah ba ke kokunya bakijiba kisamu marainiyà kina zalunta” kebaki kawomataba kidauki nata””

      Bàrima nahadaki dahukumà suje hargidàñki sudibomatà kayanta”” dannasan bawannan nezuwanki nafarkobà!!

Aisha✍🏼

[10:40PM, 2/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 14

       By

Gentle Lady💃🏽

Cikin fushi kubrah tajuya dakin domin dauko waya”” aidasauri huwaile tafita ko takalmanta batajirah tadaukaba yau Allah yahadata da hatsabibiyar yarinya kuma take taji tsoronta harcikin ranta
Tana rayawa aranta lallai kubrah ba itah kadai takeba kokuma tanada tabin hankali”” dasauri takoma gida tareda danbaro tasoma jido kayanda suke gidan wadanda bata salwan tarba tadorawa danbaro tace yakawo gidan dataje dashi yanzu yadawo tabashi kudinsa”””
Tashige dakinta takulle”” jikinta sai kyarma yakeyi”” bayan fitarta gidan kubrah tafito daki tana kallon ameena tasheke da dariya tace Anty yanaga duk kintsurene????
Tanisa badoleba bakisan halin inna huwaile ba wlh masifaffiyace babana ma tsoronta yakeyi nayi mamakin daharkika mareta batace komaiba”” 
Kubrah tasake shekewa da dariya tace aiyauta gamuda daidai itah kudinne kuke kyaleta na tabbata yau saitakwana gudawa”” sallama sukaji akofar gidan””
Ameena tace shikenan wlh tadaukoman yan sanda”” kubra tsaki tayi tace kwantarda hankalinki Anty indai inagidan nan wlh ba dansanda zatadaukoba tadauko alkwali ni daidai nakedashi danni walkice daidai kugun uban kowa”” tayi maganar tana Jan mayafii tafitaa fuuu
Tana bude kofa taga maibaro dakaya”” akatunan da Usman yayiwa ameena duka tadibe”” kubrah cike da mamaki haka tayita daukar kayan tanakaiwa cikin gidan saida takwashe duka sannan tacewa danbaron kafadamata nace ta saurari sammacii akotu sainasa andaureta””
Takoma cikin gidan”” tasamu ameena tanabuda kayan””” tace waiyanzu Anty fisabilillah duk kayanki matar nan takwashe kallifa harda abinci kuma kizubamata ido???.
Matar nanfa ba itah tahaifekiba??? Tanisa toyazanyi kubrah ni fitinane banaso kawai Dan azauna lafiya itah abun duniya yadama “” nakyaleta aiba anan za atabbata ba”” kubrah tace hakane Amman hakurinki yayi yawa Anty aiwannan wlh tacutardake sosai tunfarko danasani aida sainasakata tsallen kwado wlh agidan nan””tare suka kwashe da dariya”” 
Ameena tace koyanzu aitatsure nibanyi tsammanin tanada tsoroba wlh”” kubra tamiyar mata”” da kayanta duka dakinta
Danbaro yana komawa yashaidawa huwaile sakon kubrah saiga huwaile tabarke dazawo”” yinin ranar daki tawuni kulle dataji motsi anshigo gidan tashige karkashin gado”” saida aka kwashe sati biyu sannan huwaile tasoma fita”” Amman batasake gigin zuwa gidan ameena ba””
Ko ameena tazogidan nan babu ruwanta da itah”” tsayin shekaru uku da aurensu Amman batasamu cikiba”” kokadan Usman baidamuba alokacin Abdul yayi aure matarsa”” Hauwa”u
Watan bikin Abdul ameena tasamu ciki”” alokacin kuma Allah yabudewa Usman kofofin arziki kasuwancinsa yafara habaka saigashi ansoma damawa dashi cikin masu kudin garin
Tuni yasiye babban fili kusa da gidansa””” akasoma gini”” hawa hudune akayi gini Wanda yakeshine”” bayan cikinta yashiga wata Tara”” tahaifi danta kyakkyawa kinkowa Wanda yarasa sati yana zagayowa akaradamasa suna khaleed
Sosai Usman yakeson yaronsa”” suna kuladashi bama kamar kubrah”” kaleed yanada shekara daya mahaifin Usman alhaji adamu yarasu bayan doguwar jinya dayayi sosai mutuwarsa tagirgiza su Usman
Sunagidan har akai sadakar uku sannan sukadawo gidà”” su hajiya sunagama takaba hajiya hannatu tace araba gado abata na yayanta damakuwa tanajin haushin Usman saboda kudinda yayi lokacinda akabasu kudi suja jari da danta kabeer duk ya halakarda nashi wajen Neman mata”” dakuma shaye shaye””
Babu wani bata lokaci akaraba akabawa kowa hakkinsa”” take ta tattara yayanta da dukiyarta suka koma bauchi damacenne tushenta”” mahaifiyar Usman tahademasa dukiyartà data kannensa yafarayimasu kasuwanci dasu shikuma nashi yahade danasa”””
Cikin shekaru uku Alhaji Usman yazama dai dagacikin masu kudin Nigeria”” idan za akirga masu kudi a Nigeria inhar baizo nadayaba babu shakka zaizo nabiyu”” tuni angama ginin gidansa yatare tareda matarsa dakuma dansu kaleed Sam alhaji Usman baida sha awar yin aure”” saboda ameena tanayin bakin kokarinta wajen biyamasa bukatarsa batagajiya da yawan bukatarsa kuma azamansu basutaba yin fadaba kowannensu hakurii gareshi”””
Kaleed yanada shekara biyar kubrah tayi aure”” mijinta yana karatu maleshia”” aurensu dasatiii daya sukadaga cikin jirgi zuwa maleshia

Dajine mai matukar duhuwar gaske”” bakajin motsin komai awajen hartakukàn tsuntsaye””” zaune take saman wata shimfida”” tana fuskantar kogon”” wata karaaa najiii wacce tayi sanadin zaburata hardawacce takezaune
Bishiyar kukarda takecikin kogon tasoma amsa kuwwwa wacce tasakani rufe kunnuwaña”” wata wutace tayi tartso tareda walkiya haske yafaltsu sama saiga bishiyar tarabe gida biyu””” 
Wacce takezauñe awajen tasaki murmushi””” lubabatu kenan wacce akafisani da lubcy!!

Aisha✍🏼

[11:44PM, 2/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 15

      By

Gentle Lady💃🏽

Lubcy yar kasar bauchi ce Amman iyayenta duka aikin gwamnati sukeyi zamane yadawo dasu”” legos 
Su biyarne awajen iyayenta hudu maza itah ce kawai mace”” iyayenta rikakkun yan boko ne shiyasa sukeson yayansu suyi zurfi wajen karatun boko baburuwansu dawai susaka yayansu islamiyya””.
Sudai burinsu yayansu suyi karatu inhar anaganin karshen biro da takarda babu shakka yaransu zasugani saikuma akayi rashin sa a lubcy dakikiya ce yanda kukasan dusa haka kanta yake bata iyah rike komai harta sunanta bata iyah rubutashi daidai
Tunsanda take primary batada wani kokari duk akayi jarabawa ita take kulle ajinsu”” babu yanda babanta baiyiba komai takeso zaisiyamata Amman abanza dayake babanta maikudine sai akarika badakudi anazauna mata jarabawa hartasamu ta kammala primary da secondary sai yaturata America
Acen tahadu da wasu mugayen kawaye sadiya”” da rabi atu sajida da anisa”” dukkanninsu hausawane”” tare suke tsula tsiyarsu saboda duka basada kokari kodasunje ajima babu abunda suke iyah ganewa
Zaune take cikin skull dinsu wata bayeraba tana kusa da itah tanawaya department dinsu daya da itah kusan duk akai jarabawa itah take lashewa”””
Aranta tace wannan dai babu alamar kokari gareta kodayake baridai nasamu nakullah abota da itah konasamu inji metakesha takeyin wannan kokarin
Tashi tayi tataka zuwa inda take tace hye”” sannunkida hutawa”” tadago takalleta tace yewwa sennude””
Lubcy tace zan iyah zama”” anan??? Tasaki fara a bademuwa zauna”” lubcy tazauna tabata hannu sunana lubabatu Amman zaki iyah kirana da lubcy

.tajinjina kai tace am heelin”” by name
Lubcy tamurmusa tace suna maidadi”” heelin tawaro ido tace dagaske kinayi?? Lubcy tagyada kai heelin tace tnx dea
Duk da lubcy batagane Hausar heelin Amman haka ta manne mata harsuka sabu”” ansoma shirye shiryen fara jarabawa suna zaune dakin heelin lubcy tanata duba littafi dukda batagane komai dankar heelin tacewani Abu saitaga itah heelin din Sam bata karatu saima danne danne takeyi awaya””
Takirah sunanta tadago takalleta tace yadai friend?? Lubcy tanisa tace waike banganki kina karatuba kinsanfa ankusa fara jarabawa “” heelin tabushe da dariya tace ai wahala saiku nibana karatu ai”””
Tace kamarya??? Toyakuma akeyi kina cinye jarabawa??? “” tayi tambayar tana kallonta murmushi tayi sannan tatashi zaune tana kallonta taciro wani biro tanuna mata tace kinga wannan?? 
Lubabatu tagyada kai”” tacigaba dazeran nadorashi akan takarda nawa dekansa zairubutamun amsa”” lubabatu tazaburah tace biron???
Heelin tamurmusa tace shifa”” wannan nasamoshine awajen wani boka” sunansa *HATSABIBIN BOKA* duk wani bukata nawa wajenshi nakezuwa take zaibiyamun dabukata 
Nitunda nake baburuwana de karatu” kuma danagama wajensa zanje yasamamun aiki mechau”””
Tuni lubcy tadawo kusa da heelin tace Dan Allah Kawata nima kikaini wajensa yabani”” heelin tace anya zaki iyah kawayenki ma sunyimun magana Amman nace bazasu iyaba saboda kinga addinina de naku badayaba”” bazaku iyah bin dokokin siba
Murya narawa tace wlh komenene zamu iyah indai zaibiyamana bukatarmu heelin tace inde wannan ne atake kuwa”” saiki fadawa kawayenki kushirya sainakaiku
Lubcy tayi ihun murna tarungume heelin”” aranar tasanarda su anisa ranar weekend sukashirya sai taraba acenne garinsu heelin Amman basuje gidansu heelin ba suka samu hotel sukahuta anan”” anasoma kiran magrib sukafita zuwa dajinda yake
Cikin kauyen taraba yake”” ka idar zuwa wajensa”” inrana tayi tsaka harzuwa dare”” tundasukashiga jejin jikinsu lubcy yasoma rawa fitiluni gasunan cikin jejin suna reto kuma ba daure sukeba basu sama basu kasa”””
Gabadaya ajikin heelin suka labe bakin wani katon iccen kuka suka iso”” kasansa anzagayeshi da karaa saman karan lullube sukeda fatuu Na namun jeji”” babu alamar kofa awajen heelince tasoma wadansu suruttai na gwalamniya”” tana kiran sunansa *hatsabibin boka* take dajin ya amsa kuwa”” takesu lubcy sukasaki fitsariii ganin wutaa Yakama bakin wajen balbal kaitsaye heelin taja hannun lubcy tatuñkàri kofar”””
Aikuwa lubcy tadaddage zatafasa ihu saidaime jitayi muryanta yadisashe”” heelin tasake jawo hannunta tana tirjewa sukashigà tacikin wutar”” saigasu cikin daki maigirman gaske”” su anisa sunawaje jikinsu na kyarma kowacce tacika wandonta da fitsari

Aisha✍🏼

[10:34PM, 2/9/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 16

      By

Gentle Lady💃🏽

Jira suke kawai ace kat su yanki nakare””wata tsawa aka dakamasu wacce tayi sanadin faduwarsu su uku duka asome””
Heelin da lubcy suna samun kansa cikin babban dakin”” saiga wata shimfida kamar tabarmar kaba”” tataso zuwa indasuke tashimfida kanta”” batareda wani tsoroba heelin taja hannun lubcy zuwa saman shimfidar cikin tsoro tazauna gefe zaunawarsu yayi daidai dazubesu aneesa saman shinfidar take kuma suka farfado tamkar wadanda aka watsawa ruwa””

Nanfa suka soma kallon kallon aneesa tasoma kuka”” Dan tarigada ta sadakar mutuwarsuce tazo
Dukansu arikice suke inka debe heelin wacce ko ajikinta da alamu Sam batadamu dakomaiba dantasaba “” wata rikitacciyar tsawa akasaki”” tayi tartso”” bakin bishiyar yasoma cidawutaa tareda wani kugiii
Yan hanjinsu lubcy har motsi sukeyi””” tsawar tacigaba da hauhawa tareda darewar katuwar bishiyar kukar zuwa gida biyu”” wata kujerace tafito zuwa daidai kusa dasu lubcy tatsaya chak”””
Kafin kiftawar ido wata guguwace mai karfii tataso wacce tasaka gabadaya wajen yahautsine baka iyah ganin komai wannan karon ba su lubcy ba hatta heelin saida ta kare fuskarta datafin hannuwanta”””
Su lubcy kuwa gabadaya suka kankame junansu jikinsu yana kyarma tamkar mazari”””tsayin mintuna biyar komai nawajen yakoma kamar yanda yake kurar wajen talafa saiga *hatsabibin boka* ya bayyana asaman kujerar””
Heelin ce tafara zungurarsu lubcy dukansu suka”” bude idonsu”” wani gabjejen mutum sukayi arba dashi Wanda basutaba ganin koda maikamadashi ba acikin duniya wannan zaifikyau akirashi da dodo
Kaiyamafi dodo muni saboda katone majiyi karfii yanada damatsa manya manya tamkar irin namasu danbe””” kowanne damtse nashi daure yake dalayu nafata dakuma wani kambum karfee
Kafarsama haka””” baya sanye dariga”” cikinsa dame yake Amman kanaganin gurayenda yatara ajikinsa””” yanada tsayi sosai dantsayinsa zaiyi kamu ashirin”” kirarsa tamkar Wanda yayi alaka da samudawa””
Bakine wuluk tamkar bakin kwalta bakaganin komai afuskarsa sai jajayen idanuwansa”” kowanne mutum tsakiyar idonsa bakine ammanshi kuma zaibarda take zakiyar idonsa”” farace tass saikuma ja azagaye da itah”””
Idan yadaga ido gabadaya”” farin facewa yakeyi “” saidai ja yamamaye gurbin ido”” sumar kansa tanada yawa Wanda yawanta yasa tazubo har akan faffadan kirjinsa tayiwa mummunar fuskarsa inuwa wannan mutum dazaifito waje babu shakka dayawa mutane zasurasa rayuwarsu sanadin yin Arba da mummunar fuskarsa mai kamada ta dodanni””
Tsayawar guyuwar keda wuya yakece dawata mahaukaciyar dariya wacce tasaka dajin gabadaya ya amsa kuwa”” yadauki tsayin mintuna biyar yana wannan dariyar dagabisani yamurtuke fuska tamkar Wanda baitaba dariyaba”” heelin tabuda baki tasoma jero masa kirari”” Saikai takadiri kuma gagare kigudu sagudu sa abokan gaba sugudu”””
Turmin karfe kake shakwaramniya””” Saikai *hatsabibin boka* sugaban duk wani tantirin ajani”” komai Tsagerancin aljani idan yazo gabanka dole yaduka nasaramaka uban maza uban hatsabibai maidakawa maza gumbaa””” take yasake kecewa dawata mahaukaciyar dariyaaa 
Heelen tasake buda baki daniyar magana yadaga mata hannu
Yace kafin kice wani Abu inaso insan kokin sanardasu dukokinmu dakuma sharadin mu??? Cikin saurii tace nafadamasu yasarkin bokayen duniyaa
Yagyada kansaa duk dahaka zansake sanardasu dangudun kuskure dakuma fadawa hafushinmu””” kusanii akwai sharadiii guda biyar wadanda zanfadamaku
Inhar kuka kiyaye kuntsira sharadi nafarko”” ma abota sallah basa shigowa fadataa””” duk ranarda zakuzo inda nake karwacce takuskurah tadorah goshinta akasa””
Sharadi nabiyu”” karwacce takuskurah tabada sadaka!! Domin yanadaya dagacikin abunda zaibata aikina”””
Doka ta uku muddin kika fara aikidani babuke basake zuwa wajen wani bokan “” yinhakan kuwaa zaijanyomaki masifa da bala.i dagake harbokan nakii
Sharadi nahudu duk abunda akace kikawo karkitsaya musu ko gardamà idankuwa kikatsaya watamagana take bakaken aljanu zasu zuke jininki
Doka tabiyar wajibine idan akabaki Abu dole ki aikata idankuma kinki to zaijuye zuwa kankiii””” sannan kuma duk abunda kukagani anan karkutaba idankun kiyaye kuzauna lafiyaa
Tunsa inda yasoma wannan jawabin jikinsu sadiya yasoma kyarma dama yalafiyar kurah kowaccensu tayi danasanin zuwa wajen 

yanagama rattafo sharadansa saisuka fara kallon kallo atsakaninsu gabadaya idonsu yaraina fata””
Lubcy tanason yin magana babu halii “” saida yabata izinin magana cikin sauri tace”” dama dama munasone mudanyi shawara
Batagama rufe bakintabà yadakamata wata razanan nar tsawaa wacce tasaka lubcy tayi danasanin maganar
Hatta dakin saida ya amsa kuwaar yace bakuda wannan damar kusani kafin azonan akeyin shawaraa basai anzobaa danhàka Ku kiyaye!!!

Aisha✍🏼

[8:27PM, 2/10/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 17

      By

Gentle Lady💃🏽

Cikin kyarma lubcy ta gyada kantaa heelin ce tace tuba suke”” uban hatsabibai”” sunji kuma sunyarda da sharuddanka idan muka fitaa zamu turoda kayan aikiii 

   yajinjina kai” saiki sanardasu zasuga abunda sukeso””” tadan dukarda kai tace godiya muke””” tasake dukawa tace munbarku lafiyaa”” sannan tamike aitana tashi su aneesa sukai zumbur suka Mike dama Kuwa kamar akan kayasuke”””

 Kamar yanda sukashigo wajen yarufe kansa babu alamar”” kofa”” suna fuskantar wajen”” heelin tasake kiran sunansa saigashi wajen yasake kamawa dawutaa suka ratsa tacikin wutar saigasu waje”” 

            Gabadaya dajin yayi tsit saiwani gurnani sukeji kamar na kuraye da zakuna suna nane da heelin harsuka kai karshen”” dajin”” tace duka surufe idonsu 
Rufe idonsu sukayi kafin mintuna talatin sukaji tace kubude suna budewa sukagansu cikin masaukinsu”” aneesa cikin tsoro tabuga uban ihuuu tashige cikin zanen gado”””
Heelin takwashe da dariya tace Amman kumanyan matsoratane nibantaba ganin masu tsoro kamar kuba”” jiyanda kuka tsure kamar kusaki zawo awando

 Lubcy tace heelin ai ba kamabane”” ni bana raba dayan biyu wlh fitsarina sau biyar awando idan ancema harda zawo bana musawa sainashiga toilet in tabbatar,”””
Sadiya datake sharce zufa tace wlh nima fitsarina shida awando kai nadaukafa mutuwa zanyi niko amafarki bantaba tunanin zantaba ganina a irin wannan wajenba”””
Wannan anyakuwa mutum ne??? Idankuwa har mutum ne anyi mumm bata karasa rufe bakintaba heelin ta dademata baki tace wlh karkisake duk abunda kikeyi tamkar agaban *hatsabobin boka* kike!!jin wannan furucin yasaka sadiyaa saurin hadiye wasu miyagun yawu masu dacin gaske idanuwanta suka firfito kulu kulu tamkar wacce taiwa sarki karya”” tace nashiga uku kardai yakasheni tayi maganar tana dafe kirjinta”””
Heelin tace bazai kashekiba saidai zaisa akaiki kurkukunsa Wanda yake ganawa bokaye azaba dakuma wadanda suka bijirewa umurninsa cikinsu kuwa harda aljanu”” zamanki acikin kurkukun saikin gwammacewa mutuwarki akan haka domin zakisha azaba iri iri wacce bakitaba tunanin irintaba”””
Zaiyafemaki sabodake sabuwar zuwace bakisan komaiba Amman daga wannan ki kiyaye kisan abunda bakinki zairika furtawa””!!
Duk yanda kike tunaninsa yawuce saninki”” nikaina awajen mahaifiyata nasamu damar ganinsa”” babuwani boka dazaishige gabansa inhar zaku kiyaye sharudansa har abada bazaku nemi Abu kurasaba kudenajin sorofa”” anisa”” nasan kinfisu jin soro”” dukanku kuyanke shawara gobe zamuje musiye kayan aiki”” saimu aikamasu
Aneesa wacce haryanzu batafito acikin zanenda tarufe kantaba tace badai wajen zamusake komawaba??? Heelin tayi murmushi tace ah ah gobedai zakuga yanda zamuyi yanxu kutashi mushi abunshi”” saimu kwanta nagajii woo
Tayi maganar tana mikewa tayi hamma”” sannan tawuce “” dukansu ido zuru zuru suma sukamike lubcy kam dayake tanada dakakkar zuciya hartadainajin tsoro
Sukai wanka suka shirya”” bayan sunci abinci kowaccensu tasamu wuri takwanta dukansu sukayi lamo tamkar masu barci Amman azahirin gaskiya ba barcin sukeyiba zuciyoyinsu sunyi nisa wajen tunanin inda tsautsayi yajefasu kokuma ince sukajefa Kansu 
Inkadebe heelin wacce takeyin chat hankalinta kwance”” sai dariya takeyi da alama tanayin fira mai dadi wacce take sakata nishadi””
Intakaice maku labari darendai kam basu samu barciba kowaccensu saiganin abunda sukajeyi take tamkar anayimata video nashi heelin kuwa tashaki barcinta
Indasuma saida asuba barcin yadaukesu”” basu suka farkaba sai shadaya narana”” bayan sunkimtsa”” sunci abinci suka shirya heelin tace suje suyi”” abundayake gabansu”” suyiharamar komawa”skull”taresuka fita zuwa kasuwa dama sunzo dakudii heelin cemaidubawa””” duk inda sukaga bunsuru baki Wanda bashida sulkin farii dakuma maifari akai”” uku kawai sukasamu sukai ciniki”sukabiya”” heelin tariko su sukafito kasuwan””koda sukafito basugakomai hannun heelin ba”””

Lubcy ce tace ke heelin ina suke??? Tayi maganar tareda soma waigen bayansu takesuma su aneesa sukasoma dube2 kowai tabarsu abaya””
Heelin dariya tasoma yimasu tace waiku kundauka nasakesune??? Ai hadiman aljanunsa sundaukesu yanzun haka akwai sauran su sunajirah mukarasa siyen sudauka tace yanzu wajen da akesiyarda kaji zamuje” 
Sudaikam binta kawai sukeda kallo haka sukaje sukasiye kaza maiwake Wake sai jajayen zakaru tareda farar kazaa”” 
Kamar yanda wadancen sukabace hakama kajin”” daganan sukadawo gidansu sukayi haramar komawa skull
Ranar sukadawo america kowaccensu tasamu Biro acikin kayanta”” zokuga murna tunkafin suzana jarabawar”” hankalinsu kwance basayin wani karatun har akasoma jarabawa
Dazaran sun kalli Question sukadorah biron takezasuga sunata rubuta amsa sukansu basusan tayama amsar take fitowaba
Bayan ankare jarabawa dukansu sukalashe”” wannan shine ainahin yakininsu akan wannan *hatsabibin bokan*tundaga lokacin inhar bukatar waninsu tatashi cenyake zuwa hartakaima suna iyah zuwa mutum daya badole saida Dan uwansaba

Harsuka kammala makarantar sunkomagida kowacce dasakamako maikyau ranar mahaifin lubcy saboda jindadi yayimata kyautar dankareriyar mota tareda babbar waya””
Tun lokacin batasake waiwayar *hatsabibin boka*ba saiyau kome ketafe Da itah oho!!

Aisha✍🏼

[9:37PM, 2/10/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 18

       By

Gentle Lady💃🏽

Lubcy tasake sakin murmushi ganin wata katuwar darduma irinta sarakai tafito acikin katon kogon kukar tayiwa kanta mazauni akasa”” nantake iska mai karfiii tatashi tamkar ana hada hadari tsawa tareda hargowa sukacika dakin kogon”” saiga *hatsabibin boka* ya bayyana asaman dardumar nantake komai dayake wajen yatsaya chak iskar sannu ahankali tanatse””
Lubcy tadago cikin girmamawa tafara mika gaisuwa tareda somayimasa kirari”” saikai hatsabibi uban hatsabibai”” abuga adaka sai kalwa””saikai namijin gaske uban duka bokayen duniya””
Shugaban shaidanu uban hatsabibai kai kanka tsoron kanka kakeyi”” anbuga dakai anbarka”” kowa yatabaka yanemawa kansa bala i
Saikai uban dawa uban kangararru”” takawarka lafiya kaci zamaninka kaci nadangi bakada tsoro bakasan tsoroba ” komai gaba kabashi ba nayaba”” 
Sosai *hatsabibin boka* yake jin dadin kirarin nan tace gaisuwa nake shugaban bokaye kaiyajinjina”” 

TaCe ayimun afuwa tsawon lokaci bandawo nanba kasancewar daga garinmu zuwa nan akwai tafiya yanzun mawata bukatace dani maigirma”” ina
Hannu yadaga mata yace bakomai munsan komai agamedake domin munatare dake”” dangane dabukatarki kuwa tuni nasanda itah wanne irin miji kikeso???
Take lubcy tawashe hakorah jin *hatsabibin boka* yasan da bukatarta”” tace inason mijine na nunawa sa a kyakkyawa maikudi kuma maitashin kuruciya tunbayan gama karatuna zuwa yanzu duk wadanda sukezuwa wajena basuyimun ba
Indai kudi sunadakudi saidai suntsufa sannankuma basuda kyanda yadace ace kamata nazama mallakinsu”” wannan dalilin yasaka nazo wajenka domin nasan Kaine zakasharemun hawayena kabani mijinda yatara dukkan abunda nalissafo ayanzu
Tanarufe bakinta *hatsabibin boka* yakece da dariya yace kinkawo kuka inda za asharemaki hawayenki yadaga hannunsa sama saigawani madubi maigirma ya bayyana ahannunsa””
Take yashafa gilashin yanawadansu suruttai””” saiga hotunan mutane sun bayyana acikin gilashin su goma sha biyar”” 
Yanuna mata yace kiduba saiki zabi daya dagacikinsu”” jikin lubcy har rawayake sai kallonsu takeyi tarasa wanne zata zaba” saboda kowanne yanada nashi kyan babu makusa”””
Idonta yatsaya akan wani matashin saurayi Wanda yafisu kuruciya daganinsa ko aure dakyar idan yayi”” takafeshi da ido batako kyaftawa””” 
Ganin hakan yasaka madubin yajuya wajen *hatsabibin boka* take yakece dawata mahaukaciyar dariya yace wannan shikika zabà??? Cikin sauriii tace ah
Yagyada kai sannan yaja layi daidai saitin photon”” zuwa yan mintuna kadan yadago yakalleta yace wannan saurayin sunansa Usman sunan mahaifinsa adamu mahaifiyarsa binta yanada kanne biyu wadanda suke daki daya Hafiz da kubra
Akwai yan uwansa kabeer da ahmad ‘abokinsa daya Abdul”” yanada mata sunanta ameena sunada yarodaya kaleed yanzun shekarar yaron biyar aurensu shekara Tara”” asalinsu yan kano ne Amman yanazaune akaduna anan yake kasuwancinsa
yanafità kashashe””” yanzun haka yana maleshia”” kwanansa biyu acen gobe zaikoma gida”” mahaifinsa yamutu yabarmasu dukiya maitarin yawa wacce basusan adadintabà 
Dukiyardà hatta tattabakunnen su bazaitaba talauciba”” yakai karshen maganar yana kallonta 

Tayi shiru Sam batayi tunanin yanada aureba”” tadago murya cikin damuwa tace yanzu yaza ayi Sam wlh banasoñ kishiya banyi tunanin yanada aureba””
Yace kwantardà hàñkàlinki komai awajenmu maisauki ne ammanfà kisañi muddin tàñaràye bazaitaba aurenkiba

Lubcy tadafe kirjinta tace nashiga uku to akasheta kawaiii
Yasake kecewa dawata mahaukaciyar dariya yace wannan daidaine”” kisa aranki yazama mijinki”” tace toyanzu taya zanganshi alhalin yana kaduna ina legos ???? 
Yasake kwashewa da dariya yace ko birnin sin yake kina sokoto kisani dazaran munturashi dole yaje inda kike”” abudaya zakikoma gida kafin mugama aikinmu akan matarsa daganan zamu sanardake inda zakuhadu
Amman akwai sharadinda zangindayamaki karki kuskurah tsautsayi yakaiki fadar sunansa inhar bashine yafadamakiba hakazalika danginsa kinuna tamkar bakisan komai gamedashiba sai idanshine yasanardake
Sannan aranar kiyi shigar mutuncii”” komai dazaifaru tsarinane saiki kalli abunda zaifaru””
Yasake daga hannunsa sama saigawañi madubi karami ya bayyana ahannunsa”” yamikamatà

Bayan takarba yace kasancewar tafiya mainisaçe tsakaninmu 

Na mallàkà miki dai daga cikin madubin taskar *hatsabibin boka* aljanin da yakegadiñ wannañ madubin sunansa dukursusu””” kisani wannan aljanin hatsabibin aljanine kuma azzalumi inharkikai wasa da madubin nan dakansa zai halakaki babuwanda zaitaba tunaki aduniya
Kirikeshi tamkàr rayuwarki karkibari wani yaga inda kike ajeshi”” bacewarsà daidai yakeda tonuwar asirinki 
Dazarañ kinada wata bukata tokishàfi fuskar madubin kikirah sunana sau uku zanbayyana acikinsa sàiki sanardani bukatarki

Aisha✍🏼

[10:40PM, 2/10/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 19

      By

Gentle Lady💃🏽

Duk maganarda zamuyi saimuyita atake tamkar kina nandin wannan saukine agareki bake kadaiba akalla akwai su wajen mutane sama da milion daya wadanda basa iyah zuwa nan saidai muyi magana cikinsu akwai yan kasuwa dakuma manyan attajirai dakuma shuwaga banni”” danhaka saiki kula Kuma ki kiyaye idan kinfita saiki kirah aljaninda ke kulada wannan madubin domin yakaiki gida”” dankiyaye lafiyar madubin 
Yana gama fadar hakan wata guguwa mai karfiii tazo”” take wajen yakaure da iska”” guguwar tayi sama saida tagama shawagi kasar wajeñ tadare gida biyu tashige karkashin kasa bat tabace komai nawajen yakoma daidai 
Lunby mikewa tayi madubin yana hannunta takaraso bakin kofar bayan takirah sunan *hatsabibin boka* kofar takama dawuta takutsa tacikin wutar tafito””” 
Tsaye tayi tana tunanin sunanda yafadamata na aljaninda ke gadin madubin Sam tamanta”” lallai dole taje hotel takwana washe gari takoma gida”” jakar hannunta tazuge daniyar saka Dan karamin madubin wata tsawa aka dakamata wacce takusan sakawa lubcy tasakii madubin
Cikin daga murya akace”” wannan shine kulawar dazaki bashiii kisani duk kika kuskure abudaya rayuwarki zatashiga hadariiii yanda maganar taketa amsa kuwwa acikin jejen tuni lubcy tasaki fitsari duk darashin tsoronta Dan abuguda takijini aduniya taji anyimata maganar mutuwa kokuma ace zatarasa ranta
Natsuwarta batagama dawowaba wata iska maikurah tataso wajen tayi sama””” wacce dazata daga kanta bazataga karshen guguwarba””” tuni lubcy ta kankame jikinta kafin tayi wani motsi kawaitaji an sunkuceta anyi sama”” take yalulaya da itah cikin gajimare 
Al amarinda yasa lubcy tasome danta sadakar kasheta zaiyi”” batakara sanin meke faruwaba saidai ta far fado taganta kwance akan gadonta”” Jakarta tana gefenta . gakuma madubin ajiye akusa da itah dasauri tamike tasoma yandube dube babushakka dakinta take”” idanuwanta suka sauka akan agogon dakin Wanda yabuga karfe hudu na dare”””tashafo fuskarta yaukam tasake tsorata da lamarin wannan bokan
dolema akirashi *hatsabibin boka* domin yaci sunansa”” mikewa tayi daga kan dagon”” tasoma neman inda yadace taboye wannan madubin””” wani karamin akwati tadauko tasakashi aciki tarufe takaishi cikin lokar karamin gado”” take akwatin yafito yadawo kasa”” 
Tayi shiru aranta tace watakil mazaunin baiyiba tayita tunanin inakuma zatasaka “” karshen lokar kayanta takasa tabude tasakashi 
Tana ajeshii”” taga yazauna daram tasaki murmushi”” sannan tarufe lokar tacire kayanta tawatsa ruwa takoma takwanta”””
Batasake farkawaba sai washe garii””” mamanta Sam batasan lokacindà tadawoba tasan kodasuka kwanta batagidan”” Amman sambata damu data tambayeta inda tajeba aganinta ai itah ba yarinya bace daza atuke da tambaya danyanzu tarigada ta mallaki hankalin kanta
Wautarda dayawa mafiyawan iyaye sukeyi ayanzu”” waisunaganin yayansu sungirma sun mallaki hankalinsu bazasutaba kaikansu indasukasañ zasu cutuba
Shinmezai hana idan yayanku zasufita kutambayesu inazasuje???” Idankuma sundawo kutambayesu indasukaje harsukai dare
Sautari yammata da samari sukan lalaceñe”” asanadin rashin kulawar iyaye mafiyawan lalacewar tarbiyar yayanmu”” munada hannu aciki iyaye sunataka muhimmiyar rawa wajen lalacewar yayansu
Kowa yasan akwai kaddara Amman Kuma akwai sakaci”” Allah yashirya mana zuri armu ameeen

Lubcy kam hankalinta kwàñce tacigaba da harkokinta
       *KADUNA*

Ameena ce cikin kitchen din gidanta tareda masu aiki tanahadawa Usman abinci domin sunyi waya lokaciñda yake shirin shiga jirgi
Tana saran kara sowàrsà biyar na yamma”” gefenta kaleed ne tsaye yana kallonta duk inda tayi yanabiye da itah kamar jela”””
Harsuka kammala hadamasà hadadden girki Wanda tasan yanaso gabaya tajeresu akan dinner”” anan tazaunarda kaleed tàzubamasà soyayyen nama tace yazauna tana zuwa

.

Ta umurci mai aiki tagyara wajen”” akashare akagoge tàjona turaren wutaa”” tuni gidan yarude da kamshi ganin harhudu tagota dasauri tahaye sama dantayi wankaa
Tana turah kofar dakintà tàyi tozalii dawasu manya manyañ beraye kowanne daya yakai girman Dan akuya sunada kunba zaro zaro hakorañsu kowanñe yafitodaga bakiñsa zuwa saman labbansa idanuwansu manyane tamkàr kwayayin fitila saidaisu jajir suke kamàr gautaa ihu tafasa dakarfi tarufe idonta ganinsuna tunkarota tàkejikinta yasoma kyarmà

Aisha✍🏼

[11:51PM, 2/10/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 20

      By

Gentle Lady💃🏽

Jikinta sairawa yakeyi tanatsaye takasayin komai jira kawai takeyi taji yakushin berayen domin tunda take aduniya bata taba ganin beranda yayi girman koda Dan kaza ba banlantana kuma akuya
Shiru taji tsayin mintuna ahankali tasoma bude idonta bataga komaiba tawaiga ko ina bakomai ahankali tasaukarda karamar ajiyar zuciya”” tayiyu bakomai bane kawai kallonda tayi dazune kaset din horo shine takejin tsoro”””
Batareda wani kokonton tunanin taba takarasa dakin kawaidai saitaji jikinta yayimata ba dadi”” fitowa tayi takoma bangaren Usman tayi wanka tayi sallah””” sannan tayi kwalliya duk da bawata kwalliyace tayiba Dan jikinta jitakeyi tamkar anlikidamata shegen duka””  
Bayan tagama shiryawa cikin kananun kaya Riga da sket””” masu karamin hannu”” tadauko Karamin hijab fari tasaka”” yar karamar fuskarta tafito tayimata kyau”” saukowa tayi kasa wajenda tabar”” kaleed””

 

Yana zaune kasa kusa dashi wadansu kadan karune manya”” masu katon kai kowanne daya girmansa yakai girman tsarii idanuwansa jajir tamkardai nawadan cen berayen””” cikin daga murya tace kaleed bar wajen nan””” tanarufe baki wadan nan manyan kadangarun suka soma keta wata muguwar dariyaa “” wacce ta karade dukan falon”” shikuwa kaleed sam baijitaba saiwasa yakeyi dasu yana dariya””” jikin ameena yasoma bariii tasoma ja baya ganin suna nufo inda take “” daidai shigowar Usman”” aidagudu taruga tafada jikinsa taboye fuskarta”” 
Cikin firgici yayarda jakar hannunsa yana tambayarta lafiya meenal?? Menene yafaru”” dahannunta ta nunamasa wajen kaleed shikuwa kaleed maganar babansa ce tasaka yadago kansa dasauri yadauko Dan kadan garensa naroba mai batir yarugo yana oyoyo papa”” jikin mahaifinsa yashige Usman yashafo kansa da hannu guda
Sannan yamaida kallonsa wajen ameena yace please meenal kidago kikalleni nigabadaya kintayarmun da hankali”” 
Shiru yaji batace komaiba yasake girgizata saiyaga ta langwabe dasauri yature kaleed gefe yadagota illaikuwa AMEENA tadade dasomewa””” Cikin sauri yakarasa jikin kujerah ya kwantarda itah”” dasauri yadebo ruwa yazo yaballe murfin robar yasoma yayyafamata”” 
Tasaukarda ajiyar zuciya ahankali tabude idonta zunbur tamike tasake kankameshi tafashe dakuka “”” jikinsa yajawota murya araunane yace waimenene meenal Dan Allah kisanardani kinsan halinda zanshiga idan inaganin kukanki???
Har abada bazanso kizubarda hawayeba muddin inaraye Dan Allah kidaure kisanarsani menene dalilin kukanki ???

Cikin muryar kuka tace Yaya kadangaru naketa gani masu magana”” akusa da kaleed
Usman yakalli kaleed shima kaleed din shiyake kallo Wanda tunda mamarsa tafadi yakuramasu ido yana makale da kadan garensa naroba
Usman yayi murmushi yace meenal kadangaren robar kikewa kuka?? Inakin saba ganinshi dashi sai alokacin tadago daga jikin Usman cikin tsoro tsoro takalli kadangaren
Tsayin mintuna tamaida kallonta wajen Usman tace wadanda naganifa manyane kuma suna dariya”” kaleed yayi charab yace mom nan ake karamasu gilma”” yamatsa wata yar kunama saigashi yayi tsayi yanadaga kansa tamkar kadangaren gaske”””
Usman yace tokingani dama bakisan haka yakeba”” idan tsoronsa kikeji kibari na konashi damacen kece kikasiyomasa danni banason ire iren wadan nan 
Dakinsa duka kincikashi da Teddy waiduk kayan wasane bakisan gunki bane kike ajewa badole saida wadan nan zaiyi wasaba kwanaki inaganifa harda macijin roba kika siyomasa”””
Ameena tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya tace wlh natsorata Yayana”” tashi muje kayi wanka kakwaso gajiya”” karan hancinta yalakuta yace bayan kintayarmun da hankali
Ninadaukama nine na aikatamaki wani gungumen laifii harna tanadi kalar hukuncinda zanyiwa kaina”””
Murmushi tasake taboye fuskarta cikin jikinshi tace rufamun asiri wanne laifi zakamun nikuwa aduniya Wanda zaisakani kuka”?? Nayi kuka lokacinda nake marainiya tunranarda na aureka bakinciki baisake tunkaroniba Wanda zaisa kabatamun rai hartakaini gayinkuka
Inaji araina nagamayin kukan bakinciki aduniya Allah yasharemun hawayena yahadani da nagartaccen namiji Wanda kowacce mace zatayi gurin samun abokin rayuwa kamarka
Ina mai addua kowacce mace tasamu miji mai kwatankwacin halayenka””” ido yakwalo yace daina zigani hakamana
Kinsa nafarajina asama ina shawagiii karkisa kaina yafasu dayawa”” 

Tayi dariya gaskiya nafada baban kaleed Dari bisa daribakada makusa duka dabi unka irinna nagartattun mutanene
Yaja hancinta yace kamaryanda kike nagartacciya ba kisani nayarda dakefiye dayandà nayarda dakaina kyawawan halayenki sune sukesakani karasonki
Babu shakka ke yar ajannace”” cikin zolaya tace idan kadagamuñ kafarkaba””” yayi dariya yace aituni nadage kafar wlh meenal da aljanna ahannuna take dakuwa kullum sainabaki itah sama dasau goma
Murmushi tayi tamike dagajikinsa yadago yana kallonta zaiyimagana tadorah Dan yatsanta saman labbansà tace ka Adana kalamanka. Harsaimun kwanta yanzu katashi muje kayi wanka kaci abinci kafin nan lokacin sallah yayi saikaje masallaci

.

Yamike yana murmushi yace tomuje Amarya dariya tasaki tajindàdin sunanda yakirata dashi sosai tanajin dadin yakiratà dasuñan
Tayigaba yanabayanta zuwa bangarensa tahadamasà ruwan wanka wadanda sukasha turareñ wanka masu kamshi
Tataimaka masa yarage kayan jikinsa yashiga toilet din”” tarufemasa kofa yana zolayarta waibazata tayashi wankanba saboda yadebo gajiya

Aisha✍🏼

[2:15AM, 2/11/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 21

      By

Gentle Lady💃🏽

Dariya tayi tace hannuna ciwon kai yakeyi kaidai kagama kafito tayi maganar tana karasa rufemasa kofar toilet din
Wajenda yake ajiye kayansa tanufa tabude tafitomasa da jallabiya”” tafesheta da turare”” wayarsace tasoma ringing
Tadauko ganin sunan little sister akan wayar yasaka tadauka cikin fara a tareda sallama dayan bangaren aka Amsa”” tace la Anty kicehar yasauka
Tayi dariya tace ah wlh yagidan yamaigida”” kodayake aibakibada sakon gaisuwa akawomun ba”” tace la anty yaya baifadamakiba???
Tace baifadamun meba ??? nasan dakince agaidani aidabai mantaba dasaukansa zaisanar dani”” kubrah tace afuwan matar Yayana takaina kema kinsan bazan rasa turo sakon gaisuwata agunkiba inajindai gajiyar jirgi tasaukarwa Yaya yamanta da babban sakona
Tayi murmushi to ankarbi uzurinki dukansu sukasa dariya kubrah tace Anty ina my son dina”” tace hmm sarkin rigima aini sonake babansa yakwasheshi dakayansa yaturah makishi cen konahuta da rigimarsa”” 
Kubrah tace la Anty wlh kaleed baida wata kiriniya kamar sauran yara”” tace aidole kice hakan tunda shine naki””” ya amarci yakuma kasar””
Tanisa Alhamdulillah wlh Anty nayi kewar gida sosai “” Ameena tace yaushe akai aure dukafa wata biyar yanzu kice kinyi kewar gida bayankuma kinatareda rabin ranki “””

Kubrah tace hmm Anty kedai ayita sha ani waidama haka aure yake kullum inason intambayeki Amman saiyakureni da kallo idan inawaya bahalin inyidan sirri 
Dariya tayi tace wannan ma sirrine zaman aure ba komai kikagani azaman”” aure hakuri zakiyi wannan itace ibadar””” tace hmm Anty bazaki ganebane wlh nihar gajiya nakeyi saikace agogo kullum babu Hutu
Ameena tanisa tace nagane mana Amman azancenki bazan ganeba kubrah shilamarin aure akwai sirri acikinsa barganin ina mace yar uwarki kiyi tunanin sanardani abunda kike fuskanta tareda mijinki 
Kisani kowanne dan Adam dakalar tashi sirrinki ki adanashi kizama maikunya nisam irin wadan nan maganganun wlh kunyarsu nakeji menene amfanin kazauna kana fadar mijina kaza mijina kaza “” duk yanda mijinki yake kibarwa zuciyarki saikiyita hakuri watarana sai labari kodai kinason yasake aurene???
Cikin sauri tace la ah ah Anty Sam bahakan nake nufiba kawaidai inadauka kowama hakan yakeyi kamar nawa”” Ameena tasakeyin murmushi tace ah ah

Aiyanda kikasan halitta akwai banbance banbance atsakaninsu hakayake ako ina akwai banbanci
Tanisa nagamsu Anty kuma insha Allah bazansake maganar ba””tace yauwa Kanwata “tace Anty wai ina Yayana??? “daidai fitowarsa wanka”” tace ga shinan yanzun yafito wanka”” yanadaure da towel daya hannunsa yanarike da karamin towel yana goge ruwan jikinsa yace naji ana gulmata
Dariya tayi tace bafa gulma mukeyiba”” yace tayazangane bayan inajinku kunata kus kus kus”” dariya takeyi harda kubrah 
Tace sister ce takira taji kasauka lafiya”” yanataje sumarsa yace ainasan itace Dan idan ba itaba babuwanda zaikirah wayana kidaga”””
Aisaiki fadamata nasauka lafiya “”” tace ainafadamata tace Allah yahutarda gajiya””” yace Ameen sai ayi sallama ayidaniko”” yayi maganar yanarike kunkuminsa dariya ameena tasoma tace kinga sister zamuyi waya anjima”” 
Usman yace anjimadai meenal saikace wasu yammata”” tokaratunfa wazai karani tuni ameena takatse kiran tunda tagano abunda zaifada
Tace kai baban kaleed wannan saikasani jinkunya agaban yar Kanwata””” baki yatabe yace wayajiyo kitaso kishiryani yunwafa nakeji”””
Wayar ta aje tana murmushi ganin yanda yayi maganar kamarwani yàro dangoye””” saida tashiryashi suka sauka kasa”” kaleed yanasaman kujerah yana gem da TV
Saman dinner suka karasa tagabatar masa da abincin ita tarikabashi abaki saida tatabbatar yakoshi alokacin magrib takawo jiki yawuce masallaci itakuma taka she TV taja hannun kaleed zuwa sama sukai sallah”””
Usman baidawoba sai bayan isha”” falo sukatsaya suna kallo saikusan shadaya sukahau sama lokacin kaleed yadade dayin barcii
Bayan sunyi wanka suka kwantaa””tunda suka kwanta ameena taketa mugayen mafarkai”” har asuba””” batasamu barci maidadiba saida sukasake kwanciya bayan haske yafito
Sai wajajen karfe Tara tafarka””” koda tatashi har angama shiryamasu break”” bayan sunyiwanka suka karya”” tashirya kaleed cikin kayan makaranta”””
Zasu wuce yasheka dakinsa saigashi yafitoda kadangaren roba”” dagudu ameena takarbe tayi wurgi dashi tace mezakayi dawannan a skull kuma???
Yace mom anty dinmu dukana takeyi idan nayi sulutu”” gobene wani kadangale yashigemata ajiki tanata ihu taluga munata dariya shine danje danawa databugeni inli amatashi”””” yakai karshen maganar yana dariyaa
Ameena da Usman masaida sukadàara tace aimaganinkà kenan”” inba shashancibà mezaisaka surutu amakaranta anacikin aji ana karatu
 Yace mom banikadai nake sulutuba” tace kodakai dawanefa kadaina sannan bakyau tsoratarda musulmi kasani
Yace to ai itah ba musulma bace sai wannan karon Usman yayi magana yace kaiwaye yafadamaka???
 To aibata saka kaya ilinna mom kuma idan tashigo aji bata sallama”” ameena tace umm kaga kuwuce zaku makara idan kabiyewa surutun wannan
Tariko hannun kaleed din sukafità Usman yabi bayansu”” harwajen mota tarakasu””” saida taga tashiñsu tanadaga masu hannu sannan takoma cikin gidan 
tana turah kofar shiga tayi Arba da katon kadangaren yanaganinta yanufota”” cikin saurii saboda tsabar firgita maimakon tayi waje saitakoma cikin falon”””

Kadangaren kuwa yatasomata haikan tuni sukafara tsere acikin falon!

Aisha✍🏼

[12:01PM, 2/11/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 22

    By

Gentle Lady💃🏽

Zagaye takeyi tanaganin kamar zaikamota kuma haryanzu bakinta yakasa furta addua Sam tama manta dawata addua
Tana tsaka dagudun siket din jikinta yatadeta tafadiii” take tayuyo tafashe da kuka mai karfiii ganin kadan garen yana dosota idanuwanta ta tamke waje daya””
Muryar maitayata aiki taji tana sallama”” Amman batayi gigin buda idontaba””” mai aikin tamatsa inda take tace uwar dakina meyasameki
Cikin tsoro tace kadangare bakiganshi ba gashinan gabana ! Tawaiga bataga komaiba saicen nesa dasu tahango kadangaren kaleed naroba yanata yawo”””
Tayi murmushi tace uwardakina babuwani kadangarefa narobane kawai na kaleed shikuma zai tsorataki??? Cikin tsoro tsoro tabude idonta taduba bataga komaiba saicen tahangoshi
Takurah masa ido”” tasaukarda ajiyar zuciya tace wlh tabawa biyana yaketayi cikin falon nan munata zagaye dashi””” tabawa tace kawaidai dankinsaka tsoronsa arankine kike ganin haka”” barikiga” tabawa takoma saitin kadangaren tana kallonsa “” tawuce aikuwa saiyabita”” tasaka hannu tadaukeshi tace kinganiko bawai yanabinki bane kawai haka na urarsa take tana aikine da inuwar mutum
Ameena tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya tace Amman ya akai kikasan haka tabawa??? Murmushi tayi tace uwardakina kinmanta nataba fadamaki nayi aiki gidan gomnan garin nan””????
Babu kalar kayan wasanda banagani awajen yayan matansa shiyasa nisam basa bani tsoro duk da wadan nan kayan basuda amfani”” dama wadan nanne wadanda alhji yake siyowa kaleed rakumi maiyin labbaikallahumma labbai”” ko wadan nan Na urorin masu addua duk Wanda” kadanna dakalar addua rda zaiyi tashiga bandakine kota fita gida dakuma ta fitowa bandaki
Haka wacce take da complete Qur’an kowace surah dakin danna tasoma karatu irin wannan ne yadace da yayanku tanan ne yaranku zasu iyah addu o.in neman tsari kuma su iya karatu idan sunabi ahankali Amman nagake Sam bakitaba kunnasuba saidai kullum kibarsa da macizai dakunamu”””” ameena tanisa hakika abunda tabawa tafada gaskiyane 
Tunfarko data nunawa kaleed son wadancen abun dabazaiso wadan nanba”” gashi yanzu yasaba dasu abune bai wahala yayarda akarbesu daga gareshi”” tabawa takatsemata tunani tace me za adorah uwar dakina????
Tace kiferah doya yau sakwara za ayi”” Ina ladidi batazoba yau”” ??? Tabawa tace wlh nabiyamata jikanta bashida lafiya saisama nayo saurii idan masu girkin safe basu tafiba juwaira saita tayani idan aikin yanada yawa
Ameena tace ina tunanin sunwuce Amman jeki kigani”” tace to sannan tawuce anan tabar ameena zaune takurawa kadangaren 

 Ido tana tunani duk da tanatsoronsa tanagani tamkar yana biyarta
Aikuwa kamar jirayake tabawa tabar wajen yayo wajenta “” cikin zafin nama tamike”” ta cakumeshi tayi waje””” sai kalle kalle takeyi”” wani katon dutse tadauko tayarda kadangaren tahau dukansa saida tayimasa”” raga raga batir da injinin sa duka sukafita dagajikinsa gefe takoma tana maida numfashi tamkar wacce taidanbe””” tayi tsayin mintuna biyar awajen sannan tatashi takoma cikin gida
Saiyanzu hankalinta yadan kwanta”” sama takoma tadauko wayarta tashige kitchen wajen tabawa
Karfe shabiyu akadauko kaleed daga skull tun abakin kofa yacikaro da gawar kadan garensa tuni yayi wurgi da jakarsa yasoma tattare kadangaren yana kuka
Yanda yake kukan harcikin gidan anajinsa cikin falon yashiga yanata kuka dakarfi tamkar Wanda akedukansa
Tabawa da Ameena kusan taresuka fito suna tambayar lafiya??? Ganinsa dauke da tarkacen gawar kadangare yasaka ameena taja tsakii cikin fada tace karufewa mutane baki””
Yace mom waye yakashemun adangalena??? Tace uwarkace akan wannan zakadameni dakuka maza kazubasu ashara ko inzaneka
Tsayinsa yayi tace bazaje kazubasuba saina hadaka kaida kadangaren nawatsaku Shara tayi maganar tanayowa wajensà
Yakwatsa ihu yayi waje dagudu yana nabani nabaniii gudu yake yana waigenta yaga kotakusa kamashi yanafita da itah da tabawa saida sukayi dariya
Danyanda yake kiran yabani kuma yanakuka yana waige sai abun yabaka dariya””tabawa ta tsagaita da dariyarta tace waiwaya kashemasa kaya??/
Tace nice wlh tabawa haka kurum Abu saitsoratani yakeyi idan baiyi hankaliba gabadaya kayan wasar wlh saina cinnamasu wuta
Kamar yasan inatsoron wannan shegen kadan garen”” kullum yana nan makale ajikinsa ainayi maganin abun tayi maganar tana shigewa kitchen tabawa Tamara mata baya””””
Kaleed kuwa wajen yakoma yayi zaune akasa yarungume kadan garensa yanata kuka””” yanasharar majina

Karfe biyu Alhji Usman yakunno hancin motarsa gidan ” idanuwansa suka sauka akan kaleed dayake kwance akasa yana barcii
Baikaiga inda ake aje motociba yatsaya yàfito dasaurii yatunkari indayake barciyake sai Jan ajiyar zuciya yakeyi alamar yasha kukaa

Aisha✍🏼

[3:51PM, 2/11/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 23

       By

Gentle Lady💃🏽

dukawa yayi yadaukeshi”” aikuwa yanajin antabashi ya zaburah yakwallah kara mom kiyi hankuli wlh inason adangalena””” idanuwansa arufe yake magana”” Usman yasharemasa hawaye yace bude idonka nine jin muryar dadyn sa yasaka yabude idonsa 
Yace yi shiru kadaina kuka wayadakeka”” ??? Yanajan ajiyar zuciya yana kuka ahankali”” yace mom ce takashemun adangale”” yayi maganar yana nuna masa””” yakalla yace toyi shiru bari kuka zansiya maka wani yaduka yadauki jakar makarantar da kaleed yayar yanufi cikin gida
Ameena tana cikin falo” taci kwalliya””cikin wani tsadadden less tahakimce saman kujerah tanajiyo maganarsa da kaleed suna shigowa tasha toka tadauke kanta gefe “” kaleed yanaganin haka yasake makalewa jikin dadyn sa””” Usman yalurah dahakan murmushi yayi sannan yayi sallama “” ta amsa kawai batasake cewa komaiba
Yace yaukuma mom hardani fushin akeyi dani ??? Yanda yayi magana batasan sanda tayi dariyaba saikuma tadaure fuska ta harari kaleed tace bance karkasake dawoda wannan shegen kadangaren gidan nanba??? 
Aikuwa yasake bare baki saida usman yarufe bakin yace yishiru sannan yakalleta yace waimeyasa mom yanzu kikacika fadane??? Dabahaka kikeba””
Tace hmm nidai kadaina cemun mom wlh dolensa yazubardashi ko inhado sauran kayan wasansa in cinnamasu wuta”” wannan kadangaren tsoratani kawai yakeyi wlh nayi danasanin siyensa””” 
Shiru yayi yana nazarinta sannan yamaida kallonsa wajen kaleed yace kaleed kaga mamanka tanajin tsoron wannan kadan garen kazubardashi shara kokanason mom tayi fushi dakai??/
Yayi sauri girgiza kai yace yauwa my son kaga itah tasiyomaka tunda yana bata tsoro aisaimu bashi kashi muyardashiko???/
Dariya yayi yace ah dady shima murmushi yayi sannan yasaukarda shi yace oya sheka kazubardashi shara”” yace to sannan yaruga dagudu Usman yakalleta yayi murmushi yazauna kusa da itah yace madam adan Samman murmushin mana”” wannan tamke fuskar yayi yawa kodai bakisan yanda kikai kyauba tamkar Amarya wacce za akaita gidan mijinta
Dariya ameena tasomayi tana jefansa dakallo mai tattarreda soda kauna”” 
Waje yakaishi saida yakarasa dandakesa sannan yawurga cikin kwandon Shara
 Dasauri yadawo cikin falon wajen Usman yakarasa yace dady nayardashi saida nasake masa bulala tunda yana olatamun mom
Usman yashafa kansa yana murmushi yace kabawa mom hakuri to yajuya wajenta yace mom kiyi hakuli “”ko kallonsa batayiba Usman yace kace Dan Allah bazansakeba yasake maimaita abunda Usman yace haryana kuka” yarike kunnensa kansa tashafa tace nahakurah Amman karkasake kansa yagyada to yajuya yace dad mom tahakurah””” 
Yadafa kansa Allah yamaka albarka”” yamike muje maza kacire kayan nan Tare suka Mike zuwa sama saida suka shirya sukasauko kasa sukaci abinci
Daren ranar mugayen mafarkai da ameena takeyi duk akan wannan kadangaren ne tanaganinsa yatashi yahade kansa” ranarma batasamu wani ishasshen barciba saida tayi sallar asuba
Bayan fitar Usman wajen aiki da tsoro tazauna cikin falon dazaran taji motsi takalla wajen dasauri”” idanuwanta sunasauka akan katon hotonsu dayake manne abangon falon saigani tayi suna motsi takesuka fara kyalkyatar dariya ba kakkautawa gabadaya suka cikamata kunne 
Hannuwa tasaka tarufe kunnenta tareda fashewa da kuka”” suma kamar hadin baki sukafara kuka aikuwa saigabaya hotunan dasuke falon kowanne yafashe dakuka
Kukan yacigaba daratsa dodon kunnenta kowanne cikin murya daban daban””” take tahada gumi awajen sallamar tabawace tasaka ameena tadago kantaa ganin halinda takeciki yasaka tabawa saurin karasawa wajenta tana tambayarta lafiya???
Cikin tsoro tace bakiji dariyaba ??? Wadancen hotunan suketa dariya saikuma sukafara kuka
Tabawa takalli hoton bataga komaiba tamaida hankalinta wajen TV dayake kunne tace to ai uwardakina cikin TV ake kukan
Inajin kinsaka tsorono aranki shiyasa kike ganin hakan dama babu amfani saka wadan nan hotunan bakisaniba mugayen aljanu sunasamun wajen zamane agida idan sukasamu hotuna agidan koda rukiya za ayi sukan labe ajikin photon tayanda bazasu fitaba 
Mizai hana kisaka na ayatul kursiyu aiyafi wadan nan””” hawaye ta share tace taimakamun incire hakan kuwa akayi duka tacire hotunan harna dakinta””
Wasa wasa ameena tasoma ramewà tana lalacewà dagatsaye abunyasomà damun Usman”” yayi tambayar duniya tafadamashi meke damunta tace bakomai 
Tanemi yakaita wajen dangin mahaifiyartà”” baikawo komai araiba yakaita bayan yayimatà tsaraba maiyawan gaske”” kwananta hudu acen yaturah driver yadaukota yan uwa sunata kewarta 
Gidansu akawuce da itah ranar tashafirah da malam haryake tambayarta meyake damuntaa””” duk tarame saidai tace masa bakomai”””
Sai dadare Usman yajedaukarta bayan isha I”” sunatafiya amota tanagefensa kaleed yajima dabarci”” takuramasa ido tana murmushi
Ya murmusa yana kallonta yace wannan kallofa Amarya kamardai bakisanniba??? 
Murmushi tayi tasanne kanta kasa tanawasa dayan yatsuntà””” Usman saijanta yakeyi dafirah harsuka kaigida””””

.bayan sunshirya sukaci abinci sukai shirin kwanciya sunraya wannan Daren fiyeda Daren amarciñsu
Sosai Usman yasamu yanda yakeso saikusan biyu sukai wanka suka kwantaa”””” karfe hudu darabii Usman yafarka agigice jin kiran sunansa DA ameena takeyi dasaurii yatashi yakunna wutar dakin abunda yagani yamatukar tayarmasa da hankali jinine yakefita tabaki da hancinta sare sare duk yabata zanen gadon”””

Aisha✍🏼

[10:35PM, 2/11/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 24

      By

Gentle Lady💃🏽

Cikin kidima yayi kan gadon yana girgizata yana kiran sunanta dakarfiii Amman ina ko motsi batayi””” 
Daukarta yayi kamar jaririya yafito gidan tacikin na urah yashigo zuwa kasa saboda yayi sauri tunkafin yasauka yasoma kwalawa driver kirah 
Cikin barcinsa yaji ana kiransa”” firgigita yafarka yafito dasauri yana ganin halinda alhaji yakeciki Yakoma dasauri yadauko key din mota riga ahannu yafito 
Haryanzu usman jijjiga ameena yakeyi idanuwansa sunyi jajir tamkar gauta kadan yarage yasoma darzar kuka saidai kawai danyana namijine yanada juriya”” tuni driver yabude masa bayan motar yashiga da itah shikuma yazagaya yafita dasauriii zuwa hospital”” 
Tunkafin sukai yakirah family doctor dinsu yasanar dashi yace yana asivitin dan yana dutyn dare ne”” sunakaiwa yanabakin asivitin tareda wadansu nurse tareda gado””” yanayin pkng yadaukota akaturahta saman gado zuwa emergency
Abakin kofa akabarshi Saikai kawo yakeyi tamkar yayi kuka”” tunda suka shiga da itah sukahau dubata saidai Ashe raiyayi halinsa”” zuciyarta ce tabuga!! 
Sosai yayi mamakin ciwon zuciya dahar yacita haka haryayi mata wannan illar Amman Sam shi baisan ciwon nata yakai hakanba”””
Jiki asanyaye yafito dakin tareda sauran nurse “” Usman yana ganinsa yasoma tambayar lafiyar meenal”” 
Doctor yajikinta ???? Tasamu saukiko???? Dan Allah zan iyah ganinta?? Banaso narasata doctor haka yayita jeromasa tambayoyi tamkar maitabin hankali
Gabadaya yabawa likitocin tausayi”” yace doctor bakace komaiba yajikin meenal din?? Yanisa yace tasamu sauki yadafashi saidai kayi hakuri Usman
Koda kukashigo asivitin nan tuni Allah yakarbi abarshi””” cikin razana yadago manyan idanuwansa yadorasu akan doctor din
Hannunsa yasaka yature hannun doctor dayake kan kafadarsa yayi cikin dakin dagudu doctor yabishi yana kiran sunansa
Yanaashiga yajaye kyallenda aka rufeta dashi fuskarta tayi fayau tamkar tana murmushi tayi haske dukawa yayi akan guiwarsa yariko hannunta cikin nashi
Cikin rawar murya yace yanzu dama tafiya zakiyi kibarni meenal duk wannan abun dakikemun na bankwanane take yafashe dakuka “””
Doctor ne yadafashi yace hakuri zakayi Usman lokacintane yayi babu magani saimuyi mata fatar Allah yajikanta yasa tahuta”” ayanzu adduarka kawai takebukata
Mikewa yayi yayi hanyar fita””” saidai yaji yarabke yafadiii dasauri yakarasa wajensa yanakiran nurse “” dagudu sukazo akadauki Usman akadorah akan gado take aka bashi taimakon gaggawa
Ganin yafarfado yasaka akajona mashi Karin ruwa tareda allurar barcii “” driver”” yana waje baisan halinda uban gidansa yake cikiba”” saida doctor yasanar dashi””” 
alokacin ansoma kiraye kirayen asuba” wayarsa doctor yadauko aka Kira hajiya akasanarda itah””” 
Karfe bakwai darabi yamata acikin kaduna tuni labari yakai gidansu ameena”” mahaifin Abdul da Abdul suna asivitin 

Tuni akadau gawar ameena zuwagida dangin ameena saidai sukaji mutuwar kamar dagasama
Koda yafarfado hajiya da Hafiz sunakusa dashi hawayene yasoma sauka gefen idanunshi hajiya tace sannu babangida”” 
Runtse idonsa yayi yace mom tatafi tabarniko??? Tashafo kansa tace addua zakaimata babangida lokacintane yayi”””
Yanisa inason ganinta kicewa Hafiz yakirah doctor”” takalli Hafiz tace yakirashi yace to tareda juyawa Abdul yadawo kusadashi yadafa kansa Amman yakasa cewa komai”” yana tausayin abokinsa danyasan yanason ameena sosai
Doctor yanazuwa yace badamuwa yana iyah zuwa”” taresuka fito suka dunguma”” saigidansu Ameena sunsamu har anyimata wanka””” Usman yamatsakusa da itah yayi mata addua tare akai mata sallah 
Tatara mutane sosai akakaita makwancinta””” Sam babu Wanda yatuna da kaleed saibayan da hajiya takoma gidan tasameshi yanata kuka sosai ta tausaya masa””” 
Saida akai sadakar uku kubra tazo tareda mijinta”” itakanta tasha kuka datasamu labarin”” Usman yakoma shiru shiru dagashi har kaleed sunrame danbasacin abinci sai hajiya tayi dagaske
Bayan wata biyu darasuwar Ameena zuwa yanzu Usman yafauwalawa Allah lamarinsà”” Yakoma wajen harkokinsa Amman haryanzu baikoma daidaiba
Hajiya takoma tareda kaleed hannunta saboda haryanzu yaki kwantarda hankalinsa”””
Kwance take tanajuyi cikin barcinta”” zunbur tatashi “” tasoma dube dube mafarkinda tayi kamar almara”””ihun murna tayi tamike yauzataga handsome dinta towadanne irin kayama zatasaka tarasa inda zatasaka ranta danjin dadi
Mikewa tayi tafada wanka”” agurguje tayi wanka tashirya cikin atamfa takawo hijabinta tasaka harkasa””” 
Wayarta kawai tadauka tafita unguwar kowa yayi mamakin ganinta da hijabi akafa take tafiya tayi nisa da unguwarsu sosai wata motace tayo cikinta sauran kadan tabugeta tayi gefe dasaurii Amman dukda haka saida yasameta aikuwa tafadiii kiiii yatsaida motarsa yafito dasauriii dasauriii yana furta innalillahi tadago takalleshi tuni tawashe hakorah tunawa dazancen *hatsabibin boka* yasa tayisaurin dukadda kanta gabanta nafaduwa
Muryansa maisanyice taratsa dodon kunnenta sannuko inafatardài bakiji rauniba??? Kaitagyada masa tamike tana karkabe hijabinta”” yakuramata ido takeyaji Sonta yashiga ransa talurah da irin kallondà yakematà dadi kamar tafasa ihu arantakuwa tana aiyanawa ashema yafi kyau afili

Aisha✍🏼

[12:20AM, 2/12/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 25

      By

Gentle Lady💃🏽

Muryansa tasake katsemata tunani yace inazakije yanzu??? Cikin sanyin murya tace mamana ta aikeni inyomata cefane”” yayi murmushi yace to idan bazaki damuba muje mana kisiyo daganan sainakaiki gida nabada hakuri 
Tadan waro ido tace hakurin mezaka bayar nifa banji ciwoba”” yasake gyara tsayuwarsa yace duk dahaka sainakaiki gida daganan sainaga waje aiko ??kobakyaso zumuncin mu yadorene?? nalurah kinaso kidatseshi iyah nan””
Munmushine ya subuce akan fuskarta tace waceni aiban isah ba Amman naga kaima kanada uzuri kawai kabarshi nagode zanhau Dan adaidaita”” harararta yayi cikin wasa yace tozanga yanda zakihau Dan adaidaita gani kusa ashekuwa yau akwai rigima
Tace la abunfa duk baikai hakaba”” nayarda muje Amman idan mukaje unguwarmu nesa dagida zaka ajeni”” yace najidai muje 
Dakansa yabude mata gaban mota sukashiga yaja yasoma tafiya kifa nunamun wajenda akesiyarda kayan miyan”” batareda takalleshiba tace kana cikin legos kace bakasan inda ake siyarda kayan miyaba”””
Murmushi yasaki yace ashekuwa yauzamuyi tayayo agari idan harsaini zan kaimu wajen”nida nake bako saiyanzu takalleshi tace wai dagaske kake???? Yace todakumafa nayimaki kamada yan Lagos???? 

Tace ausu yan legos harwata kamane dasu???? 
Yace sosai aidakingansu zakiganesu kullum suna sanye da dangakallun kaya”” sannan Kuma basada Faraa gadukkan alamu kema ba yarnan dinbace””tace ya akai kasanhaka??? Yace dabi unki mana”” ke komainakima so nice
Murmushi tayi maidan sautiii tace kaidai wlh kafaye zolaya!” Sunakawowa daidai wata kwana tace nan zakabi””” tayita nunamasa hanya harsuka kawo 
Karyafa tasheramasa dankuwa bata tabazuwa siyen kayan miyaba”” toyanzu idanma tafita batafitoda ko asiba”” karfa asirinta yatonu yagano karya tashekamasa jitayi yabude mota””” zatafita yayi saurin dakatarda itah yace dame dame za asiyo??? Cikin rawar murya tace komaima
Kaitsaye yawuce wajen maikayan miyan dayake inyamurine yace yahadamasa kayan miya”” na dubu biyar komai ahada””” 
Nankuwa akahada komai harda cucumber da kabeji dasu carrot” saida yanuna mata yace dubakiga ko akwai abunda babu asiyo”” tace komai akwai sannan akazuba bayan but sukakoma 
Tace kayan miyanfa sunyi yawa”” yace to kibawa wani idan sunyimaki yawa”” kidai nunamana hanya karmu bace””
Dariya tasoma kai malam akwaika daban dariya wlh”” takasan ido yake kallonta tana matukar burgeshi sosai”” yace basunana malam ba sunana Usman”
Ido tawaro tace sunan uncle dina”” yace dagaske kenan nima nazama uncle” dinki””” tace sosaima

Yanda sukeyin firah hankali kwance idan kagansu saika dauka sundade dasanin juna”””
Suna kawowa unguwarsu tace ajeni nan zankarasa”dakafa

Batareda yakalletaba yace babu amfanin zuwan nawa kenan tunda banga gidaba””” 
Ahakan tanuna masa gidansu””” yayi hon maigadi yahangame masa kofa yakutsa kan motarsa kamar wani dangida””” bayan yatsaya da motar”” yajuyo yana fuskan tarta yace gashi harmunkawo Amman bakifadamun sunankiba”””
Naga abun yar rowar sunace””murmushi tayi taboye fuskarta cikin hijabi tace sorry aiban isah nayiwa uncle rowar sunanaba”””
Yamurmusa yace nifa banyarda da uncle din nanba”’ tarausayarda kai tace saime???? Yace aboki daganan kuma saiyayi shiru yana kallonta yanadariya kasa kasa
Murmushi tasakeyi tace bari nashiga gida kar mom taga nadade””” yaduba agogon hannunsa yace shikenan ataimaka abani phone no”””

Wayarsa yamika mata afuskar wayar PIC dinsane da Ameena kaleed yana tsakiya””” talurah da pic din saikawai tawuceshi tasaka masa Tamika masa 

Tace katsaya koruwa kasha””” ah ah inasaurine wlh akwai abunda nazoyi gobema zankoma Amman zansake zuwa gobe saimu gaisa”” 
Tabude motar tafita”” kayan miyar yafitomata dasu tabawa maigyaran fulawa tace yashiga dasu cikin gidan
Sukai sallama tasake masa godiya tawuce yace amm jimana”” tajuyo ciikin wani salo Wanda yakusa sumarda Usman da ido tamasa akamar menene??? Yace sunan???/
Tadan dafe kai sorry namanta lubabatu tanafadàr maganar tayicikin gidan Usman yabita da murmushi wani sanyi””yaji yanaratsa dukkan sassan jikinsa rabonsa dayaji farinciki haka tunranarda meenal tabar duniya 
Murmushi yayi yashiga motarsa akabude masa get yafita Sam baiso zuwa legos dinba Ashe arzikine yake kiransa aransa yake ayyana hakan
Tanashiga tasamu mom dinta tanadubà kayan miya””” tanaganinta tace lubcy wadan nan kayanfa??? Batareda takalletaba tace kiyi amfani dasu wanine yasiyamun tawuce bangarenta
Mom dinta tajidàdi aranta tana adduar Allah yasa saurayintañe dantamatsu lubcy tayi aure
Tanashiga daki tacire hijab tawurga akan gado tasoma tikar rawa tana murna harda ihu wayartace tasoma ringing tadauko dasaurii ganin sabuwar nomber tasan shine takidagàwa hartayanke akasake kirah batadaukàba saida yasake kirah tadauka cikin yanga kamar yanaganinta ta amsa sallamarsa sannan tace waye

Aisha✍🏼

[8:23AM, 2/12/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 26

       By

Gentle Lady💃🏽

Murmushi yasaki maidan sautiii yace nashiga tara yanzun har ammanta dani ba aje ko inaba anya kinason zumuncin nan yadaure kuwa”””
Gabantane yafadi karfa garin jan ajinta ta lalata komai””” tayi saurin taran numfashinsa tace bahaka bane uncle kaga aibansan nomber nakaba kuma kasan waya yana sauyawa mutane murya dat way banganekaba!! Amman kayi hakuri
Ajiyar zuciya yasaukar wacce har lubcy tajiyota yace najisanyi araina”” itama murmushin tayi”” sukataba firah daganan sukai sallama 
Lubcy tamkar tazuba ruwa akasa tasha Dan Murna”dole”yau taturàwa *hatsabibin boka* kayan aiki nagodiyà!”””

 daren da itah dashi kasa barci sukayi kowa yana tunanin dayansa Usman jiyake tamkar kirjinsa yafaso zuciyarsa tafito saboda tsabarso nda yakeji nata yanahudashi”””
Kwance take cikin dakinta tana danne danne dawaya saiga kiran Usman yashigo”” da murmushi tadaga tareda sallama daya bangaren ya amsa”” 
Yace gani akofar gida”” tawaro ido harkazo??? Harararta yayi kamar tana ganinsa yace dolekice harnazo danke bakidamu da niba nida nadamu dake darenjiya kasa barci nayi”””
Tarike baki yihakuri uncle bawai haka nake nufiba ganinan fitowa”” takashe wayar akahau safe safe da feshe feshe saigata tafito das da itah tasaka hijabinta tafita””” mom dinta tanacikin falo zaune tace mom nayi bako kibawa kande kayansha takaemasa muna falon bakiii
Tawuce abunta” yanajingije jikin motarsa yakurawa kofar gidan ido yanaso kawai yaga bullowarta”” kirjinsa sai harbawa yakeyi dasauri dasauri yakuramata ido yanda take tafiya tamkar hawainiya komai nata tsaf
Kamar yanda yaraja.a akallonta itama haka shigarta yau Tayimasa kyau yau kananun kayane ajikinsa sabanin jiya dayasa manyan kaya idan kaganshi wlh koda anrantsemaka bazaka yarda yatabayin aureba sai idan kaganshi da matar kakuma tabbatar lallai itace 
Damurmushi takaraso inda yake tagaidashi”” tace karaso ciki sukajerah harcikin falon bakin”” tazauna nesa dashi suka gaisa””” yace badadewa zanyiba zuwanayi kawai mugaisa zanwuce
Sam bataji dadiba Dan fuskar tama. Tanuna hakan cikin sanyin murya tace sai yaushe kenan?? Nasan dakyarne idan zakasake dawowa legos tunda bawajen zuwanka bane
Yayi murmushi yanawasa da key din motarsa yace zancen baya kikeyi aiyanzu zuwa legos yazama dole dankuwa nayi babbar mantuwa acikinta
Tace mantuwa?? togashi baka fitaba kakoma kadauko mana”” murmushi yasaki maidan sautiii yace kinaso ayimun ihu ace nasaci abunda banawaba!! zandauka Amman bayanzu zanjirah har abun yaxama mallakina
Tace inamaka fatan alkhairi””yace nagode daidai mai aikinsu tashigo dauke datire cike dakayan motsabaki na marmari dakuma danbun nama”” saida ta aje taduka tagaisheshi “”” 
Ya amsa cikin skin fuska”” zatafita yakirata kudii yaxaro cikin aljihunsa zasukai dubu goma yabata”” taki karba saida yamatsa mata sannan takarba tayi godiya””
Bayan tafita bajimawa yaduba agogo yace yakamata intashi haka”” karnayi dare ahanya”” gashikuma ban gabatar maki dakainaba”” 
Nasandai bakimanta sunanaba”” inaxaune a kaduna yanzu haka anan nake tafiyarda harkokina Amman iyayena akano sukeda zama 
Mahaifina Allah yamasa rasuwa inada kanne biyu kubra tayi aure sai Hafiz nataba aure karkiyi tunanin ni saurayine fuskarsa cikin murmushi yafurta hakan””
Yanisa Amman Allah yadauki abarsa tatafi tabarni dayarona daya kaleed tuni idanuwansa suka koma jajaye yace inasonsa sosai fiye dakomai arayuwa banajin zanso wani Abu samadashi 
Idan naganshi yana debemun kewar meenal azuciyata”” banason abunda zaitabashi komai kankantar abun” wlh lubcy yaron tausayi yakebani 
Yanzun yana hannun mahaifiyata “” inason narikajiñ dimin jikinsa akusa dani nasan mom bazata banishiba tunda bansan yanda zanrika kuladashiba aganinta zanraba hankalina gida biyu
Shine nakeson nayi aure” kozansamu wacce zatakula damu dannikaina inabukatar kulawar””” yadago yakalleta yace kinji takai taccen tarihina aranta tace duk nasan wannan”””
Afilikuwa tace Allah sarki Allah yajikanta””” yace Ameen toyanzu mekikace??? Tadanyi yake tace nikuma mezance???? Yasake gyara zamansa yace tomenene amfanin sanardake tarihina???
Takada kafada maybe kasanar danine as ur friend””” “”” yace ya inatubka kina warwarewa”” dariya takwacemata ganin yanda yayi maganar
Yace dolekimuñ dariya danbakyajin abunda nakeji gamedake””basaina tsaya kwanakwanaba agaskiya lubabatu tunda naganki naji nakamu dasonki 
Sobana wasaba””” kuma aurenki zanyi bansaniba kozaki iyah aurena amatsayina nawanda yataba yin aure yakai karshen maganar yana kallon fuskarta
Tadanyi Jim yace please lubcy”” tarausayarda kai tace tokabani lokaci inyi shawara”” yayi saurin tarar numfashinta yace yanada kyau hakan amman nanda gobeko????
Tawaro ido gobe kuma??? Nanda satidaya dai”” bakiyabude cikin mamaki yace um lallai dasaurana bansamu shigàba””bari nasamu wajen zama a legos
Dariya tasoma tanarufe bakinta tace lala nina isah nafurta hakan ayihakuri to abani nanda kwana uku”” yace biyudai koshidai sainakai zuciyatà nesa danzata iya bugawa!! tace to abarshi biyun

.

Yace yauwa amman please karkice baxaki aurenibà”!! Danzan iyah shigawani halin”” tayi murmushi saidai kajini kasha lemun mana tayimagana tareda nunamasa tirenda kedauke dakayan marmari””” 
Yace banajin zan iyah cin wani Abu harsainaji matsayina yayi maganar yanamikewa”” tace Amman kasandai banji dadiba acekayi bako koruwan gidanku baishaba
Ahakan nasan iyah matsayinà”” yace yihakuri kinsan bansan yanda akeyin zancenba Ashe idan kazo dole kasharuwa
Zansha Amman bayanzuba sainasañ matsayiña

Aisha✍🏼

[9:39AM, 2/12/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 27

      By

Gentle Lady💃🏽

Tace shikenan”” saimunyi wayako”” yace ah Amman aizakimun rakiyaba ko anan zakibarni kamar saniyar ware??? 
Dariya tayi kai wlh kacika sa mutum dariya mujeto”” yace tofa dagayanzu kuka zanrika sa mutane.
Nidai banceba baban kaleed””” sosai yaji dadin sunanda takirashi dashi har farincikinsa yakasa boyuwa yace nagodefa” daidaii get din gidansu tamasa sallama takoma gida”” 
Yabawa maigadi kayanda yasiyo mata yace yakaimata cikin gida sannan shima akabashi dubu goma”” zokuga bakinsa harkunne saikirari yakewa Usman shikam saidai yace kara da akayi
Cikin gidan yashiga dasauri yana sallama niki niki dakaya”” ya aje gaban mom yace uwar dakina gashi inji alhaji”” takai bakin kofar dakinta tace barsu wajen mom tayi shigewarta
Mom tabita dakallo aranta tace anya lubabatu batada aljanu??? Koda tafita gidan nan tana fara a Amman tadawo fuska yakunai yakunai kamar lawashin albasa”” idan yakwana
Maigadine yakatsemata tunaninta yace yaunashiga uku uwardakina tana nema tamun bakinciki yanzun wannan Dan zinariyar tana nufin baiyimataba???.
Hajiyarce tace wayafada maka ado?? Kaidai bakagani saika maganta tashi katafiii”” yace toya za ayi hajiya wayaki alhairi”” dubu gomafa tashi daya wlh hajiya kingansu a aljihuna yayi maganar yana bubbuga aljihunsa yacigaba tunda nake samartakata kawowa yanzu babu Wanda yataba mun kyautar dubu goma
Keko dubu biyu ma duka alhazan dasuke zuwa wajenta shegiyar rowa tayimasu kanta aduwawu babuwanda yajeso yacire naira yabawani””” 
Amman wannan tunda naganshi nasan Dan albarkane””🤓 Dan Allah hajiya kirarrasheta kartace batasonshi 
Dama inada kwadayin dakwalen kajii kafin ayi auren na murmure”tace ado fisabilillahi kakoma wajen aikinka waikai meyasane kafaye shegen surutune uwa aku”””
Yace saihakuri hajiya sai hakurii”” matsalarda akasamu kenan”” ranarda aka haifeni gidanmu anataron biki wannan hayaniyar tayan bukiii haya haya sanadinta tatakulo nakuda nayowaje
Ashe surutun yanbikin yataba kakwalwata tun ina jariri idan nasoma dariya ina witsil witsil sai abun yabaki tsoro”” 
Yanbarka kowayazo saboda dariya sai yayi hawaye babana yakaini wajen likita yana tsammanin haukace takamani koda likita ya aunani yagano inada dauke da ciwon surutu kuma babu maganinsa harsaina cinye kaza Dari
Tunda aka haifeni zuwa yanxu inakan lissafi naci kaxa ashirin dabiyar hargamida ta amarcina kinga koyanzu akwai sauran 75 tukuna inwarke
Hajiya tace aikuwa baburanar dazaka warke dawannan surutun”” yace dainamun wannan fatar hajia kina raina surutuna kinsanfa magana jarice inaji ajikina dawannan surutun nawa zanyi arziki
Tace ahakan? Aiwannan surutun bayan duka babu abunda zaijamaka”” aisaidai yajamaka tsiya”” um um hajiya raina kamafa kaga gayya”” inamai tabbatar maki sainayi govno agarin nan
Hajiya batasan sanda takwashe da dariya “” auwal ne yadawo yayan lubcy yanata faman hon yaji shiru afusace yafito zuwa cikin gidan 
Yace haba ado waikai saiyaushe zaka daina wannan surutun Mara amfani nayi minti goma inabuga hon Amman kananan kanazuba
Yace haba maigida toyazanyi banjikabane kasan bakyau akunkume baki saiyayi duyi””😆
Hajiya tanadariya tace waifa cewa yayi saiyayi governor agarin nan akan surutunsa”” auwal yaharareshi yace Na mahaukataba
Ai wannan nangaba gadinma saiyarasashi “” yawuce fuuu kazokuma kabudemun kofa”” ado yawuce yana ta zuba ganinan zuwa karka gididdibani gida gida
Lubcy tanashiga dakinta tayi wurgi dahijab tacije danyatsa tanakasa tanadabo kenan “”” asheni banyi komaiba
Dasake wlh kenan yafison dansa akaina???zai aurenine dannakula dayaronsa”!! Babbar magana nasan muddin yaron yanaraye lallai bazansàmu wata soyayya awajensaba
Zairaba soyayyarsa gida biyune”” ina bazaitaba yiyuwaba dole naga *hatsabibin boka* yaudin nan Saikai kawotake acikin dakinta tanajiyo hirar ado da hajiya taja tsakii mstw surutun ado haushi yakebata idanyana magana bakinsa harkunfa yakeyi
Tana zaune saman kujerah tana tunanin maganar Usman saigakiràñsa yashigo”” tadauka sukagaisa yakesanarda itah yakai  
Tayimasa sannu Allah yahutarda gajiya”basujima suna firaba yamata sallama yace ansoma kiran magrib zaiwuce masallaci sukai sallama yakashe wayar sake mikewa tayi akan kujerah batajima dakwanciyaba barci yadauketà
Momdinta tashigo tasameta tanabarci saitafita karfe daya tafarkà taje tawanko idontà tadawo lokar kayantà tabuda tadauko karamin akwatin tabude tadauko madubin yana nan”” yanda ta ajeshi
Saman gado tazauna tasahanñu tashafiii madubin tareda kiran sunan *hatsabibiñ boka* sau uku saigawani haske yashiga tacikin madubin saigashi yawashe *hatsabibin boka* yabayyana samañ kujeràrsa
Cikin damuwa tace akwai Matsala sarkin bokayen duniya haryanzu tanakasa tanadabo””” yace yakikeso ayimasa??? Bataredà fargabar komaiba tace aturashi wajen mamarsa aganina zaifisàmun kwanciyar hankali darayuwa ataredani

.inaso gabadaya danginsa sumanta dashi sukuma mantada mahaifiyarsa
Inaso Usman yaji aransa baitaba haduwa dawata diyamaceba saini aciremasa son kowa adasa nawa”””
*hatsabibin boka* yakeceda wata hatsabibiyàr dariya yace angama lubcy jeki kikwanta abunki kafin nandakwana 2 angama komai
Bakaken aljanu sunagaisheki sunyaba dajininda kika aikomasu kamar walkiya hasken yafita daga madubin boka yabace tamkar walkiya.
Lubcy tamaida madubin cikin jindadin bukatàrta tabiya takoma saman gado tayidaidai tañabarçiñta cikin kwanciyàr hankali.

Aisha✍🏼

[1:02PM, 2/12/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 28

       By

Gentle Lady💃🏽

Bayan kwana biyu kamar yanda sukai da Usman saigashi yakirata”” cikin zumudi tadauka cikin rausaya”
Tace aminci yatabbata agareka annurin zuciyata”” wani sanyine yaràtsa sassan jikinsa yalumshe idonsa sannan yabude
Yace taredake ma abociya sassanyar murya
Dafatar kina lafiya??? Tasake rausayarda kai qalau nake tareda tarin dinbin soyayyarka
Yace wow Amman najidadin hakan sosai abisa dukkan alamu tarkona yakama tsuntsu
kanta tagyada tace aitunima “” yace Amman shine baki sanar daniba kikabarni inata shawagi duniyarda bakowa acikinta saitarin furanni da ababen more rayuwa. Tace to aikuwa hankali kwance tunda kasamu jindadi aduniyar 
Yace kisani bazasu burgeniba matukar babu tauraruwa acikinta”” 
Zuciyata tayita jiran bakuwar soyayya wacce zata tallafeta zuciyata tazama fanko bakomai acikinta tana bukatar abokin zamanee
Cikin zolaya tace to ai akwai kaleed”” gakuma marganyiya mamarsa”” shiru yayi kamar maison tunawani Abu daga bisani yace makotanku suke??? Cikin rashin fahimta tace suwaye??? 
Yace kaleed danaji kin ambata mana”” takyalkyale da dariya tace kainifa danka nake magana akai””
Yace danakuma??? Wanda zakihaifamun inmunyi aure??? Tace dankadai nayanzu yace Wayafadamaki inada da??? Yaushe harnayi auren dazan haifi da??? Wani sanyine yaratsa zuciyarta lallai boka yagama aiki saitace bakaine kasanardaniba kanada yaro mamansa tamutu
Dariya yayi haryana rike ciki yace badainiba abunda nafadamaki kawai nacemaki nataba aure Amman fa ba azahiriba cikin mafarki mukai auren kuma munyi soyayya doguwa da itah Amman bata haihuba saitarasu tanarasuwa nafarka abarci wlh yanzu ko kamanninta bazan iyah kawomakiba kingakuwa shirmene
Tasake shekewa da dariya tace hakane” yace yanzu idan kin amince zansanarda mamana anemamun aurenki 
Dannagaji dazama gauro abokina yayi aure nibanyiba nasan rashin auren ne yasaka naketa mafarkin nataba aure tace shikenan zan sanarda dad komai yace zakaji bayani yace yauwa tawan
Sunkwashe tsayin wata daya sunabuga soyayya usman yamaida legos tamkar dakin kwanansa bayawuce kwana biyu baijeba
Yasaba da ado maigadi sosai lubcy tagabatardashi ga mahaifinta a matsayin wanda zata aurah tasanardasu saurayine baitaba aureba
Baban lubcy yace yaturo magabatansa”” ranarda lubcy tasanar dashi ranar yayiwa kano tsinke”” tunda mom taganshi sai fara a yakeyi sunazaune cikin falo yatankashe kafarsa kasa yanashan kankana
Hafiz yana saman kujerah yanabuga game hajiya tace wainikuwa babangida wanne irin farinciki kakeciki nagatundazu saiwasar hakorah kakeyi???
Yasaka kankana cikin bakinsa yace hmmm mom albishirinki”” tace goro fari tasss tana gyara zamanta”” Allah yasa alkhairine
Yasake murmusawa yasosa kansa yace sosaima “” tace tofadamun inji”” yace nasamo maki suruka mom Allah yakarbi adduarki nasamu wacce nakeso
Aikuwa hajiya tarangada guda kai Amman najidadin wannan labari haba kokaifa duka abokanka sunyi aure Amman kai katsaya ganin garii inason nima insamu jika 
Yasunan surukar tawa??? Yana murmushi maikunshe dajindadi yace lubabatu saiyanzu Hafiz yayi magana yace Allah yasanya alkhairi
Suka amsa da Ameen”” aikuwa hajiya tasanarda abokan mahaifinsa kasancewar yan uwan babansa bakusa sukeba”” Dan asalinsu buzayen Niger ne””
Cikin satii daya akagama komai anbiya sadaki dakudin angani anaso”” akasa bikin nanda wata daya””” ranar lubcy tasiye dabbobi guda goma ta aikawa *hatsabibin boka*
Usman dakansa yaje Dubai yahadomata lefe Wanda ya amsa sunan lefe akwati talatin kowanne akwatin shake yakeda kaya sannan dasabuwar mota hul duk acikin lefen
Lubcy saida tahada gagarumin farty gabadaya kawayenta sadiya.aneesa.rabiatu.larai.sajida”” suma saida kowaccensu tazo datata tawagar kawayen awani babban hotel sukayi fartyn kowannensu saida yagirgiza daganin kayanda akadirkowa lubcy amatsayin lefe
Ranar sun gwangwaje sosai saikusan magrib suka watse””
Cikin watadaya lubcy da Usman tamkar suhadiye Kansu Abdul ma saubiyu Usman yana zuwa dashi wajenta
Biki yakarato kowanne bangare sai shirye shirye ake kubra matazo da dankaramin cikinta ansoma hidimomi Usman yagyare gidansa an sake komai kuma anyisabon fenti
Bangaren lubcy kusan sati biyu sukayi suna program event itakanta tasan takere sa a ta auri mijin nunawa sa a
Bikinsu Na gogaggun yan boko ko ince yankarya Dan yanboko akwai karya kankanba danuna sudin wata tsiyane 
Ranar lahadi dubban jama a suka shaida daurin auren lubabatu da Usman akan sadaki million 1 

Karfe uku motochin Amarya sukadauki Amarya zuwa kano wajen mahaifiyar

Usman yankai Amarya censukà kwana tareda kawayenta
Washe garii akawuce da itah dakinta ai kawayenta basu tsureba saida sukayi arbada aljannar duniya acewarsu 
Dan babuce kawai babu acikiñ wannan katafareñ gidan kowa sai santin gidan yakeyi saidare akawatse akabar amarya
Daren Usman ya angonce zokuga ririta tamkar zaimiyarda itah ciki sosai takemasa ladabi hartakan mantar dàshi kowa muddin yanatare da itah
Bayan wadansu watanni lubcy tafara gajiya dabukatarsà saitatsiri ciwon karya kofashin sallah”” lokacinne kubra tahaihu mace akasamata suna bilkisu hidimar kwana biyu tasaka lubcy tadan sarara

Aisha✍🏼

[9:49AM, 2/14/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 29

        By

Gentle Lady💃🏽

Bayan wata uku lubcy tafara laulayin ciki ranarda doctor yasanardashi tanadauke daciki zokuga murna daga hajiya har Usman tamkar suhadiyeta tuni labari yakai wajen kubra
Takirata tatayata murna taimata fatan sauka lafiya cikin sosai yake wahalda ita gakuma yawan kwadayi kamar manya”” 
Aikin komai tadainayi acikin gidan saidai taci takwanta saikuma Usman yasake manne mata da lakuwa kamar danyaye”” 
Cikin yana shiga wata Tara kafafuwanta suka kunburah komai bata iya yikobanza gatada sonjiki sai akagamu akadace 
Ranarda nakuda takamata akadauketa sai hospital tasha wuya Amman haihuwa tayi tsayinta gashikuma tagalabaita
Likita yace dole Usman yasaka hannu aimata aiki aciro yaron domin dan cikin yawahala tareda mahaifiyarsa “” Usman hankalinsa yayi matukar tashi
Saida doctor ya rarrasheshi yasaka hannu akashiga da itah dakin tiyata akaciro kyakkyawar beby maikamada Usman sak tamkar yayi kaki yatofar
Bayan anyimata dinki aka kaita dakin Hutu”” sosai Usman yakejin son jaririyar harcikin ransa take yadauki waya yasanarda hajiya da Abdul da kubrah yakirah gidansu lubcy yasanar
Ranar duka sukazo saigashi ancika asiviti makil damasu dubiya har makotanta saboda tanada mutane sosai”” satinta daya sannan aka sallameta kaitsaye Lagos akawuce da itah”” aikuwa Usman yamaida Lagos garinsu kullum yana zaryar hanya
Anasaurah kwana biyu biki kubra tazo””” sosai sukejida yarinyar ranar suna akaradamata suna labila
Usman gida biyu yakasa kansa”” bayawajen aiki baya Lagos aikuwa tanayin arba in akahadota tadawo
Sosai tadan huta da jarabar Usman kwana biyu Amman ranar taraina kanta dankuwa saida yafanshi nakwana arba in datayi basatare danyagaji iyakar makurah
Labila tayi wayonta sosai ko ina tanazuwa tanada shekara daya dawata bakwai aka yayeta”” lubcy batasake samun cikiba saida labila tacika shekara uku
Shima wajen haihuwa saida aka fasata saboda wahalarda tasha yaron yamutu cikin ciki”” tunlokacin batasake samun cikiba
Saida labila tacika shekara goma”” sannan tasamu ciki shima hallau tiyatarsa akai mata tace ajuye mata mahaifa dantagaji Amman badasanin Usman ba””
Katon danda akaciro mata shima kyakkyawa Amman labila tafishi kyau Dan ita ta fidebo kamannin mahaifinta””ranar suna akasa masa suna abdul-majeed sunakiransa majeed
Yana isah yaye tayayeshi domain sun shirya wata tafiya tareda kawayenta “” tatambayi Usman duk da badason ransaba Amman bazai iyah musamataba ita tadauki nauyin tafiyar har aje adawo
Sukayi shirye shiryensu ranar talata jirginsu yadaga zuwa charo satinsu biyu acen usman yadameta da azarbabi yace wlh tadawo hakanan badan tasoba dandama gudun hijirane taimasa tadan huta
Ranarda sukadawo tsautsayi ya afkamasu akan hanya dukkansu sunji ciwo sosai bakamar lubcy dangaba gareta yaji chiwo sai alokacin akalurah dakarinda kejikinta yagirma tamkar bishiyar kuka haryazubarda Yaya
Shiyasa batason Usman yakusanceta likitoci suka tabbatar sai anyimata aiki kuma Karin babbane danhaka zatafara dashan magani
Usman kamar yayi kuka danyasan tashi takare dankuwa likita yace karya kusanceta saida suka kwashe watadaya hardasati sannan suka murmure Tass alokacin Duk hankurin Usman yakare
Kawai yafada Neman auren wata suwaiba acikin kaduna take sosai sukeson junansu yasanarda hajiya bata tambayeshi daliliba tunda tasan yanada halin yin auren
 Tadaimasa nasiha akan yakwatanta adalci cikin sati biyu akagama komai harlefe Amman yakasa sanarda lubcy
Dankunya yakeji yazata dauki maganar kenan baigodeba duk da hakurin datakeyi dashi danyanzu matsala tasameta zaigujeta kumashi Sam baida burin hakan
Zaune yakecikin falonsa yana tunani wayar sa tasoma ringing kamar bazai dagaba saikuma yadauko cikin sauri yadauka danharta katse an sake Kira hajiya ce yadauka tareeda sallama ta amsa”” yagaida itah cikin ladabi ta amsa tace ina yaransuke
Yagyara zamansa yace suna islamiyya tace hakane Sam na sha afa yaune asabar mamansufa????
Yace inatunanin barci takeyi”” tace toyajikinta??? Yace todasauki za ace”” Hafiz yana gida?? Tace yanzun nan Na aikeshi wlh
Dama kiranka nai insanarmaka kamar yanda kabukata ansaka bikin sati biyu “” yasaki fara a kai alhamdulillahi Amman najidadi
Tanisa Allah yasanya alkhairi yace Ameen tace babangida”” yace Na am tareda saita natsuwarsa tace inafatardai kasanarda lubabatu batun aurenka???
Shiru yayi yanasosa kai kamar munafuki yayi karya””” tace shirunka yanuna kenan baka fadamataba
Cikin kunya yace ah hajiya wlh nakasa tunkararta da maganar kayanda nazodasuma suna falon baki na aje dazaran naso sanarda itah sainaji tabani tausayi
Hajiya tace totunda tausayi takebaka kafasa auren mana”” idanuwansa ya kwalalo aransa yace kice inmutu kenan””
Cikin zuciya yayi maganar baisan tafito filiba hajiya tace wacce irin mutuwa duk wadanda suke zaune damata daya kaga sun mutune??
Yayi shirudai aransa yace hajiya bakisan halinda nake cikiba””” tace totunda har kaidin bazaka iyah hakuraba yazamar maka dole kasanarda matarka
Amman muddin karufemata harsai randaurin aure kokuma taji ashanun tallah tokuwa liki za atono

Aisha✍🏼

[10:00AM, 2/14/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 30

      By

Gentle Lady💃🏽

Yanisa shikenan hajia zansanar da itah “” tace yauwa kokaifa ai boye boye bashida wani alfanu ansan kowa yanada kishi Amman hakuri zatayi ai tunda mijinta yanada bukatar kari
Yace zanfadamata insha Allah tace hakan yayi sunjima suna firah sannan sukai sallama yayi shiru yana kallon wayarsa shikam gabansa sai faduwa yakeyi 
Mikewa yayi yasauko dakinsa”” hawayayi zuwa bangarenta cikin falo yasameta kwance remote ahannunta tana cenza tasha tana ganinsa tamike da fara a
Alhaji Kaine dakanka bayan kakirani inzo”” yayi murmushi bakomai aigani nazo yayi maganar yanasamun wajen zama kusa da itah
Yace hutawa akeyi”” tace ah wlh kafin majeed yadawo kasanshi akwai Rigima jiya da dare damuna yayi dakuka kamar karamin yaro
Yace todakumafa haryanzu bakimasa kaniba aidole yayi sakuwa dar taji agabanta Sam tama manta da anjuyemata mahaifa Kuma bazatayarda wani tsautsayi yasaka tasanarda Usman hakaba 
Dantalurah sosai yana mutuwar son yara gashi biyune kawai da itah” yakatsemata shirun tahanyar kiran sunanta
Datago ta amsa cikin fara a”” yanisa dama akwai maganarda nakeson yidake”” tadanyi shiru sannan tagyara zamanta dandama kishingide take gahannun kujera
Takalleshi inajinka alhaji”” yadanyi jim sannan yace kafin nacekomai inamai baki hakuri akan abunda zanfurta maki nasan bazakiji dadiba Amman kiyi hakuri wlh nadade ina kumuiniyar maganar dantayi nauyi akan harshena
Yasake nisawa karkiyi zargin naraina kokarin da kikeyi akaina kodaya wlh najinjina maki hakaxalika ina alfahari dake
Karki zargeni dawani Abu Dan Allah wlh haryanzu inasonki sonda bantaba yiwa wata mace makamancinsaba aduniya
Lubcy dai tayi shiru tana saurarenshi haryakai karshe murmushi kawai takeyi yadago yakalleta murya araunane yace aure nakeson karawa kuma maganarda nakemaki harnasamu wacce zan aurah
Nakasa sanardake ne tuntunii”” nasan kinsanni kuma kinsan lalurarda nake dauke da itah bazan iyah rike kainaba nasoyin hakuri Amman nakasa doctor yasanar dani akallah zakifi shekara komafi kafin ayimaki aiki Dan likitocin dasuke wannan aikin sunakan wani aikine tayiyu sugama kafin nan kuma ka idar aikin saikinsha magani akallah nawata biyar sannan
Yasake kallonta idanuwansa sunkada jajir banaso na aikata zina abarda nakyamata tun ina saurayina yanxu dagirmana da Yayana bazanyiba dankuwa zansiyawa Yayana halaka dahannuna dankuwa duk abunda nayi nima sai anyimun
Nayi kokarin fara azumie amman duk dahaka nakasa Amman kiyi hakuri kinji matata yayi maganar yanariko hannunta ga mamakinsa saiyaga tatintsire da dariya
Bakisake yake kallonta tace wlh baban labila kasakani dariya yanzu akan wannan maganarne kakasa sanardani?? 
Tundazu kakeson fadar abudaya Amman kakama kwana kwana kawai kacemun aure zakayi zanhanakane??? Nasan mata sunada kishi Amman nisam banadashi kuma bawai Dan banasonka bane kodaya 
Amman kasani dole inhar soyayya tacika soyayya kaso abunda masoyinka yaso kome kakeso aduniya komai muninsa gareni inhar kafurta kanaso tonima dole naso abun
Kaddarama abun bakine aguna inhar yazama fari awajenka nima yazama tuntuni nasobaka wannan shawarar tunda nidai banada jimirin dauke lalurarka kuma sainaga 
Kamar zanyi shishshigi sainakama bakina Amman bakomai awajena kasaki ranka Allah yasanya Alkhairi tsuru yayi yanakallonta
Baisan sanda yarungumetaba yafara sunbatarta ganin yasoma fita hayyacinsa yasa tatureshi tace kamantane
Karamin Tsaki yaja yace wlh kamar namutu nakeji tanisa cikin alamar tausayi tace tomezaihana asabikin kusa kusa kozaka samu abunda kakeso
Yace ah sati biyu akasaka bakomai zancigaba dahakuri zuwa lokacin””” tatausaya masa matuka yace nagode sosai lubcy hakika ke Yar aljannace inama sauran mata zasuyi amfani da shawarata surika hakuri idan mijinsu zaikara aure
Dazasukoyi irin halayenki nakwarai da duniya tahaska”” murmushi tayi nidai kadaina zugani wannan zuzutawa haka
Dariya yayi aikin chan chantane”” yasake riko hannunta nagode sosai tace bakomai yasunan kanwar tawa??? Cikin nunajin nauyi yace suwaiba””😌 tace wow suna maidadi yakamata kafin akawota anunamun photo n kanwar tawa yadan Sosa kai yace bari nadauko wayata kigani Yar duma dumace kamarke
Yayi maganar yana mikewa tace bansaka wahalaba??? Yace kodaya daganan kobirnin sin kikaturani dakafa zanje saidai indade bandawoba tasa dariya ko maigidana ashedai kanaji dani ??? Yace kamar kwai kuwa yawuce 
Tabi bayanshi damugun kallo yanafita taja wani dogon tsaki aranta tace wai aure???🙄 To ayi auren mugani ai wlh danabarka kakusanci wata matar amatsayin matarka nafiso kamutu
Inaruwana da lalurarka saidaifa kaje kayi zina komata Dari zakanema ni lubabatu bandamuba kazantarda bakaganiba tsabtace:roll:
Amman bazan taba yarda kakawo wata acikin gidan nanba Dan nawane danida Yayana”” bazantaba bari Yayana susamu yan ubaba
Karuwai ka ajedari awaje aidama akan abun zakayi aure nikuwa inamai tabbatàr maka bazaka samuba hmm namiji munafukiñe jiyanda yakewani lallaf yadauka salihar mace yakawo agidansa baisan kububuwa takeba cinnaka bakasan nagidaba zumanake maizaki ammankuma gaharbi harbinama yazarta Karin maciji dafii

Afili nake mumina Amman azuciyata nafikowa sharri jin motsin dawowarsa yasaka lubcy tadaidaita natsuwartà
Yashigo da sallama ta amsa”” kusa da itah yazauna yajawota jikinshi yakamo mata pic din tana kallo
Tace kai ammanfa kanwar nan tawa bakaramin kyaune da itaba”” yadan hararetà yaçe batakai kiba lubcy aranta tace kunji munafuki waya sàñima koharzagina kukeyi 
Amman afili saitace ko??? Yace sosaima yanda kikasan kyawawan fure haka nakeganinki wai anyama wani yataba fadamàki kinada masifàr kyau?? Dariya tayi cikin nuna alamun jindadi tace ah ah Amman gashi aikai kana sanardañi

Aisha✍🏼

[6:20PM, 2/14/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 31

     By

Gentle Lady💃🏽

Ya murmusa bafa wasa nakeyiba””” ta sagalo hannunta akan kafadarsa tace nasanda haka
Yace sonake kiyarda ai”” tace ainayarda yanisa tareda cewa yanzu dame dame kikeda bukata????
Yakai karshen maganar yana kallonta”” tace meka rageni dashi??? Bannemi komai narasaba 
Yace nasani Amman kifada kome kikeso”” tana kallonsa tace idan akwai wani Abu dazan nema ayanzu bazaiwuce soyayyarka ba”” kuma nasan nasameta tomekuma zan nema bayan wannan???/
Yayi murmushin jindadi yashafo gefen fuskarta yace indai soyayyar Usman ce kindade dasamunta”” kisa wannan aranki Usman nakine
Murmushi tayi tace namudai””” yadan waro ido dakedawa??? Tace Kanwata Mana yadan takura fuska yace kinsanni sarai inasonki!! Tokidaina kokonto akaina..
Tace aiba kokonto bane yace tokifadi abunda kikeso

Totunda kamatsa kayimana abunda kaga yadace dani dayaran
 Yadanyi shiru sannan yace nikam inhar badakanki kikace kinason abuba bazansan kinji dadiba nadaibaki lokaci kiyi shawara”” sannan yamike yana kallon agogon falonta bari nadan watsa ruwa nawuce masallaci tace to saikadawo 
Yanafita taja wani wawan tsaki gabadaya natsuwarta ta kaurace tana nan zaune saida ta kwataanci yafita takulle bangarenta tashiga daki dasaurii domin yiwa tubkar hanci
Tajawo Dan akwatinta data sanya madubin tadaukoshi tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* take hasken yashiga acikin madubin saiga shi yabayyana yanamai kyalkyatar dariya
Dariyarsa sosai tatunzurah lubcy domin tasan da itah yake saida yakwashe rabin sa a yana kyakyata dariyar ba kakkautawa
Sannan yayi shiru yatamke fuska tamkar Wanda baitaba dariyaba yace meyafarune yaukika yi kiran rana tsaka???
Cikin nuna damuwa tace nasan kasan komai boka tunda harnaga kana dariya rufe bakinta keda wuya yasake shekewa da dariya

Daga bisani yace bake nakewa dariyaba Ina mamakin karfin haline irin naki aranki bakyason Abu Amman bazakitaba nunawaba kina batarwa mai hankali hankalinshi da tunaninshi komenene manufar yinhakan???
Saiyanxu ta murmusa tace saboda inkauda hankalin duk wani maitunani inhar nafitoda rashin son auren afili komai yafaru nangaba kaitsaye za ace dama banason auren nayi yanda zanyi narabasu
Wannan dalilinne yasaka banaso kowa yasan sirrina”” yajinjina kalamanta yace hakika kekanki *hatsabibiyace* 
Tace bawan nan ba menene mafita boka??? Yace Mafita tana gareki mekikeso aimata??? Tace dama zaiyi aurenne saboda yagusarda sha awarsa inaso kar abari yakusanceta
Kaibama itaba kar abari yataba kusantar duk matarda zai aurah daganan harkarshen rayuwarsa indai banibace
Yace angama kikwantarda hankalinki duk da wannan aikin naki mai wahalane domin za ayi aiki sosai akansa
Danhaka Abu biyu zaki samo mana”” nadaya maniyyinsa saikuma gajeren wandonsa Wanda yacire batareda an wankeshiba”””
Zamu tura aljanu su debomana awazar macijiya maishekara hamsin aduniya”” sudebo gashinkan dodanniya da idanun bakar kasa
Sauran aikin maisaukine Amman babban abunda mukeso abubuwan nan guda biyu kuma ki aikoda kayan aiki domin suji karfin zuwa
Tace wannan mai saukine””” gobe zakagansu”” yakece da dariyaa take hasken yafito yabace bat dasauri

 

Tamiyarda madubin mazauninsa tadawo saman gado tabuga tagumi duk abunda yace kakawo wajibine kakawoshi
To itah tayama zatasamu maniyinsa”” kai dawahala gashi bahalin yakusanceni
Tanisa aikuma yazama dole insameshi koya yake dawan nan tunanin tawuni zuwa dare tasheka wanka tacikwalliya Wanda rabonta dawanka ita kanta tamanta kullum saitsami takeyi
Usman dayayi arba da itah kasa natsuwa yayi yayita hadiyar yawu kusadashi tazauna
Su labila sunakasa yanakoya masu assignment sai hankalinsa yakoma wajenta karshemadai cewa yayi sutashi sukwanta dareyayi gobe zai karasa masu

suka Mike sukai masu saida safe tadauki majeed sukai daki saida sukawuce yajuyo yafuskanceta yana lumshe ido”” jikinsa harrawa yakeyi yajawota jikinsa
Sam batayi kokarin hanashiba”” saida yayinisa sannan tadantureshi daga jikintà yadago araunàce idanuwansa duk sun sauya yace please lubcy wlh zan iyah mutuwà tadago dasauri tarufemasà bàki tace kamanta inda muke banason yaran nan sufitone muje daki ammanfa zan taimaka maka kawaine kasamu karage lalurar Amman”” bazaka kusanceniba”” Dan banwarkeba
Cikin muryar tausayi yace shikenan muje haka tamike tanagaba yana bayanta saijuya mazaunai take yañàhadiyàr yawu dañtasaàke harzukashi ta matakala tabi aikafin sukaimà yamatsu sosai
Yadanrage zafi itakuma tasamu abunda takeso yakoma gefe yana maida nunfashiii

Aisha✍🏼

[9:41PM, 2/14/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 32

       By

Gentle Lady💃🏽

Dasauri tamike zuwa bandaki yabita da kallo tunda suke tare bata tabayin wanka aLookacinda suka taraba
Koda yace tatashi tayi wanka cewa takeyi bayanzu zatayiba saida safe idan suntashi sallah Amman yanzu dabama Kusan tarta yayiba tajeyin wanka yanatsaka da tunaninsa tafito daure da towel
Yasake binta dakallo yana hadiye yawu shikam baisan yawan bukatarda yakeda itah ba baitabajin ya gamsuba komenene dalili
Ruwan jikinta tadan watsamasa yadago yana kallonta gira tadaga masa tace tunanin me kakeyi??? 
Yace kekanki kinsan tunanina bayawuce matsalarki wlh kokadan banji nasamu natsuwaba hartausayin kaina nakeyi
Kusa dashi tazauna tana goge kanta tace hakuri zakayi basaura kwana sha huduba aikamar gobene zaka angwance ni idan kayi auren nayafemaku kayi wata daya dakinta kasamu kamore amarcinka
Cikin alamun nunajin dadi yace dagaske kikeyi??? Talunshe ido tabude kadaina shakka ko kokwanto akan maganata babu abunda bazan iyaba indai akankane”” fatana shine kasamu abunda kakeso
Inason ganinka cikin kwanciyar hankali yalumshe ido yabude yace nagode matata farincikina 
Tace karka damu kaje kayi wanka ko yace hakane yamike yadaura towel yashiga toilet dasauri tadauki wandonsa tareda abunda kecikin kwalba lakame da towel dinta tafita zuwa dakinta
Tanazuwa ta ajesu waje daya tasaka kayan barci tafito zuwa dakinsa koda yafito yasameta hartakwanta wasu kayan barci yasaka shima yahau gadon
Yajawota jikinsa tareda saukarda ajiyar zuciya sosai yanason jin duminta Amman tunsanda batada lafiya batasake hada shinfida dashiba kullum dakinta take kwana sake jawota yayi cikin jikinsa barci maidadi yadaukeshi tareda mafarkai masu dadi washe gari saida yasake wanka kafin yaje masallaci
Bayan kwana biyu yashigar mata da kayanda yasiyomata tanata murna tanayaba kayan”” yadaukesu sukaje kasuwa yace kowa yazabi kalar abunda yakeso 
Sunkawo kaya sosai duka yabiya kudin Dan sainan nan yakeda itah” tuni tasanarda kawayenta suzo ranar asabar maizuwa akwai fatynda tashirya Na musamman”” agidanta Sam bata sanardasu aure Usman zaiyiba
Ankai lefe gidan Amarya kuma duk wadansu kudi da ake bukata ankai dagashi sai Abdul sukeyin hidimominsu saboda”” bashida wasu abokai””
Ranadai bata karya saida”” uwar diya taji kunya””yaune dubban jama a suka shaida daurin auren Usman da suwaiba akan sadaki dubu Dari biyar”
Daurin auren yasamu halarta mutane sosai dayake Usman mutumen mutanene”” ango yasha farar shadda sai wasar hakorah yakeyi shikadai yasan abunda yatanada adaren yau
Lubabatu ce cikin dakinta tareda kawayenta sadiya larai sajida aneesa rabi atu”” sadiya tace waini kince muzo gidanki Amman bakisanardamu komaiba kuma munga gida cike da alamun biki akeyi”” 
Tamurmusa tace biki akeyi kuwa”” larai tace bikin mene??? Tace aure dadyn majeed zaikara kusan tare suka hadabaki aure???? 
Tagyada kai tana shan lemu “” sajida tace tirkashi kuma kike zaune anan??? Takalleta tace tome kikeso inyi kinasone intada hankalina bayankuma mijina yanasona???
Rabi atu tace soyayyar banza ai wlh duk sonda danamiji yakemaki dazaran yakara aure zakizama photo”” aiyanzu yadaina yinki tunda yasamu yarinya bayankuma shine yamaidaki hakan
Ta aje kopin hannunta tace ninasan mijina yanasona sosai”” kuma babu tayanda wata zatafini matsayi acikin zuciyarsa
Sajida tasheke da dariya tace naga alama giyar soyayya batagama sakinkiba tokibude kunne kiji namiji dakike ganinsa tsohon munafukine bazaki gane hakanba sai ankawo matar
Barinma ya tas tata yagano tafiki sweet hmmm sunanki sorry kinaji kinagani zakikoma borah agidan nan

.takarewa gidan kallo kinga wannan gidan wlh kinagani zai gagareki zama
Dake dayayanki gidan nan zaikoma maku tamkar kurkuku bari kiji yanda mukayi da dadyn ihsan lokacinda yakeson yin aure Sam bainunamun komaiba kamar yahadiyeni dama gayanda muke kullum sai riritani yakeyi da dadin baki
Nikuwa ahaukana sainaga aisonda yakemun kamar baxaiso wata bayan idona ba”” saiban dauki matakin komaiba nayita rawar kafa har aka kawo Amarya
Nikam sai lokacin nasan natabka babban kuskure na aminta da danamiji dansaboda kawai yamun dadin bakin soyayya
Idan yanadakinta wlh ko motsinsa bakyaji saidai inshige daki inyita kuka saboda takaici sairawar kafa yakeyi inhar girkinta yazagayo Amman ranar girkina sainaga baya walwala bayanuna zakuwarsa 
Lubcy tace toyakikayi??? Tace hmm aisaboda naga wankin hula yanashirin kaini dare” kawai nakai sunanta wajen *hatsabibin boka* aka kadamun Yar banza hatta cikin datafita dashi aka narkardashi yabi mazubar ruwa
Sukasa shewa suka taba rabi.atu tace wlh kinmun daidai”” aikishiya ba abokiyar zamabace mekike jirah kinsandai yanda kikashigo rayuwarsa danhaka idan kikatsaya wasa wata tashigo takarbemakishi
Lubcy hmm kawai tace sajida tace kaikudaina wahalda kanku tasan abunda tataka”” lubcy takwashe da dariya tace kudai akeji mahaukaci yafada rijiya 
Kamar ance sudaga Kansu sukayi arba da labila tanarike dakugu takallesu dai bayan daya tace hmm wannan muguwar hudubar kukazauna kuna koyawa mamana duk danasan batada mugun hali Amman bazan shedetaba danzata iyah sauyawa 
Danzama damugayen kawaye irinku hatsarine garayuwar iyali “” lubcy tadago afusace takunduma mata zagii abunda bata tabayiba tace asheke shasha shace??? Anandin kinunamun abokin wasanki
Wlh karnasake ganin kin shigomun daki waima tsaya labe kikemana ko??? Idanuwanta sunakawo kwallah tace komadai menayi wlh muddin matar dady wani Abu yasameta saina sanardashi gun boka kikezuwa lubcy tataso daniyar dukanta taruga dagudu tace kukuma kuji tsoron Allah inkuwa bahakaba kuyi mummunan karshe takafro kofa ganin tana niyar dankotaa

Aisha✍🏼

[2:36PM, 2/15/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 33

       By

Gentle Lady💃🏽

Lubcy tadawo”” tanata sababi saida su sajida sukaita bata hakuri sukace ai kuruciyace zatadaina nan gaba”” 
Aranta kuwa tanatsoron shegen surutun labila tunda hartace hakan bamakawa zata sanarda Usman
 kuma zaiyarda da maganarta danbataimasa karya sosai tasan yana yarda da maganar labila 
Lallai kuwa yazama dole tayiwa tubkar hanci zata sanarda *hatsabibin boka* dawan nan tunanin sukacigaba da harkokin gabansu
Yanbiki sukafara cika gida alokacin taiwanka tafita cikin mutane akafara jidoda kayan ciye ciye”” 
Karfe hudu nayamma akatafi wajen faty Wanda uwargida tashirya awani babban hotel namaza damata inda Amarya dakuma ango tareda uwargidansu agefe aka zauna saman dandamali
Bayan anbude taro da addua akafara gabatarda shirye shirye inda maikida yayita wasa uwargidan Alhaji usman akan wannan katafaren biki data gayyacesu
Aka umurci Amarya da ango sufito tsakiyar taro sutaka rawa haka sukafita anatakemasu baya
Nan take akasaki kida tareda sowa””” lubcy tayi ruwan kudi tamkar dagasama suke zubowa sailiki takewa Amarya inda Usman shikuwa yakeyimata 
Kawayenta suma sukafara yimata likiii”” sosai masu kida suka kwashi kudiii”” tarokam yayi taro duk inda lubcy tawurga maganarta akeyi anayaba halinta
Lubcy macece wacce ta iyah zamada mutane sosai tasan yanda take tafiyarda rayuwarta macece wacce tasan takan kissa dakuma kisisina
Shiyasa har makotanta””suna sonta sosai” dakuma yaba halayenta”” basu suka tashi wajen Fatyn ba saida akasoma kiran margin sannan akatashi bayan anci ansha anyi katt
Amarya anazuwa akasoma shiryata domin Kaita gidanta”” karfe takwas motocin daukar Amarya suka faka kofar gidansu
Bayan iyayenta sungama yimata huduba akadauketa sai katafaren gidanta bangaren uwargida aka Kaita akabata amanarta taredayi masu nasiha
Tacee bakomai ai kanwace niban dauketa kishiyaba aikuwa dazasu tafi har bangaren Amarya tarakasu kowayatafi dayabon halayenta
Karfe goma kowa yawatse akabar Amarya agidanta tareda uwargida gidan yayi tsit
Tasake wanka tadawo cikin falon tana zaman jiranshi zamanta babu jimawa Usman yashigo 
Yana yin arba da itah yasaki fara a yace haryanzu kinafalo bakyajin tsoro ina labila??? 
Tamike cikin fara a tace sunyi barci nimadai shinakeji natsayane inrakaka wajen Amarya karkashiga kaidaya
Yace kamar kinsani bazan iyah shigaba” tace tomuje karage kayan jikinka kawatsa ruwa sainarakaka Amman yabanganka da kazaba
Kansa yadan Sosa yace tana mota wlh namanta”” tace tokadauko bari nahada maka ruwan wankaa yace yauwa nagode yajuya cikin zumudi tabishida murmushin mugunta dakinsa taashiga tahadamashi ruwan wanka yadawo yashiga yawatsa tadauko masa kayan barci masu kyau
Tafeshesu da turare yana fitowa yasaka kayan suka fita tanarike da plate da madarar shanu bakin kofar dakin tatsaya Tamika masa
Yace yahaka bazaki shigo bane??? Ido tagwalalo ah ah kaikam damadai rakiya naimaka kagaisheta dai 
Tamika masa kajin yace tokebaki dauki takiba tace ainima nacitawa lokacinda aka kawoni wannan ta amaryace tasunbaceshi akumatu asha amarci lafiya tawuce abunta tana murmushi yabita dakallo cikin soyyya yana fatar Allah yabarshi da matarsa 
Baisan wanne irin so takemasaba dahartake iyason abunda yakeso duk abunda akeyi bisa kunnen suwaiba tagodewa Allah dayabata kishiya tagari 

Yashiga bangaren da sallama ya aje kayan hannunsa saman gadon yahau yaciremata mayafi yana murmushi Amarya ta ango murmushi tasaki cikin jinkunya
Yace yaudai Allah yacikamana burinmu kitashi muyi alwala mugodewa Allah”” bamusu tamike domin dauro alwala saiga jinin al ada jiki asanyaye tafito
Ganinta dayayi sai ahankali yatambayeta tafadamasa tanafashin sallah baice komaiba yagabatar masu dakajin sukaci saida yayi nafila yakwanta 
Yadade yanajuyi kafin barcin yadaukeshi saikusan asuba washe gari sukuku yawuni Sam baida walwala
Bayan sunyi break dazasuci abincin rana yahau samanta saiyasamu tana sallah bayan jiya yatambayeta kwana nawa takeyi tace biyar kenan karya takemasa???
Baicekomaiba yace tafito suci abinci”” itakanta jikinta yayi sanyi daganin yanayinsa””
Dadare bayan sunyi saida safe da lubcy sukayi dakinsu wannan karon saida komai yakusa kankama tasomajin amai”” dasauri tasauko tashiga toilet
Tanashiga taji batajin komai””” Usman tunyana saran fitowarta haryagaji yaje bakin kofar yana bubbuga mata shiru kuma tasa sakata karshe dole yahakurah yakoma bangarenshi
Tundaga ranar dazaran yashigo dakin saitaruga toilet karshedai centake kwana har akakusa kwashe watadaya karshema saiya samata ido
Duk halinda sukeciki baisanardà lubcy ba itakuma bata nunawani abuba suna zamansu lfy zaman gaskiya da mutunta juna tadauki yayan Usman kamar nata
Zaune suke da marece lubcy tamike zuwa kitchen tazubo lemu a cup biyu tadawo falon tazauna tayiwa suwaiba bisimillah tadauka tasha sukaciga dafirah
 Dadare bayan Usman yadawo dayake anraba girki yau hannun lubcy yake bayan sunci abinci suntaba firah sukaiwa juna saida safe

Aisha✍🏼

[3:54PM, 2/15/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 34

       By

Gentle Lady💃🏽

Bangarenshi suka nufa tayo wanka shima yayi”” suna kwantawa yakuramata ido”” tasaki murmushi tace akwai matsalane??? 
Ido yalumashe sannan yabude yace sosai ma tace mekake bukata inyimaka yanzu?? Yace ke kawai nake bukata”” tayi masa kallon rashin fahimta tace haba jiyafa kabaro bangaren kanwata kana nufin haryanzu baka koshiba??? Tonayafe kwanan nawa wlh kakoma cen wajenta
Yakalleta da tausayawa aransa yace mace tagari kenan kekina tausayamun bakisan waccen bata tausayinaba “” tadan tabashi tace injidai bawata matsala naga kayi shiru??
Yace hmm bakomai nidai kitaimakamun zatayi magana yadorah lallansa akan bakinta daganan yacigaba da aikamata sakonni jikinsa yanda kukasan Mazari saidai babu yanda zaiyi saidai kawai yayi wasa da itah yadan samu natsuwa kadan
Bangaren suwaiba kuwa tunda tashiga daki takasa barci wata muguwar sha awace tataso mata tarasa yanda zatayi takwanta Amman Sam barcin ya gagara daukarta
Mikewa tayi cikin sanda tafito waje tafito daga bangarenta tasauka kasa tafita waje”” dakin driver gidan tawuce kaitsaye babu wani tsoro ko shakka acikin zuciyarta
Taturah kofar saitajita rufe ahankali tasoma bubbugawa cikin barci yaji anabuga masa kofa yace waye cikin muryan rada tace nice kabude ba lafiya dasauri yazo yabude kofar yana budewa tayi kududuf tashige
Dagashi sai gajeren wando takalleshi tundaga sama harkasa tahadiye yawu wani irin shu umin kallo take jifanshi dashi
Yana kallon kofa cikin tsoro yace suwaiba meyakawoki dakina??? Murya takaryar tace haba kb yazakace meyakawoni dakinka 
Harkamanta soyayyarda mukayi dakai??? Tsaki yaja yace soyayyar banza aikinsan inasonki kina sona Amman danbanida kudi akahanani aurenki
Kituna shekararmu biyar tare”” sake matsowa tayi kusa dashi tace kayi hakuri masoyina wlh nikaina badason raina akayi auren nanba kaikasan inasonka babanane dayaga kudi yace bazan aurekaba
Yace kinga malama banason dadin baki kifita kibarmun daki banaso alhaji yasan wata alaka tataba hadani dake danzan iyah rasa aikina kuma dashi na dogara
Tamarairaice fuska haba KB baidace kajuyamun bayaba kayarda dani wlh ina mutuwar sonka Allah yarigada yakaddaro saina auri wannan alhajin Amman wlh banasonsa

Yawatsamata wani mugun kallo yace kifita kibarmun daki wlh konaimaki ihu
Ninarigada nafiddaki araina tunranarda nasan maigidana kika aurah””” abunda suwaiba takeji bazaisa ta iyah hakurah takomaba”” zanenda yake jikinta tacire tadawo daga itah sai wasu arnayen kayan barciii 
KB yasoma kallonta tundaga kasa harsama tuni jikinsa yasoma kyarma yadimauce daganin surar jikinta sha awarta ta tasomasa shedan yanata haskomasa ni imarda zaikwasa ajikinta

 

Ganin natsuwa takauce daga gareshi yasa tatako cikin takun Jan hankali tafada jikinsa tasoma kaimasa Sumba tako ina take yasoma maidamata da martani
lubcy ce tamike tanarike da kirji tashinta yasaka Usman mikewa yace lafiya??? Tagirgiza kai cikin damuwa tace ba lafiyaba gabana nakejin yana tsananta faduwa 
Anya antynsu lafiya take! Dayake hakan take kiranta yace kikwanta bakomai bane bakiyi addua ba dazaki kwanta tace nayi Amman haryanzu baidaina faduwaba
Tamike nidai barnadubata ganin tamike shima saiyatashi yabiyota harbangaren suwaiba saisuka kofar abude
Dasauri taturah tashiga da sallama harkurya basugantaba gabaya suka bade dakunan danema batanan hankalin Usman yatashi dasauri yasauko kasa
lubcy tanabiye dashi sukadubà kaf bata gidan yanaturah kofar fita yajita bude kaitsaye yafita dayake dakin kabeer shine farko yayi hanyar dakinsa arude
Damamaki yajikofar abude dayaje domin kwankwasawa”” yaturah kofar yanacewa kabeer taso gida ba bakinsa yasankame ganin abunda idanuwansa sukai arba dashi
Kalu innalillahi wa inna ilaihir rajiun”” shine abunda kawai yake furtawa take hawaye sukafara sintiri akan fuskarsa
Ganin baifitoba lubcy tace alhaji nataada maigadi yace bata fitaba tayi maganar tanashiga dakin ganin abunda yake faruwa lubcy tabuga salati dakarfi salatinta yafargarda KB yadago kansa dasauri
Lokacin yana kokarin shigar suwaiba dayake budurwaçe baisamu hanyaba yanashiriñ shigarta dakarfi lubcy tayi salati Wanda yadawodashi duniyar gaskiya aidasauri yasauko yaja zanin gadon yarufe jikinsa saizare ido yake gawani zawo dayaji nantake
Muryar suwaiba yaji tanacewa haba masoyina yakadaina abunda zakayi karkaji komai dama jikina nakane kasan kaikawai nakeso” tamiko masa hannu kazo mufaranta ranjunanmu nadade inajiran wannan ranar dazan mallakamakà Kaina
Ido rufe take maganar dukda turarta da KB yakeyi dantarufe bakinta ganin bazaitasoba tadago tafada jikinsa tasoma lalaubàr bakinsa
Usman daya sandare waje daya tamkar gunkii wani bakincikine yatokareshi gakahon zucii baisan sanda yararumi wayar TV ba yatuzgeta dakarfiii yasoma aunamata itah saukar bulalar dataji ajikintà yasaka takwallah kara
Ko kakkautàawa bayayi idonsa yarufe tuni yazulawa KB shima Wanda yasoma kuka ganin abunda yake faruwa ga suwaiba
Da itah dashi sukarude gidan tuni ma aikatan gidan sukafito kowayaga abunda kefaruwa saidai yajuya yana tsinemàsu
Ganin zai iyah kashesu yasa KB yadauki kayansà ahannu yafita dagudu”” tuni suwaiba tasuma Amman Usman baidaina dukantàba saida lubcy tarike bulalar cikin kuka tace sokake ka kashetañe hàbà tundazu naketa bakahakurii
Wani mugun kallo yawatsomàta idanuwañsa sunyi jajir itah kañta tàfirgita dàyana yinda taganshi danbatà taba ganiñsa cikin irin yanayinbà bulalar hannunsa ta rike kam dole yasakarmàtà yàfità dakin dasauri ko kallon masu aikinda suke tsaitsàye baiyiba yayicikiñ gidaa
Labila tanafalo saikuka take tana rungume da majeed Dan hayaniyar gidance tatasheta takasa fita saizagàyen falon takeyi gànin dadynta yashigo taruga tafada jikinsà tanakuka tureta yayi yahau sàmañsa Dasauri

Aisha✍🏼

[8:43PM, 2/15/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 35

       By

Gentle Lady💃🏽

Mamaki matuka yacika labila tana tambayar kanta meyasamu dadynta yau”” majeed tuni yakoma barci daman”” 

Bangaren lubcy kuwa” tana ganin yafita tadauko ruwa dasauri tawatsawa suwaiba take tafarfado tachandara ihu 
Lubcy tarufe mata baki tace Dan Allah kidaina ihun nan makota sunajinmu fa”” sai alokacin hankalinta yadan dawo jikinta takallijikinta taga batada kaya dasauri tajawo zanen gadon tarufe jikinta dashi tafashe dakuka tana girgiza kanta nashiga uku
Yazanyi Anty”” lubcy ce tadafata tace kiyi shiru kinji kanwata tashi mukoma cikin gida “” idanuwanta tadago zuna zubarda kwalla tace Anty na aikata babban kuskure arayuwata wlh aikin shaidanne ninasan idan mahaifina yaji wlh saiya kasheni
Lubcy tanisa tace bama zaijiba insha Allah kitashi muje kigasa jikinki gobe zanbashi hakuri”” tasake kallonta akaro nabiyu tace wlh nasan bazaitaba hakura ba kakama matarka da yaronka suna aikata zina ai hankalima nazai daukaba ballantana tunani
Lubcy tace hakane Amman meyakaiki aikata hakan da iliminki??? Tashare hawaye tace Anty wlh banason baban majeed wannan shine saurayina atadalilin kudin sa dayace yanasona sai mahaifina yadage saina aureshi nima sainaji inasonsa narabu da kb saboda baida kudin aurena
Tunranarda nazo gidan nan sainaji Sam banasonsa soyayyar kb tasake linki acikin zuciyata hardai ranarda naganshi gidan nan amatsayin driver duk hanyarda zanbi dannaga nakadaita dashi bansamuba saiyau da shedan yakadamun gangarsa batareda kokonton komaiba naziyarceshi domin yakawarmun da muguwar sha awarda tatasomun tasake fashewa da kuka tace wlh Anty niba yar iska bace bantaba yin iskanci dakowaba yanzun ma ina mamakin kaina da abunda yakawoni dakinsa nayi takaicin wannan ranar
Lubcy tajawota jikinta cikin alamun tausayawa tace na fahimceki Amman mahaifinki baikyauta makiba aiyanzu andaina auren dole kinga saka kayanki mukoma cikin gida
Tadago dasauri tana girgiza kai tace wlh zai iyah kasheni tatoshe bakinta saboda kukanda yakwacemata
Tace taya zaikasheki kitashi muje kinga masu aikin gidan nan suna waje mujeciki Dan Allah tamike tajuya tace kisa kayan
Bakin kofa tafita tasamesu tsaitsaye bata fuska tayi tace tomekuke jirah kowa yakoma yakwanta sumui sumui sukawuce tana tsaye saida takwatanci tasa kayan sannan tashiga taja hannunta suka wuce cikin gidan
Cikin falon suka samu labila zaune rungume da majeed tana ganinsu ta ajeshi tace mom lafiya??? Meyasamu Anty??? Me akaiwa babana???? Wadan nan tambayoyin tajefowa lubcy tace bakomai kidaukeshi kukoma daki dagahaka batace komaiba tawuceda suwaiba zuwa dakinta
Harkuryar daki takaita ta zaunarda itah fita tayi zuwa kitchen tasamu ruwan zafii tagasamata jikinta tabata magani tace tasamu takwanta
Ta share hawaye wadanda suketa zubowa akan idonta tace Anty konakwanta wlh bazan iyah barciba
Tace kiyi hakuri kidaina kukan nan saiya haifarmaki daciwon kai kikwanta kinji kaitagyada mata itakuma tamike taimata saida safe hartakai kofa takirata Anty
Ta amsa tareda juyowa tace nagode da soyayyarki agareni agaskiya kinchanchanci duk wata soyayya dankuwa samun mai irin halinki sai antona nagode
Tasaki lallausan murmushi tace karkidamu yiwa Kaine tawuce tana sakin shu umin murmushi aranta tace kadan kenan yarinya wannan aikin *hatsabibin boka* ne kaitsaye bangarensa tanufa
Taturah kofa tajita kulle tayita bugu yayi banza da itah karshe takoma bangarenta takwanta
Daga labila har Usman suwaiba babuwanda yaruntsa nasan bangaren KB ma hakanne Amman lubcy barci harda minshari 
Bata farkaba sai bakwai agurguje tasauya kaya”” koda tafito masu aiki harsungama komai saidai tazuba akula tadaura saman dinner
Bangarenshi tanufa taturah kofar saitajita bude da sallama tawuce ciki tsaye tasameshi yanadaura agogon hannunsa tace ina kwana
Batareda yakalletaba yace lafiya yadauki takardunsa da key din motar sa yafita”” dasauri tabishi tana kiransa kowaigenta baiyiba harsuka sauko kasa
Labila tsaye da itah da majeed sunyi shirin skull cikin uniform

Lubcy tasauko kamar tafadi tace abban majeed Dan Allah katsaya 
Afusace yajuyo yace wai lafiya??? Idan natsayà mezanyimaki”” gabanta saida yafadi tadan dake tace bakomai naga zakafita bakayi break ba
Yace nakoshi yasakai yawuce labila””tabishi dasauri zuwa waje tanakiràn sunansa kamar karya tsaya bayaso labila tafuskanci hàlinda yakeciki ya juyo tareda kirkiro da fara a 
Takaràso tace dady morning”” yace morning my doter kintashi lafiya tace kalau idanuwanta sunakawo kwallah
Yace menene nakuka labila” yayi maganar yana dago habarta tace dad nagakamar kanacikin damuwa
Dariyar yake yayi yace bakomai banada damuwa maza Kira majeed insaukeku makaranta
Tace dad kabeer fa??? Yadanyi Jim sannan yadago yace bayajin dadi yatafi gida maxa kirashi karku makara
Tace to sannan tajuya cikin gidan yabita dakallo yacije kasan lebonsa”” 
Lubcy kuwa tunda yafita tayi tsaye sakeda bakiii suwaiba wacce tasauko duk akan kunnentà komai yafaru dasauri takoma saman tanakuka

Aisha✍🏼

[11:02PM, 2/15/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 36

        By

Gentle Lady💃🏽

Tana shiga batako kalli wajenda mom dinta takeba tadauko jakarsu tariko hannun majeed sukawuce
Murya asanyaye tace inakuma zakuje baku karyaba”” batareda tajuyoba tace munkoshi tafita abunta driver n dady ne yatukasu yafara kaisa company sanan yabiya yakai labila yakai majeed shima
Lubcy guiwa a sake tahau saman ta takasa tsaye takasa zaune karfa wannan abun yashafeta ranarda aka kawo Amarya aranar tasanarda *hatsabibin boka* bayanin labila da abunda tafada
Yace kwantarda hankalinki nasan mezanyi mata”” cikin saurii tace karfa aimata wani abun nacutarwa yatace
Yamurmusa yace nasanda haka bakomai zanyimata ba zankullemata bakine koda tayi niyar sanarda wani abunda kikeyi zatakasa magana
Kodakuwa akan idonta kikai kisan kai bazata iyah sanarda kowaba tamurmusa yauwa hakan yayi saikuma maganar wannan shegiyar matar wlh boka banason tadade gidan nan
Inatsoron karwani Abu yashiga tsakaninsu kasanshifa dashegiyar lakuwa”” yakece da dariya yace abunda naimasu wlh koda dagashi sai itah ne acikin duniyarsu bazaitaba kusan tartaba
Yace gobe kiduba cikin drower dakike aje madubinki Zanbada wani magani akawomaki dazaran kinji kina ra ayin tabar gidan kizubamata a lemu abunshadai tasha 
Toranar zatanemi namiji mukuma zamu turata wajen driver ngidanku Dan tsohon saurayintane idan bakimantaba nafadamaki

.

Tagyada kai dazaran kinji gabanki yafadi to sunacen tare saikiyi yanda zakiyi kifitardashi harkuje dakinsa
Inda za akawo maki maganin zakiga wani Abu cikin kwalba saiki daure bakin kwalbar bayan kin tabbatar tasha maganin daganan komai zaifaru zakigani
Godiya tahauyimasa sannan tamaida madubinta”” watan suwaiba biyu yanzu agidan saitazuba mata maganin kuma takulle bakin kwalbar
Shine dalilin abunda yafaru tadan nisa akwai matsala watakil nayi kurene gashi laifinta yana nema Nina yashafeni gashi dasafe bahalin kiran *hatsabibin boka*
Ranar babuwanda yakarya agidan tana ganin ranatayi takulle bangarenta tadauko akwatin tadauko madubin bayan tagama kiransa saigashi yabayyana tazayyana masa komai
Saida yayi dariyarsa wacce yasaba sannan yace laifinkine keda nacewa kidaure bakin kwalba shine kikadaure tamau kisani zuciyarsace kika kulle babu inda iska zaishiga danhaka kuncine yaketa mamayar zuciyarsa
Bayajin sanyi kokadan wannan dalilinne bazakiji dadinsaba idanma kika matsa hukuncinda zai yankemata yashafeki
Ido tawaro tace nashiga uku to yazanyi yanzu??? Yace abune maisauki kisassauta kamunda kikaimasa shikenan zai sauko 
Tasaukarda nannauyan ajiyar zuciya nagode boka ahuta lafiya tana miyarda nadubin tadauko abun ta sassauta daurin tamiyar ta aje saiyanzu taji hankalinta yadan kwanta

Baidawo da ranaba koda dare baidawo dawuriba”” yanashigowa dakinsa yanufa bangarensa yayi wanka yasaka kayan barci yafeshe jikinsa da turare yasauko zuwa dakin lubcy
Kwance takesaman gado abun duniya yashamata kai tunaninta daya karfa reshe yajuyeda mujiya?? Duk da tayarda da boka tasan bazaiyi abunda zai cuyarda itaba
Da sallama yashigo dakin Amman batajishiba saman gadon yahau tabayanta yarungumota yasunbaci wuyanta
Kamshin turarensa tareda sunbatardà yamata sukadawo da itàh duniyar gaske ahankali yaradamata akunne juyo kikalleni
Shiru tayi komotsi batayiba hànñu yasaka yajuyoda itah dakansa

Tasanne kanta kasaa hannu yasaka yatallafo fuskarta yace meyasamu gimbiyata????
shiru taimasa haryanzun take yasoma aikamata dayan sako tuntana share shi hartasoma maidamasa martani
Sundade suna wasa dajunansu saida yasamu yar natsuwa yasake jawota jikinshi
Tadago tana kallonsa idonsà yanarufe kamar maibarci tace baban majeed murya atausashe yace inajinki akwai matsalane???
Tace akan kanwat batagama rufe bakiba yàsà hannu yarufematà bàki yace barci nakeji night 
Baisake dago kai yakalletaba yajata jikinsa yacigaba dà barcinsa itama ahakan barcii yadauketà 

.

Tundaga ranar baisake haduwa da suwaiba ba itakuma batada aiki saikuka duk tarame saboda tunanin makomarta

.

Girki yanadawo wà hannuñta lubcy tace tashirya susameshi dàkinsa tabashi hakuri dadare lubabatu dakanta tashirya suwaibà
Cikinwàni bugaggen less tanajin dawowarsa tariko hannuntà sukai bangareñshi kirjin suwaiba sàifaduwa yake
Lubabatu cegaba taturah kofar da sallama yàña xaune saman kujeràh yana danna laptop lemune ahannunsa yanasha
.yadago yakallesu kallodàya yamiyada hankalinsà wajen abunda yakegabansa

Aisha✍🏼

[12:35PM, 2/16/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 37

       By

Gentle Lady💃🏽

Lubabatu tace barka da hutawa yace yauwa barka batareda ya dagoba”” tadanyi jim sannan tace dama dama wajenka mukazo
Yace inajinki to”” tasake gyara zama tace akan kanwata ne Dan Allah kayi hakuri akan abunda yafaru
Tayi shiru tanajiran taji mezaice yace yakiikeso ayi yanzu??? Saida gabanta yafadi karfa yace ya yafemata saikuma tadake tace kayi hakuri karkayanke mata hukunci mai tsaurii
Sai wannan karon yadago yakallesu suwaiba tunda suka shigo kanta yanakasa saikuka takeyi wani mugun kallo yawatsamata yace munafuka kawai aransa 
Yamaida kallonsa wajen lubcy yace wane hukunci zanyimata bayan tazabi abunda yazama daidai arayuwarta
Saiyanzu taimagana cikin kuka tace Dan Allah Alhaji kayi hkuri wlh bahalina bane wannan shairin shaidanne
Baki yatabe yace ban iyah ganewa yace waima menene dalilinda yasaka kika shigomun da itah dakina??? Wlh banason ko kallon fuskarta dazaran naganta raina baci yake
Lubabatu tace nasan ranka zaibaci Amman hakuri zakayi tunda babu abunda yafaru tsakaninsu kadaure kahakurah Dan Allah badan halinmuba
Yace waikina nufin incigaba da zama da itah??? Hmm abunda bazaitaba yiyuwa bane tunda aka kawo yarinyar nan agidan nan ko hannunta bantaba rikawaba 
Amman hartayi wayonda zaraje wajen yarona waitabashi kanta tatube agaban wani katon banza suna aikata masha a kuma batsoro aranta batajin tsoron Allah ballantana na mutane tace Dan Allah kayi hakuriii alhaji cikin kuka take maganar 
Yamike afusace tashi kibarmun dakina banason sake sakaki acikin adanuwana nayi bakincikin aurenki wlh danasan haka halinki yake tunfarko bazan kai kainaba
Bata tashiba yasake daka mata tsawa wacce tasakata mikewa dasaurii tajuya lubabatu tace meyasa kakehakan nifa nasanka da hakuri
Yajuya mata baya yace banda irin wannan sannan kema ina gargadarki karki sake zuwada itah gurinda nake
Tace wannan bahujja bace to akanme”” yace nasaketa itace kalmarda suwaiba taji aidasauri takara wucewa tana kuka
Jikin lubabatu yayi sanyi batasake cewa komaiba tajuya tafita abunta farinciki fal ranta amman idan kakalleta zakadauka tanada damuwane sosai
 kaitsaye bangaren suwaiba tanufa tasamu tanakuka tana hada kayanta “” lubabatu takarasa dasauri tace inakuma zakije suwaiba???
Inazanje bayan inshiga duniya kinsan sarai bazankoma gidan mahaifinaba Dan muddin yaji ansakeni kuma yaji labarin dalilin sakin nawa kashina yabushe
Dan wlh zai iyah kasheni”” lubabatu cikin alamun tausayawa tace toki zauna anan mana”” harkisamu miji saikiyi aurenki
Tagirgiza kai tace Anty duk yarda kikesona dole kibarni natafi saboda gidan nan”” bawajen zamana bane
Lubabatu tace nasani Amman aidarene kibari mana hargari yawaye”” tace bazan kwana agidan nan ba wlh Anty tafiya zanyi
Jakarta tadauka tayi gaba lubabatu tabita dasauri tana kiran sunanta Amman takasa tsayawa hartakai bakin kofa sukaji muryansa
Yace ina zakije??? Tsaye tayi chak! Batareda tajuyowa tace zanshiga duniyane amsarta saima tabashi dariya
Aikuwa yasoma dariya harsuka juyo suna kallonshi cikin mamaki yatsagaita dariyar yace idanma shizakiyi kece kika zabarwa kanki hakan
Amman kafin nan dole kizauna kiyi idda adakinki idan kingama idda daganan komai kika yankewa kanki daidaine dagahaka baice komaiba yajuya dakinsa”” 
Tsaye tayi itah bata fitaba kuma bata komaba saida lubabatu takarbi Jakarta tamiyarda itah
Tundaga lokacin suwaiba takoma rayuwar daki saidai idan bayanan lubabatu taje suyita firah yawancin abincima taresukeci
Hartayi idda yabata takardar sakinta tareda motarda zatakwashe mata kayanta lubabatu ce tarakata hargida 
Tabawa babanta hakurii akan karya daketa dantuni dama yasamu labarii makudan kudii tabaiwa suwaiba sukarabu kowa yana kukan rabuwà saidakuma Innar suwaiba takoma rarrashinsu
Tace aibasu rabuba tunda mutuncine yahadasu saikusan magrib lubabatu taimasu sallama tawuce Dan gidanma taci abincin dare
 bayan kwana uku dafaruwan hakan sunayin break dasafe labila tace dady magana nakeso muyi takai karshen maganar tanakallon lubabatu””

Itakuwa saida gabanta yafadi
Yamurmusa to yarlele kyabaridai nagama cin abinci tundayau bafita zanyiba kaitagyada masa”” bayan sunkammalà
Sukadawo cikin falon sannan yacemata inajinki maganar mezakiyi tanisa tace inaso kasa a kaimu gidan hajiya murmushi yayi yace saboda wannan kawai?? tokushirya zanyiwa Sunday magana yakaiku
Tace dady idanfà mukaje badawowa zamuyiba yagyara zamacikin rashin fahimta yace wani Abu mom dinku takemaki Wanda bakyaso???
Tadanyi Jim sannan tagirgiza kanta bakomai dady nidai nafison zama agidan hajiya kabarmu mukomacen islamiyar nan basucika karatu sosaiba cendin zamufi jindadi kuma uncle Hafiz zaikoyamana karatu
Yajinjina maganarta sannan yakalli lubcy yace kinji abunda tace menene ra ayinki???
Tace mefa tunda ita tazabarwa kanta kabarta tatafi duk inda zataje mana Amman tabarmun Dana”” tagallàwa labila harara aikuwa majeed yafasheda kuka yace 

  wlh dady nidai wujin Anty nakeso “” yace daina kuka zakabita jikin labilà yalake tasoma bubbugar bayansa cikin lallashi
yace tozuwa yaushe zakuje tayi karaf tace harnashirya kayanmu gobe zamutafi yayi murmushi to Allah yakaimu”” hajiya zatayi manyan bakii labila tayi murmushi yace Amman zanyi kewarku tace mumahaka
Washegari sukawuce wannan shine mafarin zaman labila kano

Aisha✍🏼

[6:14PM, 2/16/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 38

       By

Gentle Lady💃🏽

Acen aka sakata islamiyya dakuma boko rayuwarsu sukeyi cikin jindadi dakwanciyar hankali tabbas tasan mamanta ce tayi sanadin mutuwar auren mahaifinta 
Amman batada halin sanarda wani koda tasofadawa dadynta saita kasa fada”” lubabatu tacigaba da zamanta sai yanda taso gida yakoma nata
Saikuma tatsiri yawace yawace kasashe wajen kasuwanci Sam tadaina zama gida babu yanda Usman baiyiba dantadaina taki yace mena rageki dashi mekika nema kikarasa tace bannemi komai narasaba Amman kasuwancin nakeso saboda kawayena duka mazansu sunbarsu suna kasuwancinsu
Dayake babanza akabarshiba duk da yanadan cijewa karshe dole yasaka mata ido wasu lokutan tanagida Amman kawai wasa zaiyi da itah 
Aibashiri yasoma azumie domin gojewa fadawa zina watarana dadare bayan sungama abunda yasaba akullum tajuya daniyar yinbarci
Yakira sunanta tadanjuyo tanakallonsa tace yadai??? Nisawa yayi yace waimezaihana muje kasar waje adubaki ni wlh nagaji hakurina yakare ina gudun infada ga hakala
Tace toyazamuyi hakurindai xakacigaba dayi” cikin daga murya yace kullum maganarki kenan hakuridai hakuridai shin hakurin haryanzu yabani abunda nakesone??? 
Sokike garinyin hakuri infada ga aikata zina??? Wlh ninasan Allah yanakareni dayanzu nadade na afkawa ga aikata alfasha
Dakudina dakomai “” Amman abunda baifi karfinaba yana nema ya gagareni haba

Tace toya kakeso inyimaka inda lafiyata qalau zaka furta hakan to banda lafiya ai
Yayi saurin gwaceta yace naji bakida lafiya Amman Allah dayasaukarda cuta saida yasaukarda maganinta 
Koda banida kudi wlh zan iyah yinrance domin samun lafiyarki Amman inadakudin nan bawai banidasuba Amman kinnace dole sai anan kikeso aimaki aiki
Dafarko nayi tunanin kobakyason zuwa wata kasane toyanzu gashi kinazuwa kasuwanci Amman Neman lafiyarkine bazakiba to wlh nagaji kara infadamaki gaskiya nadaina cutarda kaina
Tamarairaice fuska tace abban majeed kayi hakuri tomezai hana kayi aure kodan samun abunda kakeso
Yace wanne irin aure zanyi agaban idonki komai yafaru nayi auren Amman baikareni dakomaiba saitashin hankali””haba wannan wace irin rayuwace
Komawa yayi ya marairaice fuska please lubcy kitaimakeni badan niba dangirman Allah kiyarda aimaki aikin nan
Baki tatabe tace nifakoda anyimun aikin Nan bazandauki lakuwarkaba kullum acebawa yanakanyin abudaya kamar abinci haba
Wani mugun kallo yawatsamata yace nafuskanceki kenan duk abunda kikemun dagayya kikemunshi ko??? Anya lubabatu kinatsoron Allah?? Mijinki yanason abu amman dantsabar mugunta kihanashi abunda kuma yazama halalinsa ranar gobe kiyama mezaki fadawa mahaliccinki
Hannu tadagamasa tace dakata usman shiruna bashine zaibaka lasisin gayamun magana son rankaba “” nihaka Allah yayoni banada jimirin daukar lalurarka danme zakaga laifina tunda banice nayokaina hakanba 
Zan iya juran komai amman banadaukar bakar magana”” da mamaki yake kallonta 

Baki budee yace umm lallai yaukinfito mun da ainahin halinki dakika koya wajen kawayenki danni bahakan nasankiiba 

Kuma

Nagode inhar kudi suna biyawa rai bukata kibani sati daya zanbaki mamaki nidakaina bazansake cewa kije ayimaki aikiba 

Kiyita kumuiniya da kayanki indai jikinkine nadaina rabarsa ballantana abunda kike takama dashii
Yatashi daga kan gadon yadaukii kayansa yawuce fuuuu yabarmata dakin”” kallo tabishi dashii ta daura hannu aka tace nashiga ukuna🙆🏿 menene yakeshirin faruwa dani haka””???
Dasauri tadirko daga saman gado tadauki zani tadaura tafito””dakunan dasuke bangarenshi tahau bidaya bayan daya”” kowanne tabuda saitajishi bude 
Aranta tace kenan bayanan dasauri tasauko zuwa kasa falon kasa tahango haske ta matakala tasauko kasan
Chak tatsaya sakamakon abunda kunnuwantà sukajiyo mata”” tasake saurarawa kodai karya kunnuwanta sukejiyomata
Yana kwance saman kujerah yadaura kafadaya akan daya alamu sun nuna yanajin dadin firarda yakeyi yalumshe idonsa yace ninedai bawaniba
Daya bangaren akace haba ammandai batan hanya kayi nikuma awa daza a kirani cikin wannan lokacin 
Dariya yayi yace aikinwuce komai awajena kingakuwa kinada mukami azuciyata dannakiraki bawani abubane
Tace hakane Amman inakabar uwargidan taka”” bakiyadan mere yace inajin tayi barci nikuma banajin barcii
Tasaukarda ajiyar zuciya tace bakaji yanda najiba lokacinda nagakirankà dannituni nafiddarai dasamunka
Dariya yasakeyi yace togani nasake dawowa tamurmusa najidadi sosai inasu labila??? Yadan shafo kansa yace suna kano
Tace kana nufinwai haryanzu basu dawoba??yace eh yanzu aisunyi shekara acen sukandanzo suganemu tareda hajiya
Tajinjina kai Allah yataimaka yace Ameen

  

Aisha✍🏼

[9:03PM, 2/16/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 39

       By

Gentle Lady💃🏽

Shirune yabiyo baya nayan dakiku sannan yakirah sunanta samrat tace na am”” yanisa maganafa nakeso muyidake bata wasaba
Tadan gyara kwanciyarta tace inajinka yace inaso gobe naturo gidanku maganar aure 

Baki tarike tace dagaske tareda kalalo ido
Yalumshe ido yabude tamkar tana ganinsa wani nishadine yakeji aransa cen kasan makoshi yace dagaske kuma banaso auren nan yawuce sati daya inafatar dai ashirye kike

.tarausayarda kai sosaima kuwa”” indai katashi ” yace wlh sosai natashi inamatukar bukatarki atare dani
Wani mugun dadi taji aranta tace maganina yayi aiki kenan”” dasannu zan mamaye zuciyarka”” yace yanaji kinyi shiru kodai barci kikeji???
Tace barcin lafiya inatare dakai kawai inaganin kamar mafarki nakeyi wainice zaka aurah”” yagyara kwanciyarsa yana fuskantar kasa yace kwarai dama kinsan kamai lokacine yanzun kokacin auren namu yayi bakiji yanda nakejinki arainaba
Lubcy wacce saboda tsabar tsurewa batasan sanda fitsarii yasoma bin kafartaba tunda Usman yasoma soyayya da suwaiba baitaba kiranta awayaba 
Haka zakila baitaba furtamata wata Kalmar soyayya ba waisaigashi yautaji da kunnenta yana fadawa wata kalamai masu sanyaya zuciya Wanda rabon dayazauna yana koramata kalamai masu sanyi tun tana amarya
Nikuwa nace kece kiKajawo bakibashi abunda yakesoba taya zaibata lokacinsa wajen fadamaki kalamai bayankuma babu abunda kalaman zasu kareshi dashi
Shin mezaihana ke idan bakyada juriyar daukar lalurarsa kibarsa yayi aure mana yasamu wacce zata daukemasa lalurarsa 
Amman kinhanashi kanki sannan kinhanashi aure kenan sokike yaje ya aikata zina bakyajin tsoron cutar zamanine??? 
Idan ma baikwaso maki cutaba wlh kincutardashi kinkuma zalunceshi saikisan amsarda zaki kare kanki ranar gobe kiyama agàbàñ mahaliççinmu
Dayawa akwai mata masu irin wannan halin musamman matanmu nayanzu inhar bazan baka farincikiba bazan hanaka aureba 
Watafa tahanashi hakkinsa idankuma yace zaikara aure tace ba aimata adalciba”” aikoda yayi auren bazaiyi adalciba dan Allah jama a kunga laifinsa??? Wlh konine shi inda nakesamun kulawa nan zanmaida shekata kuma komai tanema zanyimata tunda nima tanabani abunda nakeso
Daga hakan saikuma tafara surutu tace anmaganceshi gashinan yanabin ta kamar bantee
Kullum yana manneda itah kamar jela dasafe bayafita aiki dawuri dadare kuma saiyadawo dawuri Amman bayahaka ranar girkina “” shinwai intambayeki wayajawo hakan??? Kome kikagani kece kikajawo kuma wlh dole kiga banbanciii

Kedakanki kinsan dole asamu banbanciii

Inakirah ga iyayena yayuna abokaina kannena mata muji tsoron Allah musan yanda zamutafida lalurar mazajenmu mukuma ji tsoron Allah musani komai mukayi sai antambayemu yazamanmu na aure gobe kiyama karmu manta da kwancin kabari tsallakar siradii sannan kuma karmu manta gida biyune alahirah akwai wuta akwai aljanna dole kasamu kanka adaya Allah yasamuna cikin tawagar yan aljanna Ameen Allah yasamufi karfin zukatanmu
Gabadaya hankalin lubcy yagama tashi jinyanda Usman yake furtawa wata Kalmar soba itaba wani wawan zagi tafurzar Wanda nikaina bansan ta iyashiba
Dasaurii tayunkura domin komawa aranta tana ayyana bamazata bari wannan tashigo gidan ba”” santsin tayes dakuma sanyin fitsarinda tasaki suka kwasheta tafadii jikake kuuuu
Tasaki wata kara wacce taisanadin dawoda hankalin Usman saman aikuwa dama bakin bene take hakan akafara gangaroda itah kamar kwallon magwaro sai ihu take tana kawowa kasa tabuga kanta dakarfe take tasuma kantaa yasoma fitarda jini daidai kawowar usman wajen
Sam baijiwani damuwa Aransaba kodan tabata masa raine oho”” atsanake yafita yakirah driver dakyar ya iya Kaita mota akawuce da itah hospital
Taji mugun rauni akai akayimatà gyara takuma goce akafa”akasamata Karin ruwa”” washe gari akagyara mata kafar 
Usman yasanardà doctor idan dahali suwuce ayimata aiki kasar waje”” yace aikin mene ai matarka batada wata matsala

.

Yadubeshi darashin fahimta yace bakagane menake nufiba kwanaki sunsamu hatsarine akan hanya towajen gyaranne doctor yace tanada kari agabanta shine dalilindà yasaka takasa haihuwa dakanta
Yabata wadansu magani yace tayi amfani dasu kafin aimata aiki” doctor yayi murmushi yace tanada kari agabanta kuma harka kusanceta tasamu ciki???

.

Inhar agabanta yake bazaka iyah kusan tartaba Usman shiru yayi dankansa yadaure”” doctor yalura dahakan yace barinasa akoremaka kokonto
Nanyakirah wata nurse yace takiramasà doctor Asma.u tace to tafità babu jimawa sukadawo tare yayimata bayaniñ komai itama yanda doctor yafada hakan tafada
Yajuya wajen Usman yace kadaijiko”” yasake kallonta yace kije rum 11 kiduba mana saikizo kimana bayani tace okay tareda fita
Doctor yacigaba da rubuce rubucen shi Usman kuwa saisake sake yakeyi aransa yanata jinjina maganar doctor

Aisha✍🏼

[12:15AM, 2/18/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 40

       By

Gentle Lady💃🏽

Bayan kamar mintuna talatin tadawo taturo kofar tareda sallama”” Usman yana ganinta yadago kansa”” kujerar kusa dashi taja tazauna
Tanafuskantar doctor Wanda shima ya aje alkalamin hannunsa yana saurarenta tace nadubata batada wata matsala”” 
Doctor yace shikenan kina iyah tafiya”” tace to tareda mikewa tafita” doctor yanisa yana kallonsa yace dama ninasan babu wannan ajikinta kamanta a hospital din nan tayi haihuwa biyu inda munga wannan matsalar aidatuni mun maganceta 
Kodama tanada wannan karin ai a take zamucireshi basai andau wani dogon lokaciba haihuwa dabata iyah yidakanta yadanganta dayanayin jikinta sannan kuma yaranta sunada matukar girma kofar jikinta bazata ishesu fitaba 
Idan munga kamar za arasa wani acikinsu shiyasa harmuke mata aiki”” yakai karshen maganar yana kallonsa
Usman yanisa yace nagamsu da bayaninka Amman meyasa doctor yasanardani hakan??? 
Yace wacce asiviti kenan??? Usman yace abuja”” doctor yanisa yace baxaicemaka hakanba inhar ba ita tace yasanarda kaiba ai itah tanajin yanayi ajikinta koda yafurta zata iyah karyatawa
Usman yadago da alamun damuwa afuskarsa yace meyasato zatamun haka??? Doctor yace to wannan amsar abakinta zakajita kabari idan tasamu sauki kuka koma gida saikaji abakinta akwaidai manufaryin hakan
Yanisa shikenan doctor nagode bari Nayi waya yabashi hannu suka gaisa sannan yafito hajiya yafara Kira yasanarda itah sannan gidansu lubcy din
Ranar hospital din yawuni sai marece su hajiya sukazo labila kinzuwa tayi waisunada harda islamiyya washe gari yangidansu lubabatu sukazo harda kanwar mamanta anan suka barta suka koma
Hajiya kwananta daya takoma washe gari aka kai kudin auren Usman gidansu samira mahaifin abdul tareda abokansa sune suka nema masa auren ko hajiya baisanar mawaba danyasan zatace yabari sai matarsa taji sauki shikuma yanason bata mamakine
Ranar litinin aka kai sadaki akasa bikin sati daya duk da bahakan Usman yasoba Amman sunce sunason yin shirye shiryene 
Sai anasaura kwana biyu daurin auren yasanarda hajiya itadai fatan alkhairi kawai tayimasa”” labila dataji labari murna tahauyi harsaida hajiya tabuge ta tace waikinji abunda akafada kiketa faman tikar rawa??
Tace najimana hajiya ba dad ne zaiyi aureba??? To idan banji dadiba mekikeso nayi??? Sainafadawa sahiba muhada faty na musamman

.hajiya takaimata duka taruga tana dariya tace banda shashanci mahaifiyarki tana gadon asiviti harta faty kikeyi??
To naga yanda zakihada Fatyn labila tayi cikin daki tana dariya tace aikuwa zakigani”” tunda lubcy tafarfado tamatsa akaita gida batason zaman asiviti
Doctor yakibata sallama yace takara hakuri hartaji sauki”” saida kanwar mamanta ta rarrasheta akan takara hakuri Usman yanazuwa Amman bainuna mata yasan komaiba saiyayima kamar babu abunda yashiga tsakaninsu

.

Wata zuciya tana rayamata kodai yafasa aurenne watakuma tana karyata hakan dole tanason taga *hatsabibin boka* totaya gata agadon asiviti wazatace yadaukomata madubin
Takaicii yabi yadameta nan take jininta yahau saida akaimata allurar barci dantasamu natsuwa

Washe gari kuwa da azahar akadaura auren samira da Usman akan sadaki dubu Dari hudu lakadan
Ranar samira tamkar tazuba ruwa akasa tasha saboda murna”” wai itace matar Usman” mutumenda yace bazai auretaba hmm gaskiya dolene tagodewa aminiyarta datakaita gun bokanta
Gashi tasamu soyayyarsa acikin ruwan sanyi yanzu dazaran tashiga gidan saikuma tayi yakin fitarda kidahumar matarsa wani murmushin mugunta tasakii
Saina rabaka da itah yazamana bakowacce mace agabanka faceni tasakeyin murmushin jindadi
Da marece motocin kai Amarya suka dauko samrat zuwa gidan Usman ranar ko asibiti baikomaba tunda yaje dasafe

Ranar Usman kam yahuce takaici dankuwa samrat batahanashi kantaba saida yabarshi Dan kanshi koshima yatausaya matane ganin tawahala sosai
Bayan yayi wanka yayi sallah yanamai godiya ga Allah daya sharemasa hawayensa yabashi samrat
Lubabatu tana asiviti batasan wainarda ake toyawaba”” yakanje dasafe kuma yajemata da abinci sambata kawo yayi aurenba Amman tagayanzu kullum cikin fara a yake kamar tatambaya saidaikuma takama bakinta
Kachar tabari takara sati tamatsa dole aka sallameta ta tattara takoma gida ranar kanwar mamanta tatafi
Tunda Usman yafita baidawoba saidare”” lubabatu tana bangarenta kaitsaye bangarensa yanufa yayi wanka sannan yatafi bangaren samrat
Cikin falonta yasameta tachanchade cikin adonta tayi kyau tana ganinshi tamike tatarboshi kiss yamata akumatu yace Amarya Kinsha kamshi
Tayi farida ido tace andawo lafiya”” yace qalau dauko mayafinki muje bangaren maman majeed kidubata tace to tareda wucewa tadauko sannan tafito suka jerah sunayar firarsu ta ma aurata
Tunda lubabatu taji muryan mace gabanta yayanke yafadiii” shine gaba tanabayansa yaturah kofa da sallama lubabatu ta amsa fuskanta tanakan matar da sukashigo tare
Usman ne yanuna mata waje yace tazauna kusa dashi tazauna tareda gaidata Anty inawuni yajiki
Duk daharyanzu lubabatu takasa yarda dagaske usman aure yayi tanakan gadon asiviti tace qalau naji saukii yagidan
Tace Alhamdulillah “” usman ne yace maman majeed ga zainab amaryatace yajuya wajenda zainab take yace zainab ga matata kuma farincikina itace ni nine itah inasonta fiye dakomai banason abunda zaibata mata rai inafatar zakitayani wajen faranta mata rayuwaa
Baki tatabe cikin ranta tace basaika fadamun yanda kakeson matarkàba jinhakan bazaihana inrabakuba
Amman afili murmushi tasaki tace karkadamu zanyima fiyedakai murmushi yayi yace nagode yajuya wajen lubabatu yace ga kanwakinan dan Allah inhar tayi badaidaiba kitsawatarmata kiyita hakuri kuma dukda nibanida matsala ta bangarenki
Tasaki murmushin yake tace karkadamu bazantaba sauyawa ayanda kasanniba fatanadai Kanwata tarikeka amana””” takai karshen maganar tanajifartà dawani kallo nikam nace dàbiyu kenan
Kusa dàkunnenta yaradamatà magana kigodewa kanwarnan taki tanaji dani sosai nasamu abunda nakeso gaban lubcy yabada rass tace nashiga uku:oops: ya akài hakan tafaru????gabadaya tashiga tashin hankali Amman dayake yarduniyace saita wayance

Aisha✍🏼

[1:27AM, 2/18/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 41

       By

Gentle Lady💃🏽

Tace kai Amman naji dadi sosai hakan nakeson ji “”” Allah yabarmun Kanwata”” yace ameeen itakuma samrat kunya duk takamata tamkar tanutse agurin
Fuskarta yashafo yace to yamaganar raba kwana tunda yanzu hartayi sati daya”” rausayarda kai tayi tace kaga banada lafiya haryanzu dasaura
Kawai kabari sai nanda satiii biyu kafin nan nawarke kaikuma kaci amarcinka sosai”” wani dadine yakamshi baisan sanda ya makaletaba yasakar mata kyakkyawar sunba abakinta
Wani mugun kishi yaturnuke samrat kamar tasaki kuka”” lubcy talurah dahakan”” cikin ranta tace ke kenan dakika tsinceshi darana tsaka inakuma gani da nayi shekara shabiyar tare dashi”” mekiike tunanin zanjiii
Afili kuwa saita dantureshi ” murya kasa kasa yace please kibarni naji dimin jikinki Sam shiya manta yana tareda samrat lubcy ce tace baban majeed Kanwata kaifa takejirah naga alama kamar barci takeji
Sai alokacin hankalinshi yadawo jikinsa wata uwar kunyace takamashi yadan Sosa kai sannan yamike yace mujeko samrat”” mikewa tayi tadan kirkiro murmushi tace Anty saida safe Allah yasauwake
Tace ameeen Amarya nagode saida safe gaba tayi abunta yana bayanta harsuka bude kofa tafita shikuma yadawo dasaurii yasunbaci lubcy abakinta nadan tsayin lokaci sannan yadago yalunshe idonsa yabude fuskarta yashafo yana kallon cikin kwayar idonta kamar mai karantar wani Abu

.

Tace kabarta tsayefa”” murmushi yasaki sannan yace saida safe yawuce koda yafita samrat bata wajen dasauri yabi bayanta”” bangarenta yasameta 
Kuka take Amman tanajin motsinsa tagoge hawayenta tasake gyara fuskarta saman gado tahau dasauri tarufe jikinta” da bargo
Yanashigo wa yayi sallama ciki ciki ta amsa masa sallama saman gadon yahaye yadaga bargon yashige ciki”” idanuwanta arufe suke fuskarta bayabo ba fallasa
Ido yakuramata daga bisani yace yahaka kuma samrat??/ tace damefa??? Batareda tabuda idontaba yace hmm yau bazamuyi firabane??? Tadan muskuta nibarci nakeji”” 
Yace tofa wannan shan kanshin wai duk Na menene?? Baki tatabe tace barci nakeji kawai”” yace kuma nibazan barki kiyi barcin ba chakulkuli yasoma yimata
Tasoma kyalkyatar dariya tanacewa bataso yabari”” yace shikenan barikawai inkoma wajen antynki dama dantanason kibani kulawane tabarmana kwananta
Yayi maganar yana yunkurawa daniyar tashi hannutasa tajawoshi yafada jikinta take sukasaka dariya subiyun yace af ashedai anasona ba ason nadaga
Taharareshi cikin sigar wasa tace zanrama wlh dariya yasoma yimata takaimasa dukan wasa hannun yarike suka soma kokawa daganan suka zarce wasa yasauya
Bangaren lubcy kuwa sunafita tatashi da dingishi tarufe bangarenta tawuce kuryan dakinta tadauko madubin tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka*
Cikin second daya yabayyana acikin madubin yanayinda lubcy takeciki kallodaya zakaimata kagano tanacikin Matsala 

.

Kafimma yayi magana tafashemasa dakuka””” kukanda yasaka shikuma yasoma sheka wata irin dariya saida tagaji dakukan tatsaya sannan yace mata menene dalilin kukanki
Tadago raunannun idanuwanta tace inaso akashe wannan matar mutuwa mafi muni waitayama taci nasaran shigowa gidan nan harta rushemun duk shirina
Yace tayanda kikazo masa kisani wannan matar tabanbanta dawadancen”” cikin tsoro murya na karkarwa tace kamarya boka???
Yace saboda itama tanada wani masha hurin boka agunsa tasamu damar ketawa zuciyar mijinki tadusashe haskenki agunshi wannan yasamo sanadi nahanashi kanki dakikai
Dama anan akeso kusamu sabani daganan komai zaifara lokacinda kikafadi aljanine yatureki harkikaita gangara zuwa kasa
Bokan yayi hakane domin karkisamu damar sanardani indau matakiii”” tace tomeyasa baka dakatar dashiba””” kaiyagirgiza yace niban isah inhana wani abunda sukaimaki yasameki ba yanzu haka Suna shirye shiryen yanda za afitardake kokuma ahaukataki
Baki tadafe tace nashiga uku toyanzu yazanyi???boka??? Yakece dawata dariya yace karkidamu aikogaba da gabanta zannuna masu babu maijadani yakwana lafiya
Sannan kisani mijinki yagano lafiya qalau kike saikisan yanda zaki kare kanki idan yatambayeki”” domin ta nanne sukasamu damar karya shihirindà mukai makiii
Dabaki hanashi kankiba dahakan baifaruba”” tashare hawaye tace nibansan abun yakai hakaba nibanason atausayà Mata tundahar tsautsayi yakaita takwanta damijina totajawa kanta mutuwa
Banaso abarta darayuwa”” *hatsabibin boka* yasake barkewa da dariya yace angama kisake yimun magana zuwajibi komenene zakiji bayanie yanzuñ inatsakà dayinwàni aikine nabarkiii lafiyàa
Yanakaiwa nan hasken yafito takeyabace lubabatu tamiyardà madubiñ tasoma zagayen falon hankalinta atashe yaukam tasan koda kwanciya tayi barciii bazai dauketaba

Aisha✍🏼

[9:42AM, 2/18/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

chapter 42

      By

Gentle Lady💃🏽

Taciji dan yatsanta yanzu kenan tashigo gidana tasameni da mijina Amman kuma takeso takoreni?? Hauka kuma to wlh nibazanyi haukaba saidai uwarta tayi
Yanda nakeganinta shiru shiru ashedai munafukace”” tanawani cemun Anty Ashe tasan tuggunda tahadamun nimadai nace taya Usman zaiyi soyayya aisaidai yayi aure domin kore sha awa Amman bazaisake sonwata halitta aduniya sama daniba
Kema kijirah nakusan fatattakarki daga harabar zuciyarsa bazanyi wasaba ko auren ma bazan barshi yasake yiba ballantana yasamu yanda yakeso

Lallai zancen duniya gaskiya duk abunka akwai irinka dubu aduniya
Yanda lubabatu tagadare haka taga safiya ko gyangyadi batayiba dasafe bayan yagama break yayi shirin zuwa aiki harsaida suka kawo kofar fita yatuna da lubcy yace wash tareda dafe kansa yajuya dasauri tatari gabansa tace mekamanta kabari indaukomaka 
Yace wlh namanta bandubo maman majeed ba kinsan batada lafiya” tadan marairaice fuska tace to aiyanzu ka makara kabari saikadawo Mana.
Murmushi yasakar mata yace nagode dakulawa Amman kinmanta company nane kuma nine shugaba koda kinzuwa nayi hakan bazai samarda hayaniyaba
Tace hakane Amman”” shiru tayi tanajin faduwar gaba Amman dole tadake dantagwada ko maganin jiya yafara aiki tace nidai katafi muje”” sake kallonta yayi cikin murmushi yace nipa bance kirakaniba naga alama kamar hawanne bakyasonyi
Kizauna nan nizanje indawo tace bazakaba Allah da mamaki yakalleta yace waike mekike nufine??? Barifa ganin ina lallabaki kidauka banason matata karfa kimanta inada Yaya biyu da itah
Kodama banasonta albarkacin yayanda suke tsakaninmu zankula da itah ballana inason matata 

Idan ma dawasa kike banason irin wannan wasar inkuwa da gaskene kiyi saurin fatattakar wannan tunanin azuciyarki yawuce abunshi
Jiki sanyaye tabi bayanshi gabanta yana dukan uku uku tabbas boka yace inhar tasaka abunnan agabanta harya kusanceta to duk abunda takeso dazaran tafurtashi Usman zaizama maibi yayya agareshi
Shima zaiso abun ufiyeda itah Amman jiya jiya Abu haryaso fara aiki yanzun kuma yaki anya banyi kuskure wajen saka abunba??? 
Kai ina daidai nayishi tanadai iyah yiyuwa ko akwai wata matsalane dole na gaggauta kiran raliya tunkafin wankin hula yakaiga kaini dare
Dawannan tunanin takarasa bangaren lubabatu kusanma tare sukashiga lubabatu tanafalo kwance saman kujerah tadafe kanta sakamakon ciwonda yakemata narashin barcinda batasamu tayiba adaren jiya
Dasauri yakarasa saman kujerar yadagota yana tambayar lafiya””??? Karamin tsaki taja tace wlh kainaciwo yakemun kamar yarabe gida biyu
Samrat tadan harareta aranta tace munafukar banza yataba goshinta zafiii rau yayi saurin dauke hannunsa yace haba meyasa zakimun haka bakida lafiya Amman kikasa sanardani 
Tayi yake tace karkadamu basosai nakejinsaba banaso nadamekune shiyasa fuskarsa duk tasaukarda alamun rashin jindadi
Samrat tamere baki saikuma tace inakwana Anty lubabatu ta amsa dasakin fuska tace ya amarci
Cikin yanga tace munakancinsa amsar tabaiwa Usman haushi ganin yanda take magana cikin gadara
Guntun tsaki yaja yace samomun ruwa kamar bazata amsaba saikuma tawuce kandai kandai kamar yartsana””
Hartafita dakin yasakejan dogon tsaki”” alamu sunnuna ambashi haushi kenan””” yamaida kallonsa wajen lubabatu yashafi fuskarta da murmushi yace kiyi hakuri kinjii
Talumshe idonta tabude saboda zafinda zuciyarta takeyi tace bakomai nifa ba aimun komaiba karma kadamu dawannan
Janta yayi jikinsa yana saukarda ajiyar zuciya”” tayi lamo ajikinsa ahankali tace dadyn majeed dan Allah kayi hakuri akan abunda naimaka
Saitafasheda kuka dasauri yadago kanta yace mekikamun kuma???? Tace ninasan mailaifice awajenka tadanyi Jim abunda naimaka ranar
Nafitone daniyar inbaka hakurii sainazame nafadi ranarnaso sanardakai lafiyata qalau dama nayihakane waidan karnasake samun ciki ganin yanda nake wahala waini anawa wautar hakan dabarace
Saigashi najawa kaina nasan yanzu bakasona ma” tunda kasamu wacce takebaka abunda kakeso “” ninajima natsani kaina Allah yasama inmut saurin rufemata baki yayi yace yakike wannan maganar
Nibanrikeki dakomaiba kuma nayarda da maganarki Amman dakinfadamuñ aisai murika shan magani duk da inason kihaifamun yara dayawa 
Tace Kayi hakurii bankyauta makaba”” yace bakomai indai tabangarena babu abunda zansamu agurin wata dazaisa nadaina sonkii
Tasaki murmushi nagode Allah yabarmuñ kai yace ameeen yasunbaceta saitin bakintaa daidai shigowar samrat wacce takelabe tanajiñ duk abunda sukefadà 

 Shigowarta baihanashi cigaba da sunbatar lubcy ba”” hartakawo wajensu tadauke kantaa gefedaya Tamika mashi ruwan Sam hankalinshi bayagun””
Saida taga yanashirin wuce gonada iri tajaye bakinta hakan baimashi dadiba danyasamu natsuwa 
Duk indayaje bayajin natsuwa matukar batareda lubcy ba”” saiyanzu yaga samràt yace au ashekin kawo ruwan??? Yayi maganar yanakarbà sorry nabarki tsayeko
Ko alamar jinkunyar abunda yayi baiyiba takaicine yakama samrat dayake macece wacce bata iyah siyasaba sannan kuma tanada kishi sosai sambata iyah boye kishinta kokadan 
Tsaki taja tawuce fuuuu tanakàiwa bakin kofa kuka yakwacematà tabude kofa tafita dagudu 
Usman yatabe bakinsa tareda daga kafadà alamar baidamuba

 Karamin towel yadauko yanatsomà ruwan yanadanna mata jikinta tace kanagani tafita tanakukafa!!! 
Cikin nunarashiñ damuwa yace tomezanyimata tunda badukantà nayiba”” zatayi magana yadorah yatsanshi akan labbantà yace bakida lafiya kidaina yawan magana yacigaba da abunda yàkeyi ahankali zàfiñkan yaraguuu
Idanuwañta suna lumshe tace katashi kabita dan Allah yayi murmushi yace waike meyasà kikacika damuwa dawanda baidamu dakeba????
Tabude idonta tace saboda matarkace kumani komai kakeso nima inasoñsa””” cikin tausayawa dakuma soyayya yashafo fuskartà yace wai anya za asamu irinki aduniya???
Kallifa kigani tsakitamun saboda inakulàda matata tanagani kuma bakida lafiya kefa harkwananki kika barmataa Amman waihartake kishiñki kebakiji haushintàba datari kemaki miji tsayin satii biyu
Aràntà tace nikuwa naji haushi bana nunawane kawai afili murmushi tayi tace aini natsufa nabarma yara aikishi bashine so ba abunda akekiràh so kasoduk abunda masoyiñkà yakeso

Aisha✍🏼

[12:13PM, 2/18/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 43

       By

Gentle Lady💃🏽

Yace Amman bakowacce mace tasan wannan ba ko??? Dankuwa dakowa yasani aida samrat kwata kwata bazatayi kishinkiba
Kodayake hali badayaba”” tamurmusa tace lokacintane taci yarintarta “” murmushi yayi yace yarinta da kishi aibazaiyiba yamike yadauko mata maganin ciwon kai yasauka kasa yahadamata tea tasha sannan yace sukoma cikin daki
Tace aikifa zakaje”” murmushi yasakar mata yace karkidamu dakinsamu barci zantafii yayi maganar yanajan hannunta suka shiga dakinta

.

Yakwantarda itah yanashafa bayanta ahankali”” cikin yan mintuna kalilan barci yashureta damakuwa barcin takeji
Bangaren samrat kuwa tanafita tayi bangarenta tanata darzar kuka”” abunda yake kasa gareta takwakwaloshi tayar tana hara rarsa tamkar shine yayimata laifi
Lallai tsuguno baikareba tana takamar tashigo gidan Usman asaukake ashebatayi komaiba yanda take tunanin yanason matarsa abunhar yazarta tunaninta
Wayarta tadauko takamo lanbar raliya tasoma kirah”” saida takatse tasake Kira sannan tadaga tafashemata da kuka
Cikin tashin hankali tace raliya inacikin matsala Dan Allah kije kifadawa mamana wlh aikin nan data bani baiyiba
Raliya tace bangane baiyiba wajenwa ta karbomaki maganin??? Tashare hawayenta tace wajen bokanta nima dai bansanshiba kuma wlh nayi duk yanda tace
Raliya tanisa tace tomenene nakuka kuma?? Kodai kinyi halin nakine nasanki dashegen kishin tsiya
Tashare majina tace haba raliya kinsan meyamun kuwa???? Tace inakuwa zansani basaikin fadamunba “” anan takwashe komai tasanarda itah
Tace haba aiko zuciyar dutsece dani dole inji haushi agabanafa yahau tsutsar bakinta kamar yasamu mintiii
Raliya tafashe da dariya hartana rike ciki abun yatunzurah samrat saitasake fashewa dakuka tace yanzun sakayyar dazakimun kenan duk irin abunda naimaki nikuma infadi bukatata kihauni da dariyar mahaukata bakomai nagode sai anjima
Tace please karki katse wlh badariyar mugunta nakemakiba ina mamakine kisamu mace damijinta harda yaranta Amman kifita kishi
Tace to aikishi halittace kikasani ko itah ba ahalicceta dakishinba””” tayi maganar tana harare harare kamar raliyar tanakusa da itah
Raliya tace kowacce mace dakikagani tanada kishi akan abunda take so damadai batasonshine zakifadi hakan

.

Amman kinsan tanasonsa tundahar tahaihu dashi kawaidai kishin watane yafinawata kuma bawai finshi yayibaa kawaidai akwai masu boyenasune
Wannan shine babbar matsalata dake rashin boye kishinki menene yakashe maki aure dafari bawannan mahaukacin kishin nakiba
Kisani komai maganinda kikeyi”” muddin kinada kishi sosai maganinki bazaiciba”” kishi yanarage karfin soyayya azuciyar miji
Bawaikuma kinuna bakya kishinba yasan kinayi Amman saikidanne kiga yanda matarsa tayi kincefa tana asiviti akayi aurenku Amman datadawo maimakon tatada fitina saimatace tayafemaku kwananta
Tabaku harsati biyu kusha amarci atunaninki tagaji damijinne??? Kodaya kawaidai tasan komai narayuwar tafiyada danamiji
Anan zandanyi magana akan mata masu shegen kishin tsiya watakishin nata kamar badiyar musulmaiba
Kisani kishi mafarin sakine domin duk macenda tafaye kishi dawuya kaga aurenta yarane ba asaketaba “” nikaina matanda nasan ansaka gameda mugun kishi bansan iyakarsuba
To kintada bakin kishinki adole kekawai zakizauna damiji kuma anfisamun haka awajen uwargida tunkinayi mijin yana lallabaki karshema yabuge iskanki

 Ninasan wata wlh tanatare damijinta baida arxiki sunatare haryayi kudii lookacinda yadace tazauna taci arziki akan yakara aure kishi yaturata tahau bala I taki kwantarda hankalinta 
Tundayayi aure baida kwanciyar hankali kullum cikin fadatake da amaryar tunyana lallashiñtà haryagaji yagano itace batason za man lafiya
Zancenda nakemaku yanzu wlh yasaketa saki daidai har uku dadaya daya akafara koda yasaketan takoma gida idan aka sulhunta tadawo maimakon tagyara hali saitadorah daga inda akatsaya
Abunda saki yakenuni jankunne ne idan anyimaki daya saikiyi hankali Amman ayimaki harbiyu sai ancike sannan kidora hannu aka🙆🏿 kice nabani Na lalace
 Shin mezaisa kafin hakan tafaru kiyiwa kanki karatun tanatsu??? Ni mata kunabani mamaki dayawa sunsanifà Amman basa aiki dasanin saisuyi aiki dazuciya kusani duk wacce take aikida zuciya lallai zatakaita gahalaka imma mata imma mazà domin zuciya abokiyar shaidance bayada wajen zama facekusa da itah domin abukadan zairayamata yikaxa yikaxa
Kuma kunsan shaidan baya sanyawa ayi alkhairi saidai akasin hakan idankuwà haryasakà kayi toyanada manufaryin hakan zai darsamaka abun azuciyarka dukdanfa kakauce hanya
Ya Allah kakaremu damuda zuriarmu dagafadawa tarkon shaidàn kahana kunnuwanmu jinsautin kidansa Allah kakaremanà zukatanmu da imaniñmu Ameen

Aisha✍🏼

[7:33PM, 2/18/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 44

        By

Gentle Lady💃🏽

bayau nasaba fadamaki hakanba kamar inakara cewa kicigaba tashare hawaye tace toyakikeso inyi.

.

Nikaina bansan sanda raina yakebaciba bana iyah juran ganin wani tareda abunda nakeso musamman Usman danban hadashi dakowaba
Raliya tace hu um abunnaki babbane tonidai yanzun mama ta aikeni idan nadawo zanbiya saina sanarda ummar hakan yayimaki???
Tayisaurin gyada kai tace yayi Amman Dan Allah kicemata taje yauyau din nan danni banaso narasa mijina tace karkidamu zansanarda itah idankuma yakasa sainasake karbomaki inda mukaje
Tace shikenan sukai sallama tana aje wayar taji tashin motarsa ta window taleka tana kallonshi watakan saiyanzu yaga damar fita takai kallonta kan agogo shabiyu saurah tayi kyacci aisaina rabaku bazan dauki wannan ba 
Cendinma da akafitardani tafi karfina Amman wannan daganinta sokuwace cikin sauki zanfitarda itah dawan nan tunanin takoma takwanta
Bayan kwana biyu dafaruwar hakan lubcy tasake kiran *hatsabibin boka* bayan yabayyana tace maganarmu taranar wlh boka nakasa samun sukuni kokadan inaganin kamar takusa rabani damijina”” 
Dariya yafashe da itah wacce taisanadin girgizawar madubin saida yadade yana dariyar sannan yagintse fuska yace”wayafadamaki akwai bokanda ya isah yayi jayayya dani 
Yasake shekewa da dariya sannan yadauko wani madubin yashafa yayi yansurutunsa saigawata wuta tayi tartso saiga bokan ya bayyana acikin madubin daure cikin sarkaa
Yanacikin mawuyacin hali yanuna mata”” yace kinganshinan yana ajiye acikin kurkukuna nakarkashin kasa”” babu wani mahalukinda yataba shiga ciki faceni 
Sannan kuma duk Wanda nasaka aciki bazai fitoda raiba saida najamasa kunne akan kodatazo karyasake yamata aiki
Amman saiyayi jayayya nikuma Na aika dakarun aljanuna suka daukomun shi”” yanakaiwa nan yashafa madubin bokan yabace
“” yamaida kallonsa”” wajenta yace naturah daya dagacikin aljanuna yayi shigar bokan domin nasamu labarin sunakan zuwa wajensa yabasu magani akan mijinki yadaina kulaki karshema saiya koreki
Yanisa dalilinda yasa mukai hakan zanturah aljani hayyanul zairi domin ya magance matsalar 
Tagyara zamanta tace kamarya boka??? Hannunsa yadaga yasoma kiran hayyanul zairii saigawani haske yabayyana kafin kyaftawar ido saigawani kyakkyawan aljani
Yabayyana ciikin shigar bil Adama kamarshi sak Usman lubcy tazaburah bakinta yanarawa tace wannan ai mijinane
*hatsabibin boka* yasake kecewa da dariya yace wannan dakikegani bamutum bane aljanine shine Wanda zaigama maki aikinki cikin saukiii
Lubcy tayi tsuru kamar tasaki fitsariii yacigaba zanturashi wajen kishiyarki azuwan mijinkune”” cikin rashin fahimta tace to ainikuma bazan banbance tsakaninsuba karfa asamu sabani
Yasake shekewa da dariya yace awajenki fuskar bokanta zakigani cikin kyakkyawar shiga mijinkima haka sauran mutanema haka
Amman awajenta zataganshi mijinki kullum zairika zuwa yanadaukarta sunafita unguwa kowasaiyasan dahakan ranarda mijinki zaiganta aranar aljanin zaikasheta yashanye jininta tareda bokanta saiya sawa motar wuta
Kowa zaidauka hadarine sukasamu sannan kowabazai zargekiba itakuma zatadauka aikintane yaci yayi shiru yana kallonta
Sannan yace dangane damijinki kuwa tunda dakinta yake kwana zamuhada maki wani maganie gobe gobe kibabbatar tashashi
Dazaran sunkebe adaki zatarika sakin wata irintusa maishegen doyi”” idankumà takwanta kafinsafe zatayita fitsariii 

.nasan mijinki babu abunda yatsana kamar kazantaa cikin kwana biyar zamumaidatà kàzama
Mijinki bazaisake shiga dakinba daganan hayyanul zairi zaifara aikinsaa Amman kafin nan sunce kituromàsu kayan aikii
Zakiga abunda kikeso”” tawashe hakorah tace gobe gobe zakagansu godiya nake daganan yabace tamiyarda madubinta
Washe garikuwa tacewa Usman tanason zuwa gidansu sajida tadubata batada lafiya “” sosai yasotabari yakaita tace ah ah aitasamu saukii zataje dakanta
Yabata kudiii masuyawa tàyiwa sajida sayyyar kayàn jinya kaitsaye kasuwa tanufa tasiye dabbobin Shannan tabiya gidan sajida sukasha firah
ice cream tasiyo tazo dashi gidan ta ajeshi yahuce saida taga maganin tabarbada tabarbada aciki tayamutse tasaka cikin fridge yayi kankarà
Dama sunadàn tabafirah akasa kafin yadawo tasaukomasu dashi”tabata daya tasoma shannata””” itama tafara shaa
Tace kaigaskiya akwài dadi Anty idandawañi kikaromàn”” tace ashedai kinasonsa sosai bari nàdàukomaki

Aisha✍🏼

[9:07PM, 2/19/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 45

       By

Gentle Lady💃🏽

Mikewa tayi tahausaman tana kallonta ganin tahaye tamaza tawarware wani Dan kulli na magani tazuba daidai inda lubabatu tatashi tamiyarda kullin saitin zanenta takulle
Tagyara zamanta tacigaba da shan ice cream dinta”” lubabatu tasauko tareda ice cream ahannunta taxauna tamika mata sanan tasamu guri tazauna suka cigaba da labari
Ba ajima sosaiba lubcy tace barci takeji zataje takwanta” tayimata saida safe tahaura sama takwanta abunta
Ita ma kaitsaye bangarenta tanufa tasake sheka wanka tadauko ragowar maganinda aka karbomata wajen boka tashaa babu jimawa dashansha taji kaman cikinta yasoma mirdawa
Tadan dafe cikin zuwa cen saitaji tusa tadan karkace kafarta tusar tafito suutttt suuttt tasa hannu tana kore warin tusarr 
Ba afimintuna gomaba tasake dage kafaa tusar tafito buuuut buttt tayanzu tadara ta dazu wari sau hamsin
Wanna karon saida ta Dade hancintaa”” motar Usman taji tashigo gidan dasauri tatashi tadage labule tareda fesa turaren daki 
Aranta tace danasani banci waken nan yaudayawaba gashi duk yabatamun ciki”” sannu sannu warin yafita koda usman yashigo kaitsaye bangarenshi yanufa 
Saida yayi wanka yashirya yayi bangaren lubcy yasamu tayi barcii saiyawuce bangaren samrat
Yana saka kafarsa bangaren yaji wani bakon al amari wani shegen doyi kamar Yakoma saikuma yayi tamaza yashiga dakin tareda sallama
Tanasaman gado tanata mutsuiniya domin wata tusar takeji

Saman gadon yazauna yace nashigo yau bansameku a faloba”

Tace ah wlh cewa tayi barciii takejii nikuma nagaji dazama nidaya shiyasa nadawo daki””” tamike dasauriii yace inazaki kuma???
Hartakai bakin kofa tace inazuwa Dan Allah harda dangudunta tasauko kasa tasaki tusarta tanata matsar ciki wai idan daragowar tusar tafito 😂nikuwa nace tusa bakashi bace samrat
Tadanjima wajen sannan takoma dakin tareda ragowar warin”” bayan tazauna yasoma jinwani chanjii yadan bata fuska yace samrat wannan kuma warin menene??? Tunsanda nashigo nakejinsaa sama sama
Tace eyem umm umm inajin berane yamutu adakin nan nima inajin warin sa sosai”” shiyasa naketa fesa turare tayi maganar tareda daukar tirare tasoma fesawa
Yayimata kallon rashin yarda yace berah kuma samrat agidan nan ??? Tunda nake gidan nan bantaba ganin berah yashigoba
Tayi saurin gwatseshi tace aishine dalilin dayashigo yasaka yamutu wlh berane maganarta tayi daidai dasurbuno wata tusar wacce batasan dazuwantaba 

Babu shiri Usman yadade hancinsa
Yana kallonta yanda itama tarufe hancin yace umm lallai dole kirufe hanciii wannan shine beran dayamutu????
Tsuru tamasa da ido uwar kunya takamata”! Yace mekika cihaka samrat yabatamaki ciki??? Cikin jin nauyi tace wlh rabon ayi nadafa wake jiya nacikuma nasan bayashafamun lafiya batamun ciki yakeyi 
Yanisa tareda cire hannunsa daga kan hancinsa yace Amman dakin kirani kinfadamun aisai insiyomaki magan” kafin yakarasa furta magani tasake sakin wata
Aibaisan sanda yazama natsayeba saigashi bakin kofa yacemata night baiko juyoba yawuce”” tayi tsuru yau Wake yatonamun asiri ina zaman zamana””
Turare tadauko takwanta dazaran barcii yasoma figartaa tasaki tusa tsabar warin tusar saiya farkarda itah 
Usman kuwa yanafita dasauri saida yakai bangarensa yasaki hannunsa dagakan hancinsa yaja iskaa yasaukarda ajiyar zuciya aransa yace wai ashedai tusar mata doyine da itah wannan abun aisaiya kashe mutum”””
Yasake nisawa nikam bazankomaba dannima idan nayi wasa cikina zai lalacene gabanza”” dawan nan tunanin yakwanta yaukotakan abinci baibiba danyasan kodayacishi saiya amayardashi
Bangaren samrat Kuwa tarasa dalilin bacin cikinta duk datasan wake taci amman warin tusar yayi yawa ahakan taketa fesa turere duk sa inda tayi tusar
Kafin safe tiraren sanyaya dakin yakusan karewa””” washe gari tamakara koda tafarka takoma qalau fita tayi tayi break dantasan Usman yajima dafita
Duk lokacinda yatunkari kofar dakinta warin tusar yakemasa maraba hakan yasaka yamadaina shiga tsayin kwana hudu batasakashi a idontaba
Zaune take cikin falo damuwar rashin ganinsa tayimata yawa tana tunanin anya aikin boka yayi kuwa
Kofar dakinta akaturo Usman ne cikin shigar kananun kaya sunyi masifar karbarsa”” yayikyau kuruciyarsa tadada fitowa
Fuskarsa tana kumshe dawani sihirtaccen murmushi tsaye yayi bakin kofa yarungume hannuwansa yajingina dakofar yana jefanta dawani salon kallo nasoyayya maimatukar kashe jikin Wanda akayiwa
Itakanta tayi mamakin ganinsa alokacin””” cikin sanyin murya tacemasa sannu dazuwa”” yace yauwa sammmratt yanda yaja sunanta harkarkashin zuciyarta tajiii talumshe idonta tabude tace ka karaso mana”””
Kafada yamake yace bayan kinki kitaso kiyimun welcome bayankuma kinsan wajenki nazo”” tadan zaro ido tace nikuma???
Kaiyagyada ahankali yace sosaima inawajen aiki gabadaya narasa natsuwata jinake kamar zanhaukace idan bansakaki a idonaba
Saiyanzu danaganki nasamu natsuwaa “” aranta tace wow maganina yafara aikii tayi Farida ido tace kaidai kodai wajen Antyna kazo
Tsakiii yaja yace nibata gabana wlh nitunfarko danasan akwai irinki mezaikaini aurenta atsarina nibanason mace maikiba sannan banason macenda tafaye fari sosai nafison Dan daidai kamardai ke
Yakai karshen maganar yanajifanta dawani kallo maisaukarda kasalaa”” itakuwa dadi duk yakumeta ganin tayi shiruuu yasaka yatako zuwa inda take yazauna juyoda itah yayi tana fuskarntarsa yace Yanaga kinyi shiru
Tarausayarda kai bakomai yace so bawan nanba yanzu mekikeso ayi”” cikin shagwaba tace yawotakeso akaita yace bakida matsala tashimuje damakuwa ashirye take mayafinta kawai tadauka sukafito
Falon kasa sukasamu lubcy tanaganinshi tace anzo gurin “”” juyawa yayi kamar baigantaba saida samrat tace bakaga antyba???
Yace idanma nagantà mezanyi mata nibata gabana muje please” cikin murmushi tace Anty zamudanje yawo”” itama murmushin tamiyar mata tace tosaikundawo azomun dayan tsaraba
Usman yaja dogon tsakii yawuce fuuuu samrat tawuce kandai kandaii ita aladole gamai miji saimundawo antyy
Tace to adawo lafiyaa sunafita lubabatu tatintsire da dariya hartana tafa hannuwa saida tasoma hawaye 
Sunafita yan aiki sukafara kallonta da mamaki dama sunga lokacinda yashigo kuma yacemasu wajenta yazo Amman sundauka yayantane saigashi sungansu cikin yanayinda zainuna soyayya sukeyii

Aisha✍🏼

[8:22PM, 2/20/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 46

      By

Gentle Lady💃🏽

Hannunta tasagalo cikin nashi harsuka kai bakin motar””” yabude mata tashiga shima yazagaya yashiga sannan yatada motar” yayi hon maikulada get din yabude masu yafitaa”””
Suna hawan titi tasukarda nannauyar ajiyar zuciya “” yakalleta yace yadai?? Talumshe ido tace wlh wani farinciki nakeji danasameka
Yanakallon titi yace dagaske???? Tace sosaima kuwa”kaifa???? yacenima fiye dahaka wani dadine yakara kumeta
Yace ina kikeso mufara zuwa???? Tace zoo yace angama””” gidan zoo sukafara zuwa ko ina tana makale dashii sunhadu damutane da dama harwadanda tasani tana gabatardashi amatsayin masoyinta abun alfaharinta
Kamar suce to mijinkifa??? Saikuma sukyale yinin ranar sunyi yawo harsun gaji saigoshin magrib yadawo da irah gida yana saukarda itah yace zaije sallah nansuka rabu tayi cikin gida cikin yanga shikuma yakoma motarsa
Yaja yafita yanahawan titi yabace batt dashi da motar”” dayake ranar baranar gurkinta bane wasa wasa kullum aljani usman saiyaxo suntafi yawon gari
Tuni samrat takara kyau tayi haske abunta” abudaya yake damunta duk yanda tamatsu dason Usman yakusanceta yakii abun yasoma damunta
Yaukam takuduri aniyar duk yazo sukafita saitasan yanda zatayi yabiyamata bukatar ta dawannan tunanin tawuni
Yanazuwa kuwa tace yajirata tayi wanka tafito daga ita sai dangalallen towel saiwani kwarkwasa takeyi agabansa”” ido yakura mata shikansa tadimautar dashi Amman bazai safa alqawarinda yadaukarwa sugabansaba koda zaiyi hakan sai mijinta yagansu tare
Duk yanda taso tadauki hankalinsa Sam baidamuba hartagama yau shigar kana nan kaya tayi sun bala in matseta komai najikinta anagani tadauko wani fitsitsin gyale tayafa tafesa turare wasu takalma masu matsakaicin tsayi tasaka”tajuyo takalleshi shimadin ita yake kallo tayi fardayan idanuwanta tace yakaganni????
Wow So beautiful”” kinganki kuwa tamkar wata tauraruwa gaskiya nayi dace dasamunkiii” tasake sakin murmushi tace tomuje sukafito tana makale da kafadarsa yanzu ko lubcy bataiwa magana suketafiya
Bangaren Usman kuwa yauyakasa zaman office wata matsananciyar sha awa take damunsa saboda yakwana biyu baijegun samrat ba saboda doyinda yakeji
Itakuma lubcy duk dayagano kalau take yashareta danyakudira aransa inhar ba itah tanuna tana ra ayiba bazaisake nemantaba abunda baisaniba lubcy ko ajikinta bataki suyita zama ahakanba
Yaso daurewa Amman yaji ina Dan maararsa tamatsamasa key din motarsa yadauko tarreda turare domin yakare kansa da warin yasanarda ma aikatan wajen zaije yadawo
Kaitsaye gida yanufa yayi hon maigadi yaduba yaga kowaye gabansa yafadi ganin Usman sannan yadawo dakallonsa ciki wajen samrat dataketa zubawa wani shagwaba
Muryar Usman yaji yanacewa sani waime kakejirah??? Kabarni anan?? Cikin rudewa yabude masa kofar yanatunanin mekuma zaifaru yau
Yanakunna hancin motarsa yagansu ido yazaro waje”” yanakallonsu da mamaki”” ahasale yataka burkii yafito kamar walkiya daidai zaibude mata mota sushiga Usman yadafe murfin motar yace malam wayekai??? Kuma mekakeyi anan ???
Mutumen yajuya wajen samrat yace wannan kuma waye??? Inakika kwasoshi??? Tashagwabe murya tace haba sweetyna ni inazansanshi yanda kaganshii nima hakan naganshi wlh bansanshiba
Usman yayi kururuwa yachakumo wuyanta”” yashakee yace nikikecewa baki saniba to wlh yaukoni koke saina kasheshi mutumen yaturreshi dakarfii yace matar tawa zaka kashe???
Wlh dakuwa ka aikata babban kuskure barganin nakyaleka da itah tsawon lokacii inason matata”” Usman baki bude yake kallonsa yajuya wajen samrat wacce tamakale jikinsa yace kifadamun samira waye wannan???
Cikin daga murya tace mijina nemana maisona kuma maison farincikina”” saunawa zanfadamaka banasonka natsanekaa waimenene yakawoka gidan nan yanzu????/
Tsaki taja takalli mutumen tace mujeko sweety nagayana nema yabata mana lokacii wai ma inazamuje yau””” kaitsaye yacemata hotel tayi ihun murna yauwaa masoyina takaimasà sumbata akumatu sannan taballawa Usman harara shikuma yabudemata kofa tashiga yazagaya mazauninsa sai murmushi yakeyi yauyagama aikinsa yatada motar ganin basu bude get ba yasoma hon kafin yayunkura hartafito tace kai sani Dan iskanci baxaka budemana kofaba tsofaffun munafukai saura kukara gaba kuce kunga wani yazo gurinà tajatsaki takoma cikin motar
sani jikinarawa yabudemasu yaharba motar kantiti tundaga Usman masu aiki dakuma lubabatu wacce hayaniyarsu tafito da itah tareda kawarta sajidaa tsaye suke kowa yana al ajabin wannan abun Usman kasa magana yayi raibace yawuce cikin gidan ko sannu dazuwan da lubcy takemasa bai tsaya amsawaba
Shikam yaga jarabta duk macenda zai aurah saiyasamu sabani da itah haryau baiyi daceba
Bangaren samrat kuwa sunafita Usman dinta yace wai waye wannan mutumen??? Baki tatabe tace barshi wani tsohon saurayinane wlh bansanma waye yanuna masa gidanaba murmushin gefen bakii yayi
Kaitsaye wani babban hotel suka zarce Yakama masu dakii tundasuka shiga tamakalemasa damashi irin wannan ranar yakejirah yamorewa jikinta kafin yashanyemata jini
Kaitsaye yasoma sunbatarta harsukakai kangado wani yanayi tasamu kanta acikinsa Wanda batasan konameyeba dagahaka batasake sanin komaiba
Hayyanul zairi yakoma ainahin suffarsa ta jinnu sannan yakusanceta samrat batasan mekefaruwaba saida yagama abunda zaiyi sannan yadafata suduka sukabace
Samrat sanyitaji yana ratsata ahankali tabude idonta cikin wani dajii tagansuu ga bokan akusa da itah zabura tayi tanajada baya tace kaiwaye??? Ina mijina??? Kodai Usman Dan yankan Kaine????
Bokan yakalleta ahasale yace wazai amsamaki wadan nan tambayoyin naki??? Kuka tafashe dashii tace Dan Allah karka cutardani banmaka komaiba kamiyardani inda kadaukoni
Dariya yafashe da itah maitsoratàrwà dagabisani kuma saiyafasheda kuka maitsuma zuciyaa samrat abun yatsoratata tuntana jadabawa hartadake tamatso kusa dashii tace kaiwaye???mekakeyi anan Kuma meye dalilin kukanka da dariya alokaci daya???
Bokan baicemata komaiba saidayayi kukan mai isarsa sannan yadago yakalleta yace yake wannan yarinyar kisani bansan inane nanba dangane dani kowaye sanin hakan bazai amfaneki dakomaiba dalilin dariyata shine kekanki nalurah bakisan halinda kike cikiba dalilin kukana kuwa inatsoron namutu bansan mezan tarar acikin kabarinaba
Tayi saurin tarar numfashinsa tace mezaisa bazaka sanardani kaiwayeba??? Yace saboda bazaki fita ananba kingakuwa babu amfanin kisanii
Zaburah tayi tace mezakamun??? Kasheni zakayi??? Menaimaka tana maganar tana kuka kaiyagirgizà mata yace nikaina mutuwar zanyi mezan kàrudashi idan nakasheki????

Aisha✍🏼

[9:31PM, 2/20/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 47

      By

Gentle Lady💃🏽

Tatsagaita kukanta tace wayene zaikasheka??? Batareda fargabar komaiba yace Wanda zaikasheki”” idanuwa tazaro waje tace laifin me kaimasu????
Yadanyi jim sannan yace sunana uwaisu nakasance nidayane awajen iyayena suna matukar sona sundauki son duniya sundora akaina bakamar mahaifiyata batason tagakomai yatabani
Mahaifina baida hali sosai saidai yanada danrufin asirinsa kwatsam sai Allah yayiwa mahaifiyata rasuwa mahaifina ya auro wata azzalumar mace batada imani kokadan bata tausayina nikuma gani sangartacce bansan komaiba na ilimin boko ko arabiya
Matar babana duk abunda takemun sainarama domin ni mugune Na iyah mugunta bana yarda kowa yacutardani dataga takasa komai dani harbokanta baiyi nasara akainaba saitasa mahaifina yaturani almajiranci
Muna zaune asokoto sai akadaukeni akaturani Maiduguri nikuma tunda aka kaini sainafara biyar yara munazuwa yawo nasake hinjirewa inasake yinwayo mukaballe dawani yaro jabir zuwa tarabà
Dagacen mukawuce jos yawomukaitayi harmuka samu wani boka yasoma koyamana bokanci”” abokina Wanda muke tare mundade muna harkar bokanci harmuka kware sosai saimukadawo zariya dazama
Acikin wani jeji kusan duk dare mukan hadu muyi tadi dani dashi kusan abunda yarabani dagida nafada bokanci matar ubace shima haka
Munakan haka saiyayiwa wata mata aiki itakuma kafin tayi aikin sai mijinta yakamata shine yatutseta saita sanardashi Wanda yayimata shine takaishi wajen abokina
Dayaje yayimasa wa azi sai abokina yadaina wannan harkar kuma yasameni akogon danakeda zama yayimun nasiha dayake shiyafini ilimin addini danshi yanada sani sosai
Nikuwa sainace nikam bazandaina harkar bokanciba saboda anan abincina yake sainayi amfani da maganar mutane dasuke cewa duk sana arda kasamu kanka acikinta to itah Allah yazaba maka
Babuyanda abokina baiyiba domin ganardani harkarnan batada amfani kuma tanada hadari Amman nayi burus nasa auduga natoshe kunnuwana
Daya nace yana fadamun Allah yace kaza yace kaza natashi afusace na soma tsibbona domin in halakashi saiyafara wadansu Abu yana daga hannuwa sama
Sambansan meyake fadaba saidai nagane addua yakeyi domin natabajin malamin da aka kaimu makarantarsa yanayi take sainaga wata guguwa maikarfii tataso tarufemun ido
Dani dakayan tsibbona aka watsamu gefe anan nasuma saidai nafarfado naganni yashe agefen kukar banga abokina jabirr ba”” yanisa daganan natattara nakoma ilori saboda nasamu labarin wani boka acen
Acen nasake shahara da aikin bokancii lokacin natura aljani yadaukomun matar babana nadaureta akogon kuka nayita amfani da itah hartamutu nayihakanne domin narama cin mutuncinda tayimun
Nadade INA aiki dabokan saiyazo yamutu dalilin mutuwarsa kuwa yajadawani bokane Wanda ake kirah *hatsabibin boka* shine yakasheshi yakwashe komai na sihirinsa nikaina nasamu labarin hakanne awajen wani aljanina kabusaa
Daga lokacin saina tattara nadawo kaduna inamai bakinciki kuma naraya araina sainaga bayan wanann *hatsabibin bokan* nayiduk bincikenda zanyi domin nagane ainahin inama yakeda zama Amman nakaa duk bokancina bantaba ganin wani hatsabibi irinshiba yabatarda komai na sirrinsa babuwanda yasan takamaiman indayake saifa masuyimasa hidima cikin rawar murya tace tonikuma menaimashi???😨 
Yace kishiyarki lubabatu itatace akasheki kirjinta tabuga tace matar Usman???? :oops:Yace kwaraikuwa yacigaba
Kwatsam watarana saiga mahaifiyarki tazonamaki aiki”” yanisa bansan kishiyarki tana daidagacikiñ masuzuwa wajen *hatsabibin boka*ba naimata aikii nafarko tabaki kekuma dake dakawarki kukaje wajen wani bokan
Bayan bikinki dashi *hatsabibin boka* yaturo asanardani karnasake nasakeyimaki aiki kuma nawarware Wanda nayi danagane shine yakashemuñ ubangidana sainace aje afadamàsa bai isaba bazan bariba shikuma dayan bokan kawarkii yace yadainà yimàki aiki
Nikuma danaso jayayya dashii aka daukeni zuwa kurkukunsa”” anata ganamun azaba damayausuke jirah suhadamu sukashee dani dake
Yakai karshen maganar yana kallontà hannutadora akaitace nashiga uku lubabatu yazakimun haka”””🙆🏿 uwaisu yace kidaina kiran sunanta domin bazai amfaneki dakomaiba sai bakinciki”” 
Cikin kukatace kakirah aljanunka sufitardamu mana”” murmushin yake yayi yace dazan iyayin hakan danayi tun lokacindà nake kurkukunsa amman kisàni tunranarda abunyàfaru dukà aljanuna suka tsere yanzun haka sunkoma karkashiñsa
Abokina jabirr yayi aure ya hayayyafa hayayyafa Yakoma wajen iyayensa yanzun nasan yama mantadani tundani nabijirewa umurnin ubangijina aidole inga badaidaiba:(
Samrat tace waikana nufin zaunawa zàkayi sukasheka??? Bayankuma munadà damar guduwa?? Kaga katashi mugudu danñibazan zauna akasheni abanzaba
Yace karki wahaldà kanki wajen gudu danbazaki tsiraba abunda yafikawai muzauna mujirah mutuwarmu muguwar hààrara tasakar masaa tace ammankai bàhone wayafadamaka zañmutu ayanzu idanzakàje kataso
Yace ah ah jeki abunkii ammankisani zakidawo”” tace saidaiwatà banibaa dama wandone ajikintà tatankwasheshi tàyañkii saitinda takejiyo wilgin motocii

Aisha✍🏼

[3:36PM, 2/21/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

Chapter 48

        By

Gentle Lady💃🏽

Gudu takeyi kamar ranta zaifita Amman kokadan bataga alamun takusa kaiga titinba””” takara kadan kenan tacikaro dawadansu manyan namun jeji masu matukar girma dakuma tsoratarwa tunda take ko atarihi bata tabajin wadanda sukace sunga wannan namun jejinba
Manyane tamkar giwa Amman kuma bagiwa bace sunada hakorah zagan zagan tamkar hakoran Damisaa harsundara nata dagirma dan tsayinsu zaiyi kamu hudu yawansu akalla sunkai su hamsin naman mutane suketa yagalgala kowa yanajan rabonsa sunayin arba da itah sukayo wajentaa
Wani wawan burkii taci tajuya dagudu maimakon takoma inda tafito saitayanki gefen hagu da dajin tanagudu tana waige ganitake kamar baifi taku uku sukamotaba
Gudu take tanakuka kamar ranta zaifitaa saikuma taji wata mahaukaciyar dariya gabadaya ta karade ilahirin dajin samrat bata daina guduba takusan shafe sa a daya tanagudu sannan tacikaro dawadansu manyan kunamai bakake kirin sukuwa wadan nan kunamai sunada wadansu faratai manya manya kamar fartanya “” da yatsunsu suke yagalgala naman mutum bawai dansuciba ga gawarwakin mutane nan bila adadin
Tunkafin samrat takai gurin tajuyo dagudu tana mai danasanin barowarta wajen uwaisu gashi tawahala gabadaya Kuma hanya tabacemata tayama zatamaida kanta gunda yake

Tanagudu tana kuka kamar ranta zaifitaa chak tatsaya sakamakon abunda tagani agabanta Wanda yafi dagamata hankali daduk abunda tagani abaya..
Wadansu manyan dodanni tagani masu matukar munin gaske kowanne daya girmansa yakai girman karamin daki dazaibude bakinsa bashakka mota zatasamu titi maikyau awajen “” 

.

Idanuwansu manya manya kamar kwan fitila jajir dasu sunada farata irinna damisaa saitin bakinsu akwai wani tsinke mai matukar tsini 
Shisuke chakawa daidai saitin kwanyar mutum suzuke kwanyar kansaa saikaga yafadii ragab

Daga gefensu akwai wasu tarin dodannin basukai wadancen girmaba dazaran wadan nan sunshanye kwanya sukuma zasu tsotse jinin jikinka daganan sujefawa wadansu dasuke bayansu gangar jiki
Sukuma dasun jefomasu zasufara wawason naman jikinka wadansu sucire Kafa wadansu hannuwa wadansu kai kafin kafarga anyi gunsuwa gunduwa dakai tamkar sauroo wadan nan halittun sunada matukar munin gaske
Dankuwa ganinsu kawai zai iyah haifarmaka da hawanjini sunayin arba da samrat sukayo cikinta dasaurii tajuya inda tafito tafi gwammacewa kunamu sukasheta da wadan nan dodannin sukamata
Gudu taketayi tanahaki kwatsam saitaganta tadawo inda uwaisu yake yana zaune yanda tabarshii kusa dashi tafada tanahaki kamar wacce aka jefo
Kuka tafashe dashi maiban tausayi”” uwaisu mezaiyi inba dariyaba yayi ta kyakyata dariya haryana hawaye yana buga hannu akasa tasharbe majina tana kallonsa Tace 
Yanzu uwaisu kana cikin wannan halin harkasamu damar yin dariya??? Hannuwa yayarbar yana kallonta yace to samrat mezanyi??? Konayi dariya konayi kuka nasandai sai ankasheni
Tobagwanda indaraba inmore kafin namutu”” yanunata dayatsa yanacigaba da dariyarsa yace Amman meyadawo dake bayankuma kince bazaki dawoba?? 
Hawaye tashare tace wani bala in aiyadara wani nagwammace namutu anan din dakalar mutuwarda nagano acen kasan duk abunda kaga yakoro bera yafada wuta katabbar yafi wutar zafi
Yatsagaita da dariyar sa yace kingano abundayafi nandin tashin hankaline?? Tace sosaima kuwa anan tasanardashi abunda tagano takarasa dacewa dan Allah kasamo mana Mafita mana domin mukubuta daga wajen nan 
Wlh koda banganiba nasan batasauki zasu kashemuba danbasuda imani tasake fashewa dakuka
Uwaisu yace hanya dayace zata fitardamu idanhar mun iyah abunda malaman makarantar allo sukeyi addua kenan
Tonikuma wlh ko alif bansaniba acikin adduar Amman tayiyu ke kin iyah maizaihana kiyimana kozamu tsira daga hannun wadan nan azzaluman
Ido tazaro tana muzurai yace yadai samrat?? Tahadiye wadansu yawu masu daci tace wlh kilanta kwara kai kataba zuwa islamiyya nikam danake yargata agidan mu 
Iyayena masu kudine sosai danhaka basu damu dazuwana islamiyyaba saidai babana yadauko mana wani malami yana koyamana agida 
Dana kwatanci malamin zaizo sainashige bandaki bazansake fitowaba saina kwatanci yatafi babana baisan hakanba 
Mahaifiyata kuma babu ruwanta saboda itakanta batasan komaiba waccema takezuwa wajen boka atsammaninka tasan addini???
Saidai Duk abunda yashigemata duhu taje wajen boka tasanar dashi idan narantsemaka banyi karyaba ko alwala ban iyaba inadai wankawa inda naga mutane sunayi idankuma zanyi sallah bana karanta komai
Saidai nakama dungura goshina sallar ma taganin damace danbanayi sai idan inaganin mutane kowajen buki dankar ace banasallah
Amman yanzu rabona dasallah tunda nayi aure gashi lubabatu batayi itama dako awajenta zan iyah koya “” takai karshen maganar tana kallonsa
Yace tokawai kigyara zaman jiran mutuwarki domin kuwa hanya dayace zata fitardamu yaukinga ranar zuwa islamiyya ..
Yaune karatun islamiyya zaiyimana rana sanin dokokin ubangijinmu shine zai taimakemu adduar Neman tsari daga azzalumai bamu iyah komaiba Hakika mutuwace tadace damu domin kuwa rayuwarmu batada wani amfani nayi danasanin barowata makarantar allo a yau
Samrat tace kadaina cewa mutuwarmu tafi amfani idan mukakoma gida aisaimushiga islamiyya
Yayi murmushin yake dagabaya kenan aibakida wata dama niyanzu kallon gawarwaki nakemana kisani Allah yabamu damarda zamuyi aiki da itah domin neman ilimi Amman mukai watsi dawaccen damar 
Hausawa sunacewa idan kasamu rana tokashanya garinka niyanzu bansan iya adadin mutanenda Na haukatarba wadanda sukamutu tasanadina
Bazan iyah kirgasuba”” nasan kema hakanne ta share hawaye yanzu kenan mutuwar zamuyii??? Yace bamakawa Kuwa”” tace yanxu lubabatuce tasakani cikin wannan halin laifin menaimata???wlh saina fadawa duniya abunda take aikatawa
Uwaisu yatari numfashinta yace idan kinrayuko??? Karfa kimanta rayuwa guda dayace dazaran kinrasata shikenan duk Wanda yamutu bayadawowa
Tasake fashewa dakuka tace idankuwa namutuuu anan wlh sainazama fatalwa nakasheta!!!!

Aisha✍🏼

[6:20PM, 2/21/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 49

      By

Gentle Lady💃🏽

Dariya yafashe da itah yace fatalwa ko?? Basai ruhin naki yatsira daga dukan da zakisha akabariba bari kiji kafin kedin kifadi hakan matar babana kafin tamutu saida tafurta hakan yafi sau ashirin
Kisani wannan abunda yasamemu sakayyace tun aduniya munga sakamakon abunda muka dade muna aikatawa”” 
Wlh samrat alokacin bansan zanyi nadamaba bantaba kawo akwai wata rana dawani zaiganamun azaba makamanciyar wacce naganawa matar baba naba
Arana daya nakan sadu da itah fiye dasau goma”” duk lokacinda naji bukata ta tasomun haka zanbiya bukata bayankuma nagama inyimata shegen duka
Abinci kansa akasa nake ajiyemata saidai tarika cinta tanaci kamar dabba”” duk da itace silar lalacewata nasan nacutarda itah 
Saitayi kwana biyu banbata abinciba kuma baburuwana datana jini ahakan zanbiya bukatata da itah hartamutu nasa aljanu sukadauki gawarta suka kaiwa namun jeji
Samrat tace Amman gaskiya kai bakada imani”” yakada kai yace bazan musamakiba dankuwa bansan ma menene imaniba”” dani dake aikuma duk daya tunda kema gashi son zuciya yakaiki ga halaka kema wayasan iya adadin wadanda kika kashe
Shiru tayi tana kallonsa dankuwa maganarsa gaskiyace mijinda tafara aurah matansa biyu tazubawa guba sukaci suka mutu
Tahaukatarda mata uku ciki harda Yar uwar mijinta dataga tasamata ido saigashi ya auro wacce tafita iyah hatsabibanci 
Itakuma duk datana magani kishinta yafiye yawa saigashi waccen tarinjayeta mijin yasaketa Allah mayasota bata kashetaba Tanisa hakane uwaisu nikaina nasan na aikata abubuwa 
Zaiyi magana tace mubar zancen hankalina bakwance yakeba inatunanin ta ina mutuwarmu zata riskemu agaskiya dazanfita anan akwai abubuwa dayawa dazanyiii
Uwaisu yace duk cikin abunda zakiyi babu Na alkhairi “” takalleshi sabodame yasa kafadi hakan??? Yace saboda halin Dan Adam idan yashiga tashin hankali zaizubarda makamansa yayita Neman tsirah Amman dayatsira zakiga yawatsarda alkawullan dayadauka zaiyi
Samrat batace komaiba”” shima uwaisu baisake maganaba duk abun nan dasuke aljani hayyanul zairi yanakusa dasu yanajinsu ammansu basa ganinsaa
Wani kalloo yakebin samrat dashi yana lasar labba daganan yamike”” yatunkareta uwaisu kawai gani yayi samrat tafadii Tanata mutsuniya”” 
Gabansa yahau dukan uku uku dasaurii yamatsa bayaa”” tuntana motsi hartasuma”” take uwaisu yasaki fitsarii awando danyasan wajenshi zatazo yanzu”” 
Anyi akalla dakika hamsin dafaruwar hakan saiyaga tayi zumbur tamike tanaduban jikinta saikuma tafashe dakuka domin abunda taji kamar Wanda taji lokacinda Usman yake saduwa da itah a hotel
Batagama tunaniba sukaji dariyaa takarade dajin takesuka hau waige waige”” dajin yasoma amsa kuwaa wata murya sukajii maikarfi dakuma kururuwa tasoma fadin “” kumore rayuwarku takwana uku kafin kumutu ayaudin nan nasokasheku. Kamar yanda shugabana ya umurceni amman ni imarda kejikinki wacce nadandana adaxu itace tahanani kasheku zanbarku zuwa kwana uku idan nagama morewa jikinki saina zukemaku jiniiii yasake haukacewa dawata dariyar
Kuma zaku iyah gwada guduwa hanya abudeee take saidai kushirya ganin mugayen namun jejinda zakuhadu dasu karkuyi tsammanin zaku tsira danyanxu haka kuna karkashin wata duniyarne 

Yasake shekeewa da dariya saigawata iska maikarfin gaske tatashi tamamaye ilahirin dajinnn kukanta kawai zai iyah kurmantarda mutum
Tsayin mintuna biyar guguwar talafa saigawani akushi shake da abinciii taredawani koko maidauke daruwaa yace ga abincinan idankuna bukata kokuciii kokuma kumutu dayunwaaa yanagama fadar hakan dajinnn yayi shiruuu
Samrat taduke inda take tasoma darzar kuka itakam yanzu tagammace mutuwarta da rayuwarta
Uwaisu ne yakaraso inda take yaduka yana kallonta yace dama kindaina bannar hawayenki dankuwa babu abunda kukanki zaijawo maki saiwani bakincikin
Yajawo akushin gabansa yace kitaso muci abinciii idanuwanta tadago takalleshi tace abinci uwaisu??? Kaihar kasamu damar cinwani Abu???
Yaushe harzan iyah cinwani Abu”” uwaisu yakalleta da mamaki yace samrat kici kokarkici kasheki zaiyi kwarama kici kirage hasahi idankuma bazakiciba nizanci Dan bazanbari yunwa takasheniba
Maganarsa tabawa samrat dariya tace karfa kamanta mutuwa zakayi ni danamutu hannun wannan marar”” imani wlh kara yunwa takasheniii
Uwaisu shikam yasa abinci gabansa yaci mai isarsa”” ya turah sauran gefensa”” sannu kan hankali duhu yafarayi saihantar cikin samrat tasake duran ruwa tasan tabbas yau anan zatakwana”” 
Gefe daya tamakure gawani mugun sanyi gashi kayanta kananun kayane saiyanzu tayi takaici inama kayan kwarai tasaka sannu kanhankali akafara yayyafo masu kankara”” tuni hakoransu suka fara bugar najuna”””
Usman tunsanda abun nan yafaru baisake lekowa wajeba”” dakinsa yashige kuma yarufe babu bugunda lubabatu batayiba danyabude Amman yayi banza da itah”” 
tagaji dankanta takyaleshi takoma wajen kawarta sukaciga ta maganarsu anan take sanarda itah ai aikin *hatsabibin boka* ne sajida tace haba dama naraya hakan araina sukataba sunamasu dariya
Ranar Usman baiciko abinciba lubabatu dakinta takwana aranar”” washe gari takimtsa tajera abinci a dinner sannan tanufi dakin Usman”””
Bangarensu samrat kuwa kwance nahangosu kamar gawarwaki saboda kankara tagama lullubesu””” ruwa aka kwaramasu masu zafiii wadanda sukai sanadin tashinsu gasanyi gazafiii
Bayan kankarar tasauka dagajikinsu wannan karon ba samrat ba hatta uwaisu saida yafashe dakuka takekuma aljani hayyanul zairi yasoma bushewa da dariyar muguntaa

Lubabatu tanashiga dakinsa tasameshi yagama shirinsa Amman yayi zaune yabuga tagumi shigowarta yasaka yadawo hayyacinsa
Kusa dashi tazauna jiki asanyaye tagaidashi”” yasakar mata murmushi tareda amsa gaisuwarta”” yace kintashi lafiya tace qalau 
Sukai shiru sannan tace katashi ga abincinka yana jiranka”” danguntun tsaki yaja sannan yace wai zan iyah cin abinci wlh damuwa tayimun yawa
Cikin alamar tausayawa tace kayi hakuri”” yanisa toyazanyi idan banyi hakurinba tunda banada naganin damuwata
Rabona da farinciki tunsanda matata Dana aurah acikin mafarki tatafi tabarni wlh inajin kamar tatafi daruhina duk da mafarki ba gaskiya bane Amman nawa nakeganinsa kamar gaske inajikamar natabayin rayuwa da itah azahiri
Haryanzu takanzomun amafarkina tanamun magana Amman dazaran nafarka zanmanta komai abudayane bana mantawa tanayawan cemun indage da addua rayuwata tanacikin hadari
Ashe wannan abunne dazaisameni taketa nunamun”” lubcy wacce tasaki baki😮 cikin tsoro dafargaba aranta taçe kardai sotake tatonamun asiri!!

Aisha✍🏼

[7:15PM, 2/24/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 50

      By

Gentle Lady💃🏽

Tsuru tayi tana saurarenshi ammanfa tashiga rudani dajin maganarsa dole tasanarda *hatsabibin boka* domin adakatarda itah Dan muddin tanazuwa masa watarana zata iyah fadamashi komai.
Kuma duk ranarda hakan tafaru aikashina yabushe dannasan bazaikara zamadaniba”” Usman yace yadainaga kinshiga damuwa?? 
Tayi yake bakomai wlh damuwar kace tahaifarmun dahaka”” yasaki fara a yace gaskiya kinasona sosai tashi Muje indan tsakurah inwuce aiki yanajirana”” 
Tace to tareda mikewa sukajerah zuwa saman dinner din yadanci abincin balaifi, tarakashi yashiga mota saigakiran labila”” cikin fara a yadauka
Yace yarleleta kina lafiya”” tace qalau dad ya kake tunjiya inata jiran naga kiranka Amman shiru banganiba harnakwanta”””
Yadanyi shiru nadakiku uku tace yadai dad ko akwai wata matsalane??? Yace bakomai labila kidai tayani da addua inacikin damuwa wlh
Shiru tayi aranta tace ga babbar damuwar nan ataredakai afilikuma tace dad kodai muzone??? Yalaso busassun labbansa yace ah ah dakinyi zamanki bafa wani abubane 
Tanisa shikenan dady”” hajiya suna gaisheka”” yace ina amsawa zankiraki anjima yanzun zantafi aikine inada meeting yau dakarfe shadaya
Tace to Allah yabada sa a yace ameeen nagode tace love u dad”” yace mee2 takashe wayar tareda saukarda ajiyar zuciya
Usman yabi wayarsa dakallo bayan yacirowayar daga kunnensa”” yamaida kallonsa wajen lubcy wacce take kallonsa yace natafi sainadawoko tace to adawo lafiya 
Tajuya cikin gida tana zancen zuci waiyanzu shikenan labila tayafeta tamkar ba itace tahaifetaba””
Yarinya saikace mai shafuwar aljanu hmm yanzu wamazaice nice mahaifiyarta””” tayi saman dakinta tanata surutu
Bangaren su samrat kuwa tunlokacinda aka watsamasu ruwan zafi sukatashi idanuwa zuru zuru sai sukahau kallon kallo”” 

Take sukaji dariyar tacigaba da karade ilahirin dajin
Uwaisu saiganin samrat yayi tafadi kamar jiya shidai jikinsa sairawa yakeyi gefe yakoma yanata makyarkyatar tsoro
Saida yagama abunda zaiyi sannan tafarfado tanashan matukar wahala duk lokacinda yatara da itah saitagammace yamakasheta tahuta bayan ta farfadone yakawo masu abinci kamar jiya tace bazataciba uwaisu shikam yalakadi abunshi
Zuwa rana dayasake Ku Santarta wannan karon kam dayakawo masu abinci saida taci danyunwarda taji saibayan tagama citadawo tanajin haushin kanta
Dadare suna kwance akan gado lubabatu takalleshi tanasonyin magana tayi shiru yakurah dahakan yakalleta yace akwai maganane??? 
Tace ah yace tokifadamana inajinki”” tanisa dama zancemaka ne haryanzufa samira batadawo gidan nan ba””
Tagefen ido yakalleta sannan yatabe bakinsa yace to shine me??? Kokuma sokikeyi infita nemanta??? Danina aiketa?? 
Tace bahakan nake nufiba Amman ainaga matarkace tanada hakki akanka”” yasake mere baki yace aini tunjiya nagama da matsalarta takardar sakinta tana nan asaman gadonta dazaran tadawo zataganta”” 
Tanisa tanakallonsa tace nidai wlh inaji ajikina ba lafiyaba ina samirah zatashiga agarin nan kuma nakirah wayarta akashe take””
Guntun tsaki yaja yace aisaikiyi nidai karkidameni barci zanyi” idan abun yadameki saikitashi kije nemanta nidai kibarni inyi barci domin banida wata Alaka da itah””
Yanakai karshen maganar yajuya mata baya”” yaja mayafi yarufe jikinsa lubcy dariya tayi ahankali tayanda bazaijitaba sannan tajuya tayi barcinta
Washe gari bayan yafita aiki “” saiga raliya tazo gidan saboda kwana biyu sunata Neman layin samrat basa samu”” tana shigowa suka gaisa da lubabatu tace tanaciki kuwa???
shiru tayi saida tasake tambaya sannan lubabatu tafada mata komai aikuwa tahau zage zage yanzu danrashin mutunci Kawata tabata agarin nan Amman kukasa zuwa cigiyarta???
Duk arzikin gidan nan saikacedai bamutum yabataba atunanina koda dabbace tabata aje nemanta ballantana mutum
Lubabatu tace nikaina saida nayimasa magana tokinsan Abu bakaine kakeda ikon kankaba yace bazashiba ai itah bayarinya bace dazata bata
Kuma bashine ya aiketaba”” raliya tarike kugu tace kicedai baida mutunci to wlh munfishi rashin mutunci kuma bari Kawata tadawo tadaina zama agidan sa dolene yabata takardarta kokuma hukuma tarabamu
Lubabatu tace kwantarda hankalinki basaikunkai wajen hukumaba takardarta tana nan ya ajemata adakinta
Bakisake raliya takalleta tace yasaketafa kikace??? Damuyake zancen tajuya fuuuu tafita tana sababi kaitsaye Dan adaidaita Tatara zuwa unguwarsu samrat
Dama mamartane ta aikota tajiya maganar aikin yayikome dantun ranarda ta aikamata dashi tadainajin duriyarta
Shine takirah raliya tadubomata itah saigashi tasamu wannan labarin gyalenta kawai tarida tadau jaka sukafita taja motarta zuwa dajinda boka uwaisu yake

.

Koda Suka karasa dajin saidai sukaganshi share babu ko alamar wani halitta yataba zama wajen sukayita tambaya a kauyukan dasuke makotaka da dajin
Saidai akaimasu kwatancen wani bokan bayan sunfadamasa komai yayi yandubansa yace wannan aikin yanada hadari bazai iyaba”” dasuka matsa da magiya yace zaibada jininsu ga aljanu dole suka mike jiki bakwari wajen bokanda raliya tacezuwa wajensa sukaje shima yace wannan aikin yafi karfinsa”” sukaita yawo gidajen bokaye dayan bori karshe sukaje wajen wani boka nabakin rafiii bayan sunfadamasa bukatarsu yayimasu yandube dube yace tana raye Amman batacikin wannan duniyar”” hajiya tace kataimaka konawa kakeso zanbaka indai yata zatadawo”” yace karkidamu za ataimaka yasanarda itah turarenda zatakawo dakuma kaji dansai anyi yanka aikine mai wahalar gaske dakuma hadari tace
Itah konawane zatakashe inhar yarta zatadawo yace takwantarda hankalinta takoma gida takwanta yarta’ zatadawo hargida tace tozata bada kudin aikin saiyasaka asiyomasa komai yace badamuwa haka tazube masa bakin aljihunta sannan sukadawo gida hankalinta kwance
Bayan kwana hudu dabatan su”” darana suna zaune duk sun rame sun lalace fargaba dakuma tashin hankali saboda tunranarda aka kaisu dajin kullum kafin safe kankara saita daskaresu saida safe atayardasu daruwan zafiii yaunekuma adadin kwanakinda yadibarmasu”” suncika”” saiyan dube dube suke suga ta inda mutuwar zatabullomasu wata iska sukaga tataso maikarfiii tayiiii samaa wani duhu ya mamaye ilahirin saman dajin take hadari yahadu yayi baki kirin anata tsawa mai firgitarwaa!!!

Kuyi hakuri wlh bansamu damar yin typn dinba kuyi hakuri da wannan

Aisha✍🏼

[6:12PM, 2/26/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 51

      By

Gentle Lady💃🏽

Tuni uwaisu yasoma sakin zawo” sabanin samrat datasoma kuka tanakiran wayyo yanzun mutuwa zanyi
Sunacikin wannan yanayi akasoma huromasu iska tamkar ruwa tafashasshi suna suraci take. Fatar jikinsu tasoma dayewa dakanta””
Dasauri uwaisu yaruga domin yadimauce dayanayinda yakeji ajikinsa”” ganin hakan yasa samrat tabishi sukaita gudu
Guguwarce tatari gabansu take tadauke uwaisu saigashi yana shillo acikin iska tamkar guguwa tadauko karmami”” samrat tasake kwalla karaaa Amman takasa guduwa uwaisu kam sai witsil witsil yakeyi da kafaa
Zuwa mintuna biyar akasauko dashi yafadi ragajab babu rai ajikinsaa idanuwansa sun kakkafe harshensa yafito waje
Wannan yanayin yasake firgita samrat dagudu tajuya tanamai kuka tanawaige waikar itama azo gurinta”” tayi gudu mai nisa daga inda gawar uwaisu take cikibis tayi da usman yashigo jejin
Dasauri tayi wajensa tafada jikinsa tanakuka tace Usman kafitardamu wajen nan wlh mugayene kashemu zasuyi””
Hannunsa yasaka yasoma bubbuga bayanta ahankali cikin rarrashi”” tasake shigewa jikinsa tana saukarda ajiyar zuciyaa
Hannuwansa dasuke cike da kumba “” yasoka mata tacikin bayanta take tagantsaraa idanuwanta suka ganomata usman bakinsa duk yabaci dajini
Kafin tayi wani yunkurii yashanye jininta duka saidai kawai gawarta yayar yakoma guguwa zuwa inda ya aje gawar uwaisu yadaukota sannan yadawo yasauki dawar samrat yatashi sama yabace cikin gajimare
Yau tsayin sati daya maman samrat hankalinta yaki kwanciya kullum takwanta barci saitayi mafarkin samrat tanakuka tanacewa mom yanzu harkinada lokacin kwanciya ??? Nikuma ganinan inashan azaba akan abunda Na aikata aduniya
Duk abunda yafaru dani mom kece sila tunda kika kasa tarbiyartar dani akan addinin Allah ban iya sallah ba bansan yazan bautawa ubangijinaba 
Kisani duk bala inda zanshiga kema kinada linkin nakii yana nan yanajiranki”” hannunta tasaka tace mom shigo ciji zafinda nakeciki tayi maganar tanariko hannunta
Aituni takwallah wata mahaukaciyar Kara tatashi firgigit tasoma bin hannunta da kallo Wanda yayi jajir saboda zafindake jikin samrat datarikata”””
Sai zazzare ido takeyi kamar wacce tai karya jikinta yahaubari dasauri tasauko dagakan gadon tayi waje
Falo takoma tazauna tanata fiffita jikinta wannan wace irin masiface kai anya mafarkin nan bagaske bane???? tarike baki komadai watace takeson korana gidan nan shine tabiyomun tahanyar yata dantaga bayana
Kai aizama baiganniba tamike dasaurii takoma daki tawanko fuskarta tasake shiga tadauki kudi da key din motar ta tayi hanyar dajinda bokanda aka kaisu da itah da raliya
Kodataje tasameshi yana ganawa dawata hajiyar bakin Yar bukkarsa tatsaya””dantasamu bukkar andan sakayata kuma taga mota bakin bukkar hakan yasa tatsaya domin tajirah
Tayi tsayin awa uku awajen sannan taga anbude bukkar saiga matar tafito tana gyara daurin zanenta da mayafi tanacewa saiyaushe kuma boka??? 
Shikuwa yana lasar baki yace kidawo zuwa jibi yamaki ko??? Tace haba boka ai wlh koda kullum kace indawo indai hakan zaihana mijina kwasomun wannan tsinanniyar wlh zanyii
Yawashe hakorah karkidamu hajiya aitunda akai wannan aikin mijinki bashi bakoma saduwa dakowace mace matukardai yakusanceki aduk lokacinda akaimaki wannan aikin 
Yanzu anyi sau uku sauran bakwai Dan aka idar aikin sau goma akeyinsa daga lokacin da aka kammala aikin shikenan kisamu waje kibarje guminki dankuwa babuke bakishiya saidai kiji sunanta awani gurin badai agidankiba!!
Tawashe baki godiya nakeboka sainadawo jibin ta bude kyauren tafito sukaiwa juna kallon kallo da itah da maman samrat tawuce abunta itakuma tarakata da ido ganin babbar mace maijidakanta ta iyah kwanciya dawannan kazamin baki duk goro Wanda bayawanka bakinsa baitaba samun wankiba”” 
Matar babbar motarta tashiga tajata tawuce ko kallon indatake batayiba”” sai alokacin tasaukarda ajiyar zuciya taturah kyauren kofar tashiga
Yanazaune yamike kafarsa saiyanxuma yake gyara daurin zariyarsa yana sharce zufa”” tayimasa gafaradai yace takaraso nesadashi tazauna danwani mugun kyankyaminsa takeji
Yayi yanzane zanensa sannan yadago yacemata meke tafedake??? Cikin muryar damuwa tace akan maganar yata wlh nayi mummunan mafarki akanta yaudin nan”” tasanardashi mafarkinda tayi
Tanagama fadamasa yasheke dawata irin dariya wacce tasaka hanjin cikinta murdawa”” saida yagama dariyarsa sannan yace bahakan mafarkinki yake nufiba kisani mijinki yanason karo aurene!! Gabanta yayanke yafadii
Yacigaba yarki tana nan raye Amman tanacikin wani halii yauyau nakeson tura aljani yadaukota kudin aikinkine sukai kadan aidatuni tadawo
Tace haba boka aiyakamata kafadamun konawane nizan iyah bayarwa “” tanisa toyamaganar kuma yarinyarda maigidana yake nema???? 
Yayi kaki yatofar yace tana nan amman kuma zamuyima tufkar hancii yanzu zakibada dubu Dari uku danaki danata saboda aikin akwai wuyaa
Tayi shiru sannan tace to gaskiya dari biyune nazodasu saidai idan zakabini gobe gobe zankawomaka yace shikenan Amman kitabbatar kinkawo dankonairah idan babu aikin nan baxai yiyuba tace zankawosu gobe gobe
Yace shikenan tazube kudin tatafi tazubeduka kudin Jakarta sannan tawuce zuwa gida tanaxancen zuci wato baban samrat aure zaikara Amman shine kullum yake lullubeta da dadin bakii humm hartakai gida tana tunanin””
Dadare dukkansu sunacikin falo suna sauraren tashar labarai”” tanagefe zaune danhaushin baban samrat takeji”” 

 

Salatinda taji yanayi yasaka itama takai dubanta akan TV gawarwakin wasune subiyu akan mota sunkunburah kuda saibiyarsu sukeyi
Daidai akanuno fuskar samrat gabadayansu sukamike suna rabka salati banda mamanta datadorah hannu akatarabka ihu nashiga ukuna asheda gaskene kinmutu??? Baban samrat yabita dakallo cikin mamaki yajuya wajen yayunta yace sutashi yanzun suje asivitin
Babu bata lokaci yaso sosai sufara biyawa tagidan Usman”” saiyayyunta sukace sufara daizuwa su tabbatar inhar itane
Dasukaje kafinma abarsu suga gawarta saida suka wahala”” sungani kuma suntabbatar itace tomeya hadata dawannan mutumen gashikuma bamijinta bane???
Yayanta ayuba yace subari saigobe dankuwa baza abasu gawarba zuwagoben da sassafe suje gidan Usman din hakan akayi ammanfa Daren babuwanda yarumtsa musamman mamanta dataketa kuka
Washe gari ayubanne yajegidan Usman maigadi yafadamasa ana masa sallama yayi mamaki wazaizo nemansa irin wannan lokacin tunda yatunkaro yagane kowaye saiyasha toka
Yakaraso yabashi hannu suka gaisaa ayuba yace yagidan?? Usman yace lfy”””
Ayuba yanisa yace dama nazone akan maganar Kanwata tunkafin yarufe baki Usman yace Toni inaruwaana duk abunda yasameta karku nemeni”” bakisake ayuba yakalleshi saida yakai karshe yanisa yace Amman Usman banji dadin abunda kafadabà yarinyar nan matarkacefa???
Yayi saurin tarar numfashiñsà yace adaba aini nadade dasakintaa yanzunhaka jiranake kawai tadawo wajen kwartancinta taxo takwashemun kaxaman kayanta daga gidana
Ayuba yace kasaketafa kace??? Yace kwaraikuwa kumabata gidana danrabontà dagidannan sati daya hardakwàna biyu  

Ayuba yace ammandai kàibakàsan mutunciba

Aisha✍🏼

[8:07PM, 2/26/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 52

       By

Gentle Lady💃🏽

Yanzun ace samirah batagidan nan tsayin sati dakwana biyu Amman kakasa Neman mu kasanardamu…
Wani mugun kallo yawatsa masa yace dayake Nina aiketa ko anfadamaka ni Dan aiken kune dazanje insanardaku inda take
Duk gidan ubanda taje nibandamuba idan kunganta kufadamata tazo takwashemun kayanta daga gidana tunkafin nasaka yara suyimun waje dasu
Maganar Usman tatunzura ayuba Duk dayana ganin Usman babban mutum ne baihanashi kaimasa dukaba saboda bacin rai
Usman yayi saurin tare dukan”” dadaya hannunsa yarike hannun daya yawanka masa mari”” yace kaiharka isah kazo gidana kace zakadakeni?? 
Aikuwa fadane yakarke tsakaninsu sukasoma jefar juna damasifa kamar zasubuga maigadine da driver sukayo wajensu sunajaye ayuba
Yatuge hannunsa daga rikonda yamasa yace badai nikamaraba wlh kabar takamar ganin kanada kudi sainadaureka komai dukiyarka bakin azzalumi
Anaganinka da suffar babban mutum ashekai bakasan mutunciba”” Sunday yarikeshi yace karfa kaga lefin alhaji saboda balaifinsa bane agabanmu akai komai”” 
Usman yacewa Sunday kubarni dashi nizanyi maganinsa wlh bari nafito yayi cikin gida dasaurii Sunday yaja hannun ayuba yace kazo kafita tunda har kaga ran Alhaji yabaci komai zai iya yi
Shikuma yace babu inda zaije saidai idan kasheshi zaiyi yakasheshi danshi baya tsoronsa

Dakyar sunday da sauran ma aikatan gidan sukafita da ayuba lokacin Usman yafito da bindigarsa kamar wani mahaukacii
Hayaniyar suce tafargarda lubabatu aitana jin masu aiki suna fadar bindiga dagudunta tahau saman tadauko kwalbar tasassautoda kullinda taimasaa
Dasaurinsa yatunkari kofar fita ana rirrikeshi dankuwa jiyakeyi zuciyarsa tanata tafasa masu aikin suna rirrikeshi yana turesu”” 
Lubabatuce tafito dasauri tarike bindigar yajuyo afusace yakalleta cikin sanyin murya tace kayi hakuri Dan Allah alhajii 
Saiya sakarmata bindigar yajuya fuuuu cikin gida tajuya tabi bayanshi Sunday kuwa sunafita yasanarda ayuba duk abunda yafaru gabadaya jiyayi kunya tarufeshi
Dangabadaya masu aikin kowayace hakan akayi harma sukafadi Wanda sukasani Wanda akai ba agaban Sunday ba”” sunday yace babban tashin hankalin yanzu ba asan inda takeba dantunda tabar gidan alhaji batadawoba”” jiki asanyaye yace aitarasu gabadaya sukace tamutu??? Yagyada kansa yanzun abunda yasaka nazoma sanardashi gawarta tana mutuware “” gabadaya sukai zugum yace damuna mamakin waye take taredashi Ashe dama samira tana Neman mazane da aurenta??? Yashare sirarun hawayenda suka saukomasa yabar kofar gidan zuwa asiviti””gabadaya sukabishi da kallon tausayawa suna jinjina Kansu
Dayaje asivitin suka tambayeshi Usman yafadamasu komai kowannensu jikinsa yamutu saikusan azahar akabasu gawar bayan sunzube masu kudi dubu talatin
Aranar akaimata sallah aka kaita makwancinta”” Usman Sam baiji labariba saida aka sake kwana biyu Sunday yake sanardashi
Dayafadawa lubabatu tayita kuka hartabashi haushi”” saida taje tayimasu gaisuwa Amman Usman kinzuwa yayi”” saboda kunyar abunda yayiwa ayuba saida gabaya yajibai kyautaba
Tundaga lokacin Mamar samrat takoma saliha kullum kasameta rike da charbii tasaka akanemo mata wani malami yana karantarda itah
Su hajiya sunsamu labarin sukaimasa gaisuwa dakuma fatan Allah yabashiwata tagari labila kam wata tsanar mamanta tasakeji tundaga lokacin Usman yacire sha awar aure aransa saidai yaje asiviti yasiye magungunan da zaisha domin yarage yawan sha awa
Idankuma tatasomasa saiyasha maganin “” tsayin shekara daya”” dafaruwar hakan watarana dayaziyarci family doctor dinsu akano akan ciwonda yake damunsa

A mararsa yanzu takaima idan yasha maganin baya masa amfani”” saboda yanada tsananin bukata kuma lubabatu babu abunda yasauya awajenta domin sukan kwashe sati biyu bata yarda yakwanta da itah ba
Kuma idan tace bataso dolensa yakyaleta”” suna office din doctor din bayan yagama yimasa bayanin komai yana kallonsa saida yakai karshe yanisa
Yace wannan laifinkane alhaji batunyauba nake sanarda kai shan wannan maganin bazaiyiba kawai Kayi aure shine kawai Mafita
Tunda kanada kudinka ballantana kace bakada kudin auren”” Usman yace doctor bakagane abunda nake guduba wlh niyanzu tsoron aurema nakeji saboda halin matan bawai banada kudin auren ba Alhamdulillah Amman matanne nayanzu kafin kasamu takwarai sai kahawala
Doctor yayi murmushi yace hakane Amman kasan ba ataruwa azama daya dole akwai nakirki nidai shawararda zanbaka kagaggauta yin aure
Dan maniyyi yatararmaka amara”” yanason fita kuma saika guji cinkayan dadi masu saka maniyyinka kara yawa”” idan bakai wasaba wannan abundakake dauka bawani abuba zaijawomaka kwanciya asiviti
Usman yayi shiru nawadansu dakiku sannan yanisa yace shikenan zanyi inshaa Allah katayani da addua”” yace karkadamu sukai sallama yawuce gidan hajiya
Labila Batasan dazuwan saba dantana gidan sahiba”” damadai bajimawa zaiyiba yabarwa hajiya sakonta yawuce
Wannan shawarar Usman yayi aiki da itah Amman abun mamaki dazaran yasamu wacce yayaba da hankalinta sai magana ta kankama yarinya tace bataso tasamu wani said ayanemi yarinya hudu kowacce hakanne tahudu saima da akabiya sadaki tace bataso da iyayenta suka matsamata ganin alhajine maikudi ta nanewa wani talaka sanadin hakan yasaka tashiga duniya
Su awajensu tabijirewa umurninsu basu saniba aljanine ake turomasu basune suke furta hakanba”” Usman kullum zakasameshi masallaçi gayawan azumie alokacinne Sunday ya musulunta””” sannu sanñu abunyasoma damun Usman saiya sanarda dahiru abokinsa””
Dahiru ne yahadashi da habiba”” wacce ya aurah daga karshe yargidan mutunci saigashi batadibo da yawaba tarigamu gidan gaskiyaa
      *CIGABAN LABARI*
Lubabatu saman gadonta tahaye tadauko madubintaa tashafo tareda kiran sunan hatsabibin bokaa shafawarta keda wuyaa saigashi yabayyana kamar kullum
Kirari tasomayimasa tanafasa masa kai yasaki wata shu umar dariya””” itakanta saida tatayashi tace boka aiki yayi kyau saidaikuma maganar yata labila take takenta yasoma isata nifa inagudun watarana tatonamun asiri yarinya kamardai banice nahaifotaba kodaya batabiyo halinaba
*hatsabibin boka* yatsagaita da dariyarsa yace waimeyasa kike shakkune akan aikina” narantse dagirman tsafina babu wani mahakulinda zai iyah fallasa asirinki tundahar kikahada damu bakida sauran bakinciki yarki kuma kimanta da itah komai kikaga tanayi kisamata ido zata iyah fadamaki magana Amman bakinta bazaibata iyah furtawa waniba kodataso fadadin
Tasaki murmushi godiya nake boka toyanzu mezanbayar amatsayin kyautar murna??? Yace abunda kikasaba bayarwa”” tace to gobe zakagansu takehasken yafito tajikin glass din boka yabace tamiyarda madubin cikin jindadi

Aisha✍🏼

[5:44PM, 2/27/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 53

         By

Gentle Lady💃🏽

Yanzukam Usman yafitarda rayuwar kara aure yabarwa Allah zabinsa yasan wannan jarabtace Allah yabashi ikon cinye wannan jarabawar
Zaicigaba da azumie yakumaci gaba dashan magani idankuma harciwon yacijikinsa inkwanansane yakare to Allah yajikansa
Tuni yakauda kai gadukkan abunda yasan zaitadomasa da sha awarsa gabadaya company nsa yasallami ma aikatansa mata baibar kodayaba bayan yabasu makudan kudi yace sunemi wani aikin daban sosai sunji bakinciki dankuwa babu inda ake biyan su albashi mai gwabigwabi sama da wannan company sosai maishi yasan darajar aiki dakuma biyan ma aikata kudinsu akan kari kuma amutunce

 
Baibar mace kodayaba yasaka duka maza”” duk satii saiyayi sadaka yana Neman Allah ya bashi lafiya” Yakuma yayemasa damuwàsa

Zaune yake cikin falonsa sama lubabatu tana gefensa suna kallo wayarsace tahau ringing”” tana gefensa yanadubawa yaga labila cikin fara a yadauka
Tareda sallama ta amsa adaya bangaren”” tace dad 

Barka dadare??? Yace yauwa kina lafiya?? Tace qalau nake dad fatan kaima hakan??
Yanisa insha Allah “” yakaratun??? Shekaranjiya ainakirah akacemun kina makaranta wajen harda” tace wlh kuwa dad abunda yasakama nakiraka kenan
Yagyara zama wani abunne??? Tace ah maganar walimarda za ayi makarantarmu tawadanda suka hardace AlQur’ani dakuma wadanda suka sauke 

Hardar mataki matakine akwai masu hizifi sittin akwai arba in akwai talatin akwai masu a shirin goma dakuma biyar
Daga kowanne aji ni inacikin masu arba in” yace masha Allah godiya tatabbata ga Allah madaukakin sarki 
Allah yataimaka tace Ameen”” wlh naji dadi sosai labila yaushene walimar??? Tace saurah satii uku Amman Dan Allah dad wannan karon kazo yace karkidamu zanzo “” tamarairaice fuska kamar zatayi kuka race sanda nasauka bakazoba ai””
Yace sha kuruminki wannan karon koda tafiya takamani zansoke tafiyar indai zuwan nawa zaisa amanta dawancen laifinda nayi
Dariya tayi tace bakayi laifiba ai kawaidai naga kowacce mahaifinta yanazuwa mata”” yace aikema haka baga uncle Hafiz nanba
Taturo baki nidai dad ah ah kainafison kazo inaso naganka”” yamurmusa tokarki damu zanzo dame dame kike bukata zan aikomaki dakudi saiki siya””
Tace la dad damakabari wlh uncle yasiyamun komai harnakai ankon wijin dinkii”” yace duk dahaka ni ai yakamata nabada tawa kyautar
Tace hakane to dad kabani duk abunda Allah yahoremaka komenene zanji dadi”” yace dagaske??? Kaita gyada sosai
Yace shikenan ga mom dinki”” saida tadan yakuna fuska kamar wacce taji anfadi abun kazanta tace bata mugaisa yace to tareda mikawa lubabatu wayar
Damamaki take kallon wayar tamaida kallonta wajenshi tace wayene?? tasan labilace Amman kuma tundatake labila bata tabacewa abata wayaba shine takeson gazgata abunda taji
Usman yace kinajifa sanda nakirah sunanta to labilace zakugaisa”” Tamika hannu takarbi wayar takara akunnenta batareda tace komaiba
Labila takatsemata tunani tace mom kinyi mamakin jinnace abanike mugaisako??? Hmm bawani abubane kawaidai inason insanardake yarki tahardace hizifi arba in acikin littafi mai tsarkii za ayimasu walima
Yanadakyau kema kisamu kizo walimar kozaki tuba kidaina abunda kikeyi kumakinemi gafaran dad dankuwa kina cutardashi nabarki lafiya
Tanakaiwa nan takashe kiran”” lubabatu tayi murmushi tamikawa Usman wayarsa batace komaiba 
Amman aranta tana jinjiina maganar labila
Usman yanisa yanamai kallonta yace waiku meyasa haryanzu bakwa barin wannan al adar taku waishikenan idan kanada darfari bazaka sakemasa fuskaba?? 
Saikanuna tamkarma bakasonsa alhalinkuma kanason sa wayezaihaifi dayace bayasonsa Amman abunda kuke nunawa yayan fari baidaceba hartakai sukansu basa sakinjiki daku”” lubabatu tasaukarda ajiyar zuciya tace to aihakan mukatashi mukaga anayi ai kunyace bawai rashin soyayyaba”” baki kawai yamere yacigaba da kallonsa
Itama batakoma kansaba tundadai basurutun takeson yiba”” washe gari kuwa ya mata siyayya kaya masu kyau ya aiki driver yakaimata tareda kudi takara wajen hidima 

Tun anasauran sati daya walimar akasoma sanarwa kafafen yada labarai su labila ansha kyau anyi gyaran gashi da itah da sahiba anko sukayi komai nasu iri dayane”” hatta kunshi da akaimasu zanen iridayane
Anagobe walimar labila agidansu sahiba takwana saboda batakarisa hardartaba”” sahiba sai dariya take mata waitafaye son wasane takaimata dukan wasa tagoce tana dariya “” labila tace wlh bawasa bane kinsan baiwa kowa da irin tasa tace hakane”” yauwa sahiba banfadamaki ba gobedai babana zaizo inaso zannuna makishi kugaisa tunda baizoba sannan 
Tace shikenan sahiba Amman kinsan wani abu??? Labila tace ah ah saikinfada”” tayi shiru daga bisani tace wlh tunsanda akacemaki saurah kwana biyu walimar nan gabana yaketa faduwa narasa dalilin faduwar gaban””
Labila takalleta saikuma takyalkyale da dariya tace Allah yasadai alkhairine”” mukam musha biki “” takalleta da harara tace dagafaduwar gaba kuma saikusha biki ?? Tobikin mene???
Labila tana linke kayansu tace kikasani ko wani kyakkyawa zakiyi gamodashi”” tace waini??? Haba sahiba ainayi kankanta dayin aure yanzu sainan gaba aikoke bazakiso nayi aure yanzuba

Labila tace saboda me?? aini tuni nazaba miki miji kawaidai inajiran hukuncin Allah ne yazabamun abunda yafi akhairi nasankuwa kowaye nazabawa sahibata bazataki amincewaba

Murmushi kawai tayi batasake cewa komaiba!!
Harabar islamiyyar cike take makil damutane bakako hangen karshensu gabas dayamma hangu da dama dandazon dalibaine wadanda suka sauke dakuma masu harda
Cen saman dandamali malaman makarantane””gefensu kuma wata babbar rumface shake take damanyan mutane yankasuwa suwagabanni harda sarkin kano yana cikin shigarsa ta alfarma”” gefensa fadawansane sukemasa fiffita gamnoni daga kasashe daban daban duka sun ziyarci wannan walimar domin taya daliban dakuma iyayensu Murnar wannan babban abudasu kasamu nahardace littafi mai tsarkii
Bayan annatsu aka kirah amirar makarantar wato khadija Muhammad domin tabude taro da addua”” 
Wata karamar yarinya naga tataso cikin shigarta ta alfarma tanasanye dahijab harkasa fuskarta lullube take cikin likab kafarta tanasanye da safa shekarunta bazasu haurah goma sha shida ba” tana tafiyarta cikin natsuwa idanuwanta suna kasaa
Takarasa inda malamin yake tadan gurfana takarbi lasifikar tasoma addua Cikin harshen larabcii gabadaya wajen kaji yayi tsitt bayan tagama bude taro da addua takoma mazauninta
Usman gabadaya yarasa natsuwarsa saibinta yakeda kallo tunsanda aka kirah sunanta yaketa nanata sunan aransa
Shikanshi tunsanda anasaura kwana hudu walimar yakejin matsanancin faduwar gaba”” saiyanzu dayaji muryanta yasakejin faduwar gaban tayawaitaa idanunsa suna kanta duk da akwai tazara maiyawa atsakaninsu
Kusada itah watace zaune itama cikin shigar kamar ta khadija tsayinsu zaizo kusan dayasam hankalin Usman bayawajenda ake gabatarda dalibai tundaga matakin sauka har aka kai matakin harda

Aisha✍🏼

[9:35PM, 2/27/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 54

     By

Gentle Lady💃🏽

Akasoma kiran masu harda” tundaga mataki nafarko masu hizifi biyar har akakai kan masu hizifii arba in labila Usman itace wacce akasoma kirah
Usman saiyanzu hankalinsa yadawo jikinsa jin ankirah gudan jininsa yasoma dube dube yaga ta inda zata bullo
Idanuwansa sundauke daga gunda labilar take tacewa sahiba kitayani addua please tana dariya tace kije kawai zakiyi nasara insha Allah”” labila tawuce cikin takunta ahankali saidai yaji tasoma kira a
Sosai yanatsu yana sauraren yarsa harta kammala akasomayi mata tambayoyi akan fikihu da kawa idi wasu hawayen dadine suka sauko akan idanuwansa yakaikaice yashafe yanamai sake godewa Allah daya nuna masa wannan ranar”” 
Bayan tagama akacigaba dakiran sauran har aka kai matakin hardar hizifi sittin akasoma kiransu dai bayan daya” karshe akakirah amerah wato khadija Muhammad tanacikin masu hardar hizifi sittin tunkafin tasoma karatu gabadaya wajen yakaure da kabbara!!
tasoma karatun fatiha acikin daddan sautiii maimatukar sanyi dakuma kashe jiki””tana kammalawa tasoma karanto suratul bakarah gabadaya wajen yayi tsit Usman sai lunshe idonsa yakeyi saboda dadin karatun kowanne harafi tanabasa hakkinsa wajen gunna tafitarda gunna kowanne harafi tana fadinsa daidai”” harwata kasala tasaukar masa””
Yayi nisa wajen tunani hartagama akasoma yimata tambayoyi tana bada amsa daidai bayan takammala takoma mazauninta”” 
Gabadaya wajen akasake kaurewa da kabbara kowayasaurari karatun khadija dole yayi kwadayin inama ace yarsace wannan kokuma yayi kwadayin yasamu mata kamarta
Usman yanadai dagacikin wadanda suka furta hakan azuciyarsu”” bayan ankammala akasoma rarraba kyauta dagukkan dalibai”” inda abangaren masu hardar hizifi sittin khadijace tazo tadaya tasamu kyauta maitarin yawa ciki kuwa harda kujerar makka”” sosai taburge kowa tayanda akabata kyautarta “” saitasoma kuka domin tunawa da mahaifiyarta inama tana raye taga yanda abunda tabari aduniya tazama
Labilace tafito tajata zuwa wani aji tasoma rarrashinta tace haba sahiba wannan fa ranar farincikice menene abun kuka kuma keda zakinuna farincikinki cikin kuka tace sahiba mamana!!
Labila tace Dan Allah kidaina kuka abun alfarine awajen mama ayaudin nan idan akanuna mata yanda kikazama bakuka zakiyiba sukarungume juna suna kuka saikuma akarasa Wanda zai rarrashi wani sunyi akalla mintuna ashirin awajen Amman basudako alamar daina kukan
Yana tsaye yana kallonsu yarungume hannuwa saidai sukaji muryarsa yace kukan ya isah haka shima yana goge guntun hawayenda suka saukomasa
kusan tare suka juya suna kallon kofa labila cikin muryar kuka tace kaiwaye??? 

Khadija takalleta cikin fara a tace sahiba Yayana nefa” ya muktar
Bakitarike tareda murmushi””tace afuwan yayanmu tamaida kallonta wajen khadija tace Amman bakifadamun yazoba ai””” 
Takalleta tace nikaina bansan yazoba danmunyi waya jiya dashi dayakirah kawu cewa yayi baxaisamu zuwaba””
Takarasa wajensa cikin jindadi tafada jikinsa saikuma tasake fashewa dakuka””daya hannunsa yasaka yana bubbugar bayanta cikin tausayawa yana rarrashinta yace menene nakukan bagashi nazoba ???
Idankuma bazaki dainaba zantafi abuna baxansake zuwaba kinkuwa San aikinda yake gabana Amman nabarshi saboda kawai inga farincikinki”” tace nadaina Yayana karkatafi kabarni
Labila tayi tsuru tana kallonsu cikin soda Kauna murmushine kwance akan fuskarta sunbala in matukar burgeta

Sunanta taji anakirah aharabar waje khadija muhammad labila usman Hafsat m shareef “” yayi saurin jayeta daga jikinsa yace kije anakirah”” hawayenta takarasa sharewa tajuya wajen labila tareda murmushi tace mujeko sahiba
Murmushi itama tamiyar mata tariko hannunta sukafita muktar yabisu da kallo sosai yanason kanwarsa dama wannan itace sahibar tata tanayawan bashi labarinta duk da baiga fuskartaba yanaji ajikinsa kyakkyawace
Sunafita wajen yasake kaurewa da kabbara”” tare suka karasa wajenda aka kiraasu khadija takarbi lasifika tasoma yin addua sannan tasoma jawabin muhimmancin ilimin Islam cikin harshen larabci inda labila take fassarawa cikin harshen Hausa”” hafsat takeyi cikin harshen turanci daki daki sukebin komai 
Hakika nayarda

Ilimi wani abune maidadi hakazalika maisanya nishadi azuciya”ilimi gishirine narayuwa”dukkan Wanda yakeda ilimin Islam bazaitaba tabewaba duniya da lahirah Allah yabamu ilimi mai amfani
Bayan sunkammala khadija tayi Yar takaitacciyar nasiha gameda muhimmancin bin iyaye cikin harshen Hausa wadansu sunyi mamakin jinyanda take magana dahausa Dan Sam basuyi tsammanin tanajin hausaba
Birrul walidaini”” wato biyayya ga iyaye “” Yakamata yan uwa musan mahimmancin iyaye arayuwarmu musaman uwa!! uwa!! uwa!!!
Kasani komai kazama aduniya karkasake kawulakanta iyayenka babban abunda yake damun al ummarmu ayanzu dayawa mutane basusan darajar iyayensuba 
Baka daraja iyayenkaba toballantana kuma iyayen wani”” shinkokasan dukkan cigaba yana samuwane idan harkabi Allah da manzonsa sannan kuma kabi iyayenka””
wasu yayan babu ruwansu sudai kawai suyi abunda yake gabansu karkumanta wahalarda uwa takesha tunsanda kake cikinta ranarda zata haifeka wahala cikin wahala harkazo duniya tayi dawainiyar shayardakai sukabaka ilimi Amman dagakarshe saikayi tamkar bakasan dawainiyarda sukai dakaiba”” shinkayiwa kanka adalci kuwa??? Kokadauka basuda hakki akankane??? Kamar yanda akace matarka aljannarta tana karkashin kafarka haka kaima taka tana karkashin ta iyayenka inhar kasaba musu bazaka shiga aljannaba.
Sukuma iyaye Susan tarbiyarda zasu baiwa yayansu domin suyi alfahari dasu”” abun alfaharinkane kaji ance wannan Wanda yacinye gasar musabaka aidan wanene bazakaso kaji ance ankama danka yana kanta daureba kokaji ance aidanka babban danfashine 

 Ku kyautata atsakanin Yaya yenku 
Manzon Allah yanacewa awani hadisi”” 

 وقال صلی الله ءليه وسلم ساووا بين أولادكم kusasanta “atsakanin yayanku a
Awani hadisi manzon Allah yabacewa وقال صلى الله ءليه وسلم إن من حق الولد ءلى والده أن يعلمه الكتا به و أن يحسن اسمه و أن يزوجه إذا بلغ رواه النجار

 

Yanadaga hakkinda yarataya akan iyaye bisaga yayansu ya karantardashi littafinshi ma ana alqur ani maigirma “” kokai zaka karantardashi kokuma kakaishi islamiyaya la ba asan”” ” ka kyautata sunansa”” sannan ka aurardashi idan yabalaga”” 
 

 Aisha✍🏼

[2:09AM, 2/28/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 55

      By

Gentle Lady💃🏽

وقال صلى الله ءليه وسلم من بلي من ه‍ذه البنات بشيء فاحسن اليه‍ن کن له ستر من النار Wanda yakeda Yaya biyu mata ya kyautata agaresu ma ana ya tarbiyantardasu harsuka girma ya aurardasu zasu zame masa sutrah daga daga wuta””” 

Inakirah ga iyayena maza da mata dasu tsayu akan Yaya yensu kusan kalar tarbiyarda zakubaiwa yayanku domin duniya tayi alfahari dasu
Kukasance kuna ciyarda matayenku abinci na halat domin samun Yaya nagari masu biyayya agareku sannan kusa ido akan yayanku abokansu makotanku yanda suke mu amala 
Musamman wannan zamanin damuke ciki wai uba zaiyi zina dayarsa Yaya. Yayi zina dakanwarsa makoci yayi zina da matar makocinsa da yayi zina da mahaifiyarsa wa iyazubillah waihartakai anayiwa kananun yara fyade kayiwa yarshekara biyar ko uku ko hudu fyade bisabillahi mezakaji??? Banda zalunci kuma dakai za ayiwa yarka ko kanwarka yazakaji??? wai wane irin lokacine mukeciki ayanzu babu shakka manzon Allah yayi gaskiya
Duk ilimi ya bace acikin alumma barna tayawaita adoron kasa tobala ine zaiyita shigowa gashinan kuwa munagani
Duk wannan tsadar rayuwar damuka samu kanmu aciki mune mukajawa kanmu”” kashe mutane sai yawaita yakeyi anmaida rayuwar mutane tamkar takiyashi kiyashima yafita daraja
Lalacewar Yaya iyaye sunada hannu dumu dumu yaro tunyana karami ake koyardashi yanda zaibi Allah Amman wasu iyayen koda sunga yaro yanayin badaidaiba wani yayi magana saisuce kukyaleshi kuruciyace
Wai kuruciya bayankuma ayanzune yadace kuginamasa komai tayanda zai zauna akansa
Manzon Allah yanacewa awani hadisi”” هفزل غلم سغرن كنكسن بلهحر .وهفزل رحل بااد ميغبر كل كتبت ألل ماء kiyayewar yaro karami kamar rubutune bisa dutse kiyayewar babban mutum bayan yagirma kamar rubutune bisaga ruwa
Idankukai rubutu akan dutse zai zaunane daram bazaitaba gogewaba sai idan zakusaka nakiya ne kufasa dutsen kodakuwa kunyi hakan za asamu wani gefen darubutun Amman bazaitaba goguwaba
Amman kugwadayin rubutu akan ruwa kugani shinzai tsayakuwa???? Tokamar hakane idan yaro yagirma babu abunda zai iyah tsayawa akansa
Hausawa sukance icce tunyana danyensa ake tankwasashi idankuwa yabushe bazai tankwasuba inharkuwa kamatsa saidai yakarye 
Tokamar hakane idankukaga yayanku sunayin abunda baidaceba kutsawatar masu kuma kuzaunardasu kununa masu illar yin hakan kusanardasu irin azabarda akeyiwa mai aikata hakan tozasuji tsoron aikatawa
Kundarsa masu tsoron aransu dashikuma zasutashi””misali kamar yanda akecewa yara Karya haramunne maikarya Dan wutane
Zakaji yara harsunayi dawaka idansukaji wani yayi karyaa”” ya Allah kashiryar mana da zuriyarmu Kaine maishiryarda Wanda kaso idan kashiryarda mutum babu mai iya batardashi idankuma mutum yabace babu mai iyah ganardashi gaskiya sai idan kaso
Allah kakaremana yayanmu da jikokinmu yan uwanmu musulmai duka kabamu ilimi mai amfaninmu duniya da lahirah kadoramu akan tafarkin gaskiya”” kasadamu da rahamarka”” رب اغفرلي وتب ءلي إنك أنت التواب الغفور. سبحا نك الله‍م وبحمدك أشه‍د ان لاإله إلاأنت أستغرك وأتوب إليك 
Tamikawa malamin lasifikar”” gabadaya akakaure wajen da kabbara

Cikin natsuwa suka karasacikin taron wajen muktar tatafi”” inda akarufe taro da addua”” akasoma watsewa saiyanzu labila taga dad inta”” yana nufosu”” da fara a afusarka””
Hajiya tace yan kaduna saukar yaushe??? Yace kafin afara nakaraso labila tagaidashi ya amsa yana tayata murna” Dukawa yayi yagaida hajiya ta amsa cikin sakin fuska yabawa Hafiz hannu suka gaisa yace kaga yarka ko banyi tsammanin haka takeda kokariba
Hafiz yace hakane Yaya ai ina shirye shiryen turata saudiya tayi karatu acen inshaa Allah sai anyi alfari da itah
Majeed yace uncle nikumafa??? Kansa yashafo yace sha kuruminka aihardakai za aje inajirane kaima kasauka kamar yanda tasauka saika miyarda hankali sosai idan kanaso katafiii
Hajiya tace tomuwuce gida ko”” labila tace nidai hajiya kukarasa nizan jirah sahibane mutafi tare”” Usman yace wainikuwa wacece sahibar nan???
Kullum maganarki sahibadai sahibadai yaudaikam inaso naga wannan sahibar 

Tace zakaganta kuwa dad”” yace lallaikam inason ganinta dankam nalurah bakaramin so kike mataba
Hajiya tace inama kasan haka kayanda kasiyomata cewa tai bazata sakasuba saboda bakasiyo biyuba da itah da sahiba saboda Hafiz yasaba komai zaisiyo dolensa yasiyo biyu idankuma bahakaba bazatayi amfani dashiba””
Yace um lallai naga alama tokutafi muje gidan gabadayansu suka karasa wajen motarda Hafiz yazoda itah”” 
Labila kam wajen sahiba takoma tacemata suwuce gida”” dayake bawani nisa dasubane tsakanin gidansu da islamiyya Amman akwai yartafiya
Motar abokin muktar suka shiga zuwa gida”” anakaiwa gidan taja hannunta tace muje kigaisa da babana””
Juyawa tayi tace Yaya inazuwa yanzun zandawo yace to ba Matsala sukawuce cikin gidan gaban khadija sai yatsananta bugawa
Zaune yake shikadai acikin falon wayace ahannunsa yana latsawa tunda sukayi ido biyu da ita tasanne kwayar idonta kasa wani abune takeji yanamata yawo ajiki tareda harbawar kirjinta
Taresuka duka tace inawuni daddy wani sanyine yaji yaratsashi aransa yace ya salam badai khadija itace Kawar labilaba??? 
Labila takatsemasa tunani tahanyar cewa dad ga kawata sunanta khadija Amman yangidansu sunakiranta da safna saboda sunan mahaifiyartane
Nikuma inakiranta sahiba dad inasonta fiye dayanda nakeson kaina itah marainiyace mamanta tarasu tana zaunene ahannun kawunta tareda yayanta
Sannan takalli khadija tace sahiba ga babana””” abun alfaharina kuma maisharemun kukana”” yaudai kinga babana ko
Khadija tasake dago kai karaf sukasakeyin ido hudu dasauri tamike jikinta yana karkarwa”” tace sahiba bari naduba wani Abu
Tayi gaba Usman yabita dakallo hartashige dakin labila yasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya labila tana kallonsa Da kuma yanayinda yashiga
Yadawo dakallonsa wajen labila saiyaga shiitake kallo nantake yaji wata irin kunya takamashi”” murmushi labila tayi tace dad barinaje gurintaa

Aisha✍🏼

[12:27PM, 2/28/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 56

       By

Gentle Lady💃🏽

Kasace mata komai yayi saboda kunyarda yaji”” mikewa tayi kawai tana murmushi tawuce abunta””
Bangaren khadija kuwa tanashiga daki tafada akan gado tadafe saitin zuciyarta inda yake harbawa tamkar kirjinta ne zaifaso zuciyar tafito

Tanacewa 

لا حول ولا قوة إلا بالله

   kasa samun natsuwa tayi duk da jero adduarda takeyi bataji wani sauyiba azuciyarta “” tagumi tayi yayinda tashiga wata duniyar daban murmushi tasaki afili batasan sanda bakinta yafurta gaskiya kyakkyawane
Daidai shigowar labila tace baban nawa?? Kunyace takama khadija tace nifa badawata manufa nafadaba ina nufin yanada kyau Ashe shikika biyo ba ummaba””” 
Nantake annurin fuskar labila yagushe”” khadija talurah dahakan tace meyafaru sahiba??? Kodai bakiji dadin abunda nafadabane??? 
Labila tace bakomai kawaidai naji raina yabacine!!! Tatari nunfashinta dakikaji na ambaci umma ko??? 
 Waime yasaka kullum naketa jankunnenki akan muhimmancin umma agareki?? Tanisa kodayake tunda kinada itah araye bazaki gane mahimmancinta ba saikin rasata
Labila tace sahiba kenan wlh dama nice ke dama tun wajen haihuwana tamutu”” khadija tayi saurin rufemata baki tace a uzubillahi Allahumma izna min hazal kalamiki”” kinkuwasan mekike fada???
Kinaso yayanki sucemaki hakan”” wasu hawayen takaici tashare tace inhar banzama nagartacciyar uwaba bazanga laifinsuba koda jifana sukai da dutse
Khadija tadafata tace kome kikeji agameda ummah hakuri zakiyi itace dai mahaifiyarki kuma kinsan babu Wanda zai karkare hakan
Labila tanisa tace babban takaicina kenan danashigo cikin tsatsonta inama ace babana ba itah ya auraba har aka haifeni
Khadija tabata fuska tace sahiba waime yasakike hakane kin isah kisauya hukuncin Allah ne”” kisani kowa dakikagani aduniya bai isah yagoge kaddarar saba 
Ballanata ummah batada wata makusa kawaidai dankina yarfarine yasa batajanki ajikinta tokuma bakece kawai akayiwa hakanba kigaggauta Neman tuba awajen Allah 
Tashare hawayenta tana maineman yafiya awajen Allah astagfirullah wa atubu ilaihi”” aranta kuwa tana mamaki yanda take kasa sanarda wani damuwarta
Khadija ce tajawo hannunta tafada saman gadon”” tace kiyi hakuri kinji sahibata wlh banason inaganin damuwa atare dake kwata kwata kasa samun sukuni nakeyi
Labila tayi murmushi nadaina sahiba kinga ya muktar fa yana jiranki muje narakaki indawo wajen dad
Tace to tareda mikewa “” aranta tanata addua Allah yasa bayacikin falon labila tanagaba tana binta baya
Yana nan kamardai yanda sukabarshi Amman yadorah kafarsa daya akan dayaa sabanin dazun dayake danna waya yanzu idanuwansa kyam sunakan kofardasu labila suka shiga
Suna fitowa yatada kansa zuwa fuskarta take idanuwansu suka sarke cikin najuna dasauri khadija tasaki likaf yakarasa rufemata yan idanuwanta dama sune kawai abude
Wani iri yaji aransa kardai yarinyar nan tagano itah nake kallo??
Muryanta yaji tanacewa dady sai anjima””” yadago ahankali yakuramata ido saikuma yasaki murmushi yace to Khady kigaida gida” taresuka fita da labila yarakasu da ido

 

Khadija kafarta har sassarfa takeyi”” sunafita Usman yadafe kansa yace ya salam meyake shirin faruwa dani wannan wane irin abun kunyane zuciyata takeson kaini gareshi kawar yata!! Yayi saurin kawarda tunanin aransa tunkafin yasamu matsuguni
Wayarsa yadauko yakunna kira a yadorah akan kunnensa yadan kishingida saman kujerar babu jimawa barci yadaukeshi awajen
Hajiya yaji tana tashinsa yatashi yayi sallar la asar gashicen anyi kirah mikewa yayi tareda mika yawuce zuwa dakinsa dayake gidan
Yana nan tsaf dashi tamkar akwai mutum aciki toilet yashiga yawatsa ruwa sannan yadauro alwala yawuce masallaci acen yahadu da Hafiz
Bayan sundawo ahanya yake masa maganar yaushe zaikoma america yace wani sati ainakusa gamawa inhuta yawon nan basonsa nakeyiba
Usman yace Allah yataimaka aini namatsu kagama in hannan tamaku dukiyarku”” Hafiz yace habadai Yaya niba fa kasuwanci zanyiba aikin gamnati zanyi 

Kawaidai kacigaba dakula dasu
Yana dariya yayi maganar Usman yace naki wayon nauyi yayimun yawa akaina bazaku ragemunba”” Hafiz yace aigirman Kane””Kaine fa babanmu dole kakarbi girman”” Usman yace naji waikai yamaganar auren inata zuba ido naji tsit karfa yarka tarigaka aure???
Kakuwasan dakaji kunya” Hafiz yasosa kai yace aini karamin ubane bazanji kunyaba tunda Ban isah aureba”” Usman yaharareshi yace ahakan??? 
Tokodai kafitarda mata ko inhadaka da Abu mai kuli kuli da awara”” baki Hafiz yarike yace abun haryakai cen tokwantarda hankalinka dazaran nadawo zakaji komai
Usman yace sauran watanawa??? Hafiz yace bakwai koyanzu walimar labila tadawo dani danbanaso ayi bana nan” 
Usman yace shikenan munadai zuba ido daidai sunkai kofar gidansu sukashiga tare sunafira suna raha hajiya bakaramin dadi takejiba idan taga yayanta cikin farinciki 
Saman kujerah suka zube labila tadauko masu abinci sukaci sukahau firah sai shida saurah Usman yayi haramar tafiya harbakin mota suka rakashi yawuce yana daga masu hannu
Labila batakoma gidan sahiba ba saboda hankalinta yanakan yayanta shima washe gari tunda safe zaikoma””

Agogon Nigeria yabuga karfe biyu nadare alokacinda nasan kowa yayi nisa cikin barcinsa saikuma masu ibadar dare. Bakajin motsin komai saikukan karnuka dasuke cikin layin
Inkadauke Usman dayake tsaye yakai gwauro yakai mari tunsanda yabaro kano yakasa samun sukuni cikin ransa”” komai yakeyi fuskarta yakegani sanye cikin nikaf haryana ayyana suffarta yanda zata kasance
Gabadaya ta dabai bayemasa zuciya dakuma tunaninsa hatta abinci idan zaici fuskarta yake hangowa akan plate wanan wace irin makauniyar soyayya ce???? Kawar labila yafurta ahankali komawa yayi saman gadon yazauna yadafe kansa wanda yayimasa nauyi

 

Kai bazaitaba yuyuwaba wlh tunwuri dama kindaina son abunda bazakitaba samun saba dawanne ido zan kalli labila ince inason kawarta ???
Taya zata kalli maganata?? Yakamata inhana zuciyata afkawa inda baichanchanci yazama muhallinaba “” wata zuciya tace masa taya hakan zai yiyu kokamanta soyayya batayin shawara dakowa 
Yayinda zatashigeka batadubà matsayi kochanchantar Abu”” yace idankuwa hakane gaskiya bataimun adalciba saboda abun nan bazaitaba yiyuwaba”” 

Wata zuciya tacemasa yiyuwa kai saidai inhar bakace kanasontaba koda kaki fada Dole sai zuciyarka ta tilas taka 

Yace wlh karyane wannan abun kunyar badanibà ganin abun yanason haifarmasa da damuwa yayisaurin kawarda tunanin abun yafaskara tashi yayi yadauro alwala yasoma nafila yanarokoñ Allah yaciremasa sonta tunkafin yayinisa
Saikusan asuba yakwanta Amman abun mamaki maimakon yaga sauyi aransa saiyaji kamar ansake linka sonnata sau ashirin acikin zuciyarsa

Aisha✍🏼

[4:28PM, 2/28/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 57

       By

Gentle Lady💃🏽

Har akayi kiran asalatu idonsa biyu bairuntsaba”” tashi yayi yasake dauro alwala yafita yatada lubabatu sannan yakarasa sauka kasa yasoma tashin yan aikin gidan kamardai yanda yasaba
Saida sukai alwala sukawuce masallaci baidawo ba saida haske yagama mamaye gari cikin masallacin ma zaune kawai yake tamkar mutum mutumi tundayake baitabajin soyayya irin hakaba
Waidama Ashe haka soyake??? Lallai Wanda baisan soba shine zai karyatashi baitaba tunanin hakan akejiba gameda abunda zuciya takeso tomeyasa banajin hakan lokacinda nahadu da lubabatu???
Kodai itakanta soyyyar matsayi matsayine da itah nasan Na auretane Dan inasonta towacce irin soyayya??? Kawaidai inajinta cikin raina yanda baxan iyah rabuwa da itah ba
Sauran matanda na aurah fa??? Sume yasa banajin haka atattare dasu??? Suma tasu kalar soyayyar dabantake
Khadija ce kawai lokaci daya soyyyarta tashiga harcikin barko dakuma jinin jikina”” tomeyasa hakan??? Saboda kanasonta”” !! Tomeyasa nakesonta alhalin kofuskarta banganiba ??? Saboda tarbiyarta to ai itama lubabatu tanada tarbiya meyasa banajin sonta kamar wannan ??? Wannan kuma daga Allah ne
Haka yayita yiwakansa tambayoyi kuma yanabawa kansa amsar tambayarsa haryabaro masallacin kwana biyu tsakani yakasa gane kansa abinci kansa yarage ci

Zaune yake office dinsa yana tunani yakamata insanarda labila halinda nakeciki nasan bazata zargeniba saboda tasan banine nasakawa kainaba”” kai anya zan iyah kuwa???
Tomezaihana kadai tsaya kallon ruwa kwado yayimaka kafa kawai kasanarda itah zata fuskanceka dawannan shawarar yayarda yadauko wayar yakamo lanbar Sannan yasoma jujjuya wayar 
Yayi tsayin mintuna ashirin sannan yakirah”” tanafara ringing yaji gabansa yafadii rasss”” tayita ringing harta katse ba adaukaba yasake kirah hartakatse bata dagaba
Khadija tana kwance adakin wayar tasoma ruri harzata daga taga sunan wanda yakirah dadyna gabantane yabada rasss tadafe kirjinta tanamairufe idonta
Waimenene hakan kikeyi babananefa”” taja tsakii hartakai hannu tadauka kuma takasa saida yayi kiran saubiyu gana uku tadauka
Jikinta yanadan rawa cikin siririyar muryanta tace Assalamu Alaikum daya bangaren wani irin sanyine yaratsa zuciyar usman haryasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya

Yace Amin wa Alaikumus salam” Wani yanayi khadija tasamu kanta aciki jin muryarsa yasaukar mata da kasala cikin sassarfar murya tace dady ina kwana”” yace lafiya qalau kina lafiya tace umm sannan tace batanan taje gida tadawo batajirah mezaiceba taka she kiran

Tace wai tareda murmushi tanadafe da kirjinta dayake harbawa”” 

Yanajin taka she yajiwani iri cikin ransa Sam baijidadin hakanba”” yaso koda muryantane yaji yanatsaka da tunani saigakirah yashigo 
Dasauri yadauka atsammaninsa itace tasake kirah yanadauka yaji muryan labila bahakan yasoba cikin sanyin murya ya amsa gaisuwarta tace dad tundakazo bakasake kiranaba
Yadan shafo kansa yace tubanake aikine yayimun yawa wlh “” tace shikenan yace yasu hajiyafa??? Tace qalau munga sako dani dasahiba mungode
Yadan murmusa bakomai tayidanjin dad akwai matsalane??? Yace ah yayi saurin cewa sorry ah ah babuwata damuwa kinga wani abune???
Tace dad aibahakan nasabajin muryankaba indai akwai damuwa kasanardani please”” yace bakomai dama nakirakiine naji idan kina lafiya
Tanisa qalau nake dad yace tosai anjima”” tace inasonka dad cikin sanyin murya yace nimahaka yakashe kiran yanamai runtse idanuwansa why why meyasa nakasa sanarda itah???
Bayankuma tatambayeni damuwata yayi wulgi dawayar yadafe kansa wani irin suracine yake fitowa tajikin zuciyarsa yanafita ta hancinsa tamkar suracin tafashasshen ruwan zafii

Labila tsuru tayi tana kallon wayar”” khadija tace yadai sahiba???? Ajiyar zuciya tasaukar tace bakomai tareda zaunawa saman gadon”””
Abu wasa wasa kullum saiyakirata kamar yasanarda itah saikuma yafasa itah tagano manufarsa Dantun ranarda yazo walima taga kallonda yakeyiwa khadija kawaidai yana jinjina sanarda itane amatsayinta nayarsa itakuma taraya aranta inhar bashine yafurtaba bazata taba nuna taganoshiba sai idan yatunkareta da maganar
Yau yakasance weekend ne karfe takwas nasafe Usman yakama hanyar kano yaukam zaisanarda labila abunda ke zuciyarshi saidai koma kunyar ne yajita danyagaji da ajiyar abunda yafi karfin zuciyarshi 
Bangaredaya kuma yanason ganin khadija koda muryantane yaji zaiji sanyi “” koda yakarasa gidan hajiya bata nan”” dama kuma Hafiz Yakoma”” bayan yayi pkng suka gaisa damaigadi yake sanardashi yace bakowa gidan kenan??? 

Yace ah ah yar dady tana nan”” kamar yacemasa tareda kawarta saikuma yashare yawuce cikin gidan tanajiyo sallamarsa tafito dagudu tanamasa oyoyo
Yace labila waiyaushe zaki girmane aiyanzu kinwuce wannan saidai majeed “” baki taturo tace ah ah banwuceba sai anhaifamun Kanwa sannan
Murmushi yayi yanasamun waje yaxauna yacire hularsa yana fiffita kaiyaufa akwai zafi babu wutane???
Tace ah yanzun nan tadauke bari inkawo maka ruwa tayi maganar tana wucewa ruwa tadauko masa tareda cup tadauro akan wani karamin faranti maikyau taduka ta ajemasa tanayimasa ya hanya
Yace alhamdulillah ruwan tazuba masa Tamika masa yakarba yanasha wani sanyine yake ratsashi saida yashanye duka tace akarane dad??? Yace kara Amman kadan
Tasake Karamasa yashanye sannan yasaukarda ajiyar zuciya yace Alhamdulillah nagode”” inakuma hajiya taje baba maigadi yacemun tafita??? 
Tace ah wlh gidan wata kawarta akayi rasuwa shine tatafi gaisuwa”” yace ayya wayarasu mace ko namiji”” tace wlh bansaniba nima
Yace to Allah yajikan Wanda yarasu tace Ameen” Amman meyasa bakibita kuntafi tareba””??? Tace dad kusa da islamiyar munefa kuma zasuga banzoba saitace induba gida sahiba ma tatafi tundaxu
Shiru yayi baisake cewa komaiba gashi yanason magana Amman yakasa…….

Aisha✍🏼

[6:33PM, 2/28/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 58

       By

Gentle Lady💃🏽

Saiya kalleta kamar yayi magana saikuma yakasa itakuwa tana kallace dashi ganin yayi shiru tamike tace dad nikam bari nadan kwanta”” tayi maganar hartasoma tafiya
Yace amm dawo labila magana zamuyi””” tace to tareda juyowa tazauna kasa tana fuskantarshi saikuma yayi shiru 
Yacije lebonsa nakasa yanasake jinjina nauyin maganar”” tace yadai daddy??? Yadan nisa yace bakomai tashi kije kikwanta
Murmushi tayi maidan sauti tace dad kadaina boye abunda yake zuciyarka hakan babbar illace atareda zuciyar
Komai nene kasanardani mana zanfuskanceka amatsayina nayarka banason damuwarka kokadan Kaine kawai kasan damuwana yanda zanfadamaka Abu bana iyah sanarda mahaifiyata
Kadaure kasanardani wlh batunyauba nalurah kanacikin damuwa kullum kakirah ni dankasanardani saikuma kafasa
Nifa yarkace menene bazaka fadamunba kaima kasani zanbaka goyon baya Dari bisa Dari idankuma abunda zanbada shawarane saina baka daidai sanina”” 
Yanisa yana kallonta yace hakane labila Amman gaskiya inajin nauyin fadamaki bukatata dankuwa tanada matukar nauyi.

Tayimun nauyi abakina hakazalika zuciyata takasa daukarta inaganin kamar bankyautaba kuma abun kunyane 
Nayi nayi incire abun azuciyata Amman yagagara fita”” tanisa bakomai dad inhar fadinsa shine zaisaka zuciyarka nishadi kasanardani please

Shiru yasakeyi nawadansu dakiku sannan yace labila akan kawarkine khadija tunranarda naji tana karatu amakaran tarku wajen walima haka kurum naji taburgeni
Banyi tunanin kawarki bace saida kika nunamun itah sainayita kokarin incireta araina amman abun yafaskara Amman karki zargeni da wani Abu please
Nasan abune maiwahalama tayarda ta aureni dannayimata tsufa”” dariyace takwacewa labila wacce tasaka Usman darawa tunfuskarsa nanuna alamar damuwa sanda yake maganar

Saida tayi mai isarta tace haba dai dad akan yar wanann maganar dakake cewa kayimata tsufa ai wlh dad babu Wanda zaiganka yace kahaifi kamata””
Saidai kuma hanzari baguduba”” cikin sauri yace menene??? Tace sahibata tuni tayi mijin aure!! Wani kululu yaji yatokaremasa akahon zuci yayita maza yace shikenan dama haka Allah yakaddara
Amman kibar maganar nan dagani saike saikuma Allah dayake kallonmu banaso tasan wannan batun kartadaina ganin girmana
Labila tace harkasaki dawuri haka dady bayan kashiga kaima agwabza dakai”” yayi murmushin yake yace aikinsan bakyau Neman aure cikin aure
Tace hakane tobaka tambayeni sunan Wanda zata auraba??? Yakishingida saman kujerah zuciyarsa nayimasa zugi yace menene amfanin jinsunan labila kawai kibar maganar kamar adole yake maganar Dan idanuwansa harsun sauya kala””

 

Marairaice murya tayi tace dad sahibar tawa??? Yace yihakuri towaye??? Tamurmusa sunanku daya ai
Yace masha Allah inatayashi murna”” tace mungode kumafa akaduna yake zama unguwarku dayama
Yalurah abunnata na ba ane yace kinsan Allah banason shashanci dariya tayi tace dagaskefa dad yanzun hakama munataredashi afalon nan
Dasauri Usman yadago yanakarewa falon kallo baiga komaiba yamaida kallonsa wajenta yace waikina nufin ni??? Murmushine akan fuskarta tagyada kanta alamar ah

Wani farinciki marar misaltuwa yamamaye masa zuciya bakinsa yaki rufuwa saboda tsananin murna tace nasan kayi mamaki danacekaine mijinta 
Tunbayauba nakeyimaka kwadayin samunta inada yakinin zakasamu abunda kakeso awajenta komenene dad tunda nahadu da sahiba wlh bantabajin tayi koda musayar yawu dawaniba 
Tanada hakuri gakuma addini bashakka zata tarbiyantarda yayanka kowanne uba anaso yasamarwa yayansa uwa tagari banada kokonto akan sahiba 
Nikaina dakaganni Allah yahadani da itah domin sanin halinda nakeciki Wanda babuwandà yasanshi sai Allah
Munyi alkawari atsakaniñmu kowacce acikinmu daya zata zabamata miji tun alokacin nazabarwa sahiba kai kamar yanda nasanka haka itama
Nasan zatayi alfahari dakai anan gaba kamar yanda kaima zakayi kumanasan baxata tabakin zabinda naimataba dukda sainayi dakyar kafin ta aminta idanhartaji nace zabinda naimata Kaine

Tanisa tana kallonsa kabani kwana uku komainene zankiraka insanardàkai yanisa bakomai Amman idan batayardaba karki tilas tata akan abunda bataso dannima bazanji dadiba
Tace in Allah yayarda zata amince”” yace to Allah yayardà labila yanaduba agogo yace bari nadanfità kafin hajiya tadawo

Ammanfa karki manta da maganar please”” tace bazan mantaba dad tanarufe bakinta hajiya nayin sallama damamaki tace kai wanga saukar y aushe??? 
Labila tace bakijima dafitaba yashigo”” tace aidanasani danayi zamana tunanin nayi nakatsemaki makaranta shiyasama nadawo dawuri
Usman yagaida itah ta amsa tana tambayarsa lubabatu”” yace qalau take hajiiya “” tace madallah saikitashi kishirya kiwuce makaranta Dan nakai majeed dagacen
Taturo baki wlh hajiya nayi lattifa kafinma nakai antashi” Usman yace kishirya nakaiki daganan sai inwuce inda zanje
Tace dad ankusa tashifa wlh danaje rikeni malam zaiyi sai azahar”” hajiya tace tosaiki zauna abokan karatunki saizu tsere maki “”
Tace ai sahiba zata fadamun idan tadawo damakuma nawucesu dasura uku tunda inayi agida tayi maganar tana dariya murmushi Usman yayi yace nidai hajiya barinaje nadawo sainawuce
Tace kaikuwa mekazoyi kano kanacikin aiki??? Murmushi yayi yadan Sosa kansa yace kawaidai nazo ingaishekune
Tace kakyauta kuwa Allah yabada ladar zumunci yace Ameen tareda mikewa yadauki key dinsa yafita”” 
Saikusan azahar yadawo yaci abinci yawuce bayan yasake jaddadawa labila kartamanta”” tace bazata mantaba
Hajiya tace waimenene aketa kumuiniya ba aso inji??? Usman yana dariya yace bakomai hajiya
Baki tatabe tace komadai menene inazaune za afadamun indai wannan ce maishegen surutun tsiya”” kamar suda”” majeed ya kyalkyace da dariya yace Anty tazama suda hajiya dama aku kikacemata
Labila tamaka masa harara”” tace zanbugeka majeed wasa nakeyi dakai??? Jikin hajiya yashige yace aihajiya bazata bari adakeniba”” 
Usman yana dariya yace saidai idan bakayi laifinba”” hajiya tace kodayayi laifi babu maidakarmun maigida inakallo”” majeed yacee yeee hajiya tanasona gabadaya sukasa dariya

Aisha✍🏼

[12:24PM, 3/1/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 59

      By

Gentle Lady💃🏽

Yace nidai hajiya natafi”” sukayimasa Allah yakiyaye yawuce cikin farinciki gabadaya jiyake tamkar anyaye masa wani katon dutse daya taushe zuciyarsa fatansa kawai Allah yasa khadija zata ameence
Dawan nan tunanin yakarasa gida”” lubabatu tana zaune cikin falon kasa tana kallo yanashigowa tabishi dakallon mamaki
Kusa da itah yazauna yace yakina kallona bazakimun kosannu dazuwaba”” baki tatabe tace aibansan inda katafiba kaida bakafita koda kofar gidane idanhar ranar weekend ne Amman yaunaga bakon al amari
Yanisa yanashafar kansa yace kano natafi”” takalleshi dahanzari tace incekodai lafiya??? Yace qalau natafi ganinsune kawai yaunatashi dason ganin Ya’yana
Har abada baida niyar boyemata Amman yasamu kansa dakin sanarda itah dalilinsa nazuwa kano tundasafe dankoda yabarta bata tashi barciba shima saman hanya yasha lemu
Tace wlh harkasa gabana yafadi nadauka wani abune yafaru”” yace bakomai wlh hamma yayi yana Shafa cikinsa yace akwai ragowar abinci yunwa nakeji
Tace babu iyah cikina kawai nace agirka kuma nacinye inda kafito bakaci abinci bane??? Shiru yayi baice komaiba “” tace sai idan kanaso nasake sakawa adafa maka wani”‘ yace shikenan barshi kawai nahakurah inci dadare””
Baijirah jin mezatace ba yamike yahaura sama tabishi damugun kallo”” sosai tanason tarika juya Usman tamkar dancikinta Amman tarasa gane dalilinda yasaka duk aikinda akaimasa baicika tasiri akansaba
Wanda akayi cikin kwalbane kawai yakeyin aiki akansa kumashi zafin zuciya kawai yake sakashi idankuma takulle barta mutane har itah kanta bata tsirah da fushinsa
                Abokanta duka suna juya mazajensu son ransu duk da batanemi komai tarasaba Amman tanason harta wanki shine zaiyi mata dagyaran daki
Tanajin tsoron sakashi tunda tasan yanada zuciya zata iyah sakashi yace bazaiyiba girmantama dayake gani yadaina gani kuma batason kowa yarika zargin wani Abu
Usman tunda yahau saman baisaukoba saida yaji kiran sallar la asar yasake watsa ruwa yadauro alwala yasauko tana nan inda yabarta yawuce abunshi batareda yacemata komaiba

Itama batadamuba Dan hankalinta yanakan TV datake kallo””
Kwance take dakin khadija itakuma tanazaune tana yankan kumba”” labila tace sahiba dama magana nakeso muyi dake””..
Tana yankan kumbar ta daina inajinki”” labila tanisa tace gameda alkawarinda mukaiwa juna yaudai inason nafurta maki sunan mijinda nazaba maki
Khadija tayi kasake tana kallonta sannan tanisa tace sahiba atsarina inasone muyi aure tare kinaganin baiyi sauriba idan kika zabamun miji ayanzu
Labila tatashi zaune tace nidai awajena baiyiba kuma nafison ayikomai dawuri”” Saidai idan zakiki zabinane
Khadija tace habadai Nina isah naki abunda kikazabamun nasan har abada bazaki zabamun abunda zaicutardaniba””
Nayarda kowaye zansoshi sahiba idan harkedai yayi maki bamasai kintsaya Neman yardataba kawai kicemasa Na amince
Labila tasaki fara a tace bahaka zamuyi dakeba inasone kifadi ra ayinki”” khadija tace inhar yayi maki wlh yayimun”” karkidamu

Labila tace shikenan Amman akwai bukatar kusamu lokaci domin kugana kafin nan zansanardashi yaturo iyayensa atsaida magana domin cikin kankanin lokaci za ayi bikin”” khadija tace haba sahiba karatunfa!??
Karkidamu da karatu zakicigaba agidanki”” tace shikenan Allah yatabbatar mana da alkhairi labila tace Ameen tarungumeta cikin jindadi

Bayan kwana uku kamardai yanda sukayi dashi saigashi yakirata tana falo tanayiwa hajiya tausa tamike dasauri tayi hanyar dakinta
Hajiya tabita da kallo tana girgiza kai labila waisai yaushene zatayi hankali”” Allah yakyauta
Tanashiga dakin tadauka tareda sallama ya amsa sallamar taredacewa lafiyadai naji shiru kodai kinmantane???
Nayita jiran kiranki gashi har dare yayi”” tace sorry dad wlh mantawa nayine””” idanuwa yakwalo aransa yace umm lallai bakisan abunda dadynki yakeji gameda itaba aida bazaki mantaba
Takatsemasa tunaninsa tahanyar cewa ta amince””” baki yawashe yace dagaske??? Tace sosai ma yace Amman tasan nine tayarda dawuri haka??? Tanisa ah ah batasaniba
Sai murnarsa takoma ciki yace mekikayi haka??? Taya zan aureta alhalin bakisanarda itah gaskiyar kowaye niba
Tace naso fadamata saitace koma waye inhar niyayimun tobasaina nemi yardar taba”” tayarda”” tasan bazantaba zabamata abunda zaicutarda itaba
Yayi shiru daga bisani yace ninasan bazata yardaba”” labila tace maisaukine dad yanzudai inaso kazo kasamu kawunta”” idan kungama magana”” saikazo danka ganta idan kaganta taganka komenene ninasan yanda zanyi
Amman fa akwai sharadi bayan amincewarta”” yanisa wanne irin sharadi kuma labila??? Tace awajena maisaukine bansaniba kodai awajenka dakuma matarka!!
Dif yayi shine illarfa kaso karamar yarinya kuma abokiyar yarsa yanisa shikenan kifadamun sharadin” tace bayanzu ba dad sai idan maganar ta tabbata yace shikenan
Sukai sallama yadade yana nazarin kalaman labila daga bisani yadaga kafadarsa alamar baidamuba kowanne sharadine zai yarda dashi matukar zaisamu hadinkan Khadija dawan nan tunanin yawuni

Bayan kwana biyu dazancen yaje kano hajiya yasamu yalabarta mata komai”” shiru tayi nawadansu lokutta sannan takalleshi tace anya khadija zatayarda idanhar tasan labila Kaine zabinda taimata???
Yanisa nikaina bansan yazata kayaba Amman banada mafita hajiya tunda kikaga harnayiwa labila magana kinsan abun nan ba karami bane
Kece mahaifiyata nasan bazakiso abunda zaitaba lafiyataba wlh inacikin damuwa sosai abun yana Neman taba lafiyar jikina likita yacemun nadaina shan maganie nayi aure
bansanarda ke bane kawai tunsanda kikaga inata aure Amman matanne duka kinga irin yanda suke kasancewa hardanacire son aure araina nabarwa Allah komai idan yazama shine ajalina Allah yagafartamun saigashi kwatsam naga wannan khadijar gabadaya narasa natsuwata”!!!
Tanisa shikenan bari zanyi maka kwatancen shagonsa danbaicika zama agidaba kafara tuntubarsa dazancen kanemi izinin ganinta idan hartaganka kuma tayarda zata aureka komai zaizo cikin saukiii yace shikenan
Tayi masa kwatance shagonsa akasuwa Yakuma sameshi yabashi hannu suka gaisa Ashe shima yasanshi”” Usman nekawai baiwayeshiba”” 

Aisha✍🏼

[4:01PM, 3/1/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

Chapter 60

       By

Gentle Lady💃🏽

Yace yanzun kazone??? Usman yace ah wlh .to ansamesu lfy ko???..
Yace cikin godiyar Allah””” to masha Allah “”Allah yakara mana lafiya Usman yace Ameen”” saikuma shiru yabiyo baya yalura akwai magana abakinsa yace Alhaji Usman mukarasa ciki ko babu musu yamike shikuma yashige gaba yanabiye dashi
Dayake shagon babbane akwai kujeru biyu aciki yanuna masa bisimillah zauna taresuka zauna yasake bashi hannu suka gaisa”””
Yace banyi mamakin ganinkaba nadauka wani kaya kazokasiya saikuma nalurah akwai magana abakinka””
Usman yasanne kansa yace hakane malam”” dama akan yarwajenkane “” tunranarda nazo walimar su labila naganta amakaranta naji takwantamun araina
Banyi tunanin Kawar labila bace saida nagansu gida tare”” tun alokacin naso cireta araina”” saikuma abun yafaskara
Kuma inajin nauyin nasanarda itah shine danasanarda labila tasanarda itah tace ta amince Amman kuma bata fadamata ainahin waye yakesontaba
Shine Nazo wajenka Neman izini inaso inda hali ingana da itah banaso intilas tamata idanhar batasona karsai magana tayi nisa yazama nacutarda itah
Danasanarda hajiya shine taturoni nan nayi tambaya har akanunamun shagonka”” inafatar ba aimata mijiba daga wurinku dagaske nake bawai wasa nazoyiba auren ta zanyi inda halima banaso adau tsawon lokaci yakai karshen maganar yana kallonsa
Malam garba yanisa yace to Alhamdulillah naji dadin jin wannan maganar Amman wani hanzari baguduba gaskiya banine mahaifin yarinyar nanba”” asali uba muka hada da mahaifiyarta

Mahaifinta Dan yolane sunrabu da mahaifiyarta tuntana ciki wata uku”” tazo tareda yayanta muktar anan garin dama nan ne tushenta”” ranar da tahaifeta aranar tarasu ko waigowa batayi taga yarba yayanta shiyayi rainonta hartagirma duk damaidakina tana kulada itah sosai bayason yayi nesa da itah
Yanzun yana america wajen karatu ni awajena babu damuwa kafara ganawa dayarinyar idanhar ta aminta zankirah yayanta insanardashi saikasamu kashirya muje yola tare dakai duk daharyanzu babanta baitaba waiwayarmuba kodai yanedai muzamu nemishi
Usman yace hakan yanada kyau Allah yajikanta”” yace Ameen daganan sukadan taba firah yayimasa sallama yakoma gidan yasanarda hajiya yace tafadawa labila zaidawo jibi yayimata sallama yatafi
Ranarda takama zaizo takai khadija akayimata lalli akagyara mata kai tashirya masa abinci mairai dalafiya”” gidansu khadija suka karbi mabudin dakin ya muktar suka gyarashi suka kunna turaren wuta”” 
Dakinsai fitarda sihir taccen kamshi yakeyi”” da khadija taiwanka labilace tayimata kwalliya Dan itah bamaiyawan kwalliya bace
Bayan tagama kimtsawa labila takalleta tundaga sama harkasa aranta tace dady hakika kayi dacen mata wacce zata share maka hawayenka
Dakuma tatunoda gidanda zataturah kawarta saikuma tarungumeta tafashe dakuka”” bataso tarasa kawarta haka zalika tanason ganin karshen bokan mamarta kuma tasan babu wacce zata iyah tunkararsu sai khadija domin itace ta chanchanta
Khadija tace lafiya sahiba idan bakyason abun nan karfa afara hankalina bazai kwantaba idan inaganinki cikin damuwa
Labila tayi saurin share hawayenta tace karkidamu sahiba bawani abubane yasakani kuka ganin wannan kyanda kikayine kamarwata sarauniya
Harara tayimata cikin wasa tace aikinfini kyau sahiba kawaidai bakyaganin nakine kina hango nawa”” zatayi magana kirah yashigo wayar labila 
Tadauka cikin fara a tayi sallama daya ban garen aka amsa tace harka iso??? Yace ah tace ok ganinan zuwa takashe kiran tana kaidubanta wajen khadija wacce takuramata ido bugun kirjinta harwaje kanajinsa
Murmushi tasakarmata tace yadai sahiba??? Tasanne kanta kasa tanawasa dayan yatsunta tace wlh gabana faduwa yakeyi
Kamar kirjina zaiballe”” labila tace please kisaki ranki nasan zaiyimaki kyakkyawane sosaifa barinakaishi dakin nadawo
Tayi maganar tanaridar mayafinta tayafa tafita”” innah tana tsakar gida tacemata innah bakon ya iso”” tace to gashi bangama dama furarba barinayi sauri tace to tawuce
Yanacikin motarsa yanaganin tafito yafito yana tunkarota da murmushi akan fuskarsa””
Tace dad inawuni”” yace lafiya qalau yagidan
Tace qalau mukarasa ciki sainakirata ko”” yace to bisimillah”” tana gaba yanabinta abaya tabude masa dakin yashiga yazauna sannan tafita tayita jidomasa kayanda suka hadamasa takaimasa
Shidai yakagara yayi ido biyu da khadija kamaryayi magana saikuma yadake kartace yafaye zumudi tazuba masa ruwa sannan tafita khadija takoma tamkar mutum mutumi duk jikinta yamutu labila tadauko hijab tasakamata”” 
Tariko hannunta sukafita haryanzu kirjinta harbawa yakeyi bakin dakin labila tatsaya tace kishiga inazuwa””
Khadija tamake kafada tace saidai mushiga tare”” labila ta kwalalo ido tace gaskiya bazai yiyuba haba””
Khadija tace tosaidai mukoma Amman kinsan bazan kebe dawani namijiba alhalin ba muharramina bane
Tace kinyi gaskiya tokishiga dazaran kungaisa wlh zanshigo tace kintabbata??? Tace ah saiki tangale kofar idan kikashiga tace shikenan
Labila tawuce tadade tsaye bakin kofar kafin tadaure tareda addu oi abakinta tasamu damar shiga dakin tareda sallama
Wani sansanyar kamshin turarensa yadaki hancinta idonta yana kallon kasa cen nesa dashi taduka muryansa maisanyi taji taratsa dodon kunnenta wa alaikumus salam”” 
Gabantane yasake fadii talumshe idonta tabude aranta tace sak muryan dad”” murya kasa kasa tacemasa inawuni

Idanuwansa suna kanta yace lafiya qalau Khady yagidan yakaratu”” wannan karon kam tunaninta yafara gagararta ahankali tadago kanta saicikin idonsa
Zumbur tamike tadafe kirjinta tace dady dama Kaine??? Yanda take magana kasan tanacikin matsanancin tashin hankali gakuma bugun kirjinta ya tsananta
Lallausan murmushi yasakar mata yace nine kinji mamakine khadija”” hawayenda suke akan fuskarta suka karasa gangarowa tace dad menene hakan?? labila dasaninta ta aikata hakan???
Yasakeyin murmushi yace balaifin labila bane nine nafara samunta da maganar”” cikin muryar kuka tace nashiga uku ni khadija menene sahiba ta aikata haka bazai yiyuba
Kafin Usman yayi magana tuni khadija taruga tafita dakin tana kuka kamar ranta zaifita usman yatashi tsaye yana kiranta ina kojuyowa batayiba yadunkule hannunsa yanaushi iska
Lebonsa nakasa yacije adayanaji kamar zai iyah hakurah da khadija Amman ganinda yamata ayanzu babu nikab yasake haukatoda soyayyarta ya Allah kasa kartace bazata aureniba
Dagudu tashiga gidan labila tana tareda innah kawaiganinta sukai dagudu tafada daki tana kuka”” suka kalleta suduka sannan suka dubi juna innah tace dama nafadawa malam tayarda da maganar kine dan batasan kowaye kika zaba mata ba 
Ainidama nasan za ayihaka”” saikishiga kilallaso abarki”” labila kamar tayi kuka takama hanyar dakin innah tabita dakallo tace Allah yasa zatayarda tunda intakafe akan Abu bamaijuyata saidai nasan yanda kuke watakil tasaurareki

Aisha✍🏼

[8:48PM, 3/1/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 61

      By

Gentle Lady💃🏽

Taturah kofar tashiga da sallama khadija tana saman gado saidarzar kuka takeyi”” labila takarasa saman gadon tazauna 
Tadade tana kallonta daga bisani tadafata tareda kiran sunanta sahiba”” juyowa tayi tarungumeta tasake fashewa dawani kukan tace menene kikayi haka sahiba?? 
Dama dady ne kikecewa kinzabamun??? Meyasa zakiyi abunda kinsan bazaitaba yiyuwaba meyasa kikamun haka meyasa tasake fashewa dawani kukan
Labila ahankali tasoma bubbuga bayanta tace sahiba saboda shine yachanchanci zama mijinki
Duk da araina nayimasa kwadayin aurenki dabaisameni yace yanasonkiba wlh bazantaba cewa ya aurekiba please sahiba karkice bazaki aureshiba
Dasauri tadago dagajikinta tana girgiza kai tace bazan iyah ba sahiba wlh tamkar mahaifina nake ganinsa bazan iyah auren babankiba””” 
Labila akufule tace kawai kifito fili kicemun bakyason babana kawai basaikincemun bazaki aure shiba 
Tanakai karshen maganar tamike daniyar fita dasauri khadija tasha gabanta tahade hannu waje daya alamar roko tace kigagarceni sahiba niba haka nake nufiba
Amman kisamarmun wani wlh kowaye zan aureshi””” labila tacije lebenta nakasa tace shi mahaifin nawa baiyi makibane????
Hannunta khadija taja tace kizauna muyi magana” tafige hannunta komai zakifada kifadamun inajinki basai nazaunaba
Tace haba sahiba Dan girman Allah kisaurareni”” tace ahakan kinamun kuka?? Dasauri tagoge hawayenta tace nadaina please kizauna 
Tanisa sannan takoma tazauna tajuya mata baya”” khadija tagirgiza kanta tace yanzu sahiba akan Dan wannan abun zakiyi fushidani??? labila tace awajenki yakedan nikam awajeba babban al a marine haba abudebaki ace ba ason ubana wlh kinbani mamaki danice wlh kowaye kikabani narantse saina aureshi tundahar kece kikafurta banice nace inasonshiba
Khadija tace bazan iyaba sahiba haba dady dawanne ido zankalli mom??? Labila taja tsaki tace dayake kinsantane bakisantaba bakitaba ganintaba amatsayin matar mijinta zakishiga gidan tomenene
Indai nizakiyiwa kara wlh banaso karkiji waidan tana mahaifiyata wlh nafison babana saudubu da itah farincikinsa shine nawa
Kodawata yace yanaso zanyi ruwa inyi tsaki danganin yasameta ballantana kuma gudan sahibata”” tariko hannunta please sahiba babu musu atsakaninmu karki ki babana wlh yanasonki”” kirane yashigo wayar labila dama tundazu taketa ringing tasan dadyn tane tanadauka yace labila idan batayardaba kibarta””” nibari inwuce Tanisa tana kallonta tace kajiramu gamunan fitowa takashe kiran tanakallonta tace please sahiba”” 
Khadija ta sake share hawayenda suka saukomata tace bazan iyaba sahiba”” 
Labila tamike tunkafin khadija takarasa rufe bakinta”” tace magana takare tajuya dasauri tasake jawo hannunta labila tabuge dakata karkisake rikemun hannu tundakince bakyason babana” 
Wlh khadija kokiso kokarkiso nasan kinasonsa dasauri khadija takalleta tana girgiza kai tacigaba wlh kinasonsa tunranarda kikaganshi nasanda kinasonsa dan nakula dake sosai
Yawan faduwar gabanda kikeji itace alamar harcikin jininki yakeyawo kuma ninasan bazaki iyah rayuwa bataredashiba kawaidai kinason hanawa kanki abunda kikeso”” tarufe bakinta tace bazakigane menake hangowaba
Labila tadaga hannu tace ki amsamun zaki aureshi ah ko ah ah??? Tace kiyi hakuri please tayi maganar tanasake riko hannunta tajaye hannunta tawuce dasauri
Khadija tabita dagudu tanafita tarufe kofar tayi hanyar gidan tana kuka hartana hadawa dagudu bawai komaitakeyiwa kukaba tanajin tausayin babantane”” 
Usman yanaganinta shima yafito yabi bayanta yana kiran sunanta”” kowaigensa batayibà saima tasake rugawa
Khadija kofar gidan taduke tanata kuka kamar ranta zaifita gaskiya labila tafada idantace batasonshi tayi karya Amman abunda kunya mahaifin kawarta
Inna ce tadafata”” tamike tafada jikinta tace inna yazanyi labila tayi fushidani” kinajifa abunda tayi”” innah tace nidai aganina ki amince kawai tunda kinasonshi
Tace innah dangan takarmufa?? Tace

Khadija meyasa kikeson haramtawa kanki abunda yake halal nee agareki”” ???
Kisani wani baya auren mijin wani hakazalika wani baya auren matar wani kidaina cutarda kanki nikaina nalurah dake tunranarda akayi walima kikashiga damuwa
Saikiyi zugum kedaya kuma wani sa in sainaganki kina murmushi harnakanji kina magana da zuciyarki kinacewa tadaina babanki”” 
Adazaki iyah kauda kai Amman yanzu bawan Allah nan yataso tundaga kaduna yazo wajenki Kuma yasamu kawunki yamasa magana
Kitunafa yarsa yayiwa magana batadauki komai arantaba tonamenene zakice baki yardaba
Ta share hawaye tace toyazanyi inna kinagani tayi fushi””” innah tadafata tace dauko takalmanki kibita gidan kibata hakuri shima kibashi hakuri kice kin amince shikenan aiko
Tagyada kai tanakara share hawayenta innah tace saikidaina wannan kukan karyace tilas taki akayi kuma tace to saida tasake gyara fuskarta tafita duk dahaka idanuwanta jajir suke kamar gauta”” ahankali take tafiya hartakai gidan gabanta kuma saidukan uku uku yakeyi
Tanayin sallama cikin falon yana zaune saman kujerah yajingina kansa idanuwansa suna kallon silin da alamu tunani yakeyi kuma yayi nisa cikin tunanin 
Yanda hartayi sallama baijitaba kodan muryanta ta dusashe tagefen ido take satar kallonsa saitaga yakara kyau yanda yayi Sam fuskarsa ba walwala
Dakin labila tashiga takosameshi abude harkuryar tawuce dan bata same ta falonba”” tana kwance saman gado tahau saman tajuyo dafuskarta wajenta
Labila tasha toka “” khadija tace kiyi hakuri sahiba nibawai naki dad bane inaganin kamar cinfuskane na auri mahaifinki” “labila tace toshine me bashine yace yana sonkiba kuma ninayarda”” 
Tanisa shikenan sahiba indai hakan shine muradinki Na amince kiyi hakuri”””sannan kibawa dad hakuri naga kamar ranshi yabaci”” labila tace anki ahakura din 🙄 tamurguda mata baki yanda tayi saiyabawa””khadija dariya tatintsire da dariya
Labila takaimata dukan wasa tagoce tana dariya itama dariyar tasaka”” suka rungume juna”” suna dariya
Khadija tace kije kibashi hakuri please”” labila tace kitashi mujedai inrakaki aibani nayilaifinba””:? 
Tace kunya nakeji wlh””🙈 labila tace ke yanzu andaina jinkunya gaskiya dole nafara koyamaki darashi tayanda zaki yimasa kwarkwasa kiyimasa Farida ido
Yanda idan yanatare dake bazaisake tuna kowaba”” khadija mayafinta taja tarufe fuskarta tanadariya
Labila tace ashedai inada aiki agabana kunyar nan zanfara ciremaki tukun tamike mujeko

Bayanta khadija talabe harsuka fita yana nan kamar yanda taganshi dazu
Saidai yanzu murmushine kwance akan fuskarsa danyaji duk abunda sukefada”” bayajin muryan khadija saita labila Dan khadija kamar rada takeyi
Kusa dashi taduka khadija talabe bayanta tasunne kanta haryanzu baidago ba kamarma baisan da zuwan suba labilace takirah sunansa daddy
Batareda yadagoba ya amsa saikuma tayi shiru dantarasa mezatace masa”” saikuma tahau zungurar khadija 

Murya kasa kasa khadija tace dad kayi hakuriii cen kasar zuciyarsa yatsinkayi muryanta wacce tasaukarmasa da wata mugunyar kasala!!!

Aisha✍🏼

[11:47AM, 3/2/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 62

       By

Gentle Lady💃🏽

Yadago fuskarsa wacce take kumshe da murmushi idanuwansa yadorah akanta duk da tadukarda kanta”” yace laifin me akamun daza abani hakuri??? 
Aini yadace inbada hakuri gashi tasanadina nasa kinyi hasarar hawayenki masu tsada”” khadija kara sanne kanta tayi
Labila ce tamintsileta”” itama tarama mikewa labila tayi tace inazuwa kafin khadija tayunkurah tuni labila taruga tashige daki tarufe kofa
Dolece tazaunarda khadija Amman sai mutsuiniya take kamar wacce take akan kaya”” Usman haryanzu baidauke idonsa akantaba” 
Ahankali yakira sunanta khaaadeeeja hardawani Jan haruffan sunanta yanayin yanda yakirah sunanta yasaukar mata da kasala kasa amsawa tayi”” 
Saida yasake kiranta akaro nabiyu sannan ta amsa cen kasan makoshi””” yanisa inafatardai ba labilace ta tilas taki kibani hakuriba

….. Kai tagirgiza”” yace tomenene ra ayinki akaina nayimaki konayimaki tsufa ??? Bakinta tarufe tana dariya kasa kasa shima yadan saki dariya maidan sauti yace kifadamun gaskiya idan banyi makiba tayiyu nayi furfura dayawa bansaniba
Wannan karon saida khadija tadago takalleshi ta sake sanne kanta kasa”” aranta tace anya kasan yanda kake kuwa??? Kamar matashi Dan shekara ashirin dabiyar”” 
Yace bakice komaiba??? Cikin jinkunya tace ah ah dad”” yamurmusa tokinyarda yanzu zaki aureni??? Tagyada kai
Yace to Alhamdulillah insanarda malam kenan kin amince”” tace ah amman dady karatunafa””” yace hakane ainasan kunkusa gamawa koba ajinku daya da labila ba???
Tace ah ah ba skull dinmu dayaba”” suna riganmu zana jarabawa”yace shikenan badamuwa aikunkusa gamawa zan iyah jirah kikammala”” 
Shirune yabiyo baya kuma Usman yamaida kansa saman kujerah wani dadine yaketa ratsashi tako ina”” jiyakema tamkar gobene za adaurah masa aure da itah
Farinciki yakeji marar misaltuwa Wanda baitabajin irinshiba”” shi run yayi yawa hakan yasaka khadija tasaci kallonsa saitaci sa a ba itah yake kalloba
Takuramasa ido tana murmushi”” tanaganin yadan motsa tayi zumut ta mike dad nizantafi gida”” yace au harkingama firar??? Cikin zolaya yayi maganar batace komaiba
Yace shikenan kigaida innah tace to dasauri tawuce hartanadan hadawa dagudu yabita da kallo cikin soda kauna saida tafita yasaukarda ajiyar xuciya mai nauyi yace Alhamdulillah
Yalunshe idonsa yasake budewa yakwalawa labila kirah”” tana kwance tana game tace na am tareda mikewa tafito kusa dashi tazauna akasa tace waihar tatafi???
Yace ah tatafi”” murmushi labila tayi tace Allah yatabbatar da alkhairi yace Ameen”” sannan yagyara zamansa yace wanne irin sharadine kikace zakisanardani inhar tayarda zata aureni??? 
Labila tagyara zama tace inafatar ranka bazai sosuba??? Yace bakomai inajinki”” Tanisa kanta yanakasa tace banaso katambayi dalili akan komai dazanfada “”
 yace shikenan inajinki tanisa banaso kasanarda mom zakayi aure kabari sai ana sauran sati daya bukin
Kamar yacemata menene dalilinta Saikuma yatuna tace karya tambaya shima anashi bangaren baidaniyar sanarda itah dansai kumuiniya yakeda maganar shiyasa yanzun ma dagawajen aiki yawuce kanon
  yace uhum inajinki saime kuma””tace inhar bikin yatashi karkabari mom tayi taron biki sannan koda tatambayeka zataje unguwa karkabarta
Waifa awautar labila sai lubabatu tasamu fitane harzataje wajen bokanta abunda batasaniba lubabatu batazuwa ko ina bokanta madubinta danmuddiñ ba madubin tarasaba babu abunda zaikaita wajen bokan
Yayishiru aransa yace kodai labila zargin mahaifiyarta takeyi??? Allah sarki batasan baburuwan lubabatuba harmatafini son inyi auren kawaidai halin matanne
labila tacigaba Kawata bazata zauna bene Na biyuba kodai kabarmata naka kokuma mom takoma naka sahiba tazauna na mom din kaisaika zauna nabiyun

Idan harkayimun wannan kagama mun komai saidai nayimaku fatan Allah yabaku zaman lafiya””
Yasaki murmushi taredacewa Ameen indai Dan wannan ne aibakomai”” maisaukine awajena”” yakalli agogon hannunsa yace wai ina abdulmajeed yashigane??  
Tanadariya tace ainaturah shi gidan abokinsa tunda nasan zakazo yana iyah kwabsamana”” hajiya ma danasanarda itah zakazo shinefa itama tafita unguwa”” 
Yamike tokuwa bazan jirasuba aiki yanacen wlh nabaro muje nabaki sako sainawuce tace to tajuya daki tadauko mayafinta tafita”” yanagaba tanabiye dashi kofar gidansu khadija suka nufa labila takarasa tarufe kofar
Tace dad koyanruwa bakashaba??? Yace taruwa nakeyi wacce nazo wajen ta tagudu tabarni dariya labila takamayi tace ayimana afuwa dad 
Motarsa yabude yadauko wani karamin kwali guda biyu yace gashi saikiduba kotayi biyu nasiyo saikidauki daya”” tace la dad nifa daya nafadamaka nitawa uncle baijima dasiyamun itaba waccema kasiyomana lokacin walima ya muktar yakarbeta ahannunta waibaiyarda tarika wayaba
Yace toyanzu kikaimata aizanyi magana dashi yabarta da wayarta inaso zandinga kiranta munagaisawa tunda bakullum sai nakirah awayarkiba idankuma bakwatarefa
Kije saiki saka mata chaji nibari nawuce tace tomungode Allah yakiyaye hanya yace Ameen yashiga motar yawuce tanadaga masa hannu
Labila takunna wayar tadauki dayar tasaka number din dad tayi serving hubbyna daya number sa tasaka my everything”” 

Tayi murmushi taka she wayar tamiyar cikin kwalinta tawuce gidan tsakar gidan tasamu khadija suna labari da innah tanaganin labila tahau dariya
Labila taharareta cikin wasa tace haka akefirah waidaga shigana daki kodanafito bangankiba tayi maganar tanazama tace wlh sainatashi tsaye naga alama sahiba batasan yanda ake tarairayar saurayiba
Bacinma kiyita janshi dafirah harsaiyamanta inda zaije dareyamasa agarin nan”” inna banda dariya babu abunda takemasu itakuma duk labila tasata jinkunya”” 
Tamikawa innah tace gawayar sahiba dad yace abarta da wayarta zairika kirah suna gaisawa saurankuma idan yakirah kiki dauka dannalurah bakisan love ba”” 
Innah tace nadaiganoki labila kamfen kikewa dad”” tace bahaka bane innah sonake tutarmu tayi sama aikingane tayi maganar tanakashe ma khadija ido daya
Takaimata duka tagoce tana dariya bari nawuce gida kitashi kisaka chaji kikunna bamamaki idan yakai office zaikirah yaji muryar maisanyinsa
Idan yakirah kilankwashe murya kice helo my love tayi maganar tanayin Farida ido khadija tamike tabita dagudu tafita gidan tana dariya
Inna ma dariya takeyi tace kecedai labila ce maishiga tsakaninku zaiji kunya”” kidauki wayar kisaka chajin tace to
Wayar tadauka zuwa dakinta takunna wayar sannan tajonata chajii takurawa wayar ido fuskar Usman takegani ajikin glass din wayar sai murmushi takesaki
*WACECE KHADEEJA!*
Kubiyo yargidan Ibraheem domin kuji cikakken tarihin rayuwarta

“” 

Aisha✍🏼

[1:02PM, 3/2/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 63

       By

Gentle Lady💃🏽

Fateema shine sunan mahaifiyar khadija innar fateema Yar nigar ce “” sunanta hauwa”u mahaifin malam garba”” Dan kasuwane yanazuwa kasuwanni kasashe daban daban
Matarsa daya”” sadiya dansu nafari Abubakar Amman amfikiranshi da garba”” saikuma tagwaye datahaifa duka mata hasana da Husaina daga garesu batasake haihuwaba
Mahaifin malam garba acen wajen kasuwancinsa yabullah Niger yahadu da Hauwa” u kunsan bozayen Niger basucika bada yayansu ga hausawaba
Acewarsu basada rikon Aure itah kuma Hauwa”u ta tsunduma wajen son buhari””. Babu yanda iyayenta basuyiba akan tafita harkansa tabuga kaidakasa tace batason kowa saishi
Duka kuwa babu kalar Wanda batashaba Amman takekashe kasa tace shitakeso iyayenta sukace tosaidai tazaba koshi kosu awautarta saitace tazabi buhari

Wannan shine babban kuskureñda tatabka
Rashin bin maganar iyaye

Sukuma sukace toduk abunda yabiyo bayan auren karta kuskurah tanemesu koda auren yakwabe saidai tanemi wasu iyayen basuba tace ta amince”” 
Yayan mahaifinta shine sarkin Niger baiso suyanke mata wannan hukuncinba Amman tunda tanace ita shitakeso saisuka cire hannunsu daga sha aninta sukace tacemasa yaturo
Takuwa sanardashi ya turo iyayensa yabiya sadaki atake akadaurah masu aure sukace yadauki matarsa babu wani biki da akayi
Taci kuka hartagode Allah gashi itace kawai awajen mahaifiyarta”” ranar sukataso daga Niger sukazo kano acikin danginta ko kuda babu Wanda yarakota
Sadiya tariketa hannu bibbiyu duk da halayensu badayaba saboda Hauwa u tanada hakuri sosai itakuwa sadiya akwai fada dakuma mita Amman baruwanta daharkar kowa saifa idan antabata Amman Hauwa u koda dukanta kayi zata tambayeka Allah yasadai bakaji ciwoba;)
Shekaranta uku taredashi sannan tasamu ciki cikin yanabata wahala sosai haka tayita fama harta sauka tahaifi yarta mace sak kamanninta ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar buhari fateema suna kara anacemata yarbaba kamar yanda buhari yake kiranta tuni sunan fateema yabace sai yarbaba buhari yadauki son duniya yadorah mata
Kamar babuwata ya agabanshi face itah yanda yakerawar kafa akanta kaikace baitaba haihuwaba hakan saiyasoma damun sadiya tanarayawa aranta bayason yayanta 
Watakilma magani Hauwa u taimata dantasan yan Niger matsafane yanda takejin labari saitasoma sauyawa Hauwa u idan yarbaba tamatso inda take saita tureta tanacewa matsanan dangin mayu aniyarku tabiku
Kowani Abu Hauwa u tadafa bataci saitace ina nasani ko saida aka barbadeshi za aban Toni ba kwadayayya bace bataci kuma batabarin yaranta suci
Saikuma takoma tanayiwa hauwau gorin danamiji tanacewa komaidai tsafin mutum dole yabarta kuma itace dagida bamai Yar maceba
Tun abun nan bayadamun Hauwa”u haryakai yanadamunta gashidai batada wani Dan uwa dazata kaimasa kukanta yasharemata hawaye
Mijinsu kuma bayazama kuma idan yana nan Sam sadiya batanuna komai agabansa sannu kan hankali tasoma ramewa tanafita hayyacinta”” tatsakure kullum sai buhari yasata gaba datambaya meke damunta tacemasa bakomai idan yamatsa saita fada masa saita azamasa kuka haryagaji yakyaleta bayan ta yaye fateema dawata hudu 
Kawai tahada kayanta tacewa buhari gida zataje shikuma yace bazataba tace saitaje yace totabashi yarsa yakarbe fateema tanata kuka tatafi tabarta sadiya tanagefe kokallonta batayiba
Tundaga lokacin batasake waiwayarshiba shidinma bai waiwayetaba Fateema babu kalar ukubarda batashaba agun

sadiya batajin tausayinta kokadan
Tuntana karama hartagirma cikin wahala take”” lokacinda tagirma saitahadu dawani Muhammad shikuma dan yola ne bafulatani
Suka Kama soyayya sunatsaka da soyayya ne sadiya tasoma rashin lafiya
Hawan jinine yakamata gakuma mutuwar Rabin jiki damuwa tamata yawa hasana aurenta hudu abokiyar zama tahanata sakat duk inda tai aure sai abokiyar zama takoreta
Itakuma Husaina tahadu dawata arniyar kishiya tamaida itah boyarta komai aikin gidan itah takeyinsa kuma miji baida halin shiga dakinda take hasalima dakin awakai take kwana 
Wannan damuwar ita tahaifarwa sadiya daciyo datagadai ciwon saigaba gaba yakeyi saita tara kowa fateema hassana Husaina garba dakuma buhari
Tanemi sufaye mata”” laifinda taimasu”” kowayace batayimasa komaiba tana kuka takalli fateema tace Dan Allah yarbaba kiyafemun abunda naimaki son zuciya dakuma zugar makociyata itah takaini ga halaka nacutardake fateema narabaki da mahaifiyarki
Ta sake fashewa dakuka buhari yace haba yazaki daurawa kanki laifi ai ba aimata komaiba tatafi danhaka idan kawai mailifi tonine”” tasake share hawayenta tace wlh bakada laifi malam nice naimaku asiri na farraku gabadaya wajen sukahada baki asiri!!:oops: Tace kwarai kuwa lokacinda aka kawo hauwau wlh dazuciya daya nariketa tamkar Kanwata hartazo tahaifi yarbaba bantaba cutarda itaba
Lokacinda naga malam yasoma fifita fateema akan Yayana sai nasoma jin haushi tawannan hanyarne shaidan yasamu yashiga zuciyata yadinga yimun huduba sainafara kyararta ina tsangamarta
Danazauna inyita zaginta inacemata mayya” Amman bata taba fadawa kowaba saidai tabarwa zuciyarta watarana ina zaune saiga makociyar mu matar kabiru tashigo tasameni nayi tagumi tayita sallama banjiba alokacin Hauwa tana barci
Saida tatabani sannan nazaburah nanisa hannuna taja zuwadaki tace menene yasameki kika buga tagumi kamar wacce tarasa mijinta
Nadanyi tsaki nace dama shinarasa dasauki kinjikinji meyake damuna nalabarta mata komai shine tace nakwantarda hankalina akwai wani boka komai nakeso zaiyimun indai dakudi
Duk danasan zuwa wajen boka baidakyau Amman shaidan yarufemun ido nace sonake kawai arabasu tabar gidan
Shine nace Amman bazaniba saidai nabata kudin takarba tatafi waini wayone nayi saboda naji ance duk Wanda yatafi wajen boka kowani Dan tsibbo Allah bazai karbi ibadarsaba hartakwana arba in idankuma yamutu akan hanyarsa tagidan bokan yamutu kafiri waini nakizuwa domin natsirah
Bayan kwana biyu takwawomun laya tace inkama bakin layar indaure dawani kyalle na kayan hauwau injefa amasai sannan tabani wani garin magani tace inbarbada kofar dakinta nakarba nayimata godiya
Washe garikuwa tanabarci nalababa dakinta nayanko gefen zaninta nadaure layar naje najefata amasai nakuma barbada maganin kofar dakinta “” inatsakar gidan zaune nakwallomata kirah
Yautaji nakirata rabonda nakirata hartamanta cikin fara a dazumudi tafito batasan ni damugun nufi nakirataba tana tsilga maganin sainaga tajuya daki tahau hada kayantaa!!!

Aisha✍🏼

[2:36PM, 3/2/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 64

        By

Gentle Lady💃🏽

Tana fitowa kana shigowa. Tace maka gidansu zataje kaikuwa kacemata bazataba takafe akan saita tafi shine kace totabaka yarka Tabaka tatafi dama shine rabuwarku ance bazaku sake Neman junaba
Nikuwa tundaga lokacin nayita ganawa fateema azaba naso tamutu harguba makociyata tabani tace nasakamata acikin abinci Amman dayake batada rabon hawala kwananta basu kareba saigashi akuyata uwar gargen da yayanta takunce daga daurinda naimata tafada madafa dayayanta sukacinye abincin alokacin tana wajen dibar ruwa
Koda tadawo saidai naji tanasalati tana kiran sunana koda nafito damasifa sainaga abunda yafaru ga dabbobina wannan shine asalin abunda yafaro ciwona domin dasu nadogara akuya bakwai duka sukai musai
Takaici yasakani nakilmawa fateema kashi nace itah tazubamasu guba dantana bakinciki da arzikina kaikuma saika yarda kasake dukanta taja majina kaji abunda yafaru tun alokacin naketa ganin i shara gashi Ya.yana sunyi aure abunda naiwa Hauwa suma anaimasu
Ninasan abunda nashukane nakegirba wlh nayi nadama Dan Allah kiyafemun fateema yarbaba tana kuka tashare hawayenta tace bakomai innah ninayafe maki duniya da lahirah
Buhari kam shiru yayi danyakasa magana saida tasake neman gafararsa yace nayafe naki sadiya bakece dalaifiba nine mailaifin tunfarko daban fifita son yarbaba akan sauran yayanaba dahakan batafaruba
Hakika nikaina na aikata babban laifi duka yayanane kowanne amanace agareni baidace kafifita danka akan wani danba koda kafisonsa aranka kadinga yin kawaici musamman idanma yaran ba uwarsu dayaba hakan zai iyah janyo rabuwar kan iyalinka kekuma dakinkirani kinyimun nasiha aibawani abubane
Amman kin aikata babban laifi wacce kika zalunta Hauwa inazakiganta kiroketa gafara kokinsan Allah baya yafe hakkin wani hakika hakkintane ke bibiyarki kamar yanda itama hakkin iyayenta yake binta
Mun aikata son zuciya munbiyewa soyayya hakan yasaka batayi rabuwar dadi da iyayentaba sunce tazaba kosu koni tazabeni rashin bin maganar iyaye shine yajawo mata haka harkuma yashafi yarta
Allah ya yafemana kura kuranmu suka amsa da amin tace malam taimako daya zakamun kaje Niger wajen danginta tayiyu takoma gidane idan kaganta kanemamun gafararta sannan kamaida matarka nasan haryanzu kanasonta ninasan ciwon nan nawa banatashi bane “””
Yace nayimaki alkawari zantafi duk danasan abune mai wahala su saurareni dansuna ganin kamar nine silar rabasu dayarsu kidaina maganar mutuwa aicuta bamutuwa bace insha Allah zakisamu lafiya dakanki kinemi gafararta tace hmm kawai dan itah kawai tasan metakeji 
ranar jikin kowa yayi sanyi sukuku suka wuni washe gari kodasuka farka saidai sukaga gawarta tacika cikin dare tashin hankali sunganshi bakamar garba yanaganin mahaifiyarshi tashuka abunda bazai barta kwanciyar kabariba
Sati biyu darasuwarta garba yamatsa aje Niger buhari yashirya suka dunguma hardasu hasana da Fateema”” Amman dasukaje gidansu Hauwa mahaifinta ko saurarenshi baiyiba yayimasa korar kare 
Dayaki tafiya fateema kuma tahau kuka bindiga yadauko yace kosubarmasa gida koya dirkesu da bindiga dole suka futa fateema tanata waigen kakarta wacce taketa kuka” dankuwa babu abunda yaraba Hauwa da fateema
Agarin suka kwana buhari yayita tambaya koda tadawo garin akacemasa batadawoba tunda ta auri wani bahaushe tayafe gida aikowa yabargida gida yabarshi
Washe gari sukadawo Nigeria saikuma buhari yakwanta jinta danyanzu soyayyar Hauwa tadawomasa sabuwa watanshi daya shima yace ga garinku
Fateema takoma marainiya garba shike tallafe dagidan haryayi aure alokacinne Muhammad yafito daniyar auren fateema 
Muhammad yanada mata daya sunanta rukayya sunyi auren saurayi da budurwa amman haryanzu bata tabayin koda batan wataba

Aurensu kuma wajen shekara takwas kuma shi yana masifar son Yaya Amman yanason matarsa hakan yasaka yakiya kara aure saigashi yakawowa wani abokinsa ziyara kano haryayi sati daya akasuwa yahaduda fateema an aiketa siyo kayan miya yabiyota haryaga gidansu kunji sanadin haduwarsu 
Garba dayaji yanada mata kuma gashi zatayi nisa dasu saiyace tahakurah dashi tasamu wani itakuma tace shiitake so tarihidai yasake maimaita Kansa domin fateema takafe kaida fata saishi
Garba yanajin tausayinta dakuma halin kuncin rayuwa datashiga bayaso yatakurah mata sanin yanda soyayya take saiya amince Muhammad yaturo magabatansa akasarana suka biya sadaki suka kawo lefe akasa biki wata uku
Wata uku sunacika aka dauramasu aure matar garba balkisu macece wacce baruwanta itace komai na fateema su hassana ma suntaka rawargani sun nuna bajintarsu amatsayinsu Na antys dinta garba yahada kudinda za asiyamata kayan daki acen yola akasiya akajerah mata babu laifi sunyimata kaya kamar diyar maikudi
Ranarda za akaita har yola saida suka rakata sukaga gidan sun yaba sosai dahalin rakayya sai nan nan takedasu sunsan kanwarsu tayi dacen abokiyar zama
Saida suka kwana washe gari kuwa dazasu taso sunsha kukan rabuwa haka suka rabu suna kewar juna saidai rukayya tayita basu hakuri
Watan fateema uku saigaciki yabullu nawata uku danbata cilge wataba”” zokuga murna wajen rukayyya harma taso tafi Muhammad murna””batabarin fateema koda chokali taka war komai itah takemata hatta wankin kayanta
Saikuma dangi sukafara jefan rukayya da habaici dama anacemata juya toyanzu zance yatabbata itace juyar gashi Amarya tasamu ciki itakuma batada aiki saidai taci takasayar 
Hasbinallahu wa ni imal wakil kalu innalillahi wa inna ilaihir rajiun waimenene amfanin yiwa wani gorin haihuwa??? 
Shinkeda kika haihu wani Abu kikayi yasaka kika haihu??? Wayonkine kokuma dabararkice??? Anasiyenta dakudi kokuma mulki zaibaki??? 
Itah dabata haihuba laifi tayiwa Allah ko anfada maki Allah bayasontane??? Waimeyasa mutane basuda tunani kisani duk wacce kikaiwa gorin haihuwa wlh hartamutu bazata manta dakeba kuma kema bakiwuce Allah yakarbe yayanda yabakiba sannan kidaina haihuwar aganina inhar wata acikin danginku matar yayanki ko matar babanki ko kanwarki kishiyarki inhar hakan yasameta saiki kwantarmata da hankali kice tacigaba dayin addua Allah maji rokon bawansane

Aisha✍🏼

[3:51PM, 3/2/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

chapter 65

       By

Gentle Lady💃🏽

Amman saikuga adinga kyararta abunma yawuce gida har yan unguwa todakuma aikomai daga gida yake tashi sunga kunayi mezaihana suma suyi
Rukayya tayita hakuri dasu hartakai sunazuwa sunacewa fateema in rukayya tabata Abu kartaci dantana bakincikin cikinda kejikinta
Dayake fateema tanada hankali Sam bata daukar maganarsu Amman kunsan dawatace ahakan saikuga wata fitinar ta auku kaimiji kanacen kana nema masu abinci

Bakasan ta inda fitina zatakunno kai agidankaba koda zaka farga wuta hartaci tacinye alokacin koda kaso ka sasantasu abun yafikarfin tunaninka
Cikin fateema yacigaba dagirma haryanzu tanabaiwa rukayya girmanta” bata daukan zugar dangin miji sukuwa abunsu saigaba gaba yakeyi cikin fateema yanashiga wata Tara tasuntulo kyakkyawan danta kinkowa Wanda yarasa babansa sak 
Waiyo zokuga murna wajen rukayya musamman tahada walima saboda murnar saukar fateema lafiya kayanda tasiyawa yaron kuwa kowadanda mahaifinsa yasiyamasa basukai yawan nataba
Ko maijego kala goma tadinka mata tayi gayyar abokananta sukansu kallonta kawai sukeyi da mamaki dangikuwa tunda sukaga fateema tahaifi namiji saikuma gori yadawo sabo
Ranar suna akasawa yaro suna muktar harsu hassana saida sukaje biki”” taro yawatse su hassana dakin rukayya suka kwana sunsha firah washe garin suna suka koma
Wata tsohuwace takekulada fateema hartayi arba in”” sukacigaba dazamansu lafiya”” saifa dangin miji idan sunzo gidan basakiran muktar dasunansa saidai sucemasa magajin gida!!
Sam abun baidami rukayyaba harma abun yasoma bata dariya watarana tanazaune alokacin muktar watanshi goma dayake bayada kiuya hannuntama yake kwana nono kanshi baidameshi ba saidai idan yana kuka da anbashi ruwa shikenan
Fateema tatafi wajen kitso da lalli tunsafe tabarmata shi sallama tajiyo anayi tata so tana am sawa tadage labulen kofa tace la la la Asma.u kece agidan nan???
Maraba maraba shigomana tadorah muktar akafadarta wacce akakirah dasunan asma u tawuce saman kujerah tazauna rukayya tace daga inakike haka cikin tsakiyar rana
Asma”u taharareta tace zakice haka tundake bakyason zumunci aini karanima inazuwa tunda bakyason zumunci sainadauke kafata
Rukayya tace habadai Yar uwa wlh aikine bayabarina fita ko kitso rabona danaje amun harnamanta saidai maman muktar takeyimun danzanen yawo
Asma” u tamere baki”” rukayya tace rikamun shi nakawomaki ruwa tayi maganar tana mikamata shi tajaye jikinta dasauri tace wa ?? Ninadauki Dan kishiya Allah yasauwake
Rukayya tayi dariya tace kice haryanzu halin yana nan???🤔 Tace hargobema indai akan kishiyane sai abunda yacigaba!!:?

.

Rukayya tayi dariya tace Allah yashiryeki Kawata nidai bansan lokacinda zaki saki makamankiba kiyarda kishiya abokiyar zamace
Asma”u tasheke da dariya tace inakika taba ganin anzubarda makamai afilin daga??? Shifa abokin gaba dakike gani duk wani kwantardakai dayakeyi na munafurcine soyake yashammaceki
Dazaran yasamu sa arki kasheki zaiyi”” ance kakashe makashinka tunkafin yakasheka”” rukayya tace kedai kikasan wannan hadisin”” tawuce baridai inbaki ruwa yana akafadarta takawomata ruwa tasha
Tazauna kusa da itah saiga muktar yasaki fitsari tace kai yaudai kasharuwa dayawa saifitsari kaketayi batagama rufe bakintaba yasaki zawo tuni yabata mata kaya
Asma” u tayi saurin rufe hancinta wai itah doyi rukayya tana rungume dashi tanabuga bayansa ahankali haryagama taje tawanke masa tasauya wani zani tasakamasa wando
Tadawo tazauna yihakurifa Kawata nabarki kedaya”” tajatsaki ahakadai zaki kare dabautar danwani rukayya tabata fuska tace menene haka Asma”u Dan mijin nawa shine danwani dakikecewa zankare abautarsa aidama bauta nazoyi
Idan inason mijina yazama dole naso jininsa Asma”u tace tosannu daddawa dadi amre najinjina maki tobari kiji kokiso kokiki yaron nan dayagirma uwarsa yasani
Dakike ikirarin bauta kikazo kefa yanzu hotoce kawai awajen mijinki” tayisaurin kallonta tace ahmana kehotoce saboda mijinki yanason Yaya sosai kingakuwa wacce zatayita haifamasa Yaya saitafiki fada keyanzu amatsayin Yar raino suka ajeki tanahaihuwa anabaki kinacinkashinsu dafitsari dazaran sungirma lokacinda dadi yazo maimakon kucidadin tare saitanunamaki kefa bakisan yanda dayake kwanciya amahaifaba
Alokacin zata nunamaki itace tahaifi danta”” aini tunranar suna kikabani mamaki nasona kyaleki saikumà naga idan naihakan bankyautaba amatsayina na kawarki.
Tagyara zama ninazomaki damafita idan kinaso??? Rukayya tayi shiru tace nidai mubar maganar nan nima indarabo zanga nawa
Tayi saurin gwatseta tace yaushe??? Inda kinada rabon haihuwar aidakin haihu tunkafin yakaro aure gashi yayi Amarya daga zuwanta tasamu ciki zauna nan wlh saitacika gidan nan dayaya kekuwa kizama Yar kallo
Shekararki takwas da aure tunyana talakansa futuk kika aureshi gashi yazama maikudi tamurmusa kibar ganin wannan daular wlh dazaran yamutu bazaki tsirah dakomaiba sai bakinciki
Bazakiyarda da maganataba saiyafadi yamutu sukuma Yaya sukoma wajen uwarsu kinga bakiga yantusa yanzawo suntsere yanzu kikeda dama idankuma kikabari damarki tawucemaki tokece zakiyi kuka baniba nidai amatsayina na kawarki naga abunda zaicutar dakene nazo nafadamaki inkindauka ruwanki idanbaki daukaba ruwanki sainangaba zakiyi danasani alokacinda danasaninki bashida wata rana
Ta mike nidai kinga tafiyata idan kin sake shawara kije gida kisameni ashirye nake da intaimaka maki sai anjima idan uwargidan Muhammad tadawo kimika gaisuwata tawuce abunta
Kotadakai rukayya batayiba har fateema tadawo tasameta cikin wannan halin tatambayeta meyake damunta saidai tacemata kartadamu bakomai”” 
Kunsan shaidan shifa danwaje yakeso yasamu ya lababa yaitayi mana busa akunne hakanne yasamu rukayya maganganun Asma” u sukaita mata yawo azuciya taso takawarda tunanin takasa 
Sati daya dafaruwar hakan fateema tafara rashin lafiya anazuwa asibiti akace tanada ciki wata uku abunda yayi matukar tayarda hankalin rukayya sai aka yaye muktar akabarshi hannunta
Kullum Muhammad yana nane da fateema mekikeso mene bakyaso rawar kafarda yakeyi yanzu saitasoma baiwa rukayya haushi hartasomajin haushin fateema
Gashikuma cikin fateema yazoda laulayi komai taci saita amayar dashi “” sai Muhammad yatarkata aiki yadawo jinyarta watarana yana zaune yanabata abinci abaki saida tagama cinyewa tasoma kwara amai
Saida ta amayardashi duka”” Muhammad duk yarude sai sannu yakemata rukayya tanazaune tana kallonsu yacemata taimakamun da Abu ingoge
Kamar tace bazaniba saikuma ta mike tafita yacema fateema sannu kaitagyada yace yanzu mekikeso kici??? Kaitagirgiza yace haba uwar Yayana yazaki zauna dayunwa kisamu koda tea ne kisha

.

Kuka tafashe dashi tace banaso banajin dadin komai yakoma rarrashinta najito uwar Yayana Amman kinsan likita yace kirika cin abinci saboda Karin kafiyarki dakuma Dana dayake jikinki shiru tayi batace komaiba
Rukayya kuwa sanda yakecewa uwar Yayana Kalmar tafada akunnenta tafara nanata sunan aranta lallai zancen Asma” u gaskiyane inhar fateema tacigaba da haihuwa agidan zatacika gidan da Yaya
Idankuma hakan tafaru itakuma menene matsayinta wata zuciya tace Yar raino mana dasauri tace wlh karyane bazan yardaba
Ganin tajima bata dawoba Muhammad yasake kwalamata kirah tazaburah tashigo dasauri tace yihakuri jinayi kamar kukan muktar nadauka yatashine sainaje naduba shiyasa nadade
Yace bakomai yakarbi ruwan da abun gogewa yagogemata bakinta rukayya tanayimata sannu tanakuma harararta😣😂😂

Aisha✍🏼

[9:22PM, 3/3/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 66

       By

Gentle Lady💃🏽

Daga fateema har Muhammad basu lura dawani chanji tattare da itah ba saidaifa tadaina sakewa da fateema kamar da
Saisuka danganta hakan da damuwarda tashiga narashin lafiyar fateema idan fateema talangaye wa Muhammad tana kuka sai rukayya taraya aranta duk kissace da kisisina babu abunda yake damunta
Shedan yadinga yimata huduba tawanke kafarta tatafi gidansu Asma” koda tashiga da sallama tasamu mijin Asma u yanawankin kayanta yashanya wasu gakuma wasu tulin kayan sannan kuma gashi yana girki
Yatara uban zufa sai sharcewa yakeyi rukayya tagaidashi sannan tawuce dakin rukayya saman kujerah tasameta tahakimtse tanacin naman kaji abun nan yamatukar bawa rukayya mamaki tana ganinta tatashi daga kishingidarda tayi tace yaukece agidan nan kodai batan hanya kikayi???
Rukayya Tanisa tace kusan haka”” ta sake kallon kofa tace anya Asma”u kinatsoron mutuwa??? Tace danayime???
Rukayya tace hmm abunda nagani mijinki kike sakawa wanki??? Tamere baki waisaboda dan “”wannan wayasa ya auroni idan bazai iyah daukar dawainiyataba
Rukayya tace lallai haryanzu dasauranki karfa kimanta aljannarki tana karkashin kafarsa”” idan baidagaba bazaki shigaba
Kunkumi tarike tace abudole tsufa da duwai aiyazama dole yadagamun inshiga””abunsaiya bawa rukayya dariya tace Allah yashiryaki 
Tace ameen bamaki addua ba”” :?rukayya tace bawan nan banidai zuwanayi akan maganarmu taranar Asma “u tasheke da dariya tace bake bace idan kaga kigudu sagudune baizoba inazuwa tayi maganar tanamikewa
Rukayya tabita dakallo yanda Asma u tagoge kamar wata hajiya miji duk yakanjame bakin kofa tatsaya tace isihu korufe bakinta batayiba saigashi dagudu yazo haryanacin tuntube yace mekikeda bukata rankiyadade
Tayatsina fuska bakomai kafita waje kasha iska zuwa anjima karka dawofa saina kiraka”” yace shikenan godiya nake yajuya yafita dasauri
Tasaki murmushi sannan takoma wajen rukayya wacce tasaki baki tanakallon abunda yafikarfin tunaninta
Asma u tace Kawata inajinki ” rukayya tanisa tace maganarda mukai ranar yanzu maganarda nakemaki cikine da itah
Asma”u tace kadanma kikagani bake tsoron Allah ba”” rukayya tace yanzudai duk abar maganar menene mafitarda kika samamun???
Asma” u tagyara zama tace duk mafita tawuce irin tawa Rukayya tace kamarya banganeba Asma”u tace akwai wani boka sunansa *hatsabibin boka* aikinsa kuwa nantakene inhar kinyarda zakije wajensa tokeda kuka har abada
Kunyi bankwana da bakinciki jinta ambaci sunan boka yasaka rukayya tazama tatsaye tace Asma u yanda nake ganinki ashema kinwuce nan boka dai! gaskiya danasan wannan itace mafitarda kikasamamun dabanzo gidankiba Allah yakareni da hatsabibancinsa
Asma”u ta sake darawa tace aini gatanaimaki tundahar nakeson hadaki da babban boka Wanda babu kamarsaa aduk fadin duniyarnan
Rukayya tace gatafa kikace ahakan??? Aibashima yadace akirah hatsabibiba faceke sunan yafi dacewa dake
Asma”u tace kinga nidai bansakaki doleba ra ayine idankinji bazaki iyaba””kitafii haka kurum kefa kika kawo kanki banice” natilas takiba idan abun yadameki dakanki zaki dawo
Rukayya tamike tace badai wajen *hatsabibin kuba* wlh bazaniba haka kurum ina zaman zamana kinzo kintayarmun da hankali duk tunani yadameni
Tace kinga tafiyata Allah yashiryeku tawuce abunta Asma u tace tokigaida uwar yayan Muhammad wannan kalmar tana matukar tsayawa azuciyar rukayya
Koda takoma gidan tasamu Muhammad gida sai lailayar fateema yakeyi taci abinci tanatayi masa kuka abun yasake kularda rukayya tanashiga da sallama tadage kanta tawuce fuuu kamar kubu buwa
Fateema tace me akayiwa Anty kuma”” Muhammad yace tobadai mune mukabata mata raiba”” idan tahuce aizata fito dayake fateema batason magana saita kama bakinta
Itakuma rukayya tayi tunanin zaibiyota taji tsit saita fashe da kuka tayi mai isarta dole ta share hawayenta ahakadai akayita gurgurawa da dadi ba dadi harcikin Fateema yakara girma tadaina laulayi “”cikin ta yana shiga wata Tara takama nakuda 
Cikin tashin hankali Muhammad yasakata amota zuwa hospital batawani jimaba ta sake haiho santalelen danta kinkowa Wanda yarasa kyakkyawa sak kamar muktar
Zokuga murna awajen yan uwan Muhammad kamar suhadiye fateema””kayakuwa tashasu kamar hauka kokayanda Muhammad yatirka mata saiwanda yagani 

Sati yana zagayowa akayi suna wannan karon su hasana kawai sukazo Dan matar garba tana fama da laulayi
Yaro yaci sunan Umar faruq”” anakiransa faruk yanbiki sukaci sukasha sukai kat kowa yawatse akabar maijego da yaronta
Muktar kullum yana makale da fateema danyana mutuwar son yaron duk da ko anbashi baya iya daukarsa danyanzu shekaransa daya dawata takwas
Fateema tanaganin yan sauye sauye atattare da rukayya Amman batakawo komai aranta tacigaba darainon danta” tuni rukayya tadaina sakewa muktar fuska
Faruq yanada wata shida saigashi fateema tasoma laulayi tunda akace cikine da itah tahau kuka ita wlh bazata yardaba saidai azubarda cikin
Shikuma Muhammad yace wlh baza a zubar dashiba shiyanason abunshi takaicima yasakaa tabaroshi asivitin
Yanata kiran sunanta kowaigensa batayiba tanafita tatari Dan adaidaita tasanardashi inda zaikaita Muhammad raibace yabaro asivitin
Anakaita gida tabiyashi kudinsa tafada gidan tana kuka”” rukayya tataso dasauri tace lafiyarki fateema ina abban faruq din??? Meyasameki kiketa kuka
Batagama rufe bakintaba yana shigowa yace fateema Ashe haka kikeda taurin kai”” taballamasa harara tace dankawai kaibakasan wahalarda akeshaba da ajikinka yake aidabazakace hakanba”” 
Rukayya tace waimeyake faruwa niduk kuntayarmun dahankali tayi maganar tana kallon Muhammad
Yace tambayeta gatanan”” tajuya wajen Fateema tace meyafaru cikin kuka tace wai Anty cikine dani
Rukayya tace ciki nashiga uku harkin kuma samun wani cikin itah batasan inda maganar rukayya tadosaba tace ah wai Anty shinefa nace azubar waibaza a zubarba
Haba kwata kwata shekarana nawa da aure ace inada yara har uku kumama ba wannan ba umar fa watanshi shida aikodan sabodashi zaiji tausayinsa
Rukayya dai daka tahana wuri magana dangaba daya hankalinta yagama tashi lallai idan tayi sake maganar Asma u gaskiyace fateema zatacika gidan da yaya haihuwa kamar akuya😾 dama matane dadan sauki koyanzu watakil namijine zata sake haihowa
Muhammad yakatsemata tunani wajen magana yace wlh fateema baza a zubarba ai wannan rashin godiyane kitunafa aurena shekara takwas Amman bansamu magajiba saiyanzu danake ganin gudan jinina kinaso azubar Yayana Na halak ne kuma inason kayana nibanki wlh kihaihu duk bayan wata taraba
Rukayya Tananata Kalmar aranta *magaji* babbar magana dolene nadau mataki idankuma bahakaba inaji inagani gidan nan zai gagareni soyayya taci ubanta🙄
Koda tafarga har fateema tashige dakinta saidai taji Muhammad yana bubbuga kofar yana hadata da Allah tabude itakuma sairusar kuka takeyi
Dasauri yafita idonshi jawur kaman Wanda akadaka yaja motarsa yayanki titi tsaye nahango rukayya kamar mutum mutumi tarasa inda zata saka kanta
Tana nan tsaye tajiyo sallamarsa bayansa kuma”” gwaggo rabiee ce kanwar mamarsa tashigo dasauri rukayya tana gaida itah kokallonta batayiba tayi hanyar dakin fateema tasoma bubbugar kofar bude Fateema nice haba Yar kwarai irin albarka kibude kinji fateema
Fateema CE tabude takoma tazauna tacigaba da kukanta”” gwaggo rabie takarasa saman kujerar tazauna Muhammad shikuma yanatsaye yakuramata ido
Gwaggo tace haba mai babban suna yazakiyi haka kitausayawa babangida mana dayake haka suke kiransa sunan babansune
Tace ai wanann abun farincikine abun alfarinkine ace kinada ciki menene amfanin azauna saidai aciyarda mutum yana tula kashi
Indai faruq ne karkisamu damuwa babu abunda zaisameshi dazaran anyi wata uku zanzo inkarbeshi saina yayeshi kekuma saikiyi rainon danku
Kinji fateema kiyi hakuri tunda kinga babangida yanason yaran nan”” kinji mai babban suna”” fateema tashare hawayenta tace tahakurah wani dadine yalullube Muhammad 
Bayan tagama bata baki sannan tafita suka gaisa da rukayya tace kiyi hakurifa wlh hankalinane atashe shiyasa bangankiba”” 
Tace bakomai ai nikam nasan taciki naciki dankuwa ranar rukayya kasa barci tayi saidai takai gwauro takai mari
Mafita dayace dolene inkoma wajen Asma” u muje wajen bokan dankuwa banada wata mafita wacce tawuce wannan ai Allah maiyawan gafarane idan nadawo saina nemi ya yafemun
Shikenan ai Allah yaga zuciyata wannan abun zaicutardani kuma Allah yace tashi in taimakeka Dan nanemarwa kaina mafita bazai kamani da laifiba
Dawan nan shawarar hankalinta yakwanta takoma takwanta tanamai murmushin jindadi “” wai hauka shaidan yazo yalailayomata wadansu banzayen maganganu wai Allah yace tashi in taimakeka aibata wannan hanyar yace abiba
Koyace acutarda wani dansamun farincikin wani waifa tace idan tadawo tanemi gafarar Allah kwarai Allah gafurur raheem ne
Amman Allah baya yafe hakin wani shinbatayi tunanin tanakan hanyar kobayan tadawo tahadu da ajalinta kafin tatuba ??shin idan taje gaban Allah tanada hujjar dazata kare kanta ??indai abunda tafada shine hujjarta lallai hujjar banzace dankuwa batariki hujjaba
Rukayya abunda batasaniba duk Wanda yaje wajen boka to Allah zai zaremasa imaninsa tamkar yanda akezare lakka ajikin kashi
Aganinku duk wacce taje wajen boka tanada sauran imani kije kawai dankisa acutarda Yar uwarki ke kodama badaniyar cuta kikajeba baikamata kijeba
Dawan nan bakin kudirin takwana washe gari lomar fari tunda take bata taba fitah gidanba batareda izinin Muhammad ba saigashi tayi satar hanya
Koda taje gidan tasamu Asma u zaune mijin yanayi mata tausa akafafunta tanaganinta tasheke da dariya tace bakebace
Tamaida kallonta wajensa tace sai abamu wuriko kanata kallonmu wiki wiki da she gun idanuwanka tuni yasanne kansa kasa
Yamike yafita tamaida kallonta wajen rukayya cikin fara a tace zauna Kawata tazauna tana kallonta”” tace koyauma zuwa kikai kicimun mutunci dani da *hatsabibin boka???* 
Rukayya tashare hawaye tace bar maganar wasa Kawata zuwanayi kitaimakamun yanzufa waikuma tasake kunsar wani cikin
Tasake fashewa da kuka”” tace wlh komenene zanyi indai zatabarmun gidana banason buda ido naganta cikin gidan dashegun yayanta
Asma “u tasheke da dariya”” tace bakebace dai ainafada maki”” rukayya tace toyazamuyi

Asma u tagyara zama tashinfida mata dukkan dokokin shiga dajinda *hatsabibin boka* yake dakuma saradansa idan zata iyah 

Tace komenene wlh zan iyah Asma” u nidai banaso naganta agidan
To Rabie da Aisha saiku shirya Dan tare zakuje kudibo mana labarai😂😂 karnaji kunce bazakubà dankodà igiyane sainajaku inda Wanda zàshi kàllo yamun magana naga kamar motar takusa cika🚌

Aisha✍🏼

[2:08PM, 3/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 67

       By

Gentle Lady💃🏽

Tace indai wannan ne karkisamu damuwa indai akwai shegun to komai kikeso zakisamu aidama tsiyar abu rashin kudi gashi kanagani Abu yafikarfin ka
Amman idan akwai kudi hmmm komai kikeso zaki iyah tambayarsa kidairike sharadansa nazuwa wajensa sannan kuma duk abunda kikagani adajin tsapappene kar wani karambani yajaki kitaba Tam
Rukayya tace nikam mezantaba Kawata ??? Tayi maganar tanarike habar gemunta tace nifa ko acikin kaset naga boka jikina har ciccira yakeyi saboda tsoro ballantana kuma inga wannan da idona”” tabdi kedai kawai muje
Asma “u tace waikina nufin yanxun??? Hmmm kinsan kowacce kasa yake kuwa??? Rukayya tace shinbama kasar nan yakeba???
Asma “u tace babbar magana aiyafi karfin zama anan kenan cikin arha zakisamu komai tobari kiji taraba yake

Rukayya tawaro ido tace tarabadai tarabadai wacce nakeji anafada??? 
Asma” u tace kawaimakuwa itah”” rukayya tabuga tagumi tace Toni tayama zanje taraba nidabantaba zuwaba??? 
Asma”u tace nima kaini akayi gashikema zankaiki bake daya zakiba dazakice kinbace hanya” rukayya tace bazaki ganebane”” taya zansanarda Muhammad zantafi taraba??? Wlh bazai narniba”” 
Asma” u tace Amman ke bahwanyace inbanda haka tayazaki sanarda miji ainahin inda zakije barikiji dazaran kinkaida kudin kamar anasaura kwana uku kicemasa Na gaiyaceki biki garinmu Kanwata za ayi aure wacce take hannun yayar mamana kaduna take
Kinga kwana biyu zakicemasa dazaran munje muyi abunda yakaimu mudawo koyakika ganie

Rukayya tace kinkawo shawara maikyau Amman Anya zaibarni naje waniguri inyi kwana biyu??? Asma”u tace barikai aiyanzu yanda yakeson fateema wlh koda wata daya zakiyi bakidawo ba bazaiwani damu sosaiba 
Rukayya tayi shiru sannan tace kinga inayin wani dashi kuma jibi za ayi kwasa tawace inaganin kawai saimu tafi tace shikenan dazaran kudin sunshigo hannunki saiki kirani kiyimun magana”” tace shikenan sukai sallama tawuce gida
Allah yasa Muhammad baidawoba da sadade takoma dakinta danko sallama batayiba ko Fateema batasan dafitar tata 
Illaikuwa tana karbar kwasarta tasanarda Muhammad zataje garinsu kawarta Asma u kanwarta za ayiwa aure yace shikenan kwana nawa zakuyi tace biyu nakeji yace shikenan yadauki dubu hamsin yabata yace tayiwa Amarya sayayya tayi murna sosai dama tana tunanin kudinta kamar bazasu isah ba”” 
Washe gari tashirya dama tasanarda Asma “u Fateema tayimata Allah yakiyaye tace Ameen”” aranta kuwa tace hmmm bakisan wannan tafiyar ta kibace ta musamman

  Tanafita tayi gidan Asma “u tasameta hartashirya itakawai takejirah tanazuwa suka wuce dayake tasha suka shiga motar bawai jirgi bane basu suka kai taraba ba saikusan goshin magrib
Rukayya tace itakam tagaji susamu gurin kwana”” Asma u tace nifa duk nazo garin nan gidan wata magajiya nake kama hayar daki kinsan hotel akwai tsada idankuma kinada kudi isassu saimuje
Rukayya tace sujedai gidan magajiyar suhuta kafin magrib hakan kuwa akayi sukaje cen dama tunda bajimawa sukeyiba dakin magajiyar takebasu Dan ita ma tana dai dagacikin costomomin *hatsabibin boka* duk wacce tsautsayi ya Kaita fadawa hannunta hardai idan taga kinaja anasamun kudi akarkashinki haka zatakai sunanki wajensa atsafeki akafeki gidan tayanda bazakisake dagawa wurinba harsai idan kinmutu
Duk wacce akaiwa auren dole tagudu kokuwa tsautsayi ya afka kanta tayi ciki kafin aure idan tagudu daga GIdan uwayenta tashiga duniya
Tahaduda tambai yarduniya tokuwa tazama nama”” akwai wani kwalli datake bawa yaranta suna shafawa Wanda takarbo wajen *hatsabibin boka* muddin suka shafashi dasunyi ido hudu dakai tosaidai wani kariyar Allah idankuma harkasoma harka dasu bazakataba bariba 
Danduk kakwanta dayaranta bazatasake jindadin mu amala dakowacce maceba”” takenta kuwa yaranta bawai saida dare sukefita kasuwancinsu ba

.sunazuwa kasuwanni dakuma manyan kantuna inda sukasan manyan attajirai sunazuwa hakazalika sunazuwa bikin manyan yankasuwa
Dakuma gamnoni kodakuwa ba agaiyacesuba saisunje Kuma ba ahanasu shiga kodakuwa basuda ticket din shiga
Suna zaune sunazuba firarsu rukayya tamike danjin ansoma kirah asma”u tace inakuma zakije?? Takalleta da mamaki tace banganeba sallah zanyi bake kikace da anyi sallah zamu wuceba
Asmau da magajiya suka bushe da dariya magajiya takalli asmau tace wannan dai sabuwar zuwaceko??? Asmau tace ah wlh bakigantaba sai ahankali
Takalli asmau tace inasharudan da nafadamaki kafinma muzonan??? Ita rukayya sam tamanta

Tace kash wlh namanta Kawata”” Asma u tace akwai aikikuwa wlh idan kikai kuskure baburuwana dake dashine dannafada maki duka dokokinsa kikace kinji kinganie
Rukayya ta marairaice fuska tace yazakice haka aikinsan daban mantaba bazance namantaba waye baya mantuwa aduniya
Asmau tace kowa yanayi Amman inaso Kituna da abudaya wlh *hatsabibin boka* baya yafiya duk kikai masa laifi babu imani zaihukuntaki danhaka kikama kanki mufita lafiya kodai ince kekifita danni qalau zanfita
Rukayya tace tonima ai idankuma harwani abu zaisameni ai anyi ba ayiba kenan ina amfanin badi barai”” kedai kawai kisake sanardani zankiyaye asmau takalli magajiya wacce taketa busar dariya itama tadarasuka tafa sannan tasake korawa rukayya bayani

 Ana kare sallah suka kama hanyar kauyenda yake bakin hanyarda zata sadasu da dajinda yake aka saukardasu suka kama hanya harsuka iso fadarsa dajin dai yana nan kamardai yanda su lubcy sukazo saidai akwai wasu sauye sauye

Danyanzu duhuwa tayiwa wajen yawa kaikobakin dajin ka iso dole katsorata gabadaya yanzu yatsafe dajin kogonda yakecikima yanzu koda kazoma baka ganinsa tayama zaka iyah shiga dajinda yake dauke damiyagun namun jeji da abubuwan firgitarwa
Kafin kakaima tsakiyar dajin kagama yawo saidai uwarka tahaifi wani””” haduranda sukecikin jejen bazasu faduba saidaikayi kokarin hana kanka zuwa gurin
Abudayane zaitserar dakai idan yasan dama wajensa zakazo kodahakan ma saidai katsaya bakin jejin karufe idonkaa saikakirah sunansa takezakaji anyi sama dakai karka kuskurah kuma kabude idonka idankuma kabude 
Namun jejin dakuma miyagun gungun aljanu masucin naman bil adama sune zasuyi kalaci danamanka yaga yaga za aimaka tayanda kowane guntun naman jikinka bazaiwuce tsoka dayaba”” 
Dakaji iska talafa bakamar sanda aka surekuba saikabude idonka take zakaganka kabayyana agaban *hatsabibin boka* idankuma zakubar dajinma hakane anan zakurufe idonku saikuji ansake sunkutarku koda zakubude ido kuganku bakin dajin daganan saikuwuce abunku
Asmau tasanarda rukayya yanda zasuyi kuma tace karta kuskurah tabude idonta rufe idonsu keda wuya sukaji ansunkuceku anyi sama
Sauran kadan rukayya ta kwamtsa ihu”suna bacewa bakagansu ko inaba saicikin babbar fadar *hatsabibin boka*
Naga sauyi sosai awajen gakuma kayan alatunan tako ina saikuma tarin kayan tsafinsa rukayya tanayin ido hudu dashi jikinta yasoma rawa 
Asma u itace tasoma koramasa jawabi kafin yace tayi shiru yasan komaiketafe dasu
Yamaida dubansa wajen rukayya yace mekikeso ayimata??? Tace sonakeyi asaka fitina datashin hankali atsakaninsu banaso tabargidan farat daya yan uwansa zasu iyah zargina
Itakuma inaso kowa yatsaneta harta mutanen unguwarmu saita gammace mutuwarta akan rayuwarta yayanda take takama dasu suma surika gudunta 
Daka karshe idantagama wulakanta saiyasaketà alokacin duka yan unguwa dama ta ishesu sai kafitarda duka soyayarta azuciyar mijina
Bayan tagama korah jawabi *hatsabibin boka* yakece dawata mugunyar dariya tamkar jakiii nakuka yace wannan babu abunda yafishi sauki awajenmu
Shanruwa ma zaifishi wahala”” yace menene amaryarki tafiso ayanzu??? Rukayya tayi shiru alamun tana nazari 🤔sannan tace agwaluma da gwaiba
Yagirgiza kai yace bashiba”” tayi shiru dagabisani tace mangwaro gaudee yace todashi za ayimata maganin
Rukayya tace to Amman inaza asamu mangaro ayanzu tunda balokacinsa bane *hatsabibin boka* yace wannan aikin mune banakuba dazaran kunkai gida zakisamu mangwaron ajakarki saikibata tasha

Zamusamu mujiya dakuma makauniyar jaba da itah za ahada ayimata maganie yandakikasàn mujiya hakazata koma cikin al ummah ke mujiyamà saitafita gata dankuwa zatarika fitarda wàñi wari Wanda makotankuma saisungaji da doyin sannan zamubaki wata laya kijefa amasai
Dazaran kinyi wannan aikinki yagama

Aisha✍🏼

[5:17PM, 3/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 68

       By

Gentle Lady💃🏽

 Maganin wannan layar kuwa dazaran kishiyarki tabuda baki daniyar yin magana wa mijinki wani mugun doyi zaiji kamar ya surnana hancinsa acikin shadda”” rukayya batasan sanda tayi dariyaba cikin jindadi tace tomenene ladar aikinka ??? Batareda ya kalletaba yace yar uwarki tasani saita sanardake tajuya daniyar yiwa Asma u tambaya yadaka mata tsawa wacce tahargitsamata kwanya yace ba anan zakiyi maganaba kibari saikun bar nan kubacemun daganie
Atsawace yayi maganar asmau tace saikirufe idonki rukayya dajikinta yaketa faman rawa tayi saurin rufe idonta saikuma akasuresu saibakin dajin 
Ai rukayya. Tanabude idonta taganta bakin dajin tayanka dagudu daniyar komawa cikin dajin dantafirgita tuncikin fadar bokan saida Asma u tayi saurin riketa tajata dasauri sukabar wajen zuwa bakin hanya
Dakyar sukasamu motarda tamiyardasu gidan magajiya rukayya saida taganta gidan tasoma saukarda numfashi ko abinci batatsaya ciba takwanta barcin wahala yasureta su magajiya sai dariya suke Dan asmau tafadamata yanda sukayi da rukayya
Washe gari kasuwar garin sukaje tasiye dabbobin ta aikamasu dasu tacewa rukayya kinga yanda zakiyi duk lokacinda kikasake dawowa rukayya ta kwalalo ido tace wa???:oops: Badainiba aiduk Wanda kikagani lafirah kaishi akayi wlh nishegen tsorone dani ni inama tsammanin sanda yadakamun tsawar nan anyama basuma nayiba?? 🤔
Gaskiya inhar aikin nan yayi aini shikenan banida wani buri aduniya indai tabarmun gidan to mezai miyardani”” ?? Asmau tace akwai kuwa Kawata kinmanta akan kishiyarki kawai akayi aiki to idankuma yasake auro wata anan gabafa??? Rukayya tanisa tace kumafa hakane Amman anya zan iyah zuwanidaya wlh natsorata sosai bantaba shiga tashin hankali irin wannan ba”‘ Asma”u tace nafarkone aibazaki sake jinhakanba
Tace shikenan garin suka sake kwana washe gari sukadawo gida “” saida tahuta gidan asmau sannan tawuce gida da sallamarta Tashiga gidan tasamu fateema zaune tanashan iska da itah da muktar Dan gwaggo takarbi faruq ..
Tana ganinta tasaki fara a la Anty sannu dazuwa wlh yanzun nan nakezancenki araina inatunanin kokin taso”” kujerah taja tazauna tanacire hijab tace wlh kuwa tunsafe mukataho yazaman gidan
Fateema tace babuwani dadi gashi abban faruq anturashi wajen wani aiki jiya Amman inajin gobe zaidawo duk zaman gidan ya isheni gashi ban tambaya ba dasainashiga makota
Rukayya tace Karma kisoma bakigani nikaina baburuwana dashiga makota yanzufa duniyar nan mutum akekiyo ba dabba ba
 Fateema tace aibama zanfitaba”” rukayya tasaka hannu cikin Jakarta saikuwa ga mangwaro guda biyu tafitar tanacewa ga abunda kikafiso nasiyomaki ai fateema tanayin ido hudu damangwaro yawunta suka tsinke”” abunkada maiciki tanakarba batawankeba babu maganar bisimillah kawai takama gabtar mangwaro
Wani shu umin murmushi rukayya tasaki aranta tace taki takare fateema “” nantake tashanye dayan tadauko dayan tafasa sai muktar yaceshima sai tasammasa takilla tabashi kamar rukayya tahana saikuma takyale dankar fateema tadauka akwai wani abun
Ta sake gabtar mangwaro tana lunshe ido saboda dadi tace wai Anty ina kikasamu mangwaro alhalin yanzun balokacinsa bane???
Rukayya tadauko bokiti tace baridai inkara maki dankarki fadi tana dariya tace bafa santi nakeyiba kumama koda santin nayi aibalaifi kinkuwaji yanda mangwaron nan yakeda zaki??? 
Rukayya tace inazansani aikinsan nibanashan mangworo”” fateema tace hakane naman ta wlh hartashanye mangwaron bata ahamoba tacewa rukayya dakinsani deyawa kika siyomun
Tace ayya wlh nima akan hanya naganshi sauranshikawai danasan kina sonsa sosai nacewa driver yatsaya dakyarma nasamu yatsaya”” 
Fateema tace Allah sarki nagode Anty”” rukayya mikewa tayi tace baridai indan mike kafata kafin la asar barci nakeji wlh fateema tace tosaikin tashi tawuce dakinta tana murmushi
Washe gari tundasafe tajefa layar acikin masansu tazuba ruwa yabiruwa yafada cikin shaddar dadare koda Muhammad yadawo fateema tayi barci baiko kalli kofar dakintaba yashige bangarensa
Rukayya tana ganinsa tahau tsallen murna washegari dasafe tanadaki saiga fateema tashigo tana yakunar fuska tasamu guri tazauna tagaida itah ta amsa dasakin fuska
Saikuma tayi shiru rukayya tace yadai maman faruq??? Kamar tayi kuka tace Anty ashejiya abban faruq yadawo Amman baitasheniba
Rukayya tace ah watakil yalurah kinajin Da din barcinne”” tanisa Anty aibahakan yasababa sai idan yanzune zaisauya”” 
Rukayya tace toki kirashi mana”” nimadai jiyan banganshiba saidasafe danaga kaya afalo nasan yadawo
Fateema tace wlh nakirashi yafisau ashirin yaki dagawa bansan laifinda naimasaba”” rukayya tace kisake gwadawa dai haka fateema tayita gwadawa hartagaji takoma dakinta 
Yinin ranar takasa cin komai harwashe gari kwanadaya rak hartasoma ramewa”” tana tsaka datunani kawai saiga Muhammad yafado dakin dasauri takalleshi kamar zatayi kuka
Yanayinda taganshi yamatukar furgitata kafin tamike yahau dukanta batasan hawaba batasan saukaba tuntana yunkurawa daniyar tatashi tagudu hartakasa tayi kwance shikuma gabadaya bayagani yasa kafa yahalbeta aruwan cikinta wata mugunyar karar wahala tasaki take jini yasoma fita takafafunta Muhammad baikyaletaba saida yaga bata numfashi sannan yayarda bulalar yafitaa fuuuuu
Saida yafita rukayya tasadado taga aika aikarda yayi damakuwa tanaganin zuwansa tashige dakinta ganin tanamasa magana yawuceta fuuuu dariya tasheke da itah tace inakuma soyayyar take ayanzu???
Muktar yana gefe yana kuka yanakirah amma rukayya tadaka masa tsawa tace munafuki rufewa mutane baki” muktar yasake bare bakinsa yacigaba dawani kukan saida tasake katsamasa tsawa wacce tafirgitashi shima atake yaja zuciya numfashinsa yai sama
Ta sake bushewa da dariya sannan tafita tadibo ruwa ta yayyafamusu kusan taresuka far fado muktar yashige jikin fateema yana kuka
Fateema bayan tagama nazarin abunda yafaru da itah Wanda take gani tamkar mafarki”” tasake fashewa da kuka”” mai tsuma zuciya
Takalli rukayya tace Anty me yake shirin faruwa danine haka?? menaiwa Muhammad yayimun wannan dukan kamardai Wanda bashida imani?? 
Rukayya tace waikina nufin shine yadakeki?? Toyanibanji shigowarsaba fateema tace wlh shine Anty
Rukayya tace kekuwa laifin mekikai masa??? Tace wanne irin laifi Anty wlh banyimasa komaiba”” rukayya tace to Allah ya kyauta tawuce abunta fateema tabita da kallon mamaki kamar bataga halinda take cikiba “” 
Rukayya tanafita takirah asmau tanadauka tace yee Kawata aikifa yanakyau”” asmau tace banafada makiba
Tace ainagani yau Muhammad yalakadawa Yar iska shegen duka inajifa kamar tayima bari”” asmau tace toyanzu tana ina??? Rukayya tamere baki tace tanadakinta kwance inda yabarta
Asma u tace yazakiyi haka aizatayi saurin zarginki banafadamaki dakissa akehadawaba yanzu kidauketa kuje asibiti dagacen kicema ayimata wankin Mara idan akwai sauran Matsiyacin yayo waje”” 
Rukayya tace toshikenan dasauri takoma dakin tasamu fateema tasake suma” fita tayi dasauri tasamu Dan tax dataimakon wata makociyarsu aka kai fateema asivibiti
Likita yatambayi menene yayi sanadin zubewar cikin??? Rukayya tace aifaduwa tayi Amman ayimata wankin Mara karyazama ciwo ajikinta”” alokacin har anjona mata Karin ruwa 
Suna nan harkusan la asar lokacin fateema tafarfado Amman bata bude idontaba”” tanata tunanin wannan lamarin””” kwananta uku asiviti Muhammad bailekoba gashi likitoci sunbar zuwa gurinda take kaibartasuma har wadanda sukejinya daki daya duk sun sauya daki
Aladole tasallami kanta tafito duk Dan adaidaitan da tatara baya tsayawa gashi jikinta baiyi kwariba tana tafiya tana tsayawa tana hutawa hartakai gida
Gashi tafiyace mainisa ajigace takarasa gidan tashige dakinta tafadi kwance tafasheda kuka muktar ne taji yadafata tadago takalleshi duk yayi damau damau cikin kashi tasake fashewa da kuka maitsuma zuciya saida tayi mai isarta tahakurah dankanta
Dakyar tatashi tashiga kichin dinta tasulala taliya sukaci bayan tawankemasa jikinsa haryanzu bataji duriyar rukayyabà Ashe tana makota tabar muktar shikadai cikin gidan
Wasa wasa fateema abusai gabayake batajin sanyi wajenkowa saiwajen rukayya danyanzu saitakwashe watadaya batasaka Muhammad a idontaba
Duk ranarda abun yacizoshi zaizo yayimata shegen duka gabada ya yan uwansama sundauke kafarsu daga gidan
Gashi tanada zurfin ciki ballantana takirah tasanarda su Anty hasana halinda takeciki saidai ciwo yayita cinta ahankali”” 

Kwanaki sunata tafiya sati haka watanni haka shekaru haka fateema ta lalace tayi bakiii kirin wacce takefara”” alokacin muktar shekaransa shida aduniya yayi wayo sosai hakazalika shine kawai kedan kwantarwà fateema dahankali
Watarana dadare tanakwance zafii yadameta tatashi tawatsa ruwa tadauro alwala”tanashirin kwanciya saiga Muhammad yafado kamar dagasama
Tatsorata daganinsa dantasan babu abunda zaikawoshi dakinta idandai badukanta zaiyiba

Aisha✍🏼

[6:43PM, 3/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 69

       By

Gentle Lady💃🏽

Tasoma jadabaya”” tanabashi hakuri hannunsa yadorah akan labbansa yace shitt alamar tayimasa shiru takekuwa tarufe bakinta hantar cikinta tana kaduwa
Kusa da itah yakarasa yajaye zaninda yake jikinta yajata akan gado yasoma wasada itah tamkar bayacikin hayyacinsa”” Sam yaubayajin haushi dakuma warinta kodan yana cikin matsananciyar bukatane oho
Fateema Sam tamanta awace duniyar suke duk abunda Muhammad yayi mata tamantashi awan nan daren ashedai darabon khadija atsakaninsu domin rabon khadija ne yatasheshi abarci haka kurum yaji yana bukatar kwanciya damace 
Wajen rukayya yasoma zuwa saiyasamu tana al ada dayake wani baya haihuwar danwani harzai koma daki yaji bazai iyaba kawai yatunkari dakin fateema saigashi baiji komaiba harsaida yagama biyan bukatarsa 
Aizunbur yamike kamar Wanda yayi mantuwa kawai yakalleta itama shitake kallo tana murmushi tsaki yaja yawuce abunshi abun ma saiyabata tsoro anya dadyn faruq kansa daya kuwa mikewa tayi ta tsarkake kanta tadawo takwanta
Tundaga ranar batasake sakashi acikin idontaba har aka kwashe wata uku talurah lallai cikine da itah”” gashi batajin dadi saiyawan ciwon ciki yaudai takudurah aranta zata sameshi tànemi izinin zuwa asiviti danciwon cikin yana matsanta mata”” 
Tana dakon jiranshi harbarci yadan figeta cen tafarka dasauri tasuri hijab dinta tasaka tafita zuwa dakinsa taturah da sallama saikuwa tasamu dakin bude tayi hamdala takutsa kai tareda sallama
Suna zaune dashi da rukayya sunacin naman kaji rukayya saizuba masa shagwaba takeyi shikuma kamar zaimaida itah ciki saboda soyayya”” 
Bakisake fateema take kallonsu Dan sallamarda tayima abakinta tamakale ganin yanda suke soyewa. Amman kullum rukayya cemata takeyi itakanta muhammad yadaina kwana da itah yadaina sake mata fuska “” wasu hawaye masu zafine suka sauko akan fuskarta
Muryar Muhammad taji yadaka mata tsawa kewacce irin jakace zaki shigomun daki cikin irin wannan yanayin kuma kiyimun tsaye akai
Fateema tagoge hawayenta taduka kanta nakasa tace kayi hakuri nakatsemaku jindadinku wlh banda lafiyane kwana biyu shine nakeso intambayeka gobe zanje inga likita
Yace bazakiba tashi kibacemun daganie”” takalleshi cikin mamaki tace Muhammad bafa wasa nake yiba katausayamun mana damezanji dawulakancin da kakemun koda ciwonda ke jikina??? 
Afusace yamike yace watoma ninakemaki wulakanci??? Lallai yarinyar nan kinsamu damar rainani dankawai inasake maki fuska tokarshen walakanci kije gidanku nasakeki saki biyu kimaza maza kifitarmun gida kafin nakirga goma
Kwatakwata neman hawayenta tayi tarasa saitayi murmushin takaici tace nagode Muhammad balaifinka bane Nice dalaifi da nanace saina aureka
Babuyanda Yayana baiyiba Amman nace saikai Amman kasani babu inda zanje sainayi idda

Kafinma tarufe bakinta yace agidan ubanwa zakiyi iddar 
Tamike ahasale tace agidan uban Yayana kuma babu inda zanje sainayi idda”” yace wlh bazakiyi idda agidanaba ke kijema na iyarda sauran sakin sai inga inda zakiyi iddar tunda ba uwarkice tabani gidan ba
Fateema tace wlh karkasake zagarmun uwa yace idankuma nasakefa “” tace sai inrama ai uwarka bafin uwata tayiba kafin tarufe baki yadaga hannu zaimareta
Tarike hannun tace Karka sake wlh barganin kadakeni ada nakyaleka dajarar soyayyace dakuma aurenka dayake kaina yanzu Kuma babu kodaya danhaka bazanji takaicin ramawaba
Ta sake masa hannu tacije lebonta nakasa zanbarmaka gidanka Amman kasani bazantaba yafemakaba bantaba cutar kowaba nikuma duk Wanda yacutardani bazan yafeshiba wannan alkawarine tanakaiwa nan tawuce abunta Sam kuka yabacewa idonta
Zatafita yace dawo dawo ko kallonsa batayiba yafada dakinta yadauko muktar yana barcinsa yajawoshi kamar Wanda yadauko kayan wankii

Tana kiciniyar bude kofa yace wazakibarwà wannan shegen dannaki tajuyo afusace tace shegen ubansa aibadashi nazoba danhaka babu inda zanidashi inkaga dama kabarshi yamutu tafita dasauri tabanko kofa
Tanafita yajefo muktar waje yarufe kofar gidansa kukanda yakwantsane yasakata waigowa dagudu tadawo tarun gumeshi tahau rarrashinsa gabadaya unguwar tayi tsit kukan karnuka kawai kakeji yanatashi
Tashi tayi tagoye muktar abayanta dukda babu zanie tasoma tafita gabadaya tsoro yafita ranta tayi tafiya mainisa hartabar unguwarsu sosai haryanzu kowa batahadu dashiba “” muktar haryakoma barciii gashi tagaji dole tasamu wani wuri tarabe tacire dankwalin kwanta tashinfida takwantardà muktar tazauna saiyanzu tasamu damar yinkuka
Tasoma kuka maidan sautiii tsayin min tuna kamar ashirin taga anyadomata fitila maihaske hannu tasaka takare fuskarta tacigaba da kukanta
Ahankali mai fitilar yatako kusa da inda take yakashe fitilar yadan rage tsawo yana dubanta yace baiwar Allah mutum ko aljan??? 
Batareda takalleshiba tace inaruwanka karabudani”” kaje kayi abunda yake gabanka”” yanisa naji Amman amatsayinki Na mace mai rauni baidace inganki anan ba kuma inkyaleki nimafa inada Yaya kamarki bazanso nima Yayana susamu Kansu a irin wannan yanayinba inaso suma ataimakesu
Tace gawanda kebukatar taimako ko??? Toni bana bukatar taimakonka”” kabarni Dan Allah tasake fashewa da kuka””

Mutumen ya murmusa yace shikenan tunda bakyaso Amman bazan bar yaron nan wajen nan ba kinga gidana cen dasafe saikishiga maidakina tabakishi yayi maganar kawai yadauki muktar 
Tabishi da kallo komotsi batayiba bayan tafiyar sada jimawa saigashi taredawa ta mata alamu sun nuna matarsace yace kinganta nan yayinuni da Fateema
Matar takaraso wajenta tace haba baiwar Allah kitaso mana kinkosan karfenawa yanzu??? Itakanta matar muryanta ta maibarcice dagaji mijinne yatasheta babu musu kuwa tamike tabi matar hargidan dakinda suka kwantarda muktar nan suka nunamata sukaimata saida safe
Itakuwa babu maganar barci a idonta harsafe bayan tayi sallah tana lazumie saiga matar tashigo dakayan kari tagaida itah sannan ta ajemata tace kisamu kici malam zaiyi magana dake tace to
Duk datasan bazata iyah cin komaiba”” tatashi muktar yayi alwala yayi sallah sannan tabashi abun kari yaci bayan haske yagama mamaye gari rana takunno kai saiga matar tasake dawowa wajenta tace kitaso yana kirah bamusu tamike tabi bayan matar”” 
Harwani daki tasameshi zaune saman buzunsa gatarin littafai nan agabansa dakuma allo da Qur ani tasamu gefe tazauna kanta yanakasa tagaidashi
Ya amsa cikin sakin fuska duk kunya takama fateema data tuno yanda sukaidashi jiyan yakatsemata shirunta yace yarinya hakika nalurah kamar kinacikin damuwa
Tunjiya la akarida yanda naganki dayaro acikin dare kuma cikin wannan muguwar shiyar'” inaso kisanardani abunda yafito dake daga gida
Shiru tayi nayan dakiku sannan tasanar dashi””komai yace wa iyazubillah Allah yakaremu dasharrin shaidan yata wannan mugun asirine akaimaki domin arabaki da mijinki
Gaban fateema yabada rasss dasauriii tadago kanta idanuwanta sunakawo kwalla tace asiri kuma baba??? Tomena tarewa wani dahar yakeso yashiga tsakanina da farincikina???? 
Yace yata abubuwa dayawa alabarinki kincemun matarsa bata taba haihuwaba??? Fateema tagyada kai yanisa kekuma gashi kinyi harbiyu ba mamaki itace dawan nan aikin
Fateema tayi shiru tana nazari ta tuna jiya dadare datasamesu dakinsa duk abunda akeyi rukayya kotado kanta batayiba saicin nama takeyi abuntaa fateema tashare hawaye tace bashakka idankuma hakane Anty tacutarda rayuwata tafashe dakuka
Saida matar malamin tasoma rarrashinta tanabata bakii

Aisha✍🏼

[10:46PM, 3/5/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 70

       By

Gentle Lady💃🏽

Yanisa yana kallonta yace kikwantarda hankalinki yata nine nan zankwatomaki yancinki”” tayi saurin kallonsa tace taya baba aikuma aikingama aiyagama”” 

Yace ninasan yanda zanyi zanmiyar mata da abunda taimaki”” inhar kin amince dahakan”??? Taja majina tana kallonsa tace idan har nayarda amiyar mata da abunda tamun menene banbancina da itah??? 
Tanisa ninabarta da Wanda yayi rana dakuma faduwarta koda nayarda amayarmata tunda babu aure tsakanina da Muhammad aikin banzane nikawai nabarta da mahaliccinta indai duniyace aigata ga duniyar niyauma zanwuce garinmu danba kinciki zai iyah kasheni anan idan inatunoshi
Malamin yayi murmushi yace hakane yata dama nayi tunanin hakan Amman tundakince kinbarta da Allah bariga Allah yafi” yagyara zama Amman kitsaya kikwana biyu akwai taimakonda zanbaki kafin kitafi””
Tashare hawaye tace kayi hakuri baba niyau gida zantafi”” banason sake kwana garidaya dashi malamin yace dolefa kiyi hakuri dantafiya bata samekiba. Kinkuwasan abunda ketare dake barta mijinki ko yan uwanki idan kikaje babuwanda zaikalleki dankuwa abunda yake ajikinki kokinfita babu mai motarda zaidauke ki kinkosan bazakije gida akafaba 
Fateema tayi shiru kamar mai tunanin wani Abu saikuma tace shikenan zata zauna”” tundaga ranar malamin yasomayimata rubutu tanasha dawani garin maganie”” dayayiwa hadi da habbatus sauda da turaren miski dawadansu kalolin turare yahada dazuma farar saka akadama daruwan zanzan kullum dasafe saisunsha chokali daya
Da itah da mukhar harnatsawon sati daya”” bayan sati daya saigashi tasoma wani irin a mai baki kirin da gudajin mangwaro aciki hakashima muktar ammanshi bayawa sosai danshi baici dayawaba yanayin cizawa daya yaji tsami saiya Yar
Abunda tagani yanzu shine yasake tabbatarmata da gaskiyar lamarin”” saida tasake kwana biyu malamin yayimata kudin motar saida zata tafi tarambayesu sunansu
Matar tace sunanta khadija mijinta kuma ibraheem ta sake yimasu godiya harwajen shiga mota yasa aka Kaita tundasuka shiga motar tashiga duniyar tunani harsuka kawo kano
Tahau Dan adaidaita zuwa unguwarsu koda tashigo duk yawanci suna masallaci wajen sallar magrib dasallama tashiga gidan tasamu matar Yaya garba tana kada miya
Ta amsa sallamarta tataso taga kowacece tanaganinta tace yarbaba !! Kece da magribar nan lafiyadai??? Saikawai fateema tafashe dakuka tafada jikinta
Tace yau nabani nidiyar mutum biyu jikar mutun hudu menene kuma yafaru yarbaba”” ??? Fateema batace komaiba taci gaba dakukanta anahaka garba yashigo dasallama yayi tsaye yana kallonsu yace kukan wanakeji kamar yarbaba??? 
Bilkisu tace wlh itace malam niduk ta tayarmun dahankali “” jinta ambaci sunan yarbaba garba yazoda sauri shima yahau tambayarta jikinsa harrawa yakeyi danyana tsoron ace abunda mahaifiyarsa tayiwa mahaifiyar fateema shine aka sake maimaitawa
Fateema yanda taga hankalinsu yatashi saijikinta yayi sanyi anan take sanardasu aurenta yamutu sukai tambayar duniya tafadamusu meyafaru haryasaketa tace laifi tayimasa takisanar dasu komai harsuka gaji sukasamata ido
Dakin ta tashare takoma ciki washe gari su hasana sukazo suma babuyanda basuyiba Amman bandakuka datakemasu idan sun matsamata da tambaya dole suka kyaleta garba yaso yaje yola din
Fateema tace karyaje tunda saki uku yamata menene amfanin zuwan tunda koyahakurah bakomawa zatayiba 
Aranta tace aikoda akwai sauran igiyar aurena dashi bazan komaba ballantana komai yakwabe yace shikenan 
Ahakan tacigaba darainon cikinta haryafito batafirah dakowa inba muktar ba”” gashi ciwo yanacinta gayawan tunani”” cikinta yana shiga wata tara tasanarda matar garba in Allah yasauketa lafiya intahaifi mace khadija takeso asamata idankuma namijine ibraheem
Bilkisu tace banda abunki kibari saikinsauka mana saikifadawa yayanku”” murmushi tayi Wanda rabonta dayin irinsa andade tace inaso komenene nahaifa asakashi islamiyya inaso yayi karatun sosai kullum maganarta kenan
Ranar wata juma” a cikin dare tatashi da nakuda muktar ne yasheka yana bugawa su balkisu kofa dama bawani barci mainauyi takeyiba dasauri ta mike tafito waje
Dakin tashiga dasauri tarufo kofa fateema tayi matukar galabaita tafita hayyacinta saikusan asuba tahaihu
Kojuyowa batayi taga abunda tahaifaba raiyayi halinsa bilkisu taduka tadauki Yar tayankemata cibi tawanketa tagyara wajen garba yanakofa tsaye da muktar yana kuka
Saifita take tana dawowa tadaicemasu ansauka ansamu mace Amman batasanardasu. Yarbaba tarasuba saida tagyara wajen tashirya jaririyar takuramato ido yarinya tamkar uwarta babu abunda yarabasu 

Hawayen tausayinta ne suka sauko akan fuskarta Allah Sarki kekuma taki jarabawar kenan fita tayi tabasu yarinyar takoma takimtsa fateema
Fuskarta tayi haske fayau tamkar tana murmushi kamar kayi magana ta amsa rayuwa kenan “” rayuwa bawani abubace dazaran anzaremaka rayuwa takomai takare
Duk kwanbonka komai kudinka saifa kadandani mutuwa menene abun dagawar ??? Dazaran anzaremaka rai yanda kasan mutum mutumi haka zaka koma shikenan taka kuma takare babu sauran jindadi masu bururruka aduniya Allah yasa mucika da imani Ameen
Tadade dakin sannan tafito garba yace yamai gejon tana lafiyadai ko ??? Tagyada masa kai kawai alokacin hawayenda take boyewa suka karasa sauko wa takauce idonta danta goge Amman haryagani dasauri yashiga dakin tana kwance inda tahaihu ahankali yataka zuwa inda take yaduka yashafo fuskarta yace Allah Akbar Allah yasa kinyi kyakkyawar tafiya yatofa mata addua sannan yamike alokacin ansoma Kiran asuba
Yakarbi yarinyar yayimata huduba da sunanda mahaifiyarta tace yamikawa bilkisu yakalli muktar yace muje kayi alwala muwuce masallaci bamusu yawuce yayi alwala shima yayi sukatafi masallaci 
Bayan an idar yasanarda liman akayi sanarwa za ayi za na izarta da karfe goma muktar baisan meyake faruwaba saida yaga mutane sunsoma cika gidan sannan hankalinsa yatashi yatambayi garba meyake faruwa ne
Bawani boye boye yasanarda shi yayi tsammanin zaiyi kuka saiyaji kawai yace Allah yajikanta yamatukar bashi mamaki gashidai karamin yaro taredashi akai mata sallah har aka Kaita makwancinta
Tundaga ranar rainon khadija yadawo hannun muktar dayake matar garba yaranta biyu duk mazane batasake haihuwaba daga garesu madara akarika bawa khadija 
Allah yarayata tuntana karama she gen wayo ne da itah makaran tarsu daya da muktar kowakuma yadakarmasa Kanwa kowaye saiya rama mata bayaso yaga kukanta kokadan
Shikeyimata wanka da kwalliya akanta yakoyi kalaba danbaya kaita wajen kitso tunda yakaita sodaya yace masu kitson mugayene kwarai suke kitsawa danmugunta “” shikuma ahankali yakemata anayi anashan minti kuma bata kuka
Tana primary 2 yagama makarantar yashiga babbar makaranta soyayya maikarfice atsakaninsu shine uwarta shine ubanta ko yayan inna balki suka daketa bayajin kunyar kowa zairama mata
Sannu kan hankali tanazuwa boko tanazuwa islamiyya Amman tafi bada karfi islamiyya datadawo boko tawuce islamiyya sai magrib ake tashinsu idankuma ranarda ba bokone karfe bakwai nasafe sukezuwa sai magrib
Tun tana yarshekara biyar takai hizif hudu kuma dazaran anyimata karatu nantake take daukesa akanta lokutta dai sunata tafiya khadija tanasake girma”” tanagama primary shikuma yanashiga ss 3 ” tashiga itakuma jss 1 alokacin tanada shekara goma shabiyu”” yana gama secondary skull yashiga bayero university”” alokacin khadija takusan sauka alokacinne suka hadu da labila tadawo kano dazama saita shiga islamiyyar su waje daya suke zama Allah yahada soyayyar su waje daya saigashi kuma ashema makotane soyayarsu tayi nisa sosai kullum zakagansu tare alokacin muktar bagida yake kwanaba cen makaranta yake kwana idankuma bakaratu yakanshiga gari yayi aikin karfi yayiwa khadijar sa siyayya “” tuni tabashi labarin sahibarta dasuka hadu duk yakirah waya maganarta kenan sahibar ta”” su gwaggo hasana da Husaina duk sun hayayyafà kowace yaranta biyar duk sungirma Amman muktar shine babba sai yayan uncle garba sulaiman da dahiru suma suna bayero
Tana ss1 muktar yatafi kasar waje waje karatu dansosai yanaso yayi ilimi yazama maikudi bayason kanwarsa tayi kuka anan gaba Amman ranarda zaitafiii tasha kuka dakyar tabarshi yatafi
Tundayaje baidawoba saida yakwashe shekara biyu anyimasu walimar sauka dukda khadija tadade dasauka ba ayi walimarba akace sai ansamu kamar mutum dari duk dahaka sai aka kaita ajin hadda alokacin yazo yaga khadijarsa tasake girma kyanta yasake fitowa kamanninsu da mahaifiyarta yasake bayyana tana ss 2 lokacin suna shirin shiga ss 3 bangaren karatun islamiyya kuma hartakusa hardace alkur ani 
Muktar baramin dadi yajiba yanda kanwarsa tazama hafiza suna zaune tana rubuta wani hadisi acikin littafinta muktar yakurah mata ido yanata faman murmushi
Ajikinta taji kamar ana kallonta tadago saisukai ido hudu itama murmushin tasakar masa tace Yayana meyafaru??? Murmushin yasakeyi yace idan ina kallonki nakan tunoda mahaifiyarmu
Kamanninku daya saidai kawai kindarata haske kadan dakuma wushiryar da kikeda itah bayan wannan bakuda banbanci hatta Dan abun nan naki dimpull tanadashi akowanne saitin kumatunta
Yanisa please Kanwata karkisa soyyya acikin rayuwarki kamar yanda nadade inasanardake mom tace tanaso kiyi karatun islamiyayya sosai yanisa banason kibiyewa abokai dannasan yanzu a skull kananun yarama zakagansu suna soyayya
Hawayene suka sauko akan fuskar khadija take muktar yarude yataso daga kan kujerar yaduka gabanta habarta yadago yace kuka farincikina 
Maganatane tabata maki rai ¿kaita girgiza tace bahaka bane Yayana natunoda mom ne inama nima nayi rayuwa da itah inji diminta kamaryanda kowa yakejin dimin mahaifiyarsa
Kuka tafashe dashi maikarfi muktar baisan sanda shima yafashe dakukanba labila shigowarta Kenan tanufo dakin tajisu suna kuka duk dabaya yabata hakanne baisa taga fuskarsaba saida sukai mai isarsu sannan muktar yayi karfin halin soma lallashinta ganin zaimike labila tayi saurin juyawa tafita batareda sungantaba
Kwanansa biyu yakoma baisake dawowaba sai lokacinda khadija akaimasu walimar haddace al Qur ani 
Dalilinda yasaka labila tacewa Usman sunan mahaifiyarta akasamata dan kawai taji yangidan suna cemata sapna wannan sunan kuma muktar ne yalakaba matashi yanajin dadin sunan idan khadija tace saboda mene bayakiran sunanta saiyace ai sunan umma ne to itama hakan tasanarda labila shine tarike
A Takaicedai wannan shine ainahin tarihin rayuwarta dakuma tushenta babukuma Wanda yasan wuyarda maman khadija tasha sai muktar danbaimanta komaiba shiyasa yakeganin anyama zaiyarda yabawa wani khadija???
*KYAWON TAFIYA DAWOWA*

Aisha✍🏼

[7:33AM, 3/6/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 71

       By

Gentle Lady💃🏽

Wayar taketa kallo tana murmushi”” saiga kirah yasoma shigowa cikin kira ar sudes tuni khadija talunshe idonta saboda jindadin karatun tanabinsa ahankali harkiran yakatse 
akasake kirah saiyanzu tabude idonta tadauko wayar saitaga ansa hubbina takwalalo ido tace hubbina kuma batasan harta dauki wayarba tanacewa hubbina sai asaitin kunnensa saitaji yace Na am
Wata irin kunya takamata kamar tanitse cikin kasa muryarsa taji yace khadija menaji kinkirani dashi yanzu???
 Duk tabi ta daburce tace dad sorry wlh banice nasakashi awayarba sahibace tasaka namanta sainakirah Ashe harnadauka kaji dakyar takeyin naganar kamar wacce akasaka dole
Murmushi yadanyi maisauti yace nikuwa naji dadi danaji kinkirani hakan”” hannu tasaka tarufe fuakarta tace kayi hakuri yace aibalaifi kikayiba khadija
Tace harka kaine saikuma tarufe bakinta da alamu batasan sanda maganar tafitoba”” yace ah konadawo ne bakigaji da ganinaba??? Tace sai anjima dad
Dariya yayi maidan sautiii yace kunya kikejine??? Kamar yana ganinta tanoke fuska tareda daga kanta yace isowata kenan harzan soma aiki nacebari nafarajin muryarki”” murmushi tayi tace tokayi aikinka lafiya dad “mungode batajirah mezaiceba taka she wayar”” yabi wayar dakallo yayi murmushi 
Khadija sunagama wayar wani farincikine yalullubeta marar misaltuwa tadade tanajin soyyarsa cikin ranta Allah yakaddara shine mijinta
Kullum Usman saiyakirah khadija Amman baitaba kiranta idan haryana kusa da lubabatu Sam batasan meyake faruwaba tsayin sati daya sannan yakoma kano yasanarda malam garba khadija ta amince..
Yace shikenan yabashi kwana biyu zaikirah muktar yasanardashi komai yace saiya fadamashi”” hakan kuwa akayi bayan kwana biyu yakirah muktar.
Tana fara ringing yadauka tareda sallama malam garba ya amsa muktar yace kawu inawuni yace lafiya kalau ya karatu
Muktar yace karatu Alhandulillah”” yace to Allah yabada sa a yabada abunda akaje nema yace ameeen muktar yace kawu ina sapna??? Yace kaima kasan tana islamiyya ni nadawo gidane indan watsaruwa saboda zafie
Muktar yace kagaidamun inna ” yace tana amsawa” daganan saikuma shiru yabiyo baya muktar takawarda shi run yace kawu ko akwai maganane??? 
Yanisa ah kam muktar akwai magana mai mahimmanci akan khadija shine dalilinda yasakama nakiraka”” jinya ambaci khadija yasaka yasaka muktar yabar abunda yakeyi yatattara hankalinsa duka yana saurarenshi
Yace inajinka Allah yasadai lafiya yace qalaune insha Allah yayidan jinkiri sannan yace watarana ina kasuwa saiga mahaifin Kawar khadija labila kaganeta aiko??? 
Cikin kosawa yajimeyafaru yace ah nagane” yacigaba yazone akan batun khadijar daganan yakwashe abunda sukai dashi yafadamsa haryanda sukai da khadija tace ta amince
Yana rufe bakinsa muktar yamike tsaye yace ai wannan zancen banzane kawu nawa khadija take dahartasan wata Abu wai soyayya bazata aureshiba!!! 
Kawu yace dakata muktar baikamata kahana yarinyar nan cika alkawarinda tadaukarwa kawartaba”” tace daina maganar wani alkwari kawu kawai kacemasa auren nan bazai yiyuba yayanta yace bayaso
Idankuma bazaku iyah sanardashiba nimai iyah fadamasane haba kwata kwata nawa khadijar take 18years fa” Kuma tarasa wazataso sai Wanda yakeda mata !! Never
Malam garba yanisa yace tonidai bansan yazanyi makaba Amman gaskiya zak asani jinkunyar bawan Allah nan tundaga kano yataso
Muktar yace Allah yasa daga saudiya yazo kawu ban yarda Kanwata ta auri mai mataba!! Malam yace to Allah yakyauta sai anjima
Yakashe wayar yanakallon innah yace Dama hakan nayiwagudu shiyasa nacemasa yabari saina sanarda yayanta
Kinji yanda yaceko??? Innah tace lallashinsa zakayi ai saiyayi hakuri Amman magana tagaskiya yarinyar nan tanasonsa “” ninalurah dahakan tunkafin yace yanasonta
Malam yayi shiru yana nazari cenyanisa yace to tundashi yakeda kanwarsa yace bayaso ahakurah mana nibanaso inyi karambani inajin tsoron maimaita tarihi duk da banada laifi
Innah tace to Allah yazaba mana abunda yafi zama aikhairi malam ya amsa da Ameen bangaren muktar kuwa sunagama wayar yakasa zama jikinsa harwani ciccirah yakeyi anyama zai iyah sake kwana a kasar nan karfa yanacen kawu yayiwa khadija aure
Kuma wai baban labila mai mata ai bazaitaba yiyuwaba “” dasauri yasoma hada kayanshi sai filin jirgi 
Koda jirginsu yasauka takwas nadare masallaci yafara zuwa yafara ramakon salloli sannan yatari Dan adaidaita zuwa gida
Suna tsakar gida sunacin abinci dayake yanayin zafine saman babbar tabar marnan suke saidai sukaji sallamar sa dagasama
Malam garba yadago da mamaki yana kallonsa lallai abun yayi tsamari suka amsa masa sallama yaduka yagaidasu baiko kalli gunda khadija takeba yatashi yakoma bangaren dakunansu”” yashige dakinsa 
Tuni murnar dakuma farincikin fuskarta yagushe takalli innah kamar zatayi kuka mikewa tayi zuwa dakin dasauri da sallama tashiga
Yana kwance saman gado yakurawa silin dakin ido ahankali tataka indayake taduka muryanta tana rawa tace yaya halan bakaganniba???
Atsawace yatashi zaune yace naganki sapna mekikeso inyimaki???? Take hawaye suka jikamata fuska tace wani laifin nayimaka Yayana??? 
Yadallah mata harara yace kebakisan ma abunda kikaiba tunyaushe nake Jan kunnenki akan karkisake kiyi soyayya??
Asheni bansaniba ihunake bayan hari” nawakike khadija dahar zakice waikinason wani kuma bama saurayiba maimata??? Kinsan sarai natsani mai mata bazantaba bari ki auri mai mataba kodakuwa mazan duniya sunkare

Tanaduke hawaye sunabin kumatunta batacemasa komaiba haryakai karshe cikin sanyin murya tace Yayana baban sahiba tane fa baikamata kajerah shi cikin sahun marasa nagartar mazajeba
Yadaga mata hannu rufemun baki nalurah kedin bakida hankali tokisani gobe gobe dake zankoma sainaga karyar rashin kunya kuma shima zankirashi inji dalilinsa duk matan dasuke kasarnan yarasa wazai ce yanaso ya aurah saike zatayi magana yace kiyimun shiru tashi kibar nan banason ganinki
Cikin muryar kuka tace nidin ya muktar??? Cikin tsawa yace kifita nace tsawarda yayimata cikin wata murya wacce itah kanta batasanshi da itaba
Dasauri tamike tarufe bakinta saboda kuka dagudu tafita tafada dakinta saman gado takwanta tasoma kuka maicinrai meyasa nabata maka rai meyasa??? Danasan hakan zaikona makarai bazantaba bari son dad yashiga zuciyataba
Su inna sai kallo kallo suke sukalli kofa sukalli juna”” sunsan koda sunshiga dakin muktar bazaitaba saurarensuba”” Dan idan yahau dokin zuciya bamai saukardashi

Aisha✍🏼

[8:47AM, 3/6/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 72

      By

Gentle Lady💃🏽

Tundaga muktar har khadija babu Wanda yaruntsa harsafe khadija takwana kuka kafin safe wani zazzafan zazzabine yakamata jikinta yagashe kamar wuta
Sallar asuba kanta dakyar tayi gashi jiya bataci abinciba”” dasafe inna takawo mata abun karinta tatasheta tace takoshi
Babuyanda inna batayiba Amman takici dataga zatadameta tace zataci inna tanafita tasake gyara kwanciya”” tana nan kwance har azahar muktar baishigo dakinba
Inna tasake kawo abincin rana tasamu nasafen bataciba”” ta ajemata tafita dakin muktar tayi saita sameshi zaifito kenan yana ganinta yadansaki ransa yagaida itah
Ta amsa tace idan zaka iyah rarrashin sarkin zuciyar cen kaje wlh yaukoruwa batasha ba rabonta da abinci tunjiya dasafe babu yanda banyi da itah dasafe ba tanuna masa kaga karinta nasafe yanzu danakai narana nadaukoshi
Yayi shiru sannan yace shikenan yajuya zuwa dakinta koda yaturah kofa idonta rufe yake yataka harbakin gadon yazauna yakuramata ido
Yasan tasan shine dangashinan idanuwanta sunsoma zubarda kwalla duk da arufe suke” sunanta yakirah bata amsaba”” baidamuba yace kitashi kici abinci
Nandinma banza taimasa yaturah hannunsa daniyar yatasarda itah mugun zafinda yaji shiyasa yacire hannunsa dasauri batareda yayi niyaba
Cikin tashin hankali yace khadija bakida lafiya Daman??? Meyasa baki sanardaniba duk arude yake maganar dasauri yafita yacewa innah kishirya ta yanzu zandawo da doctor yadubata yafita dasauri yana dauko waya cikin aljihunsa
Abokinsa Abubakar yakirah yasanardashi yana kano yanzu haka yanason ganinsa “” yace toyasameshi gida danyanzu Hutu yake yace toganinan tafe
Yanagama wayar yatari Dan adaidaita zuwa gidan sa bayan yakirasa yace yakaraso saiyafito motarsa sukashiga zuwa gidan
Yashiga yasanarda innah zaishigoda doctor tace to saida yashiga yasamu khadija kwance yagirgiza kansa sannan yafita”””
Yashigoda Abubakar din yagaida innah sanan sukashiga dakin “” yataba jikinta dazafi sosai sannan ya aunata”” haryagama abunda yakeyi muktar yana kallonsa
Yatashi tsaye yana kallon muktar yace me akaimata halan??? Muktar yace mefa akaimata doctor mekedamunta??? Yanisa yawan tunanine yahaifar mata da damuwa gakuma kirjinta yanazafii 
Tunyaushe rabonta da abinci?? Jiki asanyaye yace jiya” yace mujeto asiyomata magani dole aimata allurar barci domin tasamu barci ko damuwar zataragu
Yace tomuje yayi maganar yana kallon khadijar taresukaje dashi akasiyo maganin da allurar yabiya sukaje inda masu fura damun injin yasiyamata suka wuce gida
Dakyar yasamu tasha furar sanann akaimata allurah takwanta yanunamasa yanda zatasha maganin idan tafarka yayimasa godiya yarakashi bakin motarsa sundade suna firah sannan yatafi hankalin muktar duk yana wajen khadija
Kodayakoma yasamu tayi barci kusa da itah yazauna yabuga tagumie yana kallonta”” wasu hawayene suka saukomasa yasadan yatsansa yataresu
Yana nan har akayi la asar yatafi masallaci yadawo yazauna ba itah tafarkaba saigoshin magrib yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah taci abinci tasha maganie takoma takwanta
Sallamar labila sukajiyo tsakar gidan tagaida innah sannan tafada dakin tanakiran sahib bata rufe bakiba sukai ido hudu da muktar yasake tsuke fuskar nan
Itama saita dauke kanta tace inawuni bai amsaba itama batadamuba saman gadon tahau tace meyasameki sahiba???
Khadija saman kafarta tahau saitafashe dakuka nantake labila tafara kukan tace me akaimaki sahiba??? dan Allah kiyi shiru
Muktar yanazaune yanakallon ikon Allah”” innace taji kukan yayi yawa tashigo tozakufara sana ar takuba kuyiwa Allah kuyishiru 
Kojinta basuyiba itama tsaye tayi tasaki baki kamardai yanda muktar yayi tsayin mintuna goma khadija tayi shiru saikuma takoma rarrashin labila sahiba kiyi shiru kinji kar zazzabi yakamaki
Saida tagama rarrashinta sannan tace inayan tafiya??? Da murmushi tayi maganar labila tace tunjiya naso inkawomaki da dare harzanfito sainaji raina abace nakoma daki nayita kuka jiya wlh banruntsaba zazzabi yarufeni
Yanzun Karin ruwama akaciremun tanunawa khadija hannunta tace inatashi nacewa hajiya kinzo tacemun ah ah shine nataso ingako lafiya
Khadija tasaki wani kayatacceñ murmushi tana kallon labila tace sahiba lafiyata qalau Nima rashin ganinkine yahaifarmuñ da damuwa Amman yanzu tunda naganki Alhamdulillah
Tace nima wlh sainaji nawarke taresuka sakarwa juna murmushii”” muktar yamike jin ansoma kiran sallah yafita baicedasu komaiba

Aransa yana tunanin wannan wace irin soyayya ce sukewa junansu aidole khadija tace tanason baban labila Kuma batai laifiba Amman anya nizan iyah barinta ta aureshi??? Nifa tsoron matan yanzu nakeyi dawan nan tunanin yatafi masallaci
Inna ma fita tayi domin tayi sallah suma sukayo alwala sukai sallah anan suka zauna sunata labari yawancin firarsu duk akan karatunsune na islamiyya har innah tagama abincin dare sukaci gabadayansu sunware tamkar basuyi ciwoba”” 

Muktar yadawo yasamesu suna tafirah yadade bakin kofar yana saurarensu basu ganshiba dan hankalinsu baya nan juyawa yayi yabar kofar dakin
Saikusan karfe Tara labila tayi gida saida sahiba tarakata sannan tadawo tanashigowa gidan tasha toka zuwa dakinta batajima dazamaba
Saiga muktar saman gadon yazauna yana kallonta yace sapna kenan wannan fushin duk ni akeyiwa ko??? Gashi kinware tunda kinga kawarki Amman tana tafiya kinkoma kina fushi
Dadago da sirarun hawayenta tace Yayana ciwona azuciyata yake bawai afuskaba nayi kokarin boye damuwa tane saboda labila muddin tasan inacikin damuwa zata matsane saina sanarda itah menene damuwata dakuma silar damuwar
Idanhar nasanarda itah Kaine kake fushidani wlh bazata sake kallonka da mutunciba”” ninasan labila batunyauba danhaka nake boye damuwata duk lokacinda muke tare
Yanisa yanzu khadija ninake fushidake??? Kodai kece kike fushidani”” hawayenda suke kan fuskarta suka karasa saukowa yace please nifa bakuka nace kiyimunba “” tace Yayana taya zanyi mushidakai Kaine ubana kuma Kaine uwata

Kasharemun hawayenda uwayena ne yakamata su shafemun banida wani babban farinciki aduniya Wanda yawuce inga nafaranta maka rai
Yayi murmushi khadija kenan aiyanzu banada wannan kimar tunda har nahanaki soyayya Amman kikayi dama bayada mata dadan sauki Amman khadija mai matafa kuma harya manyanta
Gyara zama tayi tana fuskantarsa tace Yayana duk da bansan dalilinka nafurta hakanba nasan kasan wannan baharamun bane
Shimai mata baza a aureshiba tosabodame??? Koshidin bamutum bane??? Kasani mata sun linka maza sosai idankowanne namiji mata daya zai aurah sauran matan kumafa wazai auresu???
Yayana idan kai aure nan gaba kana bukatar kari kaima saiwacce kakeso tace batasonka tunda kaima kanada mata”” shinzaka saki uwar yayankane saboda kanason Karin aure???
Idan kasaketa ka auri waccen kasake ra ayin karawani aurenfa??? Aganina mai mata bashida wata illarda za ace aurensa bazai yiyuba sai idan ansan shidin ba nagartaccen mutum bane tanisa banyimaka wannan maganarba waidan kabarni Na auri dadyn labila
Tundahar bakasonsa wlh nahakurah dashi zansanarda labila kayimun wani mijin kokuma inbika cen kagama bangantaba ballantana inji damuwa Amman Yayana nasan kanada dalilin fadin haka

Dan Allah kasanardani meye dalilinka

Aisha✍🏼

[1:40PM, 3/6/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 73

      By

Gentle Lady💃🏽

Yayi shiru daga bisani yace khadija tace na am Yayana ” yace kinsan bazanso abunda zai cutardake bako??? Tagyada kanta yanisa tundakike bakisan labarin mahaifiyar muba 
Babu Wanda tasanar mawa kisani bayanni kinada wani yayan”” dasauri tadago tace Yaya kuma a ina?? Yanisa mu uku mahaifiyar mu tahaifa
Nima naji wannan ne lokacinda zamubar garin mahaifinmu tanasanarda wani malami alokacin ban fuskanci labarin sosaiba bayan nagirma nasake komawa yola
Da mamaki takalleshi duk da inayaro banwani sha wahalar gane gidansaba Amman da tambaya da yake malamine sainayi dace tunda nasan unguwar awajen gwaggo hasana na tambaya
Nasameshi yatsufa sosai baima ganeniba saida nayimasa bayani yanisa kwana na daya agarin hargidan mahaifinnawa natafi Amman baigane niba
Naso sosai nasan inda Dan uwana yake duk Wanda natambaya saiyace babu faruq agidan malamin shine yasanardani labarinda mahaifiyarmu tasanar dashi
Yanisa anan yakwashe komai yafada mata”” duk irin wahalarda tasha dayanda malamin yacemasa asirine akai mata komai baiboye mataba 
Yanakai karshen labarin khadija tafasheda kuka baiyi kokarin hanataba saida tayi mai isarta dankanta tashare hawayenta 
Yace wannan dalilinne yasaka banaso ki auri maimata Dan bazanso kema hakan tafaru dakeba”” khadija tadago jajayen idanunta takalleshi tace nagane Yayana Amman inaso kasani babu Wanda zaiwuce kaddararsa
Kataba tunanin za ahaifeni???? Duk da kiyayyarda mahaifinmu yakeyiwa mamana dayake akwai rabon saina shigo duniya gashi anhaifeni
Ya muktar kaddarata rubutacciyace bakada ikon sauyata inhar Allah yarubuto nima zansha wahala babu makawa hanawarka bazai kareni dakomaiba”” 
Kataba tunanin zan iya auren marar matar dagabaya yasake aurowata wacce zatayi nasanin fitana gidan??? Shifa Allah ba aimasa wayo baka isah ka karkare abunda yake arubuceba tunfil azal 
Baikamata kayiwa kowacce mace kallon hakaba Dan idanharkayi tonima wani mai irin hangenka dawannan zai kalleni
Kasani ba arasa nakwarai acikin al ummah komai lalacewar zamani zakasamu akwai nagartattuñ mutane acikinsu
Tanisa abunda kawai yakamata kayi kace Allah yakare maka kanwarka daga fadawa hannun irin wadan nan azzaluman matan”” kuma kabawa kanwarka makami wato ilimin Islam Wanda kowayake takama dashi
Dashi zata iyah kare kanta Allah yashiga tsakaninta damiyagun mutane kumani bana zargin mom wlh baruwanta halinsu daya da labila
Idanhar tanada wani mugun hali da awajen yarta zamugani Dan duk Wanda yatsotsi nono bazai yarba kamar yanda naji anafada
Nikuwa nace wannan zancen burr ne inji tusa saunawa uwa take haihuwar Yaya Amman babu Wanda yagadota wani lokacin maishegen fada saita haifi salihar yarinya
Wani lokacin saliha saita haifi masifaffiya danhaka masucewa waisu bazasu auri yayan masifaffuba bawai halin uwar zaku dubaba nayar dankowa da halinsa
Muktar yanisa yana kallon agogon hannunsa yace dare yayi kikwanta kihuta”” kai tagyadamasa tace nagode kaima kasamu kakwanta nasan jiya bakai barciba
Murmushi yasaki maidan sautii yace ya akai kikasan banyi barciba??? Itama murmushin tayi tace gashinan inagani a idanuwanka
Yamike yadauko mata maganinta yace aikece kikajamun kinfita kina kuka badole hankalina yatashiba””” tace ayimun afuwa duk laifin nan dai nawane baice komaiba yabata maganin tasha yayi mata saida safe yakoma dakinsa yadade yaana nazarin maganganunta kafin yayi alwala yana sanarda Allah yazabawa kanwarsa abunda yafizama alkhairi arayuwarta

Washe gari dasafe yana dakinta zaune suna firah saiga wayarta tasoma ringing jikinta yasoma rawa dantasan shine jiya silent tasaka wayar bayan fitar muktar tadauko wajen miss call ashirin tayi mamaki sosai”” saitacireta silent saiyanzu gashi yakirah 
Tanakallon wayar tana kallon yayanta yalurah da itah saiyashare yace wayar waye take ringing tsuru tayi alamun rashin gaskiya tace dama dama wayar sahibace tamanta da itah
Dakagan yanda take magana. Kasan batada gaskiya yayi murmushi yace tokidauka kice batakusa dawayar mana”” tadan sosa kanta tace ah ah kawai barta idan yagaji zaidaina kirah kowaye
Wayar hartakatse akasake kirah muktar yamika hannu yadauko wayar yaduba hubbina yaga anrubuta yadaga ido yakalleta saita done kanta yace kinganima inaganin kamar saurayintane yake kirah
Shirudai tayi batace komaiba hartakusa katsewa yadauka tareda sallama dayan bangaren aka amsa “” yace barka dasafiya yace yauwa Dan Allah Khadija nake nema
Muktar yadaga kai sukasake yin ido hudu tasosa kanta kamar wacce zatayi kuka”” yace togata nan tafe yakashe wayar baiko kalletaba yafita rike dawayar
Jikin khadija Yakama rawa tace yaunabani mekuma yakawoshi yanxu??? Saileken kofa takeyi””

Muktar da murmushi kwance afuskarsa yakarasa wajenda Usman yake tundaga nesa yaga matukar kamarda sukeyi da labila kuma tamkarma bai isah haihuwartaba”” 
Shima yana ganinsa yasaki fara a kafin yakawo inda yake haryasameshi yabashiy hannu suka gaisa “” daganan suka karasa kusa da motarsa 
Suka sake gaisawa yace yan america saukar yaushe bayan malam yacemun bakanan”” sosai Usman yayiwa muktar kwarjini a ido Sam yakasa daga idonsa sama yakalleshi”” 
Yace shekaranjiya nazo”” yace toya hanya inafatar dai lafiya?? Yace ah lafiya kawune yakirani yasanardani sakonka
Usman yatari nunfashinsa yace Allah yasadai yayan namu ya amince”??? Wata kunyace ta sake kama muktar yace ah gaskiya lokacinda naji Sam banyi Na am ba dalilinda yasaka nataso aranar kenan
Nazone daniyar natafi da itah dankawai nace banyardaba saiyarinya tazubemun balafiya jiyama saida tasha allurah Usman yace subhanalillahi yayanmu meyasa zakaimana haka
Muktar yace dad inada nawa dalilin saboda nayi alkawarin Kanwata bazata auri Wanda yakeda mataba saboda shine silar dayasa mukarasa mahaifiyar mu yanisa
Amman sapna tayimun gamsasshen bayani kuma nayarda dahakan yanzu danaganka yasake nisawa yadago yakalli Usman kamar zaiyi kuka yace wlh inason Kanwata sosai itace kawai take debemun kewar mahaifiyarmu
Banaso tashiga tashin hankali da matsatsin rayuwa” yasanne kansa nidama banda natauyemata hakkinta bazantaba bari tayi aureba
Danba zanso wani yacutarda itaba”” Usman yamurmusa yadafa kafadarsa yace nagane abunda kakenufi kuma nagamsu nayimaka alkawarin babu abunda zaisameta inasonta sosai bawai son wasaba dasanina kaima kasan bazantaba bari wani yacutarda itah ba
Muktar yanisa shikenan Allah yazaba mana abunda yafizama alkhairi usman yace Ameen”” muktar yace bari nakiramaka itah
Yayi maganar yanashirin juyawa Usman yasake basa hannu suka gaisa sannan yawuce aransa yanacewa ashedai baban labila haka yake bashida girman kai”” 
Usman kanshi yaga saukin kan muktar”” yanashiga gidan innah tace wai inakaje naga khadija sai tsautsauniya take”” murmushi yayi yace innah dadyn labila ne yazo”” yayi maganar yana shiga dakin yace kishirya yana jiranki ya ajemata wayar akan dago harzaifita tace Yayana tsayawa yayi batareda yajiyoba tace nidai banason fita bakafadamashi gobe zamutafi dakaiba
Adarare takeyin maganar yajuyo dafuskarsa wajenta dauke da murmushi yace inazanje dake kiyitamun kuka ainalurah soyayyarku hartayi nisako 
Tace wlh ah ah ya muktar yace hakane shiyasa naga kinyi serving din numbersa da hubbina
Kafin tace wlh banice nasaba yace karkibata masa lokaci yanajiranki Amman karkidade yawuce abunsa”” murmushi tayi mayafinta kawai tadauko tasaka tasa talkamanta tafito tana leke waiko zataga ya muktar innakuwa sai dariya takemata
Tafito dasauri tafita”” tunda yahangota yasoma aikomata dawani kyakkyawan murmushi Wanda itakanta bazata iyah daukarsaba akarancin shekarunta jitayima kamar kafafuwanta suna hardemata tuni tasanne kanta kasa

Aisha✍🏼

[1:30PM, 3/7/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 74

      By

Gentle Lady💃🏽

Ahankali tataka harzuwa wajenda yake tsaye shikuwa haryanzu baidauke idonsa daga kantaba tafiyarta tamkar dawisu natsuwarta kalamanta komai natadai yana matukar burgeshi
Ko amafarki baitaba tunanin wai zaitaba soyayya dawataba saigashi kwatsam ya afka kogin so kuma yayi nitso tayanda baxai iyah fitaba
Da tsadadden murmushinta Wanda yake matukar dimautarda Usman tayi sallama dakyar ya tattaro sauran natsuwarsa wajen amsa mata sallamarta
 Tace inawuni dad”” yadan gyara tsayuwa sanann yace lafiya qalau mom” dasauri tadago takalleshi batareda tayi maganaba”” yadaga mata gira yace yes indai bazaki kirani Usman ba nikuma mom zandinga kiranki dashi
Bakinta tadafe 🙊Dan Allah dad karufamun asiri dawanne bakin zankiraka aikuwa danayi rashin kunya takai karshen maganar tana kallon kasa
Murmushi yayi maidan sautii yasake gyara tsayuwarsa yace yayammu yace bakida lfy??? Kaita gyadamasa yace shine jiya akaki daga wayata wlh duk hankalina yatashi inata tunanin kobabu lafiya
 Shiru tayi cikin tsokana yace khadija meyake damunki?? Shiru taimasa saida yasake tambayarta tace bakomaifa dad
Yace badaikiso insani ai yayanmu yafadamun”” baima karasa rufe bakinba tace nashiga uku mekuma yafadamaka???
Yanda tayi maganar tanaware ido tayi matukar burge Usman yasoma dariya haryana tafawa”” ido takuramasa talangwashe kai sai murmushi takeyi gaskiya dad kyakkyawane inama nice yafara aure danasan nahuce takaicin soyayya indai nasameshi
Yatsagaita da dariyar yana kallonta Sam batasanma yana kallontaba saida yakada yatsunsa sukai kara sannan tadan zaburah 
Tanoke kanta tana Sosa kai alamar jinkunya sosai taji kunya dayakamata haka tana kallonsa””
Murmushi ya sakeyi yace toyajikin naki inafatardai kinji sauki??? Tasake gyada kanta yalurah sosai khadija tanada matukar kunya “” ganin firar tasu kamar atakure take saiyace tunda batada lafiya takoma gida shizai wuce wajen hajiya
Tace masa to Allah yakiyaye hanya”” tawuce gidan tsaye yake yana kallonta harta shige “” yasaukarda sassanyar ajiyar zuciya”” motarsa yabude yadauko siyayyarda yayi mata yabawa yaro yashigar matadasu 
Yashiga motar sa yawuce “” koda yashiga gidan hajiya lokacin suke break yana yin sallama abdulmajeed yataso dasauri yarungumeshi yana gaidashi
Yashafa kansa cikin fara a yace katashi lafiya??? Kaiyagyada masa yace Amman jiya Anty saida akamata allurah yace dagaske?? Amman ba afadamun ba
Yayi maganar yana karasawa saman dinner yagaida hajiya ta amsa cikin sakin fuska labila ma tagaidashi ya amsa yayimata yajiki tace taji sauki sosai”” dama bawani ciwo bane hajiyace tatashi hankalinta hajiya tace yaunaji lalata nicema natashi hankalin nawa bayan kukanda kikaitayi kinacewa akiramaki dad”” dariya labila tayi tace aini bansan Yar tsohuwar nan tanasonaba sai ranar”” 
Abdul majeed yace tafisona danni idan nagirma mota zansiya mata!” Suka kwashe da dariya labila tace sannu sarkin soyayya kaikuma mezakayi da tsohuwa??? Kowa yana yayin sabon jinie

??? 
Yace nidai inason abuta tunda tanafita dani unguwa”” sukasake darawa “” hajiya tace kai maigidana kyaleta zauna kaci abincinka”” karka makara kara labila sai anjima kadan zata tafi”” 

Usman yace tonima asammun abincin banci komaiba wlh anayin sallar asuba nataso”” labilace tasoma zubamasa “” 
Hajiya tace kaikuma lafiyarka wannan uban sammako??? Yakarbi cup din tea daga hannun labila yace hajiya wannan tambaya hakafa??? mutum yanada uwa sukutum agari atambayeshi danyayi sammako danyaganta”” 
Konayi laifine yayi maganar yana kallon labila tace inafa laifi dadyna ai zumuncine kasamu lada maitarin yawa
Hajiya tamere baki tace saikuje kufadawa wani badai niba kadaisan abunda yakawoka”” ‘Usman yakurba tea yana dariya ciki ciki yace hajiya gaskiyar kenan
Yajuya wajen Abdul majeed kaiyi sauri kashanye inkaika dagacen inwuce yau wlh aikine dani office din nan”” hajiyadai batace komaiba”” 
Labila tace dad bazakaje wajen sahiba taba batada lafiya”fa” ashagwabe tayi maganar abdul yayi kududum yace me dady zaiyi wajen kawarki
Yakalli Usman yace nima jiya ai abokina baida lafiya Amman bakaje ganinsaba sai Kawar Anty”” kamar zaiyi kuka””
Usman yashafa kansa yace aibaka fadamunba danaje ko yarona maza dauko jakarka muje”” Abdul majeed yaruga shikuma yamike
Labila tabishi da kallo tace kai daddy yanzun bazakaba kabari driver yakaishi mana kaisaikaje”” yakalleta yana murmushi yace Ashe yayanta yazo???
Tace yakirakane””” daidai fitowar Abdul yamikamasa jakar yagoyamashi itah yace cen nafara zuwa ai”” yakai karshen maganar yana kallon hajiya takasan ido yana dariya kasa kasa
Murmushi kawai tayi tana girgiza kai yace mujeko nagoyamaka”” yarike hannunsa mujeto daddy”” yace haba Abdul aikanajirah nagama magana da hajiyata ko
Yakalloshi da sauri hajiyarka??? Wlh hajiyatace”” yace najito hajiyarka”” yayimasu sai anjima sukai masa Allah yakiyaye yawuce yana dariyar Abdul majeed

Da dare muktar yasanarda kawu ya amince khadija ta auri dadyn labila bakaramin jindadi yayiba””” yayita sakamasa albarka washe gari Yakama hanyarsa yakoma skull
Usman yanadan zuwa kano akai akai”” haryanzu uwar gayyar batasanda komaiba gefe daya sunfara zana jarabar karewa balaifi sunawaya duk da haryanzu batasakin jiki suyi firah”” 
Usman yaturoda magabatanshi anzauna akayanka sadaki yabiya ansaka rana wata biyu”” kenan bayan sati biyu da kammala jarabawarsu

Aisha✍🏼

[6:38PM, 3/7/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

chapter 75

       By

Gentle Lady💃🏽

Ranadai akace bata karya saidai uwar diya taji kunya”” komai nisan dare gari zaiwaye watarana jariri zaizama ango koba hakaba??? 🤔

Su khadija sun kammala jarabawar su cikin sa a Usman dakansa yahado mata kayan lefe Amman baizo dashi gidan ba ranarda yadawo Dubai gidan hajiya yasauka anan yabar kayan
Saida yasake kwana sannan yakoma kaduna”” hajiya dakanta tasamu wasu makota aka kai kayan lefen tareda labila Dan itah hannu biyuce tana wajen dad kuma tanawajen kawarta
Kayanda aka tirkawa khadija kainiban taba ganin lefenda yayi yawansa dakuma kyansaba komai akwai aciki babuce kawai babu kananun kaya kuwa gasunan kamar kazanta”” nikuwa nace sa kananan kaya aisai khadija Amman su agwagwa koda sun saka jemewa zasuyi baridai kartajiyoni🙆🏿
Komai nacikin lefen dakagansu kasan sundace dawacce akasiya dominta””” labila taji dadi dangodiyar da taiwa dadynta tamkarma itace aka kawowa kayan”” masu ganin lefe kowa yazo saiyarike baki bangaren awarwaro dakuma kayan kwalliya abunsai Wanda yaganie masu karatu nabarmaku wannan aranku kukiyasta yanda kayan zasu kasance
Danni idan nace zantsaya fadinsu bashakka zankwana ina bayyanamaku kyan kayan Amman bangamaba dannikaina kayan sun matukar burgeni kamardai ace lubcy tagansu wink😜
Yanganin lefe dayan tsegumi hade dayan gulma duka sungama gani sunkama gabansu””” gwaggo husaina ce tadauki nauyin dauko maigyaran jiki asoma gyaramasu Yar su
Tunranarda aka kawo lefe tadauketa itama labila takwashe kayanta takoma gidan gwaggo Husaina danbataso tayi nisa da sahibarta
Zuwan Usman biyu Amman baya ganinta Dan gwaggo Husaina tahanata fita ko ina”” saidai labila takezuwa idan sakone takarbo yanason ganinta sosai Amman yazaiyi
Saidai suyi waya kuma batawani magana musamman idan labila tanakusa saitayita zungurarta””” yauma suna zaune an dama mata gumba tanasha labila tanagefe tana game jefi jefi tanayi mata mita waime takejirah haryanzu batashanye ba kinsanfa akwai wani tsimin yanajiranki
Ta wullamata harara kamar tayi kuka tace wlh sahiba bakyasona kinsan kuwa yanda abun nan yake??? Ta aje wayar tana kallonta tace so kai aibandama karnayi barin baki sainace nafi dadyna sonki wlh
Sahiba nasan zakice badadi ko??? Aibarashin dadinsa zaki dubaba amfaninda zaimaki”” tundahar gwaggo tabaki nasan yanada amfani shan nashi awajenki tagyara zama kenifa sonake kisiye zuciyarsa banaso yasake kallon kowa agabansa faceke
Takarasa maganar tana dariya Khadija takaimata duka tagoce tana dariya””” khadija tace waike meyasa kike hakane kokadan ke bakyataya mom dina kishi””
Labila tace kishinme ai itah batada kishi kinga mukuwa munadashi Dan Munasonsa fiye da kammu”” itah dai labila tasan inda maganganunta suka dosa sautari tanayin nazarin hakan cewa mahaifiyarta batason dadynta dakuwa tanasonsa bazata taba cutardashiba
Kodakuwa taga abun cutarwa zata iyah taremasa karyasameshi danhaka tuni tacire lubabatu cikin sahun masoyan Usman tajerata acikin makiyansa
Sukuma wautarta sukegani kodan bata tashi hannun mom dintaba shiyasa batajin haushi”” kowanne da abunda yake sakawa aransa
Wayar khadija ce tasoma ringing”” gabadaya suka maida hankalinsu”” wajenda wayar take kara”” my everything sukagani rubuce akan fuskar wayar
Khadija ta harari labila tace aitunranar naso nayimaki magana”” labila tace to aiyanzu kinyi kidauka kartatsinke””” kuma kifadamasa munazuba idofa haryanzu baikawo mana invitation ba”” 
Khadija tawaro ido🙄🙄 tace nicema zanfada ??? Wlh saidaikuwà kar agayyaci kowa damadai walima kawai zamuyi koda baki kyafada
Kafin tagama maganar harkiran yakatse wani yasake shigowa

Labila tace kidauka mana karta katse””” saida tasake ballamata harara sannan tadauki wayar tadauka takara akunne tareda sallama”” daya bangaren aka amsa kema amincin Allah ya tabbata agareki ma abociya kyakkyawar fuska”
Wani farda ido tayi””” bakisake kafin tayi magana yace amaryata kina wani abune??? Tadaga kai takalli labila sannan tagirgiza kai”” kamar yana ganinta
Saida yasake tambayarta sanann tace ah ah maganar kanta tamkar tanayimata wuya”” gabadaya muryanta takashe masa jiki”” yace khadija maganar invitation dinku”” naturo akawo maki dan gaskiya bazansamu damar shigowa gobe ba aiki yayimun yawa”” cen kasan makoshi ta amsa dato”” yace hmm yanzu hardake wajen yimun rowar ganin kyakkyawan murmushinki
Dariya tadanyi marar sauti tace yihakuri wlh balaifina bane “” yasake gyara zama danyanajin dadin muryanta “” yace towaye??? 
Taballawa labila harara tace sahiba ce”” labila tayi saurin rufemata baki”” tanagirgiza kai”” yace labilar ko”” Deejaarh!
Aranta tace ya salam talumshe idonta yanayin yanda yakirah sunanta yasaukarmata dawata muguwar kasala”” cikin sanyi murya tace umm
Yace Amman deejaarh meyasa zaki biyemasu kinkuwasan halinda nashiga narashin ganinki??? Wlh jinakeyi kamar zanmutu kinkuwaji yanda kirjina yake bugawa dakina kusadani dazakijiwo sautinsa”” 
Idanuwanta alumshe suke maganganunsa sunashiga cikin kofofin jininta”” jintayi shiru yasaka yace Deejarh”” sannu ahankali tabude idonta tadorasu akan labila anya dad yasan metakeji idan yakirata da wannan sunan
Jitakeyi aduniya kaf babu Wanda yafishi iyah kiran sunanta “” yasake kiran sunanta cikin wani salon murya Wanda shikanshi baisan yanada itah ba”” tabangaren Usman idanuwansa harsun rikide saboda chananin sha awarda take damunsa kwana shidan dasuka rage bikinsu ganiyake tamkarma shekara shidane
Saiyaga lokaci yadaina gudu kwanaki ganinta yakandan ragemasa damuwa Amman yanzu tsawon wata dasati uku baisakata”” a idonsaba saidai kawai awaya kuma koshi batadauka saitajamasa rai kokuma duk kunyace 
Yacigaba please Deejarh kitaimaka zanzo gobe saikifito naganki koda bazaki dadeba”” aranta tace nima inason ganinka”” dad inajima kamar nayi kuka rashin ganinka”” jinshirun yayi tsayi yace Deejarh bakice komaiba idan bazansamu ganinkiba kidaure kifurtamun kalmarda zata ragemun kewarki”””
tsuru tayi kamar wacce tai karya “” yace kobaxaki iyah ba??? Tace nifa dad kunya nakeji”” labila mikewa tayi tarankwashe ta akai tafita dagudu”” saida khadija tasaki kara
Dasauri Usman yamike yana tambayarta lafiya??? Tayisaurin saita kanta bakomai kafata nadanbuge”” yace ayya sannu amaryata
Kunya takeji idan yanakiranta dawan nan sunan”” hannutasaka tarufe fuskarta”” yace yadai amaryata kunya kikejine??? Tace umm tanagyada kai
Yace ainakusa rabaki dawan nan kunyar”” watakunyar ce yasake jefata aciki”” yana kallon agogo yace kingama lokacin sallah yayi”” Amman bakifadamun kalma kodayaba
Shiru tayi”” yace please ! Kokinaso inzo yanzu kokifada koyanzun nataho”” ido taware tace darefa yayi 
Yace toki fadamun”” ahankali tafurta I

L

O

V

E
You 

Tayi saurin kashe wayar taboye kanta ajiki filo” bangaren Usman wani dadi yaji yakalli wayar yanasakin murmushi kamar yana kallon fuskar Khadija
Tashi yayi yasallami ma aikatan sukayi haramar sallah”” bashi yafitoba”” sai bayan isha”” i
Khadija kam tana kwance tundasuka gama waya dayake tana fashin sallah batayi yunkurin tashiba harbarci yadauketa awajen
Usman ne bayan mota Muhammad yana tukashi zuwagida hannunsa katin daurin auren sune da khadija yau yakeson sanarda lubabatu maganar aurensa saboda yasan halin magulmata shiyasama baibawa kowaba danyasan muddin yarabashi tokota halin yayama saitasamu labari
Jinginawa yayi jikin kujerah yalumshe idonsa tundayake baitabajin fargabar sanarda lubabatu yanason kara aureba saiyau kirjinsa saibugawa yake
Sunakawo wa kofar gidan yasakejin gabansa yafadiii dasaurii yasoma furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun حسبنا الله ونعم الو كيل

 

Aisha✍🏼

[2:00PM, 3/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 76

        By

Gentle Lady💃🏽

  

Bayan motar tatsaya inda ake ajiyeta driver yafito yabude masa kofa Amman Sam hankalinsa baya jikinsa” saida yakirah sunansa sannan yafarga”” 
Yadan murja idon sa kamar Wanda yayi barcii”” dauko kayansa yayi da card din yama driver saida safe”” yawuce cikin gida jiki asanyaye
Koda yashiga bata falon kasa yasaukarda wata gajiyayyar ajiyar zuciya”” Allah yasama tayi barci sai inbari saigobe nikuwa abun ma dariya yabani to aikogoben kafada abunda kake gudu zaifaru bafasashi za aiba kaidai kawai kafada musam makomarmu
Ahankali yasoma hawan step din baima tsaya hawan na uraba zuwa sama tadaukeshi tsawon lokaci kafin yakai”” bangarensa yanakaiwa lubabatu tana kawowa dantayi mamaki yau yadawo dawuri
Dan tunda yahadu da khadija baya dawowa saiwajen karfe Tara alokacinne yake kiranta danbadama yayi agaban uwarguba! Au sorry🙊 uwargida tunda labila tace basuyardaba tasanie
Yana ganinta yatattaro sauran natsuwarsa yasamu yasakar mata lallausan murmushi itama tamiyar masa da martanin murmushinsa “””
Tace sannu dazuwa yauwa yagidan yyi maganar yana turah kofar dakinsa tabishi abaya “” tace gida saitarin kadaici ai kwanan nan nakeson naje yawon kasa dani da su sajida”” yace ko??? Tace eh yamere baki baice komaiba
Tace bakace komaiba”” yana rage kayan jikinsa yace Toni menene nawa ??? Da inaso dabanaso inhar kinaso saikinyi ra ayinki nasanma kina fadamunne dankar naga bakyanan Amman banda haka watarana aisaidai nabuda ido bangankiba””””
Maganarsa saima tabata dariya ganin tana dariya kamar wacce kare yaciza yakalleta baki bude yace wannan dariyar haka kumafa???
Tatsagaita da dariyar tace tomekuma nayi dankawai nayi dariya??? Yace bakiyi komaiba Amman kisani ire iren wan nan dariyar batada kyau acikin addini manzon Allah yace tana kashe zuciya tanakuma rage imani” jibifa harda hawaye kike shaidanne yakee irin wan nan dariyar”””
Take annurin fuskar lubcy yagushe tace kana nufin nidin shaidance???? Yakwalalo ido yace wani banfadaba baza aji mutuwar sarki abakinaba”” 
Karki karagaba kifada Allah yabaki hakuri bahakan nake nufiba yadauki towel dinsa yashige bandaki yarufo kofa anan yabarta sai nanata maganarsa take aranta
Haryafito batako motsaba””” yana taje sumar kansa’ yadan kalleta tajikin miro yaga yanayinta yasauya”” takowa yayi kusa da itah yazauna yana kallonta yace uwargidan Usman badai maganar da nayi dazuce tasosa rankiba????
Saurin kawarda damuwarta tayi takirkiro murmushi la bakomai dankawai kasanarda ni gaskiya dannakiyaye gaba
Aini nagode Allah dayahadani dimiji irinka wasu mazan zasuga matansu suna aikata badaidaiba Amman saisu kyalesu kodan kada ran matar yabaci kodan wani Abu 

Tace nagode kashirya abincinka yana jiranka”””yamike bari nashirya amma kafin Naci abinci akwai wani albishir dazan baki
Nantake lubabatu tawashe baki tace toshikenan bari nakawo abincin nan”” tayi maganar tana mikewa tasauka waje bayan yashirya yazauna jiranta saigashi tashigo dauke da tiren abincin ta aje kasa””” cikin zumudi tacemasa tofadamun””” 
Yace yanzu kuwa”” hannunta yajawo zuwa saman gadon yace zauna bamusu kuwa tazauna””yana fuskan tarta yace albishirinki
Tace goro fari kalkal”” ya murmusa Usman dinki yasamu wacce zai aurah!!! Kamar saukar aradu haka taji maganar batayi saurin saita natsuwarta ba cikin tashin hankali Wanda batasan yabayyana afuskar taba tace ban ban banfahimcekaba wane Usman din???? 
Yace kinada wani Usman dinne bayan wannan Wanda yake gabanki??? yakalleta damamaki ganin yanda har idonta yasauya”” yace yadai lubabatu kobakiji dadin furucinaba ne??? Kefa kike matsamun kullum akan nanemi mata na aurah inaki kinmanta harfushi kikeyi idan nace nida aure har abada yalokaci daya nafadamaki abunda nai tunanin zaisanyaki nishadi saikuma naga sabanin hakan???
Saiyanzu lubabatu tasan taso tabka kuskure dayake yarduniyace ta iyah tsara magana “” tayi saurin boye damuwarta takirkiro murmushi tace wlh nafika jindadin wannan ranar abunda yasa kaga nashiga damuwa inatausayin Kane dakuma kaina danakasa biyawa mijina da bukatarsa tsayin shekaru
Tanisa inajin tsoron Karka auro wacce zatazo ta tayarmaka da hankali narantse danaga tashin hankalinka nagwammace naga mutuwata!!!!
Wani dadine ya lullube Usman baisan sanda yamannata jikinsaba yana sakamata albarka”” tace bakomai dadyn Abdul”” nidai fatana Allah yabaka wacce zatadauki nauyin lalurarka kamar yanda kakeso Allah yabaka tagarii yace ameeen ameeen kamardai yanda yabani ke
Ta murmusa wanne gari yarinyar take??? batareda fargabar komaiba yacemata kano”” aranta tace munafuki 🙄yanzu dama zuwanda yake kano soyayya yake”” kafin tatambayi sunanta yacigaba sunanta khadija marainiyace

tace Allah sarki Allah yajikan iyaye yace Ameen jiki asanyaye
Tace inafatardai yan uwanta sunyarda dankar ayimana kamar nasauran dakanema saimunsarai da aure saikuma Abu ya lalace””
Yace ah ah sukam bazasuyi hakaba”” kafin tayi magana yadauko card din duka yamika mata yanacewa sauran kwana biyar daurin auren
Saura kadan lubabatu takundumo ashar”” takarbi card din jikinta harrawa yakeyi takurawa card din ido kamar maisabuwar makanta”””
Ga rubutu nan taryen taryen takaici baibarta karasa karantawaba”” tamika masa ” Yace harkin kare??? Tace ah Allah yasanya alkhairi yace Ameen”” yakarbi katin””
Yace saikiyi list din abunda kikeso duka zanje dakaina insiyomaki”” dakayan dazakici biki”” tace habadai dawainiyar tayi yawa ai” gana fatenda amare zasuyi kuma gahidimarsu aisaina karamaka nauyi
Nadaigode babu abunda nanema narasa agidan nan”” yamurmusa nasanda haka Amman nasan baxaki rasa abunda kikesoba
Tace wlh bakomai saidai kayanda kawai za a baiwa yanbiki””” yamike daga saman gadon yace barma maganarsu nidagayau nakashe taron biki agidana
Damacen banaso Dan bidia ce kece kike kafewa saikinyi kuma dagakarshe kafin awatse sai anyimaki sata kidawo kinafada bance kigayyaci kowaba
Idankuma Mace takawo kanta nasa aka koreta karkiga laifina
Tace waishi wannan wanne irin tsarine yazodashi meyake nufi dahakan??? Ko anyisata aini akaiwa bashiba
Yazauna yasoma cin abincinsa baidamu data yardaba kobata yardaba danshi yasan matakinda zaidauka maigadi zaifadawa karyabar kowa yashiga gidan koda kuwa lubabatu ce tazo dakanta
Haryagama cin abinsa tana zaune saida yagama tamike zatadauki kayan yace xakidawo ko??? Tace meyafaru kana bukatar wani abune??? 
Yalangwashe kai kamar karamin yaro yalumshe ido yabude alamar ah”” 

Murmushi tayi tace tome kakeso??? Yace goron albishir dina mana”” kuma kinsan abunda nafi bukata ayanzu”” tagane inda maganarsa tadosa tace ayya gashi inafashin sallah””” yace kash!!! Tokitaimaka koyan dubarune kiyimun Dan Allah”””
Tace please baban Abdul wlh harda Dan zazzabi nakeji kafin zuwankane nadansha maganie kabari basaura kwana biyarba aini namatsuma amaryar nan tazo nahuta
Yayi dariya lallaima matar nan watakan harma gajiya kikai dani saikace wani maye”””😾 tana dariya itama tace kafadi sunanka aikai mayene Amman bamaicin mutaneba mayen……..😂😂😂

Bata karasaba tasoma dariya yace najidai Amman babu Wanda yasan dahakan saike bayanke bawanda zaiganni yace inada lalurah saifa idan kece kika sanarda kawayenki
Tarike baki waceni dazanbude sirrina agun wasu banzayen kawaye”” ai idan nafada watama saita kwacemun kai””” yace kedai fadi ainasan kumata tunaninku ragaggene dazaran kunhadu waku waku mata zakuta bararda zance
Kuyita fadin sirrin mijinku mijinki koda katuwar loma yake wajen cin abinci baidace wata tasan yanda yakecin abinciba
Shimadayake bakomaiba ballantana abunda akeso yatsaya dagake saishi waihar kina iyah sanarda wasu kawayenki bakyako jin kunya waike wautarki aimatane yan uwanki
Allah yasanda hakan Amman ya la anci matarda take barbada sirrin mijinta gawasu mutanen”” haba Yar uwa lubabatu ma tasanda haka tana boyewa bata taba sanarda kawayentaba toballaike wacce bahalinku daya da lubabatu ba
Kodai kiyarda dahakan kidaina fadawa kowa sirrin mijinki kokuma muce lubabatu ma tafiki wlh”” karkimanta anason mace maikunya
Duk matarda batada kunya da itah da dabbobi daya saboda sune suke yawo tsirara suyi komai agaban kowa basajin kunya

Aisha✍🏼

[3:54PM, 3/8/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 77

       By

Gentle Lady💃🏽

Anason mace mai kunya hausawa sunacewa kunya adon yammata”” mace ballagaza itace batada kunya
Nidai shawarda zanbaki Yar uwa inhar mijinki yazama irin haka kokuma akasin hakan kisamu kuwarware matsalarku atsakaninku batareda kunyiwa juna tonon asiriba
Danwannan babu abunda yafishi zama tonon asiri “” shinwaima idan kinfadawa wata tanada maganinda. Zatabakine ??? Ninasan babu abunda zatacemaki saidai tace kiyi hakuri shine kawai
Shawarda zanbayar itace idan mijinki yakasance kinkasa biyamasa bukatarsa ta auratayya tokirika hadamasa da dubaru wadanda kikasan basu sabawa addiniba zaki iyah yin koma mene danyasamu gamsuwa ajikinki saidai banda waje daya Wanda Allah yamana iyaka dashi wato bayagamutum
Koya mijinki yakai kolokuwar bukata inhar yanuna maki yinhakan karkiyarda Amman bayan nan ko inane halal ne “” idankuma bukatarsa tawuce duk wata dabara dazaki masa tokibarsa yayi aure
Karkuma kitada hankalinki idan kikaga ya auro wacce take iyah hakuri da bukatarsa”” karkiga laifinsa bashine yayi kansaba haka Allah yagadamar yinsa saiki tausaya masa
Idankuma baida halin auren Yar uwa inkinada hali kibashi kudi yayi bawai faduwa kikaiba sakamakon aikinki yana wajen Allah” idankuma bakida hali kema tosaiki bashi shawara yarika hadawa da azzumie domin kare kansa daga fadawa ga aikata zina

 Manzon Allah yanacewa awani hadishi dayake kwadai tarwa akan aure”

 

وقال صلى الله ءليه وسلم يا معشر الشباب من استطاع منكم الباءة فليتزوج فإنه أغض للبصر وأحصن للفدرخ ومن لم يستطع فعليه بالصوم فإنه وجاء رواه البخاري ومسلم

manzon Allah tsira da amincin Allah sutabbata agareshi yanacewa yaku taron samari masu iko daga cikinku tosuyi aure ma ana wadanda sukeda kudin auren kuma sunkai munzalin yin auren sunada bukatar mata “” cewashi aure yanakarewa daga ganie dakuma sha awa

” Wanda kuma bashida iko ma ana baida halinyin auren kokuma idan yayi auren bazai iyah daukar dukkanin hakkin matarba sai manzon Allah yace nahoreshi dayayi azumie sabodashi kariyace
Wannan hadishin basamariba harmai mata zai iyah aikidashi inhar yaga yakusa fadawa ga aikata zina
 Yar uwa saikibashi shawara yafara azumie kema zaki iyah tayashi kinga yasamu ladabiyu galadar azumie kuma galadar kiyaye kansa dadi biyu kenan
Idankuma kece dayawan bukata shikuma bayada shima zai iyah wasadake danyaragemaki kamardai shidin saikuma kikara da hakuri idankuma kinji bazaki iyaba zaikaiki ga hakala saikisameshi kuzauna kifadamasa karkiboye komai
Tsakaninku kuwarware matsalarku idan baida lafiyane saiyanemi maganie idankuma haka Allah yayishi saiya sauwake maki kisamu daidaike kuyi rabuwar mutunci Amman gaskiya indai harzaki iyah hakuri tohakurin zaifi zakici ribarsa agobe kiyama Allah yasa mudace
Lubabatu tace wlh bayabon kaiba nikaina idan naji masu sakin baki sunafadawa wasu matan sirrin gidajensu haushi sukeban saikuma kaga wadanda sukafisu wayo subasa fadar nasu saidai su saurari naka
Usman yace aishine rashin hankalin nagode Allah da matata batacikin ire iren wadan nan matan”” nikuwa nace Allah yasa masu karatun wannan labarin basacikin wadan nan matan
Idankuma kinayi tokinji dagayau saikigyara rawarki kisauya taku wadanda kuma basuyi aurenba sukiyaye dangaba yayimasu amfanie
Zaki iyah turawa wata domin takaru kema kin isarda sako Allah yasa muzama masu rike sirrinmu Ameen
Lubabatu tamatsu tabar dakin danfayau tashiga rudanie
Tayakuna fuska nidai zankwanta kakula dakanka””” yace shikenan Allah yasauwake konazo natayaki barcin???
Tayi saurin cewa ah ah nagode nahutardakai saida safe tayi maganar tana bude kofa”” yace tosaida safe tafita taturo kofa”” wai wata sabuwa lubabatu harda gudu gudu take hadawa jitakeyi kamarma tazama iska takai kanta wajen *hatsabibin boka* tanashiga dakinta sauran kadan tafadi garin mugun saurinta”” 

Takulle kofa tafada dakinta wajen drawer tadauko akwatin tabude tafitoda karamin madubin sai walwalniya yakeyi tashafa cikinsa jikinta yana rawa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* muryanta tanarawa kamar maikuka
Daka ganta kasan tanacikin tashin hankali shafawarta keda wuya saiga wani duhu gabadaya ya mamaye dakin abunda bata saba ganiba gabadaya dakin yayi baki kirin wutar dakin tadauke bataganin kotafin hannunta
Wani tashin hankali tasake shiga al amarinda yasoma saukarmata da faduwar gaba lallai wanann matar kilanta wajen boka takaishi shine abunda lubabatu tasoma rayawa aranta
Batagama tunaniba haske yasoma samuwa acikin dakin sannu ahankali haryagama mamaye dakin saiga *hatsabibin boka* yabayyana asaman tsafaffen zakie ido hudu kawai lubabatu tayi dazakin tasaki fitsari daga zaune ganinhakan yasaka *hatsabibin boka* yatintsire da dariya kamar bazai dainaba
Zuwa dakiku ashirin yatsuke fuskarsa tamkar Wanda baitaba dariyaba saiga idanuwansa masu munin gaske sunkoma koraye shar yasoma wani irin hucii kamar mesa hucinsa haryana fesowa lubabatu
Cikin tashin hankali tace yakai wannan hatsabibin matsafi kasani yauban kirakaba saida mummunan labari saiga hawaye sharrr akan kumatunta suna zarya
Tacigaba waini Usman zai ha inta??? Haryatashi aure baisanarda niba??? Sai anasaurah kwana biyar waiyama akai aikinda kaimasa baikama wannan shegiyar yarinyar ba
Haryanxu bokan kallonta kawai yakeyi baice uffanba saida takai karshen maganarta sannan yabushe da dariya yace wannan ranar batada sa a gareki
Tunkafin kisanardani gabadaya aljanuna sunce bazasu iyah jayayya dawan nan yarinyarba sanadinda yasaka kikaga batakishiba aljaninda yake yin wannan aikin yakasa shiga jikinta
Hasalima yanzun yanacen yanajinya sanadin rauninda yasameshi dayaso rike hannunta”” kozaisamu kafar shiga jikinta
Cikin rudani lubabatu tace nashiga uku boka wannan kuma wace irin hatsabibiyar yarinyace???
Wajen wane irin boka takaini Wanda yakeyiñ aikinda yagagari aljanunka su shafeta???
*hatsabibin boka* yasake kecewa da dariya yace nikaina yau banacikin yanayi maidadi lokacinda kika kiranie ina karkashin kurkukuna dayake kasan kasa”” ina ganawa wata aljana azaba!!!
Cikin lubabatu yaduri ruwa kamar tazunduma dagudu yacigaba kirankine yasaka nahau dokina nazo gareki kisani wanann yarinyar tasha banban da irin matanda mijinki yake soyayya dasu
Wannan takere duk wani tunaninki saboda hafizace kuma tanada yawan ibada narantsemaki da karfin tsafina dana gadà kaka da kakaññi babu wani aljani aduniya daya isah yatunkareta haryashiga jikinta batareda yakone kurmus ba yamutu
Kebarta mutuwama ko tokarsa ba azasamuba!!! Take lubabatu tasoma yarfe zufa tace togaskiya banaso ya auri wannan yarinyar danmuddin tashigo gidana zatayi wuyar fita “” kaiyagirgiza yace babu makawa saiya aureta!!! 
Saidai kiyi hakuri idan akai auren kisake kirana kafin lokacin ninasan hanyarda zanbi domin mukasheta danwanann muddin tana raye tosaitaga karshenki
Lubabatu tadafe kirji tace wlh saidai naga karshenta Dan ubanta tafashe dakuka”” yanzun dole saitashigo gidan???
Yace tabbas kimadaina barnar hawayenki babu abunda zai gagari *hatsabibin boka* idankuwa har akwai wani aiki dazai gagareni tonikuwa banchan chanchi akirani *hatsabibin boka* ba
Kikwantarda hankalinki kamar tsumma aranda”😆😆😆” tace wane irin kwanciyar hankali zanyi bayan anashirin kawomun annoba!! 
Waikunjitafa🙄 wai annoba! Bayankuma itace annobar:?

Masu karatu kuyi hakuri da iyah abunda kukesamu baidace kuna rainawaba inama laifina inayin wannan kullum karfa kumanta inada aikinyi bawai zaman remote nakeyiba kurika hakuri daduk abunda kukasamu kunsan typing dinnan kansa wuyane dashiii bawai yawan typing ba Allah yasa kuna amfani da abunda kuke karantawa
Idankuma kawai dannishadinku kuke karantawa babu amfanin inrika bata lokacina😒

Aisha✍🏼

[3:06PM, 3/9/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

Chapter 78

       By

Gentle Lady 💃🏽

Yasake kecewa da dariya yace yakike kuka kizama jaruma mana aikinsan nibana magana biyu kijirah kafin tashigo gidan munsan yanda zamuyi ai akwai bakaken aljanu dakuma masu shan jijin bil adama
Hayyanul zairi yayi tafiya kasar iraqi na aikeshi nemomun wadansu kayan danakeso nayi tsafi dasu”” zaidaukeshi tsayin wata kafin yadawo dankuwa dajinda zaishiga yanada hadarin gaske bartashi aljani saboda akwai miyagun dabbobi masu cin naman aljanu acen idankuma mutum yasake tsautsayi yakaishi cen saidai uwarsa tahaifi wani
Inason Gina fadata acen saboda wani dalili”” dayana nan tuni aikinki yagama danhaka saiki jirah kafin yadawo yanakai karshen maganar yadafa tsapappen zakinsa take yabace dashi da zakin lubabatu saida tazaburah tamiyarda madubin mazauninsa
Tagumi tabuga aranta tace anya wannan bokan baihada iri da aljanuba??? Nidai naga abunnashi saigaba gaba yakeyi yanzukuma waifada za aginamasa a Iraqi lallai wani Abun sai matsafa
Hmmm yanzun inaji inaganidai Usman saiya auro wannan shegiyar yarinyar”” tayi shiru aikuwa inyasan wata baisan wataba bakin zuciyarsa zan kulle tayanda zaiyita masifa da mutane baburuwa koni tashafeni Amman saina lalata wannan auren badai Saurah kwana biyarba hmm ayimuganie to
Mikewa tayi tabude drawer tadauko wata Yar battar karfe tafita zuwa kitchen takunna gas takara battar karfen ajikin wutar tasoma daukar zafii saida tayi zafiii rau sannan takulle bakin battar takoma daki tana murmushin mugunta
Lokacinda wannan abun yafaru Usman yadade dayin barcii acikin barcinsa yasomajin ransa yabacii zunbur yamike yakalli agogon dakinsa asuba takusa tsaki yasoma yi kamar Wanda akaiwa laifi
Jiyakeyi tamkar yarufe kansa daduka”” yarasa yazaiyi hannuwa yasaka yadafe kansa yanakiran innalillahi ahankali yadan samu natsuwa yasakeyin addua Yakoma yakwanta danbarci yakeji
Washe gari lubabatu batamasan sanda yafitaba wajen aiki kuwa gabadaya suka rasa gane kansa koda maganar arxiki kaimasa saiyamiyar maka datatsiya
Idankuma kadameshi da surutu yahauka da masifa kamardai Wanda kare yaciza yanazaune akan kujera yakurawa tarin takardunda suke gabansa ido kamar maitunanin wani Abu gabadaya jinkansa yake kamar banashiba
zuciyarsa sai tururi takeyi kamar hayaki”” wayarsa yadauko yakuramata ido yaukwanansu biyu basuyi waya da khadija ba tunranarda yaji ransa yabaci yaji bayason kiranta lambar yakamo yana kallo kamar zaikirah
Yacigaba da jujjuya wayar cenyadanna kirah tayita ringing hartakatse ba adaukaba nantake yaji ransa yabaci yasake kirah 
Khadija tana zaune tareda labila tanayin karatun suratul bakarah labila tana saurarenta saboda walimarda za aimata sai Amarya tayi karatu
Shine takeson labila taduba mata duk da tasan bata mantaba wayarta tana hannun labilar sanda yakirah dayake bata ringing sosai bata daukaba..
Dakiran yasake shigowa garin takatse kiran Ashe tadauka kuma hankalinta bawajen wayar yakeba Sam batamasan tadaukaba

.

Shikuma usman yanaganin andauka haryabuda baki daniyar sakin magana yajiyo zazzakar muryar khadija tana karatu.
Wata irin sassanyar ni imace yaji tasauka azuciyarsa tuni yanemi damuwarsa yarasa”” aitake yasoma record yasaka Hans free 
Idanunsa yalumshe tamkar maijin barcii harcikin kopofin jininsa muryar khadija take shiga tsayin wajen mintuna ashirin barci maidadi yayi awon gaba dashii
Cen cikin barcinsa yakejin ana helo dad kanajina maryar labilace tatasheshi baimasan yayi barcinba tashi yayi”” yayimika tareda hamma lahaula walakuwati illah billah
Save din recodin din yayi sanann yasake kirah danwasai yakejinsa kamar ancire masa dukkan damuwarda keransa
Tanasoma ringing labila tadauka da sallama ya amsa yanasake lumshe idonsa tace dady barka dahutawa ya aikin??? Yace Alhamdulillah ina khadija??takai kallonta wajenda khadija take tace gatanan yanzun mukagama karatu zamufita raba invitation ne”” yace saiyanzu zakufara rabawa??? Tace ah ah tunjiya muka fara dare yayi saimuka dawo gida Dan akwai mutane dayawa wadanda yakamata mugayyata
Yace shikenan tokarna tsaidaku saikundawo kikula kinji yarlele”” tace to daddy nagode”” yanaso yace tabawa khadija kuma yakasa danhar yanzu yanajin Dan nauyin labilar
Takatsemasa tunani dacewa dad gasahibar tayi maganar tana mikamata wayar takarba itakuma tafita dantalurah inhar gabantane sahiba bata iyah wata firah dashi 
 takara akunnenta kafin tayi magana yace amincin Allah yatabbata agareki hasken zuciyata”” wani daddadan sanyine yaratsa kofofin sadarwarda ke kaisako ga zuciyarta talunshe ido tanamai saukarda ajiyar zuciyar wacce Usman yajita
Tare dakai ma aboci fara a dakwarjinie”” wani dadiyaji marar misaltuwa waima anya khadijarsace tafurta masa wannan Kalmar??? Kafin yagama tunani tace inafatar kanacikin koshin lafiya???
Sumar kansa yashafo yace INA lafiya fatar kema haka??? Tabude idonta ahankali tana kallon ko far dakin tace idan nacemaka haka nayi karya hubbyna
Wayyo dadi kasheni kusan Usman sumar zaune yayi”” cikin kasalarlar murya yace meyake damunki Deejarh Na??? Tanisa akwai wani Abu dazaidameni aduniyar nan inatareda gwarzon namijie kawaidai kaunarka dakuma kewarka sune sukataru suka dameni azuciyata
Harnakejima tamkar narasa wani muhimmin bangare ajikina”” yagyara zamansa yanalaso busassun labbansa haryanzu idonsa kullesuke dantsabar yanda yake jin dadin firar jiyakema tamkar asararin samaniya yake yawo
Deejarh yakirah sunanta akaro nafarko ta amsa na am hubbyna”” yaja ajiyar zuciya yace waidagaske bamafarki nakeyiba??? Tarausayarda kai tace kamarya hubby ???
Yamurmusa wlh jinakeyi tamkar inawata duniyarda babuwani mahakuli acikinta face nidake bantaba tsintar kaina atsantsan soyayya irin wannan ba”” waidama haka soyake da dadi hakika nasake yarda soyayya tafi Zuma dadi inhar mafarki nakeyi banafatar nafarka daga wannan daddadan mafarkin harkarshen rayuwata
Inaso incigaba dajin wadandan dadadan kalamanki sunamatukar sanyaya manie zuciya””” khadija tadan kishingida tace kokadan masoyina ba mafarki kakeyiba a farke kake kabude idonka zakaganni akusa da zuciyarka indai har kalamaina suna sanyaka nishadi nikuma bazangajiba wajen furtamaka su harsaisun cika duk wani bango dake zuciyarka
Nikaina bansan soyanada dadiba saida nayidace da ma aboci soyayya irinka hakika ninasan nayi dace samunka agareni babbar nasarace inarokon Allah yasake mallakamun kai hasken zuciyata
Usman bakin nanfa yakirufuwa wai Ashe Usman ya iya soyayya??? Abunda baiyiba koda budurwarsa ta mafarki yanaji ajikinsa kamar yanzune zaiyi auren soyayya 
Matarsa ta mafarki ya auretane saboda yanajin tausayinta akan abunda matar ubanta takemata “” haka sauran matansa daya aurah azahiri yanasonsune kawai danbukatar sha awarsa lubabatu kuwa jiyakeyi kamar adolene ya aureta
Soyayya tagaskiya kuma kwaya daya tak babu macenda yadamkawa itah sai khadijar sa”” tsayin lokutanda suka dauka labila tanashigowa khadija tacemasa zasufita
Yayimasu Allah yakiyaye tareda kafuzza masu dadi tanakashe wayar tadafe kirjinta labila tahauyimata dariya tace inafatardai bakimanta ko kalma dayaba
Harara takaimata taçe wlh kinbani aiki sahiba bakiji kunyarda najiba”” labila tazauna tana fuskantarta tace haba khadija mijinkinefa Wanda zaki aurah wllh ajiye kunya zakiyi agefe kirungumi mijinki idankuma bakiyiba kinaji kinaganie kunya tacutardake kinga tashi muje abarwannan darasin saigobe
Khadija tamike sukafita suncewa inna suntafi tayimasu adawo lafiya

Aisha✍🏼

[6:04PM, 3/9/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠

Chapter 79

      By

Gentle Lady💃🏽

Akwana atashi hasarar mai rai yaune ake daurah auren khadija”” kawu shine yazama waliyin khadija Dan muktar yace wlh bazasu je yola ba aibadole sai anje wajensa za aiwa kanwarsa aureba tundahar yace shibayada wadansu yaya tosuma sunmanta dashi kamar yanda yamanta dasu
Duk da bahakan kawu yasoba Amman yakyale babban masallacin jumua dayake kano bayan antashi sallar jumua akadaurah auren 

          *Usman Adam yunus* &

          *khadija Muhammad*

Akan sadaki dubu talatin kamardai yanda khadija tace akarba dan samun albarkar aure”” tunda aka daurah auren Usman yasomajin wani irin farinciki acikin ransa”” 
Waiyau khadija tazama mallakinsa Abdul saitsiya yakemasa danshima baya kasar yana minna dashi da iyalinsa acen yakoma dazama da iyalinsa bikinne yasa sukazo farincikinda Usman yakeciki bazai faduba mai karatu ka kwatantashi aranka”” Usman yanacikin dakakkiyar shadda fara saol tasha aikin wuta da babbar rigarsa”” takalmansa hularsa agogonda yake daure akan hannunsa komai iri dayane muktar ne tareda abokansa suka karasa sukabashi hannu sukagaisa sunatayashi murna 

Daurin aurensa yatara dubban jama a anci abinci tareda abubuwan sha kamar gabanza akesamosu naman kajikuwa kamar suyi magana
Anagama daurin aure suka kwasa da abokansa saigidan hajiya”” huuuu nikam naceyau nasan baza agane labila ba”” 
Da la asar za agudanarda walima makarantarsu khadija gidan hajiya yacika da yan uwa da abokan arxiki ko inakaduba mutanene gasunan kowa kaganshi yanacikin farinciki ” kubrah matazo tunjiya da faruq kubrah yayanta uku yanzu suma sungirma tubarkalla” 
Bari muleka gidan Amarya muganie tundaga zaure nasomajiyo kamshin turare dagaji kaima kasan hadaddiyar Amarya ce agidan waiwai masha Allah yanda naga khadija badan naganta tareda labila ba dabazan ganetaba” muktar kansa dayaganta bakinsa kinrufuwa yayi saboda ganin yanda kanwarsa takoma tamkar tauraruwa duk inda tawurga saimutane sunjuya”” tayi kyau matuka zanen lallinta yabada ma ana sosai gidayacika dayanbiki masu cinye shinkafar mutane😝
Hayaniya nasomaji awaje naduba naga kosuwaye mezanganiey:oops: taron yan group din Haneefa Usman ne wato zangon labarai”” su rabie da Aisha harture fateema Ali sukeyi saboda zumudi
Bayansukuma zugar su kausar luv” ne Jidda Aliyuu” Haneefa Usman” hafsat m Sharif” fateema zuhurah ” fateema Shuwa”rahmaluv” naanyluv” jameela muhd Ali” Shafa atu Umar maryam Lele Style”” Aisha iliya”” Anty Jidda billy baby”” ummu fauzan ” kaikai wadansu digaya Nagano sun lunka nafarkon danabiyu idan manatsaya rubuta sunansu aikuwa sai nacika safin harma inbude wani shafin🙄
Gefe guda nakoma nadauko wata takardar nasoma rubuta sunayen wadanda sukaje✍🏼 naany rabie Aisha sune nafarko sanann sauran sukabiyo baya saida nacika shafi bakwai najinjina wanann karartasu nalinke takarda Na ajeta dazaran munkai amarya zandankata gahannun lubabatu domin tayimasu kyauta maitsoka tukuicin murnarda suka tayata wacce bataji sunantaba kuma taje yawan people baisa nagantaba saitamun magana akwai sauran takarda daya😂😂
Gabadaya suncika gidan nikam nace anyakuwa wadan nan duk angayyacesu🤔 inajikamar akwai gayyar sodii labila tarasa inama zata sakasu danjin dadi takaisu babban falon gidan hajiya tajido masu abinci sukaita narkaa nikam koruwa banshaba!!😑
Baridai muleka bangaren Amarya” au sorry uwargida muga wainarda aketoyawa acen”” tunda nashigo unguwar najita tsit tamkar ba biki akeyiba nakarasa wajen maigadi domin yabudemun kofa yace alhaji Usman yace ko kuda sukazo kar abarsu sushiga harsai ankawo Amarya
Nayi murmushi nace kowayacemaka??? Yace ah kowafa nace kirashidai kaji nikam nasan bazai hanani shigaba idan baniba babu mai iyah dannar kirjin lubabatu babumusu yaciro waya zaikirashi Na kaikaici idonsa nakude gidan saidai yajuyo baiganniba “” tunda nashiga gidan naji shiru nace wayyo labila tayiwa makota bakinciki dayanzu sunanan sunadibar gara
Nayita kwada sallama najishiru nahaye harbangaren lubabatu tunkafin inturah kofa nakejin kukanta baki narike yaufa akeyinta uwargida nakuka
Kwance take kasa sairusar kukatake takeyi tun lokacinda Usman yashirya yacemata yatafiii tayi zaune tana kallon agogo tanata addua Allah yasama yayi hadari yamutu ubankowa yàhuta
Nikuwa nace cenkigani atukunyarki :?in Allah yaso qalau zaikai tunda taji biyu tabuga tasan andaurah aikuwa tafado kasan gado tayita rusar kuka gashi Usman yahana kawayenta shigowa dansaida sukazo maigadi yace babuwacce zatashiga
Saida suka kirah lubcy tazo dakanta yace ogane yabada wannan umurnin takirashi awaya yace shine yabayar dolensu suka koma tadau alwashin saitasa *hatsabibin boka* yayiwa wannan khadijar kisan gilla mutuwa mafi muni acikin kowacce kalar mutuwa 
Gawartama bataso asamu ballantana aimata sallah tundatake babu wacce tataba sakata adamuwa tazubarda hawayenta sama dawannan amaryar aibasaida tsafiba takissa kawaima saita fitarda itah kuma bazata huceba muddin khadija tana numfashi adoron kasa saitaga karshenta!!!
Nikam bakin kofa natsaya ganin har anyi la asar nasan yanzun haka antafi walimar sallah nagabatar sannan nawuce alokacin lubabatu barcin wahala yashureta””

Harabar babbar islamiyyar tacika makil abokan kasuwancin Usman dakuma yan uwansa tarin masoya dakuma makota tarin malaman makarantar dakuma manyan malamanda aka gayyata wajen ba masaukar tsintsiya bayan anbude taro da addua akakirah Amarya labilace tatake mata baya sanye take cikin atamfa mairatsin bakii daja sai babban hijab dinta harkasa tasaka safa hannu dakafa gakuma likaf babu hanya ko daya dayayi Saura ajikinta takarasa wajen malamin takarbi lasifikar tasoma karatu gabadaya wajen yayi shiru 
Usman baisan sanda yafurta Alhamdulillah har takare karatu takoma mazauninta Usman baisaniba saida babban malaminsu yafara wa azi akan zamantakewar aure
Aure rahamane ba karama bawani bangarene najin dadi rayuwa duk Wanda yatakashi yaji dadi sosai “” Allah ne yace ayi aure domin rahamace bakarama yayimana
Allah yanacewa 

 (فانكحو اماطاب لكم من النساء مثنى وثلاث ورباع فإن خفتم ألا تعدلوا فواحدة أوما ملكت أيمانكم)
Ku auri mataye wadanda aka halartamaku aurensu daga cikinku Ku auri biyu ko uku ko hudu idankuma kunsan bazaku iyah yin adalciba atsakaninsu toku auri daya ko abunda dayanku ya mallaka ma ana kuyanga suratul nisa i
domin aure yazama rahama agaremu Allah yacewa annabin rahama ” 
(ولقد أرسلنارسلا من قبلك وخعلنا له‍م أزواجا وذرية)

Mun aikoda manzanni gabaninka mukasanya mata dakuma zuria agaresu suratul ra adi
Aure wata bbbar rahamace dakuma jindadin rayuwa agaremu kamar yanda Allah yakece awata aya datake cikin suratul rum 
(ومن آياته أن خلق لكم من أنفسكم أزواجا لتسكنوا إليه‍اوجعل بينكم مودة ورحمة إن فى ذلك لآيات لقوم يتفكرون
Acikin wata aya anhalittamaku mata ku auresu domin kunatsu da itah matar kuma akasanya kauna dasoyaya atsakaninku dakuma rahama  
mace idan tayi aure alokacin tacika Rabin addininta sauran saitayi biyayya gamijinta yake wanann Amarya kisani aljannarki tana karkashin tafin mijinki nasihardà zanyimaki Anan shine ki kiyaye hakkokan mijinki idan kikaji ance hakki toyasafi komai dakomai abunda yarataya awuyanki ke Amarya  
Manzon Allah yanacewa awani hadisi” إذادعا الرجل إمرأته إلى فرشه فلم تاته لعنته‍ا الملاعكة

 حتى تصبح

Idan miji yakira matarsa zuwaga shinfidarsa idan batazoba “” mala”iku zasuyita la antarta hargari yawaye 
Tokunji mata dayawa yanzukuwa masu gudun mazajensu bazasuy kirguba”” 

Kiyiwa mijinki biyayyya duk abunda yasaki jikinki yanarawa kije kigabardashi cikin dadin rai”” 
Manzon Rahma yanacewa acikin wani hadisi لوكنت آمرا أحدا أن يسجد لأحد لأمرت المرأة أن تسجد لزوجها” رواه الترمذي”
Daza a umurci wani yayi sujada gawani lallai daza a umurci mace tayiwa mijinta sujada
Acikin wani hadisi manzon Allah yanacewa duk matarda tafita gidan mijinta batareda izinin mujintaba tanacikin tsinuwar Allah da la antarsa hartadawo gidanta kukama tanemi yafiyar mijinta ma ana tanemi gafararsa yayafemata
yake wanann Amarya nahoreki darike sirrin mijinki kisanI ke sitrace gamijinki baidace kibayyanawa wata sirrin mujinkiba koya kike da itah
Kikasance mai tattausan lafazi agareshi karkisake muryarki takere tashi awajen magana karkirika magana dashi kamarwani yaronki Dan asabe nafadamaka magi yakare babu daddawa gishirima sauran nagobe haba Yar uwa ahakañ tayakikeso kisamu rahama “” 
 kizama maikwalliya dakuma kyalkyali kullum aganki tsaf dakinkima yayita kamshii kizama maitsafta karkibar bakinki yanadoyi ansha miyar kuka tsami gaye Dan matsitsi dasauransu 
 Ba ahanaki cinkomaiba Amman dazaran kinci lokacinda zakije bangaren maigida saiki tsabtacesu karkijemasa baki yana hamami kamar shaddar Masai
Idankika gyara kekanki zakifijin dadi””kirika aske gashin gabanki dana hammata duk inda kikasan wata dauda zata makale kiwanke wlh wata saikuga gashin hammatarta kamar iccen kwakwa natabbàta wata kwararriyar maikitso zata iyah kitsashi har asamasa ribon
yake wannan amarya inahoronki dakarki sake kibudabaki kicewa mijinkii yasakeki!!
Manzon Allah yanacewa duk ranarda mata tacewa mijinta yasaketa batareda wañi daliliba Allah yaharamta mata jin kamshin aljanna aljannama bazataji kamshintàbà ballanta tasaran shigarta Allah yakiyashemu

Aisha✍🏼

[8:42PM, 3/9/2017] gentle lady💃🏽: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠

Chapter 80

      By

Gentle Lady💃🏽

 Karkisake kibar kawarki tazauna maki kangado ” gadonda mijinki yake kwanciya kuraya sunnar ma aiki wata shibgegiyar katuwa tadosana duwawunta inda yake kwanciya batako jinkunya”” inbanda lalacewar zamani mezaikaiki dakin kwanan kawarki??? Koda kinje wajenta kikwahe falo mana kofalon asamarwa maigida kujerah ta musamman ko yaranki karkibari surika zama akanta”” 
Haka kwanonda yakecin abinci kokuma cup dinda yakeshanruwa karkibari wata takafamiki baki inda yazamana mijinkima idan zaisha ruwa awajen zaikafa nasa yadace komai namijinki yazama dabanne danakowa
Yake wannan Amarya kisani tubalinki shine gidan mijinki yadace agareki duk inda kikaje karkisaki jiki awajen face kinadakin mijinki kiji aranki koda gidankune bazaki sakeba bisaga dakinki
Kizauna dayan uwansa lafiya dakuma makotanki idankinada abokiyar zama kidauketa tamkar Yar uwarki karkizama cikin sakarkarun matannan masu shegen kishin tsiya sudai bashason koya dagasu sai yayansu”” ramin kurah kenan
Idan kikace haka tokinyi kamaice ceniya da kurar kenan”” kirike abubuwa guda shida wadanda zanfadamaki
1 Ibada 

2 tsabta

3 iya magana

4 rike sirri

5 hakuri

6 iyah abinci
Dadai sauransu inhar kika rike wadan nan zakici ribar zaman aure anan zandakata dankuwa idan nace zanfadi fa idodan aure dakuma hakkokansa zamukwana muwuni banfadi ko kwataba inayiwa wannan Amarya da agonta fatan samun zaman lafiya dakuma zuriya dayiba ma assalam
Daganan yamikawa wani malami yatashi yasoma dajawabin godiya duk abunda zanfada malam yarigada ya fadeshi inarokon Allah yasa kowa yayi amfani da abunda yasaurara kuma yayi aiki dashi “” Ameen munayiwa dalibarmu kuma malamarmu fatan samun zaman lafiya dakuma kwanciyar hankali agidan mijinta Allah yasa ace kara da akayi Allah yakauda fitinardake tsakaninsu Allah kakore shaidan atsakaninsu Allah yabasu Yaya nagari ” 

Subhana kallahumma wabihamdika ash”hadu anla ilaha illah anta astagfiruka wa atubu ilaika
Daganan akabaiwa wani malamin yabude taro da addua”” akasoma raba takeaway”” kowa Yakama gabansa saifatan Allah yabasu zaman lafiya
Sunakomawa gida akasoma shirye shirye”” kai Amarya su gwaggo hasana suka haushirya Khadija tuni labila tagama shirya kayanta””” anagama sallar magrib akafito da itah muktar dakinsa yashige yanata kuka kamar karamin yaro
Hakan yakasa khadija tasoma kuka itama dakyar akafitarda itah gidan su inna masunkara datasu nasihar labila motarsu daya da khadija sukahau hanyar kaduna
Sai wajajen karfe takwas sukakai duk da gudunda sukeyi harcikin mota banda kuka babu abunda khadija takeyi har akakai gidan maidagi yahangame masu kofar gidan motoci sukafara shiga gabadaya saida harabar tacika labila tayimasu jagorah hawa nahudu gabaya ansauya tsarin bangaren komai sabo hul akazuba gashi wajen yasha fentii sai kyalli yakeyi”” Amarya tashiga dakafar dama tareda addua 
Bayan tazauna sannan akataso gabadaya zuwa bangaren lubabatu balaifi tayi wanka tashirya Amman dazaran kacika kallonta zakasan tasha kuka tun nan labila Tasha jinin jikinta
Dantunda sukashigo gidan tasan dadynta baibari akayi taroba sugwaggo hassana sukabata amanar Amarya Dan marainiyace takarba kuwa hannu biyu akaimasu nasiha daganan suka rankaya bangaren Amarya
Akasoma kallon dukiyarda aka narkamata kai abun saiwanda yaganie”” Usman baishigo gidanba sai wajen goma hawanabiyu yatsaya Dan nan yamaida kayansa yarage kayan jikinsa yawatsa ruwa yayi sallah yanamai nuna godiyarsa ga Allah dabaiwarda yayimasa
Ranar kwanan farinciki yayi washegari tundasafe lubabatu tasa akahadawa dangin Amarya abun karinsu saihada hadatake taware kamar ba itaba”” dangin khadija sunata yaba halayyar maman labila
Anan sukaci abincin rana sannan sukasake gyarawa Amarya bangarenta dazasu wuce sukasake yimata nasiha tanakuka sukarabu labila takoma rarrashi haka akawatse hardare khadija batasakeba
Suna zaune falonta bayan isha I”” Usman yaturo kofa yashigo da sallamarsa labila tagaidashi sannan tamike tabasu waje
Falon kasa tasauka takunna kallo tana zaune lubabatu tasauko sosai tayi mama kin ganinta danbatasan sanda tazo gidanba kokuwa tareda Amarya tazo oho
Labila tagaida itah ta amsa cikin sakin fuska tace yaushe kikazo??? Batareda takalletaba tace jiya aitare nazo dayan kawo Amarya
Lubabatu tagyada kai batasake cewa komaiba tamiyarda hankalinta wajen kallon
Usman ahankali yataka harsaman kujerah yazauna”” khadija gabanta yasoma dukan uku uku hannu yasaka yadago habarta saiyaga hawaye cikin muryansa maisanyi yace meyasaki kuka Deejarh na??? Kodai su inna ne dasuka tafi suka barki??? Kamar yace tasake fashewa dakukan yajawota jikinsa yasoma lallashinta haba Deejarh na kedaya kamata kiyi farinciki wannan baranar kukabace gidankifa kikazo karkimanta kinatareda annurin zuciyarki
Kukanki zaisakani adamuwa Dan Allah kidaina yimun asarar hawayenkin nan masu matukar tsada”” shiru tayi saidai tanajan ajiyar zuciya sannu sannu saboda kukanda tayi”” yace kokefa idankuma kikasake yin kuka nima zantayaki kintaba ganin kukan babban mutum??? Dariya tasoma tasake shigewa jikinsa tana girgiza kai”” shima dariyar yayi yace toyau zakiganie inhar nasakejin kukanki nima zanbude bakina harmakota sujiyo
Dariya takamayi tanaboye fuskarta cikin rigarsa murmushi yakeyi sosai yace kinci abinci kuwa??? Kai ta gyada yace banyardaba yanaji cikinki yadame??? Yayi maganar yanashafo Dan lafaffen cikinta
Tace wlh naci dasahiba kuma banajin yunwa”” yace kintabbata tasake gyada kai yace shikenan kitashi kishirya saiki kwanta kihuta nasan haryanzu gajiyar biki bata fita jikinkiba zanturo labilar saiku kwanta tare hamdala tayi acikin ranta tace to
Jayeta yayi daga jikinsa yadago dafuskarta yana kallo duk da tasaukarda kwayar idonta kasa cen kasan makoshi yace Deejarh Na kinyi matukar kyau jinakeyi kamar intasaki gaba inyita kallonki hargari yawaye. Bana gajiya dakallon kyakkyawar fuskarki
Idanuwanta talumshe dukkansu wani yanayi suka samu Kansu aciki Usman karamin bakinta kawai yaketa kallo sosai danbakinta yana burgeshi 
Baisan sanda yamanna labbansa akan nataba””” sosai kirjin khadija yacigaba da bugawa Amman batayi kokarin hanashiba Yajima sosai yana sunbatarta ganin yakusa rasa natsuwarsa yanashirin wuce gona da iri
Yabaiwa kansa hakuri saida ya tattaro sauran jarumtarsa sanann ya iyah raba kansa dajikinta mikewa yayi dasauri haryakai bakin kofa sanann yacemata saida safe dakyar muryansa takefita
Khadija batace komaiba haryabar dakin tadade zaune awajen sanann tamike tawuce dakin tasoma rage kayan jikinta tawatsa ruwa tadauro alwala tana fitowa tasamu labila hartayi shirin kwanciya darduma tashinfida suka soma karatu
Saiwajen daya saurah suka kwanta””” kowanne zuciyarsa fariii nikam nace banda mutum daya saida suka kwanta khadija tasoma tunanin abunda yafaru dazu wani nishadine taji yakamata filo tajawo takankame jitakeyi tamkar Usman ne aga banta bangaren Usman ma hakane danko abinci baiciba yadade yana tunani kafin barci yakwasheshi
Washe gari anayin asalatu Usman saida yafara tashinsu sannan yawuce masallaci dayan aikin gidan tunda sukai sallah basu komaba sukasoma karatu da azkar din safe
Saida haske yafito sukagyara dakin dakuma falon suka kunna turaren wuta nantake gidan yagameda kamshi””.

Sukai wanka sukazauna sunafirah Usman yashigo dakin””” 

Labila tagaidashi ya amsa cikin sakin fuska yatambayeta yasuka kwana tace lafiya qalau fita tayi tasauka kasa tasamu har lubabatu tagama hadawa kowa abunda zaici gefedaya tazauna bayan tagaisheta
Tacigaba dalatsa wayarta”” bayan fitar labila kusa da khadija yazauna tagaidashi ya amsa yacemata ya bakunta??? Tace babu hannuntà yariko yace tataso suci abinci bamusu tamike sukafito
Tunda sukasauko taga mom din labila tayisaurin cirehannunta jikin nashi shima baiyi kokarin hanataba sunakaiwa harkasa taduka tace mom inakwana
lubabatu ta amsa bayabo bafallasa

Lafiya kalau Amarya yakwanan bakunta??? Tace alhamdulillah Usman yajamata kujerah yanuna mata tazauna sannan shima yazauna lubabatu tazauna gefe sunsakashi tsakiya kenan sai lokacin labila tataso tazauna kusa da khadija tature nata gefe tasoma cin dankalin dakecikin farantin khadija suka kalli juna tasakarmata murmushi tace bisimillah
Usman baice komaiba sai lubabatu tace labila menene haka baganaki nanba yazakisaka mata hannu anata saikace warinki
Labila hannunta ta tsantsame acikin plate din tana kallon Usman tace dad inaji kamar bakasanarda mom yanake da wannanba??? Tayi nuni da khadijar batajira mezaiceba tacigaba
Tanamai kallonta mom wannan kawatace ko agida tare mukecin abinci anandinma tare zamuci inasonta fiye da kaina “” wlh koruwa banyarda sahibata tashaba saitaredani 
Idankuma ba za abari naci tareda itah ba to itama bazataciba saidai muje mugirka namu ta mike sahiba tashi muje”” khadija takalleta kamar zatayi kuka Sam bataji dadin abunda tayiba wannan yanuna tana zargin mamantane 
Usman ne yakalleta yace haba labila meyasa kikeyin haka??? Tace tomenayi dad daganafadi gaskiya nibana iyah cin komai saitareda itah
Yace shikenan zauna kuci yakalli lubabatu wacce tasaki bakii hangaga tana kallonta yace kiyi hakuri kibarsu surikaci tare”” tasaki murmushi bakomai dadyn Abdul nibandamuba abunda yasama nayi magana naga kamar baidace taci abinci da matar ubantaba bansan kawarta bane

Tunda hakan tafiso aishikenan nimeye nawà aciki

Aisha✍🏼

[4:37PM, 11/26/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳          61-62

DAGA TASKAR

Aeesha Ibraheem

Yakalleta yace toya karatu???? Talankwashe kai tace ya akai kasan daga skull nake??? Batareda yayi maganaba yanuna mata littafan hannunta tace au namanta dasu ai” tanisa aini wlh nasadakar bazansake ganinkaba yashafo kyakkyawan sajensa yace kinmanta danieko??? Tayi murmushin yake fuwail abune maiwahala in mantadakai saidai idan bana numfashi yatsareta damayun idanunsa yace haryanzu inanan acikin yayinuni da kirjinta tayi murmushi tace yauwa bakafadamun mekazoyi anan dinba kuma dubi shigarka damaganarka sak ta kado yayi shiru daga bisani yace mezaihana inbiyo farincikina aduk inda take takalleshi sukahada ido wani sihirtaccen kallo ya aikomata dashi wanda yasaka tayisaurin kauce idonta yacigaba wlh kyauta aduk indakike afadin duniyar nan zan iyah biyarki bana danasanin soyayyarki acikin zuciyata bansan yazanyiba Allah ne yadoramun sonki yanda bazan iyah fitardashiba kowanne safiya soyayyarki sake hauhawa takeyi acikin zuciyata “”” kalaman fuwail sunsaka zuciyar kyauta raunie dakuma matsanancin bugun zuciya tayi murmushi fuwail kenan duk yanda kakesona nima hakan nakesonka takalleshi amman ya akai kasan muna wannan garin yakalli gefensa ranarda kukabar rugarku nima washegari nafito nemanku danasamu labarin abunda akaimaku naje garuruwa kafin nakawo nan saigashi yaunayi gamda katar daruhina inafatar nazo asa a ??/ hmm ah zance dannajidadin ganinka da inafargabar nabarka bakasan halinda nakecikiba nimahaka ta sausau toda murya Amman munrigada mun makara “” yace bangane mun makaraba ??? Takalleshi damurmushi wanda kamar nadolene tace yausaura kwana biyar aurena ! Yace wat!! kyauta mekike nufiyanzu duk wahalar nemanki danayi yatashi abanza???? Tace hmm yazamuyi dama Allah yakaddara kaidin ba mujina bane???
A harzuke yakatseta yace karyane wlh babu wani mahaluki aduniyarnan dazaiyimun katanga da farincikina babuwani mutum adoron kasqrnan dazai aureki bayanni!!! Tace taya fuwail zaka aureni???? Yace kenan kinasonsa??? Babu anfanin cewa ah ko ah ah danbabu makawa sai anyi wannan auren kagakuwa babu halin nuna rashin sonsa hawayenda take buyewa suka saukomata tace fuwail narasaka rashinahar abada “” wani tukukin bakinciki yakeji azuciyarsa wanda maganarta jiyake kamar anayimasa feshin wuta yahurarda iska maizafi tabakinsa yace eeesha wani abutaji yaratsata duka jinin jikinta batareda takalleshiba yace bakirasaniba nima bazan rasakiba ketawace nikadai ‘Allah yahalittakine sabodani kadai “nikadai kedake babu wanda zairabani dake inba mutuwaba!! 

Tayi murmushi wai kanatunanin tatsuniya nake maka???/
Tunfarko kaine kaso hakan yafaru datun arugarmu munyi auren mu babuyanda banyi dakaiba katuro iyayenka Amman kaki babana da inna basutaba saninkaba haka zalika basu sankaba wannan kawai ya isah yanuna cewa bakasona dakana sona kamar yanda nakesonka nakejinka araina dabaka bari har hakan tafaruba tashare hawaye kasani bazantaba bijirewa iyayenaba nadade dasallamaka kuma ahankali zancireka shikin zushiyata kaima inaso kahakurah danie kasamu wata nasan bazakarasa samun wacce tafiniba “””” keee dakata kalamanki sunfara tsauri banajin zuciyata zatacigaba dasauraren kalamanki masu kamada tafasassshiyar ruwan dalma eeesha wlh bazan iyah hakurah dakeba har abada bakida wani mujin bayanni” tadaga masa hannu kalamanka sunfara yawa shinkataba ganin anyi neman aure akan aure???? Murya narawa yace Amman kyauta maleeek zakifadawa hakan baniba kasancewar narigashi fara soyayya dake shikanshi ganganci yayi ko ince iyayensa sukayi dazasu hadashi Neman aure danie
Mamaki kam yagama rufe kyauta yanda fuwail yake magana kamar wani zararre yakoma kamar mahaukaci sabon kamu” itah kanta yabata tausayi yanda duk yasusuce tashare kwalla tace zanwuce gida fuwail inamaka fatan alhairi taja ajiyar zuciya bazan taba mantawa da soyayyarkaba kuma zantayaka da addua Allah yabaka wacce tafi.. Eeeesha waime yasakikeson gasamun maganganune kimadaina bata bakinki bazaki aure shiba bakida wani miji bayanni yayi nuni dakirjinsa wlh karki kuskurah ki aureshi eesha 
Tadalla masa harara tace saikuma kayi tunda nalurah bakajin hakuri dankawai ina lallabaka shine kake wani tuburewa tokayi abunda zakayi Amman aure babu fashi danbazantaba cewa iyayena banason shiba taturah kofa dasauri tafita gabanta yayi mummunan faduwa ganinta wani guri maishegen kyau ga fulawowi nan gwanin ban sha awa itah daitasan tundasuka shiga motar abakin hanyane kuma bataga sunatafiyaba kodai saboda firgici da tashin hankalida tashigane takasa gane tafiya suke???? Tayi saurin yarda dahakan hakan yasatasamu damar daga kafa tasoma takawa yacigabanta please eesha karkitafi kibarni tarufe ido tace fuwail kabani hanya inwuce jinshiru yasatabude idonta tadorah akan fuskarsa wasu hawayene taga sunasaukowa akan kumatunsa 

Gentle ladyy馃拑馃徑

[11:08PM, 11/26/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

         63-64

DAGA TASKAR 

Aeesha Ibraheem

Ta kawarda fuskarta dankuwa tausayinsa baida wani alfanu saimadai tafama ciwondake cikin zuciyarta nasonshi tahakurah dashi dantasan yamata nisa bazata sameshiba yadawo gefenda take yace kitausayamun eesha karkibarni wlh zan iyahyin koma menene domin nasameki” tadafe kanta waikai ya kakeso inyi fuwail dame zanji da tawa damuwar kokuma dataka yazanyi duk fa wannan abun kaine kaso yafaru danhaka nikadaina batawakanka lokaci nima kana batamun nawa dan ba abune maiyuyuwaba dama inada kanwa sainabaka tobanada itah 
Tasausauto murya please kabani hanya zanwuce “” idanuwansa sunkada sunyi jajir kokadan bayaso yarasa eesha yakalleta da runannun idanuwansa yace eeesha wlh bazan iyah hakurah dakeba koda tasanadinki zanrasa raina bazan hakurah dakeba yaja iska duk hanyarda zanbi dannaga bakiyi auren nanba nabita hakan baisamuba to wlh muddin kika kuskurah kika aureshi sainarabaki dashi “” tajiyo afusace tace mezaka masa fuwail???? Kana nufin zakashiga tsakanina da farincikin mom??? shinee kawai danda suka haifa aduniya wlh zan iyah rasa nawa farincikin domin samuwar nasu kaine katsaya kallon ruwa kado yayi maka kafa tunfarko Kaine kaja wannan abun tacigaba da tafiya abunta yasake shangabanta yace eesha sabosamene zaki gujeni???? Kinkuwasan wanne irinso nake maki??? Cikin karaji tace bansaniba kuma banaso nasani waikai wanne irin mutum ne alokaci daya duk ka birkitamun lissafi bansan dawanne kalar yare zanfuskantar dakaiba yanda zakagamsu danhaka kabani hanya inwuce nalurah bakada lokaci tayi tsaki murmushi yayi maikamada ciwo yace Aisha inason kisani inasonki inasonki kuma banajin zandaina sonki hargobe inamai sanardake babu bil adaman daya isah yarabeki inkyaleshi tsabar kaduwa sukasata juyowa baki nasassarfa tace ban banganeba fuwail yace kwarai eesha ni bamutun bane!!! Tadafe bakinta da hannu indajikinta yafara rawa kamar mazari saura kadan tasaki fitsari awando tsabar rudanie baidamu da yanayinda take cikiga yacigaba nafara sonkine tun a rugarku ni dandan sarkine haka zalika nine babban dansa yanajidani sosai munkasance musulmai kuma babana bayason zalumci watarana nafito yawo shan iska da hadimaina nasameki saman wata yarbishiya kinje kiwo tundanake bantaba ganin halittarda taburgeni farat dayaba saike ” ko acikin jinsinmu bantaba ganin wacce takama kafarki dakyauba nantake naji soyayyarki takama zuciyata kuma nadaukarwa kaina alqawarin saina sameki banajin zan iyah barin wani ya aureki kullum wajen kiwonki shine mazaunina wajen san iskana inyi zaune inata kallonki anahaka nagakinfara soyayya da taneemu banajin zanbari wani ya aureki shiyasa nabi duk hanyarda zanbi dannaga narabaki dasu bayan nayihaka shine narikada zuwa suffar bil adama nakezuwa wajenki aduk lokacinda kikazo kiyo yayi shiru tayi kasake tana saurarenshi wasu hawaye masu zafi suka saukomata
Tace ashedama kai mashushine???? Azzalumiene maha inshi ahakan kakeshewa kana sona kana ikirarin kanasona tadalilinka ne ashe yan uwanmu suka koremu inatunanin inada MATSALA ashe dama KAINE MATSALATA!! wlh kashusheni bazan yafemakaba mugu azzalumi fuwail bazakayi kyakkyawan karsheba yanzu wannan kake kirah soyayya kukane yacikarfinta taduke inda take tana rera kuka

Kalaman kyauta saitafasa zuciyar fuwail suke kamar anadahuwar zuciyar yakeji Amman kukanta yafimasa ciwo akan abunda tafada mashi yatako inda take zaidafata tadago firgitattun idanuwanta dasuka rine tace karka kuskura katabanie natsaneka banason sake ganinka akusa danie wani irin gunji yayi Wanda gabadaya dajin yatsanza launi daga korayen fulawa zuwa bakake gabadaya annurin wajen yagushe furannin wajen suka fara zuba kamar kanyarda bazaki hawayenda suke fita ta idonsa sukakoma jinie baka ganin ko kwayar idonsa

 

Gentle ladyy馃拑馃徑

[12:17AM, 11/27/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

         65-66

DAGA TASKAR 

Aeesha Ibraheem

TSabar rudewa kyauta takasayin koda addua idanuwansa sukacigaba daruwan jinie yaduka saman guwanyunsa wlh eesha inasonki bansan yazan kamantamaki sonda nake makiba duk da tsoronda takeciki baihanata maganaba tace wlh bakasona fuwail haka ake soyayya???? Indai wannan abunda kamun shine so to Allah yawadaran wannan soyayyar dahar zakasaka masoyiyarka shikin tashin hankali ikirarin dakakeyi kanasona da bakasa ankoremu garin muba inda yake tushenmu shikin yan uwanmu kasa aka tsangameni akaguji babana da innana harnake tunanin nazame masu MATSALA!! Haihuwata dasukayi “Akayimana korar wulakanshi bamusan kowaba kayi tunanin wanne halizamu shiga???? Zamu rayu ??kobazamu rayuba?? taya zamu samu abunda zamushi gamu shikin jije duk wannan zaka kirah da soyayya?? Banbarkuba aranarda kukabar rugarku inatare daku duk lokacinda baba zainemi abincinda zakuci nakan rikida nafitomasa sainabashi farko nabashi wasu zomaye tareda hura dakuma ruwa dana kwatanci zasu kare batareda saninkuba nakansake zuba wani hakazalika bafulataninda yabaku nonon nagge nine nariiikida ” bukkar da kukashiga nina hakata danku zauna anan akullum inatareda Ku bantaba barinkuba inda banasonki mezaisa inyi haka kyauta???? Tayi shiru tacigaba dakukanta yace Kyauta banason kina kuka wlh kukanki tamkar anazubamun tafashashin ruwan dalma nakeji takalleshi tareda girgiza kanta fuwail ninasan kafi kowason kukana tunyaushe nake kuka kuma nasan harnakoma ga mahaliccina bazandaina wannan kukanba karigada kashutardani babuwani sauran darajarka a idona “” tamike tana karkabe jikinta kamaidani inda kadaukoni” yamarairaice haba eesha bazaki tausayamunba wlh inasonki nasan na aikata kuskure Amman natuba karkibarni “” takalleshi fuwail koda nayafema bazai alfanuba danbazan aurekaba !! Yace saboda menene menene banadashi eesha yanakallon kansa !! Tace saboda kai ba bil adama bane kagakuwa babu aure tsakanin aljani damutum “” yace mezaihana afara akanmu wlh nayi maki alkawarin zanzame miki rakumi Da akala zanzama tamkar bawanki kumazanci gaba darayuwa acikinku inbar jinsina indai kika amince zaki aureni” fuwaiiiil kanafadin abunda bamai wiyuwaba inakataba ganie toni gobena yazata kasance wadanne irin yaya zanhaifa???? Kaima kasan hakan cutarwane agareni
Kifadamun waime maleek yafini dashi Aisha ????? Wlh idan kika aureni har abada bazanbari kiyi kukaba zanrikida aduk wacce irin halitta kike sha awar ganina koda asuffar maleek ne dama wanda yafi maleek kiyarda muyi aure nayimaki alqawarin bazan rabaki da yan uwankiba da inason cutardake dana aureki batareda saninkiba zanyi tarayya dake amafarki harki haifamun yara Amman batahakan nakesoba shiyasa kojikinki banshigaba ” ranarda maleek yakure sanyin A.C harmurah taso kamaki nine nazo nakashe aranar naso hukuntashi bisa abunda yamaki Amman sanadin sonda mahaifiyarsa take nunamaki shiyasa nake dagamashi kafa ” Amman kisani muddin kika aureshi nikadai nasan mezanmashi yaja hannunta tana turjewa harwajen motar yasakata sannan yashiga kafin tabude baki tayi magana taganta akofar gidansu yabude yafito wasu kayane ajikinsa wadanda basune taganshi dazu dasuba yasaka bakin glass afuskarsa yanakallonta yace kije Amman inaso kisani karki. Kuskurah kifadawa wani labarin nan fadinsa tamkar kinyi sadaka daruhin Wanda kikafada wa dan aranar zaibakunci lahira barinsa acikin zuciyarki shine kintserarda duk wanda yaketare dake yadaga mata hannu nabarki lfy karkimanta aduk inda kike ni inatare dake INASONKI!!! Kiss yayi ahannunsa yahurah mata ta iska yashige mota bat yabace dashi damotar kamar walkiya ko alamarsa babu tatankwashe zaninta taturah get dagudu tafada cikin gidan security suna tambayarta lafiya Amman kotakansu batabiba tayi cikin gida gudu gudu tafada dakinta tarufe kofa ta dafe kirjinta zuciyart脿 sai halbawa take wanda tsabar bugawarta kamar tafaso kirjiin tafito anan taduke tacigaba da darzar kukanta kamar ranta zaifita “”
Aeesha banason kukan nan fa yanadagamun hankali kamar dagasama tajiyo muryansa hannutasaka tatoshe bakinta tareda mikewa tanakallon ko ina nacikin falon tanaja dabaya ko alamar akwai wani awajen babu batasakejin maganarsaba
Tayi dabas kamar wacce akayiwa gashin dankanoma sairabon idotake jikinta yana kakkarwa juwa taji tanadaukarta anan tasulale kasa warwasss

Gentle Ladyy馃拑馃徑

[7:07PM, 11/28/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

        67-68

DAGA TASKAR 

Aeesha Ibraheem

“”” Ruwa taji ana watsa mata tabuda ido bataga kowaba tashi tayi tanajada baya hartakai saman kujerah tazauna tanasaukarda ajiyar zuciya” shikenan dama duk abunda yakesamun samarinta aikin fuwail ne Amman yacuceta” kuka take marar sauti tasa gefen hannunta tashare hawayenta Allah kashiga tsakanina dawan nan bawan naka ”
Zaune take bakin ruwa tana latsa waya akalla tamanta rabonda tasamu maleek online kuma tasan baisake nomber ba kotakirah shikuma baya dauka ” tayi tsaki cencikin zuciyarta dad yacuceni wlh har inatunanin maleek zai aureni idan baisamu wacce zata aureshiba gashi duk yabatamun plan dina nasan yanzu bazaitaba aurenaba zaimace dahadin kaine akeson kashemasa mahaifi bayankuma nibanada masaniyar abunda dad yake aikatawaba ” ashe dama yaso auren mune akanwani banzan dalilinsa tasakeyin tsaki ” itah zaman sudan din ya isheta tagaji dayawon kasashe”yakamata takoma kasarta hakanan wayartace takatse mata tunani tadauko tareda dubawa ganin sunan teema yana yawo akan fuskar wayar tadauka hello teema “” daya bangaren aka karba zahra kenan ” manya nauyi nayita kiranki kwana biyu Amman baki dagaba kuma baki kiraba tayarfa hannu sorry teema ranar banason yin magana meyake faruwane???? Koda wata matsalane???? 

Ummm matsala babba kuwa zahra ” tayi tsaki indai bangaren gidan mune manta kawai danni banajin damuwa akansu ‘ teema tace kodaya yanzu mekikeyi???? Takai kallonta wajen wasu dasuke wanka tace inabakin ruwa aharabar hotel danake tace tokisamu waje kizauna” tace nidai kifadamun kwancema nake akan kujerah tanisa you saurah kwana biyar auren Abdul !!!! Zahra takunduma ashar tace wanne Abdul din badai nawabako???? Tace Abdulmaleek dai nakie konasan wani Abdul din bayanshi” tagirgizakai wlh bazai yiyuba kenan duk abunda nayi yatashi abanza kinsan makudan kudinda nakashe akansa????? Teema tace nasani zahra nikaina nashiga mamaki kuma naje wajenda kika rufe abun yana nan Amman nayi mamaki kuma wlh kullum saina gasa wannan hantar ” tace teema yanzu babu sauran lokaci bari inyanki ticket zanbiyo jirgin yamma sainazo batajirah me zataceba takashe wayar

Dayake tanada manyan mutane datake hulda dasu babata lokaci tasamu karfe 7:00pm jirginsu yadago daga kasar Sudan gabadaya hankalinta atashe yake ” ganitake tamkar jirgin baya gudu jitake kamar tayi tsuntsuwa
3:05am suka sauka awani hotel takwana danbatajin zata iyah karasawa gida “tunda safe takirah teema tace tasameta tagayamata hotel dinda take” ba ayi tsayin mintuna ashirinba takaraso bakin hotel din tasamu zahra suka karasa dakin saman kujerah tazube tana dafe kai kusa da itah teema tazauna tazuge jakarta tadauko invitation card din ta aje gabanta zahra takurawa sunan ido Aisha tacigaba da nanata sunan cikin ranta daga bisani takalli teema tace inafatar kinzo dashirinki???? Tace shirin menene tace zuwa wajen bokanki mana kinsan bazan iyah kara kwana batareda an gargada mun wannan tsinanniyar matarba nariga nadau alQawarin maleek bazai taba aureba kamar yanda nima bazai aureniba taya darana tsaka zansamu wannan labarin kema kinsan banga zamaba 
Wlh jiya kasa barci nayie nidai kitashi muje”” tadafata hakuri zakiyi kinsan ba azuwa wajensa sairana takusa faduwa kiyi hakuri bayanda zatayi dole tahakurah haka sukai zugum kowa da abunda yake sakawa aransa “tunkafin rana takusa faduwa suka fita dan zahra tamatsa suka kama hanya cikin motar teema sunyi daidai kuma suntaki sa a yanatsaka da aiki” yana ganinsu yakece da dariya yace shegu ba aganinku sai tabaciiii meyake tafedaku zahra tace boka aikina dakamun akan maleek kace bazaitaba aureba kuma bazaisamu maisonsaba gashi yanzu saurah kwana biyar aurensa yace karyaneeee  
Aljani Dan kuduki baya Karya hannu yanarawa tadauko katin tamika masa yaduba kwaryar tsafinsa yadauko maiwasu ruwa aciki yajefa katin yarufe ido yanawasu sambatuu yadau tsayin lokaci yabude idonsa yana girgiza kai yace aure babu makawa sai anyishi”” gaban zarah yabada rasss tace banganeba boka to akasheta kaw….wata mahaukaciyar kara sukaji wacce tasaka dabbobin dajin Neman gurin tsirah yace kirufamun asiri wlh wannan yarinyar tafi karfina aljanuna Kansu kinji kararda sukayi sanadin abunda kika furta babu wanda zai iyah maki aiki akanta 
Tace boka kataimaka mani konawane””””” yakatseta tashi tashi inbaso kike akasheniba dagani harke bazamu tsiraba jiki bakwari sukabaro dajin zahra tace bakisan wani gurinba muje naga wannan aikinsa dasanya ashema shi karamin bokane tunda akwai abunda zai gagareshi 
Teema tace akwai haka sukatafi Amman maganar dayace bazasu iyah yin aiki akantaba” shina maleek bazasu iyah yinkomai akansaba saida sukaje wajen malami da bokaye kusan goma duk maganar dayace karshe sukaje wajen wani malamin kallo daya yayi ma zahra yahade yawu bayan tagama korah masa jawabi yace takwantarda hankalinta za aimasu aikiiii Amman akwai wahala za akashe kudi sosai tace zata iyah tazube masa kudi rubutu yayimata yawanke yabata tashanye yabata wani danturare yace taturara idan zatakwanta sauran aiki tabar masa zahra tajisanyi aranta haka tazubemasa kudiii sukawuce sai murna suke hankali kwance sukadoshi hotel tadauki kayanta teema takaita gida 
“””””WACECE ZAHRA??????????

gentle ladyy馃拑馃徑

[9:26PM, 12/10/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

         69-70

DAGA TASKAR 

  Aeesha Ibraheem

zahra yace ga Alhaji jameelu kabakaa matarsa dayaaa hajiyaaa bintaaa aurene sukayi nayan boko saida sukasha soyayya tsayin shekaruu goma sannan sukayi ra ayin samun haihuwa tasamu cikin Amman kuwa tasa wahalaaa cikin yanashiga wata tara saida akamata aiki akafitoda tangageriyar yarinya kinkowa wanda yarasa saidai kash sanadin yawan magungunan datakesha sunbata mata mahaifa inda akace mahaifarta bazata iyah sake daukar wani danba koda nasatiii biyu 

 Hakan yamatukar tayarda hankalinsu bayan sati biyu da haihuwar akaradawa yasuna fateema zahra sunakiranta da Zarah sukadauki son duniya sukadora akantaaa basason duk wani abuda zaitabata ko tsawa basason yimata 

Tsakaninshi da Alhaji kabeer yan uwane danwa dadankanie suke Allah yayiwa iyayensu rasuwa su haipappun garin bauchi ne kasuwancine yadawo dasu kano dazama harsuka soma kasuwanciii
Alhaj kabeer mutum ne maifara a dakuma sanin yakamata hakan yasaka mutane sukesonsa saboda yanayin haba habadasu wannan yasaka kasuwancinsa yahabaka haryafara damawa da yansiyasa
Mutane sukadameshi akan yafito takarar gamna ajahar kano yanada magoyabaya sosai tun alokacin alhaji jameelu yafara yimasa hassada Amman aboye yakeyin abunshi cikin sirri batareda kowa yaganeba taredashi akeyin komai saidai yanayimasa zagon kasaa 
Ganin duk hanyarda yabullowa alhji kabeer maimakon kasuwancinsa dagirmansa yafadi saiyaga yasakeyin sama kunsan hassada gamairabo takiice
Tabangaren hajiyaaa bintama ahakan”” sunazuwa gidan alhajie kabeeer saboda samun shiga anan ne zahra tafara son maleek 
Gabadaya batada rayuwar hausawa duka dabiunta namutanen kudancine kaidakaga shigarta bazakace iyayenta suna dorah goshi akasaba 
Sannan baburuwanta dakana namiji koda abokintane zatakaimaka runguma itan adole aibawani abubane gaisuwacee
Sunyanke shawara da hajiya binta akan yanaso yahada auren zahra da maleek kodansu samu burinsu yacika alokacin zahra tanakasar rashaaa
da sukafadamata kudirinsu bakaramin dadi tajiba dama tadade tanajiran wannan ranar saidai sam itah din batasan kudirinsuba 
Cikin satiin tadawo Nigeria kullum tanagidansu maleek shikuwa dama dabiunta basui masaba sosai basa jituwa tunyana mata kara tadaina matsemasa haryafara fitowa filiyanuna mata yana kyamar halayenta wannan abun yabakanta ranta yanda yake yarfata har gaban abokansa ko kawayenta
Tasamu dad nata tasanar dashi itah dai ayi maganar auren dama yasamu Alhji kabeer yafadamashi yabashi yarsa wadansa yace tozai tuntubi maleek danshi bazaimasa doleba
Hakan kuwa akayi dayafadamasa baice komaiba hakan yasa alhj jameelu yakaimasu wata ziyara lokacin maleek yanagida yazo gaidashiii shine yake sanardashi yabashi kanwarsa duk da yafadama babansa Amman yaji shiru
Maleek yayi shiru baice komaiba dad nasa yace kayi magana nimafa danafada masa shiru yayi kamar haka 
Alhji jameelu yace son dina kayimagana mana kasandai bazamuso muyimaka doleba idan bakasonta aishikenan
Yanisa uncle Dan Allah kayi hakuri da abunda zanfada gaskiya halayyar zarah kwata kwata batamunba kuma kasan idan ba ajituwa aure bazai doreba da ayi auren nan kuma dagabaya asamu matsala nakegani barinsa yafi amfanie Amman kayi hakuri idan maganana bataimaka dadiba banfada danta sosa rankaba
Yayi murmushin yake ah haba bakomai son karkadamu “” aidama nadauka kanasontane aiyanzu andaina auren dole Allah gazaba mana abunda yafiii alhairi yace Ameen yamike yace kuhuta lafiyaa alhji jameelu yabishi da harara afakaice shege yabatamana tsariii duk dahakan aibazan rasa abunyiba 
Shirunsa yasa alhj kabeer yace kayi hakuri wlh kunya nakeji abunda yaron nan yayie yakirkiro murmushi karka damu Yaya aibakomai wlh banga laifinsaba gaskiyarsa yafada kasan yaran zamanie ba ayimasu dole idan basason Abu kaitsaye sukefadaaa 
Aransa kuwa shikadai yasan abunda yake sakawa aransaaaa baiwani jimaba yayimasa sallama yatafiii aranar yasanarda zahra kuka sosai tayi tace wlh bazata yardabaaaa itah shitakeso sosaiiii hajiyaaa tayita bata hakuri karshe takoma dakinta tarufe kanta babugunda basuyiba Amman taki budewa kuka take kamar ranta zaifita hardasu majina wayarta tadauko takirah kawarta suby tasanar da itah damuwarta
Tsaki tayi haba zahra dandanwannan zaki zubarda hawayenki kishirya gobe zamuje wajen bokaa aikece tuntuni kikayi sanyaaa 

Hakan kuwa akayi takaita wajen bokanta bayan sungama yimasa bayanie yace mekikeso ayimasa yanzu???? Tace sonake adasa masa soyayyata acikin zuciyarsa yajibayason kowa saini koda iyayensa 
Bokan yace ha ha haah yayi wani rubutu saman ruwan dasuke cikin kwarya yanawasu sambatu wani abo akawatsimasa wani haske yafittooo jikin ruwan yahaskaka waken dasauri yakare fuskarsa hasken yabace yakallesu yana sheshsheka kamar Wanda yayigudu yace wannan aikin bazai yuyuba 
Suby tace kamarya boka????? Yace meyasa kukeson kawo ma abota sallah da addu oi wajenmu wannan dakukeganie bayawada da addua abunda kukenema bazaku samuba kuma duk wanda yace zaiyimaku aiki akansa karya yakeyanasone kawai yayaudareki
Suby takalli zahra tace tokinjii “”tace naji idankuwa bazai aureniba saidai yamutu baiyi aureba kamaryanda itah ma tarasashi tolallai babuwacce zatasameshi!!!!!!

Gentle Lady馃拑馃徑

[12:09AM, 12/14/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

          71-72
DAGA TASKAR 

Aeesha Ibraheem

Babu yanda za ayi na iyah ganinshi dawata matar indai harbani bace “” Bokan yakecee dawata hatsabibiyar dariyaaa yace indai wannan ne zakisamuu “” zamu hanashi soyayya dakowa duk wacce yahango aransa yaji yanasonta zansaka aljanie kudugu yadinga binsa abaya darazan sunyi ido hudu dashi zataji batasonsa bama zata saurareshiba
Shikanshi zaiga takoma masa wata kalar halitta har abada maleek bazaiyi aure ba zahra murna fal ranta tazubeewa boka kudiii sukataso da itah da teema (sorry nadanyi mistake garin nasaka teema nace suby) duk dahakan batahakurah da maleek ba kullum tanazuwa gidansu hartakai yamareta wata rana itah kuma tayi ikirarin tunda bayasonta shima har abada bazaiyi aureba wanda har mom dinsa tajie
Lokacinda maleek yatafiii karo karatu itah ma tabar kasar alokacinne Alhji jameelu yaturah akashe Alhaji kabeer da matarsa ahanyarsu tazuwa super market sai kuma makasan sukai rashin sa a securityn dasuke kula da Alhaji kabeer suka biyosu abaya 
Tun alokacin basu sake dawowaba duk da anyi bincike Amman ba agano kosuwayeba saboda fuskokinsu arufe suke sunsaka abun rufe fuska 

Saikuma lokacinda suka kaimasa hariii ahanyarsa ta yola wannan kennan
CIGABAN LABARII
Yinin ranar kyauta sukuku tayinie babu tambayarda mom bataimataba ko akwai abunda yake damunta Amman tace bakomaiii “” zuwa yamma tacewa mom zatakoma gida kanta yanamata ciwo mom tabata maganie sannan tafito zuwa gida dasallama tashiga tasamu innah tana dama gunba tasha nono tana ganinta tace yauwa dama kamar kinsan ina nemanki”” saman kujerah tazube tace toganie innah “” tamikamata kwaryar hannunta ungu kishanye duka fuska tayakuna haini inna menene amfanin wannan abu dakuketa durawa mutum “” tace bansaniba kikarbaa kishaaa nashee tamika hannu tana kunkuni takafa kai tana yakunar fuska kamar maisan madaciii saida takusa rabii tamikawa innah tace ki aje anjima zanshanye wlh banajin dadi yanzuu
Maganinda mom tabata tasamu tasha sannan takwanta cikin falon bajimawa barci yayi awon gaba da itah “” washe gari tanakwance adaki inna tashigo ganin ta makarah batashiryaba tace hai kyauta bazakije makarantar bane??? 
Tadan muskutaa tace innah banajin karfin jikina saidai zuwa gobe”” tace Allah yasauwake taso kikarya “” tace to ganinan tafee “” Sam batakoson tashiii saida innah tagaji ta bawa muhd yakawo mata sama sama tasha tea din takoma takwantaa
Kwana biyu bataje skull ba saiga hafsat tazo gidan mom tafara zuwa inda tasamu yan biki dayawa dakyar tasamu ganin mom din tagaisheta ta amsa tace ya antyn ta tace tana lafiyaa 

Mom ina Amarya”” tayi murmushi tana gidan innah tun shekaranjiya data dawo makaranta narasa gane kanta saicemun tayi kanta yakeciwo kuma babu abunda akaimata makarantar??? 
Hafsat tace babu wlh momy nima hakan nayita tambayarta saidai tacemun bakomai tamike bari nakarasa wajenta mom tace toh idan kinje kice tabude wayarta yayanta yana nemantaa”” tace to momy taimata sallama tawuce
Hartakai gida tana tinanin meke damun aminiyar tata gashi ana bikinta Amman Sam bata gayyaci kowaba kodayake itah din batada abokai Amman aikoyayane yakamata Amarya tayiii tarooo
Da sallama tashiga gidan tsakar gida tasamu inna tanayankewa muhd kunba tana ganinta tasaki fara a wa alaikumus salam hafsat keshe tafee sannu sannu “” tace yauwa inna inawunie”” lafiiya qalau kinwuni lfy ya antynki tace qalau tana gaisheki “” kishe ina amsawa ina waleed danrakiyaa yaubakizo dashiba””
Ah wlh innah sunje islamiyyane nima kwana biyu banga kyautaba shine nabiyo sahuuu naji ko lafiya ranar koda mukarabu nalurah batacikin walwala.innah tace tana daki kwanshe aitun ranar hafsatuu kyauta batasake yin abun kirkiba kullum tanadaki kwanshe batashin komai sai babanta yamatsamata kuma munyi tambayarta damuwarta Amman takifadamana nashemata ko auren ne bataso kuma tashe ah ah 
Nidai al amarin kyauta yasoma banie tsoro idan akan matsalartane muma munakan addua”” Amman kishiga shiki tayuyu kaiyafadamaka damuwanshii
Hafsat tamike tace toh innah dakin kyauta tashiga tasameta Zaune saman kujerah tabuga uban tagumie Sam batasan dazuwan hafsat ba kusa da itah tazauna takurah mata ido zuwa wani lokaci tadan tabata akafada aikuwa kyauta tazaburaaa alamu sun nuna amatukar tsorace take tana ganin hafsat ce tasaukarda nannauyar ajiyar zuciya takoma tazauna “” tana fuskantarta tace kawataa yaushe kikashigo banjikiba
Hafsat yacire mayafiii tace inazakijinie kintsunduma wajen tunanin sahibinki waime kikeci nabaka nazuba saurah kwana uku fa kizama mallakinsa “” saida gaban kyauta yafadii tayi yake tace ya antyna dasu waleed??? Hafsat tace sunanan sunce saisun shigo biki” tadan mere baki tana kallon gefen tv tace kinje gidan mom bakisameniba ko”” 

Ah wlh kawata tagyara zama waimeyake damunki Aeesha ????
Takalleta mekikaganie ne hafsat??? Kokinga sauyi atare daninie??? Tace sauye sauyema eesha aibahaka kikeba wlh

Gentle ladyy 馃拑馃徑

[4:13PM, 12/14/2016] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

               73-74
       DAGA TASKAR

       Aeesha Ibraheem

Kwata kwata yanzu bakida walwala kodan bikinki yakaratone oho abunda akefada dai gaskiyane 

Kyauta takalleta tace kamar name kenan???? Hafsat tace da akecewa idan aure yagabato zakaga Amarya tanata ramewa kuma batacin abinci”” kyauta tamere bakiii waikina nufin auren zaihanani shin abinsine??? Tabdiii wlh bashibane””

Hafsat tace tomenene??? Kyauta tayi murmushi waike yar jaridashe bansaniba??? Hafsat takada idanunta tace kwarai niyar jaridace Amman awajenki””
Kyauta tace shikenan saikishi gaba da tambayarki Amman bazaki samu amsa kodayaba “” takatseta sabodame??? Tayarfa hannuwa shinwai karya kukeso infadane dake dasu innah kunrasa meyake damun mutum kudameshi da tambaya saikawai tafashe da kuka”” hafsat tayi sakako tanakallonta da mamaki saida tadau dogon lokaciii tana kuka tamatsa kusa da itah haba eeesha bawai munason takuraki akan abunda yake damunkiba kowa kikaga yadamu da damuwarki maisonkine danmuna sonkine mukadamu
Bawaidan musaka maki wata damuwarba idan bazaki sanar damuba saikice mutay脿ki da addua Amman kiyi kokari kisaki ranki ko iyayenki zasujiii sanyi tadago fuskarta tana sharemata hawaye “” kinga yi shiru inshaa Allah bazansake tambayarkiba
Mom tace kibude wayarki yaya zaikiraki awaya”” kanta tadafee saiyanzu tatuna aigaba daya kittafanta har wayar cikin motar fuwail tabarsu aranar”” 

Saida hafsat tace yadai kikadafe kai kociwo yake”” tace ah ah natuna wayana kwana biyu batada chajii”” taharareta haba eesha kuda kukeda wuta kullum sannan kuma ga gen kuma zakirasa chajiii tokidauko insaka makii tabude kafin yakirah””
Nanma taishiru saima tasake lafewa cikin kujerah hafsat tamike zuwa kuryan dakin tana neman wayar kyauta tabita da ido tana dariyaa dantasan babu wata wayama adakin
Hafsat ce tafito tanacewa kawai ganepa agida Amman mutum yayita barin wayarsa akashe takarasa wajen jonin tasakamata chajaa saida tabude sannan tabude mata wayar 
Karar budewar wayar kyauta taji tabude idonta dasauri lallaikuwa wayartace toyaushe tashigo da itah itah daitasan ko littafanta batabi takansuba ballatana waya kodai shine yakawo mataa tunda bataganinsa
Ajiyar zuciya tasauke mai nauyiii ” Allah yakare Abdul daga sharrrin wannan aljanie “” nibansan yazanyiba banaso mom tarasa dantaa akaina “” Sam tamanta suna tareda hafsat tasake fashewa da sabon kuka
Itah dai hafsat tazama mai lallashi duk yanda kyauta taso tasanarda itah data tunada gargadin fuwail saitatsuke bakintaa “”
Saikusan magrib hafsat tace itah daizata komaa saikuma gobe kyauta tadauko mayafiii tacewa inna zatarakata Innah tace to hafsat kigaishesu””tace zasujii innah 
Sunatafe sunadan taba firah yawancii duk hafsat kemagana kyautaa iyakarta ah “” ko ah ah saida tasamu abun hawa sannan sukai sallama tace tanagaida maman waleed sannan tajuya zuwa gida 
Tadan taba tafiya taji kamar mutum yanabinta abaya har yakawo daidai itah suka jera kamshin turarenshi yabugar mata hanciii sosai tarike zaninta zata yanka anakare yadanko hannunta kekibi ahankali bakyaganin ana kallonmu saida taji muryan maleek sannan tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciyaa shikuma wannan yaushe yadawo????? hannunta tafizge tamaka masa harara inaruwana da mutane shine zakawani rikemun hannu””yayi murmushi dannarike maki hannu shine me??? Kokindauka zanji wani abune “” ni tamkar Dan uwana namiji nake ganinki danhaka kibar yaudaran kanki waiko asan raina narikeki “” tamere bakiii kai akejiii”” bandamuba duk abunda zakafada Amman kasani dolene ka auri Dan uwan naka namiji ” tamurguda masa bakii ya cije kebensa nakasa kiyi abunki yarinyaa nakusa gyara maki zama “” “” tace kodai mugyarawa junaba “” idan kahangosu daga nesa kaika dauka firan arziki sukeyii  
Ganin sunkusa dagidan mom kyauta tasake sauriii tawuceshi yabita da harara aransa yace ballagaza kawai jibiwai tafiyar mace “” 
Rana dai bata karya ranar asabar dubban jama a suka shaida daurin auren Aeesha Abubakar& 

         Abdulmaleek kabeer
Akan sadaki dubu dari “” daurin aurenda akayishi a babban masallaci dakarfe 1:30 bayan an idarda sallah daurin aurenda yasamu halarta manyan mutane daga suwagabanni gwamnoni dakuma rikakkun yan siyasa ” ango yana sanye dafarin yadiii mai layi layiii kayan sunkarbeshi sosai komai nashi farine hatta agogon hannunsa mutane sai hannu suke bashiii suna gaisawa anayimasa fatan akhairii abokanan ango suma shigar fararen kaya sukayi sai tsiya sukemasa bakamar Usman mahaifin kyauta tamkar yazuba ruwa akasa yasha yakejiii yaudai burinsa yacika koyanzu yakwanta dama baidawani sauran damuwa yaga auren kyautaa
Kuma yau yasake yarda chanfiine kawai yarsa batada wata matsala dama wadanda suka mutu kwanasune yak are
Alhj kabeer shima bakinsa bairufuwa yau Allah yanuna masa yacika alqawarinda yadaukarwa kansa “” kowa awajen yana farinciki inkadebe fuwail Wanda yake tsaye agefe idanuwansa sunyi baki kirin bawanda yake kallo bayan maleek yanahuchi “” saikuma yabacee batt
Zaune take cikin dakinta tabuga tagumi tunjiya takecikin fargaba “” tanatsoron taji mummunan labariii yanzuma tanayi tanakallon agogo haskene yafara sauka cikin dakin take bangon dakin yadare fuwail yafito 
Ajikinta taji alamar shine tayi saurin daga kaiii tanaganinsa tajaa baya akan gadooo dasauri tadafe kanta dahannunwa zata kwamtsa ihu yacemata shiiiiiiit
Atake tadafe bakinta tana muzurai fitsari taji yana Neman gagarar mararta”” kallo dayatayiwa fuwail tadauke kanta Dan idanuwansa bazata juran kallonsuba 

Gentle ladyy馃拑馃徑

[1:56PM, 1/11/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

           75-76
      DAGA TASKAR 

    Aisha Ibraheem

Murmushi yasakar mata maikamada kuka yace eeshaa kinkine ko???? Kaitasoma girgizawa tace fuwail kaima kasan bazaitaba yiyuwa in aurekaba”””

         Yace karyane!!! Azafafe yayi maganar”” tayazakice bazai yiyuba wai laifina ne dana kasance cikin jinsin aljanu??? Kokuwa laifin zuciyatane datakamu dasonkii””

             Meyasa nibakyasona eesha menene banadashi wlh komeye kikeso ataredani zanzama ayanda kike ra ayina””

       Hawayen fuskarta tashare tana kallonsa tace kayi kuskure fuwail bazan taba auren kaba jinsina danaka badayaba kuma Allah dayahalishshemu akowane jinsi yayi mata damaza ashikin jinsinku akwai mata mezaisa bazaka auraba
       Katseta yayi azafafe yace kenakeso eesha kuma kisani bazan yarda narasakiba ketawace har abada wannan jikin naki nawane babu wani mahalukinda ya isah yarabeki muddin ina raye””

         Dasauri tamike tace karyane fuwail Allah bazaitaba baka sa ar shika kazamin burinkaba kuma nibataka bashe karka manta nazama mallakin wani 

      Ni ayanxu matar maleek ce!!! Yanda kirjinsa yaharba tamkar anbuga ganga”” tace kafita hanyana fuwail wlh natsaneka natsani ganin wannan mummunar fuskar taka bazantaba yafemakaba kashutarda rayuwata””
          Hannu yadagamata eesha kidaina ganin inamaki sanyi wlh sonda nakemaki yakawo hakan niko acikin jinsina banadaukar rainiii 

           Nasan kina nan kinatunanin mezaisamu mijinki yayi murmushi bazanyimasa komaiba saboda bakyasonsa shima bayasonki “” Amman kisani duk ranarda yafara sonki kokika fara sonsa” aranar zandau mummunan mataki nashi kuwa saiyafi nasauran muniee saboda yayi nasarar tsallake iyakarsa harya aureki”” hawayenda suke sauka idona yanzun najinine banason kigansu kunarda zuciyata takeyi harfeshin wuta takeyi saboda tsananin kishinki eesha kisani bazan taba daina sonkiba haka zalika bazan barkowa yarabekiba 
Yajuya kamar zaiwuce yatsaya inabaki shawara karki sake kibawa zuciyarki dama tafara son maleek yinhakan tamkar kinyankarwa maleek ticket ne na wahala yamurmusa idan kuma tsautsayi yasaka kikafadawa wani basainafada maki mezai sameshiba 
Yanakaiwa nan yayi bat yabace kyauta tadafe zuciyarta datake harbawa tamkar zatafaso kirjinta tafito la ilaha illah antassubhanaka inniku帽t脿 minazzalimin!”a uzu bikalimatull脿h tammat minsharri mahalakaa
Saiyanxu bakinta yafara addua”” tana karanto ayatul kursiyu”” Sam idan taga fuwail mantawa takeyi da addua kodai tsabar tsoronsa ne datakeyi oho
Sallamar hafsat taji atsakar gidan tayi kokarin saisaita natsuwarta bataso wani abun yasametaaa dantasan idan hartasameta cikin wannan yanayin zatashiga damuwa dole sai kyauta tafadamata abunda ke damunta
Dasauri tayi toilet din dakinta tawanke fuskarta saboda kukanda tayi “” hafsat tashigo dakin tana ina Amarya naji dakin tsit”” tafito cikin toilet din tareda murmushi wanda dazaran kaganshi kasan nadolene kamar antilasta mata yinsaa”” tace Kawata harkinshigo””???
Harara tamaka mata tace tokarnazo ke wlh yar iskace”” kallekifa kamar bayaune aurenkiba saikace wata guzuma
Aiko guzumar ranar aurenta takan Dan haskaka ammanke bakomai ba lalli bakitso”” tsaki kyauta tayi tace toshine me??? Idan banyi lallinba za afasa auren ne??? Koshimijin lallin zai aurah?? Kinga nifa auren nan wlh bayashiikin raina tamkar akaya hakan nakejina””

Tayi maganar tareda zubewa saman kujerah tazubeciki tana lumshe idonta
Hafsat tazauna kusada itah tacire gyalenta tadafata tace haba eesha meyasa zakifadi hakan??? Kinsan abban bazaiji dadin halanma kuma ai aikingama yagama tunda andaurah”” 
Tace tonikinji nashe wani abune??? Kawaidai shewa nayi banason auren kwalliyar mezanyi “” kinga abar wannan maganar ina maman waleed??? 

     Hafsat tanisa tace nakaita wajen mom ne yanzun nan zatashigo dama nasan haka zansameki shiyasa dashirina naxo wlh””
Kyauta tamurmusa tace shirin mene??? Baruwanki idan Anty tashigo zakigani”” tayimata kallon sama dakasa”” kyautaa takama dariya tace hafsat kenan saida kikasakani dariya dai dukda banasonyii
Guda sukajiiii anfara daga wajee”” kyauta takalli hafsat tace suwayekuma??? Tace taso kiganie”” taresuka fita”” takwalalo ido maman waleed”” murmushi tayi tasake rangada gudaaa “” inna ce taketa shimfidamasu abun zama”” tanayimasu maraba”” maman waleed tace kunga kanwar nan tawa”” inaso cikin awanni biyu karnaganetaa duk abunda kukasan anayiwa amare kuyimata kamshi kawai nakeso inga yanatashiii

Gentle Lady馃拑馃徑

[12:49AM, 1/13/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        77-78

 
DAGA TASKAR

  Aisha Ibraheem

Kyauta tabata fuska tace kai antyy “” nifa banajin dadin jikina”” harara takaimata tace hafsat “” tace na am Anty” tace dauko mata zani tadaura akan wadan nan kayan”” 
Tace to tanayiwa kyauta dariya tashiga dakin zani tadaukomata tadaurah duk badason rantaba jitakeyi kamartafasa ihu wannan auren Sam batasonsa”””

             Haka tazauna saida akafara dilketa sannan akazana mana lalli”” dan simple akaimata yafito dass akafantaa gwanin bansha” awa”” gashinta akatsefe kan”” aka wankeshi duk da batason kitso yanzu lokacin yakure dasai asakamata mai””
Haka akayarfa mata kitso abun saiwanda yaganie”” kunkuwa gantaa !! Nikaina dakyar na iyah ganetaaa”” karfee hudu angama komai”” maman waleed tace sutashi suyi sallah”” suma sukai sallah”” dakanta tahadama kyauta ruwan wanka sunsha kalolin tirare”” bayan tafuto wankan”” tazauna saman madubiii dama tareda maikwalliya suke” ” haka aka tsantsare amaryaa””

           Karfe biyar mom takirah tace ga motoci nan zuwa!” Gaban kyauta saidukan tara tara yakeyi”” wata hatsabibiyar rigace akasaka mataaa”” blue Amman mai haske sai net da akayanemata kaida shi haryasauko akan kafaduntaa
Sardar diamond ce awuyantaa sosai tazauna akan madaidaicin wuyanta sai karamin agogon hannu shima na diamond”” kananun yankunne sune manne akan kunnentaa”” salon kwalliyarta yatafi dayanayinta”” 

        Wasu shegun takalmane masu tsini akan kafartaa”” masha Allah kawai xance nikaina inataya fuwail kishi dannasan yana bakinciki ganin yanda kyautaa ta chanchade tamkar wata sarauniya””
Motarda sukazo haka suka gunduma suma duka sunsha ado”” basu zame ko inaba saigidan mom”” tunda akawuceda Amarya kowanne yadaga kaiyakalleta bayason dauke kansa daga kallontaa”” mom bakinta harkunne dantakasa korufeshi jitakeyi babu wanda yafi danta sa armata aduniyaa”””

              Tamarasa ta ina zatafaraa kudiii tabamasu gyaran dayawa duk danjindadin yanda suka gyaremata yartaa “” nikam inagidan kyautaa ashebuki yanagidan mom”” saiyanzu nakeganin jigajigan yan bikiii””””zuhurah nafara hangowa”” saiga haneefa Usman su kausar dama amarorine suna gaba gaba”” nayi mamaki dabanga jedda aliyu ba”” nasan idan hartasamu labari saitazo”” su ummukhady da maryaty”” sunsha ado buki nasu dankurah da sarkar kitsee”” sulfat nahango tasha ado nace umm cindango hardasu kaza kowanne su yaci abinci yayinakk barimma”” su oiii banfadi sunaba”” sukam su hafsat aisune amare””
Bangaren”” maleek kuwa”” yanacen Usman yasakashi gaba damitaa haba maleek katashi mana kasan dinner din nan karfe biyar ne gashi harbiyar tagotaa bakashiryaba”” 

Maleek wanda akeyiwa magana yana kishingide saman kujerah yana latsar waya tamkar badashima akeyiba”” wayar hannunsa yakwace yace wai wace uwar kakeyi cikin wayar kabarni sai haushinakeyi”” yanxun kanagani abdulkareem yakira nakidagawa nasan angama komai kukawai akejirah””

     Maleek yace wai usy dolene sainaje dinner din nan ??? Nifa nafadamaku banason yawan hayani”” yaharare shi kaji danrainin hankali malam kaga katashi ko wlh inkirah mom””
Mikewa yayi yayi mika tareda hamma”” yace to dangama fitina kaidai nalurah bakaso azauna lafiyaa”” inharbantashiba bazakabarni in sararaba”” yarike kugunsa waiku haka akeyi “”??? Kuncika tunbinku da abinci nikuma ko oho cikina saikugiii yakeyi”” 

Usman yayi dariya yace aikai baidacema kajiyunwa ayauba””kallon kasan ido yamasa yace danni bamutum banekome???? 
Usman yace banceba Amman murna aibazata barkama kacikomaiba”” baki yamere yayi hanyar toilet
Usman yabishi dakallo yana girgiza kai”” shikam baisan wani irin rayuwane da maleek ba”” yayi tsayin mintuna shabiyar sannan yafito saidai sukai dirama da Usman danshicewa yayi atafau bakayanda akabashi zaisakaba”” saida Usman yayi dagaske sannan”” yasaka”” koda sukafito biyar harda rabie”” gabadaya kowa yagama shiga motarsa””
Amarya da ango kawai akejirah”” motarda takegaba itace ta Amarya”” usman saida yasakashi sannan yazagaya mazaunin driver”” hafsat ce datawagar mom sukarako kyautaa”” kowa saibinta yakeyi dakallo”” usman neyafito dasauriii yabude mataa kofaa”” 
Hafsat tasakata ciki tanamata dariya”” tarufe kofar”” kusan tare suka kallijuna kowa yayi karamin tsakii yajuya kaigefe kamarwasu kadangaru””
Maleek aransa yace ammanfa tahadu yarinyar nan Amman bakin jijidakanta yayi yawa”” yamere baki””

Kyauta tace cikin zuciyarta ashehaka yakeda kyau”” bantaba luradashi ba saiyau”” shiyasa yakewani daukar kai danyasan yanada kyau
Tare suka juya suka kallijuna dankusan atare suke zancen zucin”” harara yaballamata itah ma tarama hardasu murgudar bakii””
Fuskarsa yasha mur kamar baitaba dariyaba yadauke kansa “” itah ma hakan”” kusan tare zukatansu sukace waimeyasa naso kara kallon fuskarta??? Itah mahakan taraya aranta

Gentle Lady!馃拑馃徑

[2:35PM, 1/14/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!.馃槳

          79-80

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Kowanne dauke kansa yayi tamkar yaga kashii”” har aka kai holl din da za agudanarda faten””motoci duka suka tsaya inda kowa yafara wucewa akabar sauran abaya wadanda zasu takewa Amarya da ango baya”” hafsat tabudewa kyauta kofa yayinda Usman yabudewa maleek”” 

             Tare suka jerah cikin taron”” inda salon kidan yasauya zuwa Amarya ta angoce”” taka ahankali Amarya yauranarkuce”” soyayya tanada dadi”” Amman aure zayafiii
 Amarya””
 taka takaa”” angonki naburgekiiii shima kina burgeshiii
Amarya daure dauree”” Abdul maleek angone”” Aisha amarya kenan shiyasa muke takawaaa

 

       Amarya murmusa bakiii angonki nagefenki kema kina gefensa”” yanayin yanda kidan yaketashi harcikin zuciyar mutum” hannu maleek yasaka yasagalo hannun kyautaa gabadaya dakin aka kaure datafiii yanayin rikonda yayimata harjikinsu yana zuzar najunaa”” kida yasake kaurewa inda masu video da pic sai wal wal suke sunadaukar Amarya da ango””
Kyauta tanason cire hannunta cikin nashi Amman nakasaa danrikonda yayimata banawasa bane”

Saida su hafsat suka rakasu har mazauninsu suka zauna”” haryanxun baisaki hannuntaba””
Gabantane tajiii yabadaaa rasss dasauri tadago idontaa basu sauka ako inaba saicikin kwayar idon fuwail”” !! Waitashin hankali sauran kadan kyauta tasaki fitsari itah kawai take iyah hango abunda tagani acikin kwayar idon fuwail”” towaishi menene matsalarsa””
Yanayin yanda yasake shan tokaaa yasa dasauri tace wash”” tareda dandukewa yanda tayi babu Wanda yajita sai maleek”” dukewarda tayi shine yaraba hannunta danashiii””
Kallon kasan ido yamata yace wannan bakauyiyar meyake damunta taduke”” yamere baki yadage kansa”” cen nesa dasu fuwail yatsaya yana kallonsu duk bidirinda akeyi kyauta kuwa hantarta harkadawa takeyi dazaran tadago taga yanakallonta 

  

Katon cake akagabato dashi maidauke da sunansu Abdul-maleek& Aisha” 
       Happy marriage

Damanyan haruffa anzagaye sunansu dakananun Zane nafulawa”” sai yar karamar wuka datake saman tiren”” 
Mai gaba tarwa ya amurci dasu mike domin yanka cake”‘ maleek ne yafara daukan wukar yayanko cake din yasakamata abaki”” 
Tsayin mintuna kafin tadibo danjikinta harrawa yakeyi”” saida hafsat tazungureta sannan tadibo”” hankalinta yanakan fuwail sauran kadan tadosanawa maleek cake cikin hanciii””
Sosai yalurah hankalinta yaba wajensa”” Amman yandatayi saikadauka masu daukan pic takekallo dansu haskata dakyau sai hakan yabada ma ana”” hannuwansa biyu yasaka yariko hannunta sai ayanxu hankalinta yadawo jikinta tajuya wajensa””” ido daya yakashemata sannan cikin shigar kwarewa yasaka cake din abakinsa yadan guzuraa”” tare da sakar mata wani lallausan murmushi
I idon mutane tamkar murmushin soyayya ne Amman itah wacce akaiwa tasan ma anar kallon cewa kadan kikaganie yasakar mata lallausan murmushi” cikin yake itah ma tamiyar masa”” akadaukesu photo”” kai wajefa saiyasake kaurewa da hayaniya” 
Ansoma cin abinciii inda kidakuma baidaina tashiba”” maleek sosai yamatsu abarwajen “” kiran Usman yayi yacemasa lokacin sallah yakusa danhaka tafiya zanyi””
Agurguje aka gama komai kowa yawatse “” kyauta tasake kallon inda fuwail yake bataganshiba tafara yan kalle kalle”” 

 Saida hafsat tazungureta tace lafiyarki wakike nema gashi har angonki yayi nisa””

      Tasaukarda ajiyar zuciya tace kyaleshi dama banason muje tare”” hafsat tarike baki tace umm lallai yarinya abunnaki dabanne”” tonikuwa bazanje dakeba dole kibishi aitare kukazo antyma zataimaki fada wlh””””” gabanmu motar ta tsaya”” yabude mana”” yace kushigo muje”” 

Zanshiga baya hafsat tabude kofar taturani gaba””” nashiga ina kunkuni””
Hafsat baya tashiga muka soma tafiyaa”” hafsat tace ango kaida kanka kaketukin motar??? Murmushi yayi yashafiii fuskarsa yace aganinki zan iyah bari wani yadauki abarda nafiso aduk fadin duniyar nan????
Hafsat tace wane kam bazaka bariba””” yasake murmusawa yace kokinga laifina hafsat danna daukotaa”” tayi dariya ina laifii maleek babuwani laifii aini kamaburgeni
Takasan ido yake kallon kyauta”” wacce tatsuramasa ido kirjinta na halbawa tabbas wannan fuwail ne ba maleek ba””
Kasa kasa tajiyace shinefa eeshaaa”” abunda kikamun kin kyautaa”” dagahaka baisake cewa komaiba harsuka kaigida”” 
Batayi niyar fitaba saida hafsat tafita sannan tajuya takalleshi Dan tabbatarda zarginta”” aikuwa tanajuyawa yadawo sak dinsa””” wani tsorone yasake kamataa”” dasaurii taturah kofa zatafita cikin sanyin murya yace eesha ninazama abungudu awajenki ko???? Waini menene laifina menayimaki wandayasaka kike kyamata”” kisanardani please!! Idan kina guduna gabadaya jinakeyi natsani kaina
Batareda takalleshiba tace saboda kanashiga huruminda banakaba”” nasankai musulmine idan adakanamun magana kaitsaye bakada zunubi toyanzukumafa??? 
Karkamanta nifa matar aurece””” bakada damarda zakamun magana”” murmushi yayi yace nasani eesha ammankisani soyayyarki tamantardani komai
Tundanake arayuwa bantaba saba umurnin mahaifinaba bana kuskure maganarsa”” Amman akan soyayyarki nasaba magaanarsa abunda bantaba tunanin faruwarsaba!!!
Tace wannankuma damuwarkashe danbani nasaka kakibin umurnin mahaifinkaba” ni inamazanganshi dasainafadamas脿 abunda kaimun”” danya yankemaka mummunan hukunshinda baitaba yankewa wani mahaluki irinsaba馃槒

Gentle Lady馃拑馃徑

[9:12PM, 1/14/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         81-82

      DAGA TASKAR 

      AISHA IBRAHEEM

Yakalleta da mamaki yace yanzu eesha zakiso ahukuntani???? Yayi maganar yana nuna kansa”” baijirah tace komaiba yacigaba atunanina soyayya bata zama kiyayya Amman saigashi yaunagani waini eesha kikecewa ahukunta””

          Murmushin gefen bakitayi tace kwarai soyayya takan rikide tazama kiyayya”” duk tarin sonda nakemaka shine yajuye zuwa kiyayya da tsana”” banajin akwai mata halitta aduniya danakejin natsaneta sama dakai din nan””” 
Wlh da inada yanda zanyi nahukuntaka tokasani dahannuna zanhukuntaka “””

       Yayi murmushi nibanga laifinaba maleek tafiyarsa yayi yabarki”” mutuncinki zairagu a idon mutane nikuwa bazanyarda dahakanba shiyasa nazodankawai nakore shakku a idon mutane cewar baya sonkii”” yanisa naji eesha kintsaneni nikuwa bantsanekiba Amman natsani duk wani namijinda yayi tarayya dake”” bazanji tausayin maleek ba kokadan muddin yakusantoki””” aranar zangama dashi”” banason wani yarabeki yinhakan babban laifine awajena””
Yana kaiwa nan motar tabude dama kamar akaya take tayisaurin”” fita hartayi zufa saboda tsoro”” ahakan kuma takegayamasa magana”” dantasan bazai iyah yimata komaiba tunda yanasontaa
Tafiya take tana waige”” karwani yagantaa sauran kadan su gaure da inna”” 

Tace kyauta lafiyarki??? Kikashigo gida kina waige””ta saukarda ajiyar zuciya bakomai innah”” ina hafsat???

Tana daki tanabawa muhd abinci danrigima yadameta dakuka abaki zatabashi””
Tanisa bari nayi sallah”” rigarta takwashe datake jaa tawuce falon””” hafsat tanaganinta tasoma dariya”” kyauta tasha toka lfy malama dagashigowana zakihauyimun dariya kamar kinga zararra
Hafsat tace”” aini dariya kukaban”” yaunefa ??zumudin mekukeyi??? Tundazu kinrikeshi nasan ko sallah baisamuba anacen anasoyewa”” ninasan yaubazaku ragawa junankuba””
Wani wawan tsaki kyautaa taja wanda dadukkan alamu maganar hafsat tabata haushiii”” ko kallonta batasakeyiba tawuce dakintaa””  
Tanashiga dakin tahaucire kayanta””tadaurah zanie”” asaman under alwala tadauro tayi sallah tana saman sallaya”” har akai isha i”” bayan tagama tatsaya addua”” hafsat ce taturo kofa tace saikitaso inji mom ta aiko kije”” innama tawuce tundazun”
Hararar ta tayi “” hafsat tasake darawa”” tace Amarya kenan”” ninasan tamatsu taganta kusa da maleek”” kyauta kala batacemataba”” tamike tagefenta taraba”” tawuce”””

              Hafsat tabi bayanta tana dariya”” toki tsayani muwuce”!” Tace innatsaki karkizo”馃檮”dannalurah haushi kike sake turamun””馃槦
Taresuka jerah”” tace haba Kawata wasafa”” nakeyin “” kinga muyi sauri tafiyaa zanyi wlh”” su anty harsun wuce”” takalleta ke hafsat kina nufin bazakiba???
Tace Abba yace babuwanda zaije kai Amarya”” angonki zaidaukeki kutafiii saidai idan ankwana biyu”” zanzocin kaza””
Kyauta tace mayyar kaza saikijirah kici taki badai tawasuba”” tarike bakii laaalaaa abun hargorine??? Nima ainakusa auren adainayimun gorin kazaa
Kyauta tace oho dai kafin kicidai narigakiii”” sukasa dariya daidai sunkawo gidan”” kyauta tarufe fuskarta”” sukawuce kayanda sukejikinta babuwanda zaice amaryace 
Gidan maduk anwatse Dan Alhji kabeer yace bamaizuwa kai Amarya”” tuni wadanda sukeso sunje tunda rana sunga”” daki”” saida hafsat tarakata harwajen mom sannan taimasu saida safee
Mom taso takwana nan tace ah ah tunda dare bairigada yayiba kara tawucegida!”” 

Haka mom tahadamata kayan kwalliya dakayan bukiii cikin jakunkunan bikinda akayi”” tabata tanata godiyaa””  

                    Sukai sallama tawuce”” mom dakanta tasake sawa kyauta tayiwanka tashiryata bayan tabata tsimin tashanye daragowar damammen ridii na nonon rakumie wandayajii kanunfarii da minan nass”””

     Saida tayi brush tasake gyaramata fuskarta””” wani rantsatstsen less tadaukomata dinkin yahadu sosai”” tashiryata tafesheta da turare”” addua tasoma yimata tana tofamata” sanna tadauko mayafiii tarufeta”” tariko hannunta tamike”” tace kitabbatar kafin kisaka kafarki agidan kinyi bisimillah kikaranta suratul ikhlas kafa uku “” da lakadja akum””” sau uku”” tagyadakai insha Allah
Tashafa kantaa Allah yamaki albarka Yakuma bakuzaman lfy dazuria dayibaa”” ahankali kyauta tace ameen sirarun hawaye suka saukomata馃槳

Gentle Lady馃拑馃徑

[2:09PM, 1/15/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         83-84

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Tariko hannunta suka fito falon inna tanadayan kujerah zaune muhd haryayi barcii”” sai Alhj kabeer da malam suna tattaunawa akan harkokin kasuwancii

     Daga kasa kuma maleek ne zaune yatankwashe kafafuwa

      Suna shiga da sallama tare suka amsa “” alhji kabeer yace to uwar diya tundazu kika tumemu anan munazaman jirah idan bakigaji daganintaba saiyabarmaki itah”” kowa azuciyarsa yace danaji dadie” mom tace kuyi hakurii natsaya shiryatane”” kusa da alhj tazaunarda kyauta kasa sannan takoma saman kujerarda innah take tazauna”” 
Alhji kabeer yace malam sai aimana addua”” Allah yakabe duk wata fitina dazata tunkaromu”” yabasu zaman lafiyaa
Malam yafara jero addu oi”” kowaya Shafa tareda furta Ameen”” daganan yafara yimasu nasiha akan zaman takewar aure””

       Bayan yagama alhj kabeer yafara magana yakirah sunan maleek ya amsa yanamai dago kansa”” yace kaidai bayaro bane dazan zauna ina jaddada maka girman rikon amana”” nasani gwargwadon haliii kasan komai toga amanar yata nan kuma kanwarka nadankata ahannunka””karnaji karnagani katakurah yarinyar nan wlh idan nasamu labarii sainayi mugun sabamaka”” kajiii nafadamaka “” 
Yakalli kyauta yace kekuma Aisha kiyita hakuri zaman aure danhakurine idan haryayimaki abunda bakyaso kikirani awaya kisanar dani nikadai nasan matakinda zandaukaa”” Allah yabaku zaman lafiyaa
Malam yayi murmushi yace wato itah baxakai mata fadan tabi mijintaba”” yakalleta tareda kiran sunanta”” ta amsa murya asake”” yace kinsandai wannan yayankine kuma mijinkine Aljannarki tana karkashin kafarsa”” idan kinbishi yadagemaki kishiga idankuma kikasaba masa kekanki kinsan makomarki

       Yinayi bari nabari”” karyasaki wani aiki kice baxakiyi”ba”kibarjin babanki yace kikawo kararsa”” muddin najihakan zansaba makii zaman aure kikaje ba wasaba kuma Ibadane 
Nasan sarai kinsan zamana da mamanki kosau daya bakitaba ganin tanadaga murya sama da tawaba”” danhaka kikiyaye”” fatana anan Allah yabaku hakurii dajuriya”” 
Suka amsa da Ameen” alhaji kabeer yakalli su mom yace kuyitaku ta iyaye”” mom tace aini nagama tawa banason kujiii dagani saiyata sukasa dariya tace saidai fatan Allah yabasu zaman lafiya
Innah kam murmushi kawaitayi da mom tace maman muhd kebaxakice komaiba”” yasake yin addua”” sannan Alhji kabeer yace yadauki matarsa yawuce”” aikuwa kyauta mezatayi inba kukaba”” tafada jikin mom tanata rusar kuka”” saida tajata gefe ta rarrasheta sannan tarakata harbakin motar maleek haryajima dashiga
Tabudemata kofa tashiga tacemasa kayi tafiya ahankali da yataa”” murmushi yayi yace nifa mom kina nunamun wariyar launin fata”” tace bawani wariya fadamaka dainayi asauka lafiya tarufemasu motar”” akawangale masu get sukafitaa
Tunda suka hau titi motar tayi tsit sai sautin kukan kyauta dayake tashi kadan kadan”” takasan ido yake kallonta yamere bakiii yacigaba da tukinsa””
Babban gidane asharada suke”” gidan hawa biyune””” tsarin gidan yaburgrni hon yafarayi maigadii yabude masu get yakutsa kan motarsa ciki gidan fayau yake saboda haske tamkar rana wajenda aka tanadar dan ajiye motoci yayi pkng din motarsa batareda yakalletaba yafito cikin motar kayansa yadauka yayi kofar shiga”” cikin sauriii tafita tabi bayanshi
Yamurda kofar yashiga bakin kofa tatsaya saida tagama adduo.in ta sannan tasaka kafardama tayi bisimillah”” masha Allah shine abunda bakinta yafurtaa katon falone kayancikinda pink ne hattama fulawoyinda sukayiwa falon ado”” fentiin falonma kasa pink sama milk”

         Gashi sumul sumul”” babban TV ne manne abangon falon saikaton agogo dagasama”” kai abundai saiwanda yaganie
Tasake karema falon kallo tana jinjina kai”” ko acikin mafarki bata taba mafarkin zatashigo irin wannan gidan ba”” saigashi yanzu tashigo kuma amatsayin matar gidan
Aranta tace shikuma wannan inayaje”” ko inane dakina?? Takai kallonta kanbene tamere baki”” kaitsaye dakindayake kasan tamurda key ido takwalalo”” ganin wani falon”” Dan madaidaici”” kujerun dakin ash color ne saikaramar TV bango 
Shima falon yahadu kujerun sunyi kupkup cikinsa saiwajencin abinci

Gentle Lady 馃拑馃徑

[11:13PM, 1/15/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

          85-86
DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

 Tasake karewa falon kallo tana jinjina kokarin mahaifinta” takarasa kuryar dakin”” shima kansa abun kallone yahadu iyah haduwa”” tasaukarda ajiyar zuciya aranta tace Allah yasa gidan zamane”” kayan jikinta tarage””” tashiga toilet din shima kanshi yahadu abundai saiwanda yaganie”” bayan tagama tadauro alwala”” 

              tashinfida sallaya tagabatarda sallah”” bayan ta idar tayi lazume tanakai kukanta wajen Allah daya kareta daga sharrin fuwail yakauda fitinarda kecikin auren su””

        Bayan tagama takashe wutar dakinta tahau gadon”” tajabargo tarufe jikintaa shiru tayi tana tunanin maganar innah””

           Kyauta kinsan meyasa nakiraki??? Kaita girgiza alamar ah ah”” tanisa tunda nakedake bantaba tsayawa doguwar magana dakeba”” inaso inja hankalinki kyauta nalurah dake sarai bakyason auren nan”” aganina shidayake namiji yahakurah ya aureki ammanke bakyako boyewa agaban kowa nunawa kikeyi bakyasonsa””

        Kisani kowanne bawa datasa kaddarar kidauka kema taki kaddararshe tazo dahakan”” koda bakyasonsa baidashe ki””na nunawaba kiga irin sonda””

         Mahaifiyarsa takenuna maki koshi bataso hakan”” aganinki zataji dadi idankina nuna bakyason jininta??? Karfa kimanta da halarshinda sukaimana”” nikaina nasan kyauta kinada matsala”” Amman mahaifin wannan yaron yashe zai auramaki yaronsa”” duk da labarinda akabashi akan”” abunda yakesamun samarinki””
Bayan wannan kuma yasaka anyi as’tihara akan aurenku anshe akwai fitinarda take tunkaroku”” kuma akwai hatsariii babba””Amman idan antsallake hatsarin akwai alkhairi maitarin yawa” malamin yashe ammanshi Sam baisan komene wannan rudaninba”” komadai menene yanatare dake”” 

              Danshi yaronsu nasa maisaukine asirine akaimasa “” Amman ba ajikinsa yakeba yanayin tasirine akan duk matarda yaganie yanasontaa””

        Kema dayana sonki datuni kunrabuu”” yace bazai iyah karyawaba danba ajinsa abun yakeba saidai adage da addua”” alhaji kabeer yace to maganar aurensufa??? Yanisa ah kamardai yanda nagayamaka zai iyah rasa ransa””Amman inhar akatsallake akwai nasaraa”” Amman abunda zaifi afasa wannan auren”” 
           ””Alhj kabeer yace ina ai wannan auren bazai fasuba”” malam dake gefensa”” tunda akafara magana baice komaiba”” yanisa yace Alhji kasaurari maganar nan idanbarinsa shine alkhairi kawai abarshi Allah yabashi wata”” alhji kabeer yace kanabani mamaki malam “” akwai wanda ya isah yakashewani inhar bakwanansane yakareba??? Yayi shiru”” yace tokasani muddin inaraye lallai kyauta batawani mijinda yawuce Abdul”” idan har lokacinsane yayi saimuyi masa addua Allah yajikanshi Dan babu wanda zaiwuce kwanansa”””
Malam yace gaskiya Alhj ina jinjinawa takawarka”” lallai hakanne”” nikaina nasan hakan saidai abunda naganine yatsoratani”” abunda za ayi saimudage da addua”” Allah ubangiji yakade duk wata fitina dazata taso anan gaba”””

                Alhj kabeer yace Ameen Ameen”” daganan sukai addua”” yabada kudin sadaka suka taso”” tanisa kinji yanda sukai Amman babansa yanashe dole sai anyi auren”” mamarsa ma dayafadamata hakan tashe”” toke aganinki wadanda suka yarda”” ki auri dansu dukda abunda ke tattare dake”” yadashe kigujesu????
Nidai inharzakiji maganana”” karnaji karnagani”” duk abunda zaimaki kidaure kiyi hakuriii hakika zakishi ribar hakurin anan gaba”” kowa dakike ganinsa hakuri yakeyi””
Kafin nahaifeki babu irin wulakanshi dashin kashinda yan uwan mahaifinki da matansu”” basuyimunba Amman naihakuri idan ma abunyadameni daki nakeshiga inyita kukana”” idan nagama nashare hawayena tamkar”” babu abundan yafaru”” tanisa”” yanzu bagashi nashi ribar hakurinba kalli irin gidan danakeshiki kalli kayanda nake sakawa”” bantaba tunanin zansakasuba””
Sukumafa sunaruga”” shikin jeji “” wlh kyauda inhar kinsan halarshi kodanaman jikinki zairika yankawa baidashe kidaga kankiba” 

      Tanisa innah inshaa Allah zankiyaye kuma bazantab脿 saba umurninsaba”” zanzama maibiyayya agareshi”” komene yasakani zanyi”” bazanbaku kunyaba in Allah yaso
Innah tayi murmushi Allah yamaki albarka”” kyauta ta amsada ameeen

Gentle Lady馃拑馃徑

[11:11AM, 1/17/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         87-88
   DAGA TASKAR 

     Aisha Ibraheem

 Tanisa”” daga dogon tunaninda tayi hakika tasan saitayi hakuri da matsalar maleek dantalurah sosai yatsaneta”” towaima itah menene laifinta””
Wata zuciya tacemata jininkune baihaduba”” tanisa duk dahakan nibazanki yimasa biyayya ba saidai banajin zansoshi dannima natsaneshi kamar yanda yatsaneni””馃槒
Tamurguda baki kamar maleek din yanagabantaa”” taja bargo tarufe kanta bayan tayi addua”” saibarci kobanza takwana biyu batasamu barciba saboda fargabar abunda zai iyah samun maleek gakuma gajiyar biki”” hakan yasa yautadan makarah sallah”” koda tatashi har haske yasoma fitowa”” bayan tagama sallah”” tana lazimi barciii yasake kwashetaa””
Yana dakinsa yana danne Danne”” ga laptop yanashigar da wasu kudiii a account dinsu”” cinikinda akayi wannan shekarar ansamu riba maitsoka”” yayi shiru ahakanma inaga sunbude companyn su dayake yola””gashi anandin basuda wadataccen madarar shanu”” Amman anasamun kasuwa sosai””” agogo yaduba ganin har tara tagota yakulle laptop din”” hamma yayi sannan yashafiii cikinsa alamar yunwa yakeji”” kaitsaye toilet yanufaa yawatsa ruwa”” 
Yashirya cikin kananun kaya”” wando ja yanada ratsin farii” sai riga karama maikaramin hannu”” yataje sumar kansa wacce takezuba sheki tamkar sumar. Macee,”” turare yadauko yafeshe jikinsa dashiii”” 

Kofar gidan yaji ana knock”” jin karar taki karewa yaja guntun tsakiii itah waccen metakeyi dabazataje tabudeba”” kafin yasauko saman bene yayi tsaki kusan uku””
         Ahasale yabude kofar atunaninsa yanbikine suka dako sammako”” saiyaga” drivern gidansu”” yasaki murmushi malam mudii Kaine??? Hannu yabashi suka gaisa””

            Yace”” Antashi lafiyaa””yashafo sumarsa qalau wlh””yace hajiyace ta aikoni”” yayi maganar yanamika masa kwandon abincin”” yakarba yace agaidasu sainashigo”” yajuya cikin gidan
      Saman dinner yadorah kwandon yayi hanyar dakintaa yaturah kofar da sallama kaitsaye kuryar dakin yashiga tanakwance haryanzu saman sallaya”” kyachchi “” yayi yajuya dasauriii kamar zaifadiii danyasan muguntarda zaiyimata
Ruwa yadauko cikin fridge yakoma dakin”” daidai kanta yatsaya”” yabude murfin robar yafara kwarara matasu ajiki”” cikin barcinta taji saukar ruwa ajikinta arazane tamike tana lahaula wala kuwati illah billah”” sosai tatsani ruwan sanyi yataba jikinta bamaruwaba ko Abu maisanyi batashaa””” hannu tasaka tashafo fuskarta”” sannan tamaida hankalinta gareshi danyanzu tagano komenene

       Shikuwa ko ajikinsa harwani shu umin murmushi yakeyi””ta bata fuska ya maleek menene haka ruwan sanyinefa kazubamun????
Yace aini bamakaho bane nafiki sanin ruwan sanyine”” Dan iskancii zakizo kikwanta anan anata buga gida kinasheka barcinki saida nasauko dakaina””
Tace Amman meyasa bazaka tasheni dahannuba saikazubamun ruwa kuma kasan saraibanason sanyi”” yamere baki ruwankii
Nidaruwan sanyi nagadamar tashinki”” aini baxanyarda jikina yataba wannan tsamurarren jikin nakibaa”” 
           Tanisa kar Allah yasa katabani damashen basonakeyiba nalurah dakai bakason azauna lfya”” dagazuwana jiyajiya kasoma tarbona damugunta nimafa na iyah kuma wlh sainarama takai maganar tana murgudamasa bakii””
Yace wakike yiwa gyatsine haka??? Ganin zaidankotaa tarugaaa bayan gadoo tace nifa badakai nakeyiba
           Han帽unsa yanacikin aljihun wandonsa yace saikifadamun dawakike bayan nidakene kawai acikin dakin””

          Tamarairaice fuskaa cikin shagwaba tace todakaina nake”” kukuma za ahanani yinmagana dakainane””” yanda tayi maganar yasobashi dariyaa saiyakanne yace dillah kitashi kiyi wankaaa yajuya yafita yana murmushi
Tace kai wannan anyi masifaffe ko inaruwansa dawankana”” inashiyayi bashikenanba”” kalin ashemutum yashika wanka yanabata ruwan gidan”””
Cikiinta ne yabada kululuuuuuu alamun yunwa” hamma tasomayi jere dajunaa kayanta tarage tadaurah towel tashiga toilet tayiwankaa tayi brush tadauro alwala”” 

       Gab脿n madubiii tatsaya tashafa mai”” maisanyin dadi dama itah ba ma abociyar son kwalliyabace”” powder kawai tasaka sai manbaki datashafa a lips nataa””
Drawer tabude tadauko wadu kayan riga da siket ne na atamfaa dinkin yamatukar matseta”” tsaki tayi”” wannan telan yacika Matsaala

Dukda takaimasa girman rigarta gashi wannan taimata kadan”””
Karamin hijab tadauko tasakaa tasake sabo cikinta “” barinaje konasamu abunda zancii tayi maganar tanasaka wasu takalma flat ne sunso suyikalar kayanta””
                  Kwandon kawai tasamu cikin falon””tanabudewa kamshin abincin yadaki hancinta kitchen tanufa tadauko plate da cup tadibi daidai Wanda take iyah cinyewa takoma daki abunta”” 
Saida tajitayi nak sannan ” nadauko wayanta tabuda tafara kiran innah suka gaisa”” tana nan kwance tajitashin motar sa”” baki kawai tamere takamo game tanabugawa

Zahra ce kwance cikin dakinta tunanin duniya duk yashamata kaitarasa abunda yake damunta wayarta tadauko takamo lambar teema”” kirah biyu sannan tadaukaa
Tace hlo zahra tace waiya maganar mune naga shiru haryanzu???

Gentle Lady馃拑馃徑

[9:51PM, 1/17/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         89-90

DAGA TASKAR 

Aisha Ibraheem

Kai zahra dadina dake zumudiii gani akan hanya nakusa zuwa”” tadanja karamin tsaki Dan Allah kiyi saurii wlh namatsu naje wajensa”” teemah tace banda abunki kinsan sai rana tayisanyi ake samun ganinsa danyana ganawa dabakinsa namusamman”” zahra tace nidai saikinzo banason yawan magana”” takashe wayarta tasakejan tsakiii tajefata gefe daya”” sake shigewa tayi cikin kujera”” tana hurah iska tabakintaa
Babu jimawa dagama wayar teema tashigo bako sallama”” tafada saman kujerah tarike kai”” zarah tatashi zaune tana kallonta tace lfy dai??? Guntun tsakii tayi wlh sai ahankali”” zahra kwata kwata kwanabiyu narasa meyake damuna””
Zahra tagyara zama tace”” kehaba??? Inadai fatar bacikine dakeba???? Gaba tabuga tace wacece Allah yakiyaye to idan nayiciki””wazance shine uban Dan??? 
Zahra tace oho maki nikam”inazan San iyah mazanda suke nemanki??? Amman gaskiya kiyi taka tsantsan”” dankuwa yinciki cikin wannan yanayin akwai matsala dama da aurenki dasaukii”” teema tace mantadawan nan maganar wlh banada komai kawaidai dadin jikinane banaji”” 
Zahra tace manta kawai mubar wannan maganar kinga ashirye nakekitashi muje

    Tace mom bata nan ne??? Baki tamere tace batanan jiya takoma Dubai kinsan zamanta agarin nan rabi darabine tafi zama acen””” 
Teema tace nikaina inaso muje ai”” dannafara ganin sanyi alamarina”” amman anya aikinsa yanayikuwa zahra nagafa Abdul yayi aure??? Jiyama yakwana da amaryarsa”” baki tatabe tace bandamuba indai naga malamin komai yayi daidai”” teemah hangaga take kallonta ganinma tamkar batadamuba””

        Tamike tadauko lemu taxuba tanasha tace”yanzudai kishirya muje naga alama amatsekike”” tayi murmushi nifa ashirye nake ke kawai nakejirah”” 

              Tamike tsaye tasagala jakartaa tayafa mayafinta tace muje dama key din motarta yana hannunta”” itah ma tamike suka fito motar zahra suka shigaa sai gidan malamin”” bakin kofar gidan sukayi pkng 

           Teema bakisake take kallon zahra ganin tadauko powder tana shafawa””” saida tagama tasake gyara yar girarta tashafa jambaki pink turare tadauko tahau fesawaa tasake gyara daurin dankwalintaa
Teema kuwa saibinta takeyi da kallo kamar wacce tawarke dagaciwon makantaa”” saida tagama sannan takalli teema tace mujeko”” bakisake tafita dantamarasa mezatace mataa
Sunyi sa a babuwasu mutane dayawa”” watace kawai aciki bayan tafito wata tashiga tafito sannan suka shiga

           Tundatashigo dama kamshinta yagama bade wajen”” tanashiga yahide wasu yawu yalaso labbansa”” kasa suka zube”” bayan sun gaisa”” idonsa yanakan zahra yana lasar baki kamar tsohon maye”” yace hajiya yanzu aketafene
     Teema tace ah wlh malam “” yajinjina kai yanakallon zahra yace to inafatar dai bukata tabiya??? Teema tayi charaf tace inafa aimalam jiya jiya akadaurah masa aure”” 
      Shine matamatsamun inrakota asake wani aikin”” yajinjina kai yace hajiya bakice komaiba””” shiru kakeji saida teema tazungureta tace uyum uyumm”” tanasosa kai kamar wacce taikarya”” 
Malam yasake murmushi yace kawarki tace aiki baiyiba”” tayi wani farida ido takashe murya wacce teema kanta batasan zahra damuryar ba tace rankayadede aini nabar waccen maganar”” 
        Tana wasa dayatsunta yasake laso labbansa yace banganeba kinhakurah dashikenan??? Tace ah rankayadede samnaji banasonsa”” ninama sake sheka menene amfanin sonwanda bayasonka”””
Kayataccen murmushi yasaki yashapo gemunsa yace to haka akayi”” tasake murmusawa “” yace toyanzu sabon kamun yakikeso aimasa???
Tadan dukadda kai tace bakomai dama zuwa kawai nayi ingaisheka”” yasaki murmushi yace ammankuwa najidadi”” teema daitakoma yarkallo saibinsu takeyi da kallo intakalli wannan takalli wannan””
Sukai shiruu saidai suka kurawa juna ido suna sakarwa juna murmushi”” 

         Tsayin mintuna sannan teema tace malam zamuyi magana dakawata minti biyu”” yace badamuwa hannunta tajawo suka koma waje”” sunafita tafige hannunta tace menene haka teema kinsan abunda kikayi kuwa???
      Ts脿ki tayi tace menayi zahra nalurah yaubakyacikin hayyacinki”” tundazamu shiga nalurah saiyan shafe shafe kikeyi kuma nalurah tundakika shiga saiwani kamekame kamar tsohuwarda tayi karya””
Tsaki taja toshine me??? Nifa bazan tsayamaki boye boyeba wlh sonshi nakeyi”” takai karshen maganar tanarike kugu tanakallonta
Teema tadaki kirji tace wakikeson??? Tace malam kaitsaye!” Teema tazaro ido tace wai malam taneemu??? Tace saikiyi shidindai shinakeso””
Teema tace Allah wadaran nakayalalace”” yanzu kirasa wanda zakice kinaso sai malam??? Duka samarinki zahra kallekifa kikalleshi tsaye dakyau zanne dakyau ko a maigadin gidanki yazauna aganina girma yafadi ballantana kicewai kinasonsa mekika rasa gaskiya dasake zahrah wannan bakyaciki帽 tunaninki

Tayishiru tana kallonta tace kingama???? Tonishinakeso baburuwana darashin kudinsa malam dinshiyamun dakikecewa duk samarina narasa wazanso saishi tonishinagani nakeso bawadancen tarkacenba””” kuma dakike maganar ko amaigadin gidana girma yafadi “” nibaburuwana yanadakudi kobayada banida damuwa kawai shinakeso bakudinsaba

Gentle Lady馃拑馃徑

[10:50PM, 1/17/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE馃槳

        91-92

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Teema tace zahra wai anya kankidaya kuwa??? Tace qalau nake teema kibarwani tunani konazauce 

     Teema tagirgiza kai tace bagaskiya bane zahra akwai abunda yataba kanki kokuma kinfara shaye shaye Amman bada hankalinkiba kicewai kinason wannan towaima kinsan komatansa nawa????

        Tace bandamuba koda matansa hamshin indai anayin hamsin dadaya tozan aureshi”” idankuma hudu yakedasu yasaki daya ya aureni””

      Teema tace to idankuma shidin bayasonki fa??? Wani bugun zuciya tajiiii tace daina fadar hakan teema wlh bakiji yanda najiba ai wlh koda zanyi yawo tsirara sainaga na mallakeshi
Kinkosan barcima bana iyah yi??? Duk nakwanta kwana mafarkinsa kawai nakeyi”” tunda nake arayuwa bantaba son wani mahaluki sama dashiba soyayyarsa harcikin bargon jikina nakejintaa

         Tanarike dabaki tace kenan bakyason Abdul??? Amman kikace kinasonsa sonda idan kikarasashi zaki iyah mutuwa???
Kidainamun maganarsa wlh natsaneshi niko sunansa banasonji mezanyi dashi??? Niyanzu nawuce ajinsa kuma banason kinasukar malam agabana banajin dadi
Teema tace naji Amman kisake tunani danwannan banga abunkaiwa gidaba”” “” kinga banason kina aibatashi jirani anan zamuyi magana Dan Allah “” teema tace afito lafiyaa kije kidawo danni bazanyarda dawan nan ba” kallon kasa dasama taimataa”” tace muje kijirani amota”” saida tasake pesa tirare tagyara mayafinta sannan akawuce ana karkada kamar wacce batason taka kasa””
    Teema tabita dakallo itah duk abunta yautaga wacce takusa wuceta”” tanashiga kaitsaye tawuce Dan babu kowa”” tashiga kanta yanakasa tasamu waje tazauna”” yana kallon nafulaninta yace hajiya harkungama maganar???
Tace ah wlh rankayadade tundazu tadameni dasurutu gashi nabarka kaikadai”” tayi maganar tana farfar da ido””” yalaso labbansa yace bakomai hajiya”” tace nidai kadainacemun hajiya kamar wata tsohuwa kakirani zahra mana”” 
            Yace hajiya ainariga danasaba”” sukai shiru natsayin lokutta shikuwa saibinta yakedakallo yana lasar labba”” centace malam wajenkafa nazo””” yawashe bakiii yana gyara zama yace Allah yasadai lafiyaa”” tayi shiru sannan tace kalau wlh najidai inason ganinkane”” yasake laso labbansa yace ko mushiga cikine??? Tace ah”” murya kasa kasa”” tashiyayi yanacigaba dalasar bakiii”” tamike yasakata gaba yadage labule saiga dakiii

Wajen shib shib shib baza acema akwai dakiba”” sukashiga katiface katuwa ashinfide”” sai toilet bakomai cikin dakin””
Yace tozauna hajiya””saman gadon taxauna shima yazauna yace hajiya aidakinbari anyi maki wani aikin akansa”” tace ah ah kabarshi wlh niyanzu banasonsa””
            Hannunta yakamo yace toyanzu yakikeso ayi???wani dadine yashiga jikinta Wanda tundatake bata tabajin irinshiba””” batace komaiba”” mikewa yayi yadauko wani tirare yafesa adakin”” yashafa wani ahannunsa
Cikin mintuna kadan sukazube akan katifar ranar kam yasamu abunda yadade yanahangen samu” yadade yanahangen kansa tareda maijikin yanhutu saigashi yaudai yakashe kwadayinsa
           Saida sukagama komai tadawo hayyacinta tatunada teema gashi harduhu yafara”” tamaida kayanta shima haka”” sukafito yana lasar baki yace yanxu saiyaushe???
Tayi fari da idotace kogobema kace indawo zandawo nisam banagajiya daganinka wlh”””yace shikenan kidawo goben”” tace to nagode rankayadade”” jakarta tazuge tazubemasa kudiii sannan tafita hartana waigensa tanacin tuntube
Yabita damayen kallo yana lasar”” baki”” wani sha awarta yakejiii gaskiya yadade baitara damace irin zahra ba komaitanada aidama daga ganin gabadabaya yasan saiyaja kayaaa yasake laso labbansa baisoma sukagamaba Amman bakomai gobe nanan”” yaumazaiyi aiki akantaa wanda zatajii tanamuguwar sha awarsa dama akwai wandayayi yanzu dazaikwanta da itah”” bazata iyah yinkwana ukubatareda takwanta dashiba”” aitariga tashigo hannu
Yakoma dakin yashiga wankaa” koda takarasa wajen mortar teema hartagaji dajirah tadan kishingida”” tabude murfin tashiga tanasaka sarkarta”” 

               Teema tanakallonta hartadaura dankwali takimtsa tatada motar sukahau hanyaa”” suntaba tafiya takalli teema tamaida hankalinta wajen tukinta tace nagasai kallonakike bakibude akwai tambayane kokina mamakine???
Teema tace hmmm dukabiyun kina nufin kanki kikabashi??? Tace kwarai”” aiba abun kunyabane”” teema tace hakane Amman meyasa bakisanardaniba????
Kallon samadakasa taimata tace”nakifadamaki kekikeda abun??? Ina ganaki nan ajikinki wannan nawane to shine Medannabawa wanda nakeso” 
Teema tace”” bakomaibane zahra Amman bakibawa kankishawarar kwaraiba”” zahra tace hmm wlh nikadai nasan abunda najiyau jinayitamkar bantaba dandana danamijiba saishi”” gaskiya malamin nan yayi nidanasan dashi aituni danadai帽a haukar banzaa

Gentle Lady馃拑馃徑

[7:41PM, 1/18/2017] gentle lady馃拑馃徑: *MATSALATACE!!*馃槳

         93-94

*DAGA TASKAR*

   Aisha Ibraheem

Teema tamere baki tace wlh zahra niharyanzu banyarda hankalinki dayaba”” tace shiikenan abar maganar tunda bakiyardaba”” dagahaka batasake cewa komaiba”” teema mahaka saidai tanakallonta jefi jefi ganin yanda takezuba murmushi tamkar baabu abunda yakedamunta aduniyaa”” zahra itah kadai tasan shaukinda take ciki jinta takeyi tamkar babuwani mahaluki aduniyar face itah dashi”” tanaji kamar zuciyarta zatafaso kirjinta tafado kasa””” saboda sonda takemasa”” 
           Harsuka kaigida babuwanda yasakeyiwa Dan uwansa magana”” tanayin pkng din motar tafito tayicikin gida”” tanawani juyiii tana talle”” teema tabita takallo tana girgiza kai batama shiga gidan ba tahau motar ta tabargidan da tunani barkatai akwakwalwartaa

Indatakeyin game barci yasureta ba itah tafarkaba sai karfe biyu”” dasauri tashiga toilet tawatsa ruwa tadauro alwala”””tatada sallah bayan ta idar tadanyi makeup dan simple”” doguwar riga tasaka tayadii dinkin yamatse dagasama yamaje daga kasa “” hijab tadauko tasaka tafita abincin taganie kuma ga alama nan andiba batareda tunanin komaiba tadibi nata takoma dakinta””
Batasake sakashi a idontaba tsayin kwana hudu”” sunan sunagida daya Amman sam komotsinsa bataji”” tana falon zaune takunne mbc2 tana kallon film yashigo gidan”” da sallama””” ta amsa sallamar tareda mikewa”” tace sannu dazuwa”” yauwa kawai yacemata yahaye sama””

       Bakinta tatabe nikuwa wannan haka halinsa yake”” takoma tacigaba da kallontaa”” tundaga ranar batasake ganinsaba”” saita danganta hakan darashin zamanta falon kasa””
Sati daya dabiikin mom ta aikomata dasauran kayantaa”” Sam zaman kadaicin yasomayimata yawa”” yaukam zata tambayeshi Monday zatakoma skull””
Karfe tara yadawo alokacin batayi barciba”” tana falon kasaa zaune”” yashigo gidan da abincin dare kusan kullum yanazuwa dashi Amman kyauta bataci dankafin yazo tadade dayin barcii idanma tajiyunwa narana takecinyewa””shiikanshi yayimamakin ganinta ido biyu saida yasake kallon agogo “”” 9;30pm tayimasa sannu dazuwa””yakarba fuska ba yabo bafallasa kwandon hannunsa takarba baimusaba yamikamata”” yawuce zatabishi yace ki aje anan zanyi wankane infito batareda tace komaiba takoma ta aje tanazaman jiransa

         Mintuna ashirin yasauko cikin kayan barcinsa”” kallodaya yamata yadauke kansa”” saman kujerah yazauna tamike tadaukomasa plate daruwa takawomasa””
           Zatadibamasa yace bayaso yakarba yazuba dakansa””” kasatakoma tazauna yafara cin abincinsa cikin natsuwa ahankali takalleshi”” idan baya magana saiyakara kyau ayanda yakecin abincin””” datalurah zaiganta saita sanne kanta'”

               Tasake dagokai sukahada ido”” yace yadai malama idan abincin kikeso kidibamana kintsaya kina kallona saina kware haba saikace mayya
Kunya taji tasanne kanta kasa””” yace ko akwai matsalane??? Kaitagyadamasa yace OK barinagama Amman kidaina kallona””

           Kyauta juyawa tayi tanakallon TV tabashi bayaa murmushi yayi kawai yacigaba daci帽 abincinsa
Saida yagama yakalleta”” yace to inajinki”” tanawasa dayatsunta tace dama dama nashe inaso monday zanfara zuwa skull shine nashebari infadamaka mamakine yakamashi ganin haryanzu batajuyoba chokalin yadauka yakwala mata aka”” tadafee kai taredacewa wash””” yace dan iskanci ahakan akakoyamaki magana danagaba dake??? Juyowa tayi tanashare hawaye tasake maimaitawa murmushin mugunta yayi yace kuka yanzukika fara badaikinzabi kiragemun jindadiba”” hmmm barganin nasauraramaki kwanabiyu
      Tayi shiru saida yayi danjim sannan yace banada damuwa dawannan danbani nasakakiba sannan daga gobe zakifara abinci danhaka kafin kifita kitabbatar kingama hadamun break “” motar dazanfita da itah kullum ke nakeson kiwankemun itah””
Karfe uku darabi zandawo kitabbatar nasamu abinci”” nadare karfe takwass baburuwana dakorafi kuma wlh idan baiyidadiba saina ballaki”” kuma banyarda kici komaiba banasoma wannan hannun nakiyataba””

     Yand脿 yakemaganar kamar Wanda yakeneman fada”” kuma fuskar nan atamke””

 

Kyauta mezatayi inba dariyaba tarikebaki tanadariya gahawaye afuskarta”” yasake shanmur ke mekika gani abundariya anan???saidatayi mai isarta tace maganarka mana ya maleek kashe abinshi yayidadi kuma karnashi”” to idan banshiba yaxanyi ingane yayi dadin””
        Tamike abinshi kanema za aimaka saida safe tawuce tana dariyaa yabita dakallo shima yana murmushi””” harmamakin kansa yakeyi sosai yayisanyi yanxu”” murmushi yasakeyi yami kezuwa sama
      Ranar Monday kyauta bayan tayisallah tanason tashi barci yadauketaa””” koda tafarka bakwai sauraa tadafe kirjintaa nashiga uku dasaurii tamike tasanyau Allah daizairabata dafitinar maleek
        Danjiyama saidayayi mita waibatagama dawuriba turus tatsaya tsakiyar falon jinkamshi yagama bade ko in脿”” ga abincinan anjere falon saikamshi yakeyii cikin tsoro tataka wajen dinner din tasoma budewa itah kanta saida tahade yawu wani kalar abincin Sam bata tabamaganin irinshiba 
Jiki asabule tarufe taleka kitchen anshareki chap anwanke komai ara帽t脿 tacekodai mom ta aiko da yar aikine???
Dasauri tafita waje motar tafara tozali da itah saisheki. Takeyi””” aranta tace kodai danrainin wayon nan yasauya shawarane barinaje dakinsa””
Saman tahauzuwa dakinsa dasallama ya amsa”” taturah kofar tashiga bayafalon tawuce dakin kwanansa yanatsaye daure da towel dasauri tarufe idonta tace yazakashe inshigo bay脿nk脿sa帽 babukaya ajikinka???
Bakiyatabe yace dama abunda kikeson ganikenan “” bayanzu dazanshiga wa帽ka kikafitaba”” meyasake dawo dake idanhar dama basonganin jikina kikeyiba”” 

       Tund脿y脿fara magana kyauta tasandare”” abunhaushi yab脿shi yace dillah dainakallon脿 haka mayya kawai”””
Tace gyaran dakinfa??? Wata harara yamaka matayace kekarkimaid脿帽i wani shashasha”” saunawa akegyaran daki agidanku bayanwa帽d脿 kikayi yanzu
馃槼Murya narawa tace wlh ba….baimabari takarasaba yakatsamata tsawa saida hant脿rta takada waike kidahumar inace??? Mazakibace mun dagani”””

 Aranta tacekodai danban gaida shibane馃???hartajuya tasake juyawa taduka kayihakuri mantawa nayi bangaishe kaba in脿kwa帽脿
Wani wawan'”tsaki”yaja Ya””’jefarda cum din afusace yakarasa ind脿t脿ke

 Kyauta tunita sadakar dukanta zaiyiii hannu帽t脿 yajadakarfiii yawucee tanabinsa kamarwanda yajawo akuyaa”””” yabude kofardakin yaturata waje

Gentle Lady馃拑馃徑

[11:48PM, 1/18/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE

       95-96

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Dayatsansa yanunata yace karnasake ganinki cikin dakina”” gyaran dakinma banaso haka kurum kina nema kisamu ciwon hauka”” yar kauye kawai”” yamaida kofa yarufe dakarfiii”” kyautaa saida hanjinta suka kada””” batasan sanda tafashe dakukaba ” tasan bakowaye yayi wannan aikinba sai fuwail metasa zaimata haka??? Kodai wani abun yayiwa maleek shisaya yaji haushintaa”” dakyar taja kafarta zuwa kasan”” tazauna saman kujerah tayi tagumie”” 
Waima mezaisa tadamu kanta danyanuna nayason taimasa gyarandaki ai harga Allah batada laifi tundashi yace bayaso”” tsaki taja””tamike zuwa dakintaa wanka tayi tahau shirin zuwa skull
Bayan takimtsa”” tadauki littafanta tafito kusan tare suka fito “” batare yakalletaba yayi hanyar waje”” cikin sauri tacemasa am bakaci abincinba”” yacemata banciii akufule”” yawuce dasauriii tabi bayanshi”” motarsa yashiga yatayar baibi takantaba yayi hon akabudemasa yafitaa””
Tsaye tayi sororo mewannan yakenufi saidai tahau adaidaita kome??? Wayarta takamo lambarsa”” saida tayi kirah biyu Rana katsewa baidaukaba sai ana ukun yadauka”” yace lfy??? Saita daburce tace dama dama zanshe”” banida kudin abun hawa??? 

           Yace kiduba saman dinner su nan Na ajemaki yakashe wayarsa”” tayi sororo tana kallon wayar daga karshe tajuya asanyaye takoma ciki tadauki kudin tafita da tunani barkatai arantaa “””
Tasoma tafiya tana waige abun hawa”” Sam bataji dadin wannan abunba kokadan”” motar maleek ce taga tasake dosowa aranta tace yauwa nasan yasake shawara”” saida yadanyi nisa yajuyo da motar yakawo daidai itah yatsayaa itah Kumar tayi kamar bataganshiba “” hon yamata tayibanza dashi””

          Adole tayi fushi”” da murmushi yakashe motar yafito yabude mata gaba yace muje kinkusa makara”” batareda takalleshi ba tace zanshiga adaidaita katafi kawai”” murya ya marairaice yace please kishiga kallifa babu abun hawa nankusa kuma 8 zakushiga saura 5mnt”!
Da mamaki takalleshi inayasan time dinda zasu shiga danko itah batasaniba”” saikuma takawarda tunanin kodai yaje skull dinne”” dahakan tashiga motar”” yakulle sannan yazaga mazauninsa yatada motar
      Tunda sukahau hanya batako kalli indayakeba”” shikuwa jefi jefi yana satar kallonta da murmushi kwance akan fuskarsa”” harsuka kai skull din hafsat tana tsaye itah ma lokacin tazo”” dan driver nta kotafiya baiyiba”” tana ganinta tafito tazo dafara a Amarya kinsha kamshii badai tarekike da angonba????
Kyauta tadanyi yake tace kinga mujeciki”” tayi maganar tanajan hannun hafsat”” tafige tace wlh baki isah ba saina gaisa dashi”” tsaki tayi saikije tawuce abunta bayan tamakawa maleek harara hafsat tace masa inakwana”” yace qalau yanafitowa cikin motar””yace yakaratun??? tace alhamdulillah barinawuce wajen sarauniyartaka akanhaka zata iyah fushidani 
Yace badamuwa hafsat sukai sallama tawuce dasauriii tasamu kyautaa”” tace haba eesha ba ayinhaka mijinkinefa??? Tace to shine me??? Nidai kidainamun maganarsa””” hafsat tajuya haryanzu baiwucebafa eesha keyake kallo”” saida tajuya tamere baki kawai”” yinin ranar tunanin maleek takeyi “” tana shakkun anyama shine??? Sambatajin yanayinda takeji idan taga maleek harsuka tashi hankalinta bayajikinta tun hafsat tanamata tsiya waikodai batagaji daci帽 amarcinbane”” kyauta takaimata dukan wasatace bangajiba tunda wani Abu akecinta cikinsa”” ni karama zamana agida dawan nan”” hafsat tace dillah banason karyaa ninasan kinsan komai zuwa yanzu maleek yamaidake cikakkiyar mace””” 
Kyauta tace waimeyasa bakyajin kunyar maganar nan??? Wlh inajima kamar Na nitsesaboda ku帽y脿”” hafsat tamike kingamuje yaudawuri nakeson komawa zanje saloon ne”” kyauta tamike tace Amman kikatsaya shegen surutu ninasan idris yadade dazuwama”” sukasoma tafiya”” hafsat tace banbaki labari ba wlh satin bikinki nahadu dawani guy”” kyauta tayimata kallon mamaki shine baki fadamunba hafsat tace shakurumi帽ki bangama yarda dashibane aidatuni nasanardake amman kinsan me???? Ah ah saikinfada”” hmmm sunans脿 Aliyu
Wlh eesha ina mutuwar son maisuna Aliyu tasanadin hakanma najiyadan kwantamun arai”” kyauta tace tabdiii zakiyifama”” ai inajin kinshe Aliyu naji haushi”” aidashi da ya maleek halinsu kusandaya damashima Aliyu akasamasa””
Hafsat takyalkyale da dariya tace kawaidai bakifahimci abunda basa sobane”” anacewa su帽脿da zuciya hmmm ammanfa sun iyah soyayya”” hardai maleek nakidakinganshi kinga Dan soyayya yanayin tsarinsa tamkar sharuchan”” kyauta tatabe baki tace ahakan???? Ai wannan yanda kik脿sa帽 dankali banatunani帽 yama iyah magana maisanyi””
Hafsat tace wlh ya isah barshidai nandakike ganinsa”” su rai nine basaso”” sunfison arikabasu girma kamar gyambo kuma sunason arika riritasu tamkar jinjiri””” analichinsu tamkar kwai”” wlh idanhar kikasiye zuciyar maleek eesha saikinji dadinsa sosai dannalurah dayanayinsa””” zuwayanzu Kawata yadace kizubarsa makamanki kirunguni mijinkiii

[1:31PM, 1/19/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE馃槳

       95-96

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Dayatsansa yanunata yace karnasake ganinki cikin dakina”” gyaran dakinma banaso haka kurum kina nema kisamun ciwon hauka”” yar kauye kawai”” yamaida kofa yarufe dakarfiii”” kyautaa saida hanjinta suka kada””” batasan sanda tafashe dakukaba ” tasan bakowaye yayi wannan aikinba sai fuwail meyasa zaimata haka??? Kodai wani abun yayiwa maleek shisaya yaji haushintaa”” dakyar taja kafarta zuwa kasan”” tazauna saman kujerah tayi tagumie”” 
Waima mezaisa tadamu kanta danyanuna nayason taimasa gyarandaki ai harga Allah batada laifi tundashi yace bayaso”” tsaki taja””tamike zuwa dakintaa wanka tayi tahau shirin zuwa skull
Bayan takimtsa”” tadauki littafanta tafito kusan tare suka fito “” batare yakalletaba yayi hanyar waje”” cikin sauri tacemasa am bakaci abincinba”” yacemata banciii akufule”” yawuce dasauriii tabi bayanshi”” motarsa yashiga yatayar baibi takantaba yayi hon akabudemasa yafitaa””
Tsaye tayi sororo mewannan yakenufi saidai tahau adaidaita kome??? Wayarta takamo lambarsa”” saida tayi kirah biyu tana katsewa baidaukaba sai ana ukun yadauka”” yace lfy??? Saita daburce tace dama dama zanshe”” banida kudin abun hawa??? 

           Yace kiduba saman dinner su nanan Na ajemaki yakashe wayarsa”” tayi sororo tana kallon wayar daga karshe tajuya asanyaye takoma ciki tadauki kudin tafita da tunani barkatai arantaa “””
Tasoma tafiya tana waige n abun hawa”” Sam bataji dadin wannan abunba kokadan”” motar maleek ce taga tasake dosowa aranta tace yauwa nasan yasake shawara”” saida yadanyi nisa yajuyo da motar yakawo daidai itah yatsayaa itah Kuma tayi kamar bataganshiba “” hon yamata tayibanza dashi””

          Adole tayi fushi”” da murmushi yakashe motar yafito yabude mata gaba yace muje kinkusa makara”” batareda takalleshi ba tace zanshiga adaidaita katafi kawai”” murya ya marairaice yace please kishiga kallifa babu abun hawa nankusa kuma 8 zakushiga saura 5mnt”!
Da mamaki takalleshi inayasan time dinda zasu shiga danko itah batasaniba”” saikuma takawarda tunanin kodai yaje skull dinne”” dahakan tashiga motar”” yakulle sannan yazaga mazauninsa yatada motar
      Tunda sukahau hanya batako kalli indayakeba”” shikuwa jefi jefi yana satar kallonta da murmushi kwance akan fuskarsa”” harsuka kai skull din hafsat tana tsaye itah ma lokacin tazo”” dan driver nta kotafiya baiyiba”” tana ganinta tafito tazo dafara a Amarya kinsha kamshii badai tarekike da angonba????
Kyauta tadanyi yake tace kinga mujeciki”” tayi maganar tanajan hannun hafsat”” tafige tace wlh baki isah ba saina gaisa dashi”” tsaki tayi saikije tawuce abunta bayan tamakawa maleek harara hafsat tace masa inakwana”” yace qalau yanafitowa cikin motar””yace yakaratun??? tace alhamdulillah barinawuce wajen sarauniyartaka akanhaka zata iyah fushidani 
Yace badamuwa hafsat sukai sallama tawuce dasauriii tasamu kyautaa”” tace haba eesha ba ayinhaka mijinkinefa??? Tace to shine me??? Nidai kidainamun maganarsa””” hafsat tajuya haryanzu baiwucebafa eesha keyake kallo”” saida tajuya tamere baki kawai”” yinin ranar tunanin maleek takeyi “” tana shakkun anyama shine??? Sambatajin yanayinda takeji idan taga maleek harsuka tashi hankalinta bayajikinta tun hafsat tanamata tsiya waikodai batagaji daci帽 amarcinbane”” kyauta takaimata dukan wasatace bangajiba tunda wani Abu akeshinta shikinsa”” ni karama zamana agida dawan nan”” hafsat tace dillah banason karyaa ninasan kinsan komai zuwa yanzu maleek yamaidake cikakkiyar mace””” 
Kyauta tace waimeyasa bakyajin kunyar maganar nan??? Wlh inajima kamar Na nitsesaboda ku帽y脿”” hafsat tamike kingamuje yaudawuri nakeson komawa zanje saloon ne”” kyauta tamike tace Amman kikatsaya shegen surutu ninasan idris yadade dazuwama”” sukasoma tafiya”” hafsat tace banbaki labari ba wlh satin bikinki nahadu dawani guy”” kyauta tayimata kallon mamaki shine baki fadamunba hafsat tace shakurumi帽ki bangama yarda dashibane aidatuni nasanardake amman kinsan me???? Ah ah saikinfada”” hmmm sunans脿 Aliyu
Wlh eesha ina mutuwar son maisuna Aliyu tasanadin hakanma najiyadan kwantamun arai”” kyauta tace tabdiii zakiyifama”” ai inajin kinshe Aliyu naji haushi”” aidashi da ya maleek halinsu kusandaya damashima Aliyu akasamasa””
Hafsat takyalkyale da dariya tace kawaidai bakifahimci abunda basa sobane”” anacewa su帽脿da zuciya hmmm ammanfa sun iyah soyayya”” hardai maleek nakidakinganshi kinga Dan soyayya yanayin tsarinsa tamkar sharuchan”” kyauta tatabe baki tace ahakan???? Ai wannan yanda kik脿sa帽 dankali banatunani帽 yama iyah magana maisanyi””
Hafsat tace wlh ya iyah barshidai nandakike ganinsa”” su rai nine basaso”” sunfison arikabasu girma kamar gyambo kuma sunason arika riritasu tamkar jinjiri””” analichinsu tamkar kwai”” wlh idanhar kikasiye zuciyar maleek eesha saikinji dadinsa sosai dannalurah dayanayinsa””” zuwayanzu Kawata yadace kizubarsa makamanki kirungumi mijinkiii
Kyauta tace todama wayashemaki yaki nakeyi dazakishe inzubarda makamaina””” mubar wannan maganar haka Hafsat”””

            Tace shikenan ambarta tunda bakyaso””” daidai sunkawo wajenda idris yakezuwa maleek mayana tsaye yajingina jikin motaa yarumgume hannuwansa”” akirjinsa hafsat tace Dan Allah kalleshi wlh nibantaba ganin hadadden guy irinsaba”” ga kyau ganatsuwa kyauta tace gakuma zuchiya kamar kuturu””” hafsat tasa dariyaa”” 
        Muje kifara wucewa”” kyauta tace ah ah ninafison ganin tafiyarki saboda tsaro”” Hafsat tamurmusa tace badaikiso nagayanda akesoyewa shikenan aikyabari mugaisako
Harara takaimata tace wacce irin gaisawar banda wacce kukai dasafe??? Nagafa kincika zakewa dayawa”” tayimata hararar wasa”” bakitarike tofa! Essha anaso anakaiwa kasuwa tace nadaiji muje”” saida tasakata mota sukagaisa da idris tayi tsaye saida tagasunwuce”” sannan tajuyaa taballamasa harara tawuce abuntaa
Motar yashiga dasauri yatari gabanta sannan yafito yatsaya gabantaa cikin masifa tasoma magana waikai wanne irin jahiline ??? Saunawa nake fada maka kadaina shiga harkata bakajie waishin dolene saikataimakeni??? Ko anfadamaka mijina yakasa danine tanunashi dayatsa banasonka fuwail kaimai sonkama shima banasonsa Allah yagaggauta daukarmun hakkina akanka kashiga rayuwata dayawa haba”” kukane yacikarfintaa”” fuwail tsaye yayi yanakallonta yayimamakin yanda take iyah ganeshi asuffar maleek
Baicekomaiba yajuya motarsa ransa abace””” yashiga yaja motar dakarfi yawuce

    tsayin mintuna sannan tasoma tafiyaa”””wani Dan adaidaita tatara akan hanyaa”” yace inaxuwa malama tace masa sharada yace tomuje

Gentle Lady馃拑馃徑

[9:14PM, 1/19/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        97-98

DAGA TASKAR 

Aisha Ibraheem

Tace to tareda shiga”” suka dau hanya”” harkofar gidan yakaitaa””” bayan tasauka”” taciro kudi zatamika masa murmushine kwance akan fuskarsa”” yatada abun hawansa yawuce”” tsaye take tamkar mutum mutumie”” tayane zata iyah banbance fuwail dasauran mutane wato dantace bazata shiga motarsaba yayi shigar mai adaidaita yazo”” tayi kwafa nasan yanda zanyi bazansake shiga adaidaitar da babu mutane ashikiba”” tawuce cikin gidan””” 

          Gidan tasameshi abude”” tanaturah kofar falon da sallama”” yana zaune saman kujerah “”” kallon sama dakasa taimasa”” tawuce abuntaa”” 
Tanacire kayan jikinta yashigo dakin””bes cekawai ajikintaa sai karamin wando wanda yadame mata ajiki yabifatar jikinta””” tana ganinsa takama neman abunda zatarufe jikinta dashi”””
            Batasamuba hijab tadauko takara ajikintaa”” idonta yanakasa”” maleek kam komai nasa yadaina aiki””” jiyakeyi gabadaya anciremasa lakkar jikinsa”” jiki asanyaye yajuya yabardakin””””

            Kaitsaye saman yahau”” yazauna saman kujerah”” yajingina dakansaa hannunsa yasaka yadafe Kansa”” shiru natsayin mintuna yalunshe idonsa eesha kawai yakeganiii
     Cen kasan makoshi yafurta ya salam!! Meyakeshirin faruwa dani??? Yashafo sumarsa”” iska ya furzar tabakinsa yasake mikewa key din motarsa kawai yadauka yafitaa
Tanafitowa wanka taji yafita da mota”” batawani damuba tacigaba da abunda takeyi”” bayan tayi sallah”” tashirya tafita zuwa kitchen saman dinner tasake ganin anshirya abincii”” hannunta tadafe dakantaa”” cikin daga murya tace fuwail wai menene haka??? Nafadamaka inaso karika yimun abincine??? Wannan abundakakeyi zaisa zargi yashiga tsakanina da mijina”” nasan kanajina wlh idan makanayine danka farantamun rai tokasani kana kara dasa tsanarkane ashikin zushiyana””
Nace banasonka kodolene??? Haba””” duk naganar nan datakeyi idonta arufe”” yake batabudeba” kuka takamayi mara sautiii tabude idonta”” haka ta hau daukar kayan abincin tazagaya baya duka tazubar”” sannan tadawo takunna gass tadorah abincin bamaiwuya tayiba jelof din taliyace taji kayanciki 
               Bayan tagama tadorah tuwon dare”” tazuba acikin kulaa takai saman dinner”” tazauna zaman jiranshi shiru shiru gashi yunwa takeji yanhanjintaa sai kuka sukeyi”” gajiya tayi dajirah tadibi nata tacii””
         Rayuwar auren eesha da maleek haka tacigaba babu ruwan wanidawani”” takanje gida “” wajen mom da innah”” taso inna tabata muhd tace ah ah ansakashi skull tabari saisun samu hutuu
                 Haryanzu babu abunda yakehadata da maleek saigaisuwa zuwa yanzu tasan takamu da soyayarsa”” takan tsinci kanta awani yanayi dakuma yawan faduwar gaba duk lokacinda taganshii
Saiyawan tunaninsa dayake addabarta””” Amman sambata nunawa saidai tashige daki taitakuka dantasan muddin fuwail yasan tafara son maleek zai iyah rabata dashi dafari Sam batadauka sonsa takeyiba”””

         Sairanarda hafsat tasanarda itah yandatakeji gameda Aliyu”” kyauta tayi shiru tana saurarenta dankuwa tanajin fiyedahakan akan maleek asheduk soyayyarda tayi ada shirmene”” danbatasan komaiba”” idan tasamu waje taishiru tana tunaninsa harwani nishadi takeji””” yanzu ko kallonsa batasonyi dantabbas idan haryaga kwayar idontaa zaigane sirrin zuciyartaa
      Tunda tafuskanci tafada soyayyarsa tadage dasallolin dare tanarokon Allah yaciremata sonshi”” Amman maimakon tajisauyi saitaji tasake dulmuya cikin sonsaa 
Wannan dalilinne yasaka yanzu tarage zamandakin”” falo take zama takunna kallo kotayi karatu Amman azahirin gaskiya bawaisu takeyiba tanason koganin tafiyarsane yanzun batabarci dawuri harsaiya dawo yaci abinci tanakallo tanasatar kallonsa”” 
Tana zargin zuciyarta akan rashin adalcin dataimata Amman takudura aranta baxata taba furtawaba saidai ciwon sonsa”” yazama ajalintaa
         San帽u kanhankali kyautaa tasoma ramewa saboda tunani”” sunazaune harabar skull dinsu hafsat takuramata ido ganin samhankalinta bayakan littafin dakehannunta”” gashidai shiitake kallo zakace karatu takeyi Amman azahirin gaskiya zuciyarta tunaninta duka sunawajen maleek hafsat tadafata tace waini eesha meyake damunki”””” murmushin yaketayi tace bakomai Kawata mekika ganie????
Hafsat tanisa tace wlh akwai abunda yakedamunki eesha badaikison kisanardani””” ailabarin zuciya atambayi fuska”” kinkuwa gayanda kika koma??? Kamar wacce tataso dagajinya 
Tasake murmusawa hafsat banada damuwar komai wlh””” saikuma tafara sharar hawaye””Hafsat tace mekuma yafaru Aisha”” tambayarda naimakine bakyaso ??? Kaitagirgiza 

Gentle Lady馃拑馃徑

[5:30PM, 1/20/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        99-100

  
DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Bahaka bane Hafsat agaskiya inashikin matsala”” inada damuwa araina”” hafsat tanisa tace mexaihana kisanardani eesha konasamu hanyarda zantaimaka maki??? Dasauri tadago tana kallonta tahau girgiza kai aranta tace taya zansanardake soyayyar maleek ce kedawainiya daruhina??? Furta hakan daidai yakeda nafansarda rayuwar maleek kenan dannasan fuwail yana taredani””” dasauri tace bazan iyah fadaba hafsat wannan *MATSALATACE* nikawai yakamata infuskansheta banaso kisaka kanki ashiki

         Hafsat tace aeesha matsalarki *matsalatace* banajin dadin wariyar dakike nunamun kina nuna kamarni bandamu da damuwarkiba””” kyauta tace bahaka bane hafsat nikawai nasan abunda kedamuna Amman bazan iyah fadaba”” hafsat tayidanjim tace tsakaninki da Abdul ne??? Kaita girgiza hafsat tace toko agidane?? Ko skull??? Nan madai kaitagirgiza “” hafsat tadan bata fuska ranta yasosu kwaraiii tace please eesha kisanardani koda bazan iyah yinkomaiba zantayaki da addua””
Tadago jajayen idanuwanta masu tsiyayarda kwallah tace kiyi hakuri idan harna sanardake wlh sanadin hakan zan iyahrasa raina”” hafsat takwalalo ido tace magana babba”” tashare hawaye inaso kawai kitayani da addua Allah ya yayemun damuwata” !!
Jiki asanyaye hafsat tace Ameen insha Allah bazandaina yimaki addua ba Allah yaciremaki damuwarda takerankii””” kyauta ta amsa da ameeen””” sukacigaba dakaratu”” 

Yaubabu skull yakasance weakened ne”” kyauta tayita sheka barcinta bayan tagama hadamasa break”” batasan fitarsaba danyau kantaa yanayimata ciwo baidawo cin abincin ranaba”” 

            Dadare””” bayan tagama hadamasa abincin dare tayiwanka tayi shirin kwanciya kayan barcine ajikinta saitasaka zumbule len hijab wanda yarufemata jikinta falon takoma takunna kallo tazauna jiranshi””

               Karfe tara yashigo gidan”” kamshin tirarenta yadaki hancinsa yalumshe idonsa yabude yasaukarda sanyayyar ajiyar zuciya”” muryanta maisanyice da dadin sauraro taratsa dodon kunnensa”” sannu dazuwa “” akasalance ya amsa yauwa”” yawuce sama dasaurii
                  Kyauta tabishi dakallo harcikin ranta batajin dadin rashin sakarmata fuska dabayayi yana nunahalin ko inkula da itah”” jiki asanyaye takoma saman kujerah tanajiranshi””””tasan wahalda kanta kawaitakeyi danbazai sotaba idankuma haryasota to fuwail zaikasheshi kanta tadafe wasu hawaye masuzafi sukafara sintiri akan fuskartaa Allah kakaremun maleek dina dagasharrrin wannan azzalumin aljanin
Tunda yashiga dakin yakasa yinkomai””” gawani abudayake tsargawa acikin jininsa”tundaga babban yatsansa hartsakiyar. Kansa”” mugunyar sha awar kyauta yakeji tana tasomasa”” idanuwansa yalumshe wadanda suka soma sauya launiii””” fridge yabude yadauki ruwa yasoma kwankwada””” saida yakusan shanyewa yafara zuba sauran akansa kosanyinsu bayajiiii saida yazubesu duka yawullarda gorar””” 
Yahurarda iska tabakinsa”” lebunsa yacijee yahaurage kayan jikinsa yashiga wankaa”” dakyar yagama wankan sakamakon ciwon cikinda yatasomasa tareda zazzabi mai nauyiii”” yanafitowa yazira jallabiyarsa””” 
Wajen karamar drawer yanufa inda maganinsa yake hannunsa yanarike da mararsa””” kafin yakai yafadi kasaa ciwonda baitabajin irinsaba”” kansa yaduke akasa”” dajan jiki yakai wajen yadafa drawer yamike tsaye”” yabudeta yadauko gorar maganin baisamu kodayaba”” shaf yamanta dayashanye ragowar””
Yaukam akwai matsala dole yakirah doctor yakawomasa maganie”” yalaluba wayarsa saman gadon batanan”” saiyanzu yatuna falo yazubarda kayanda yashigodasu
Yanadafe damararsa yayihanyar falon”” ruwanda yazubar”” dakuman santsin kafarsa hadida santsin tayil din sukadaukeshi yazame kasaa”” sosai yajizafiin faduwar yayunkur脿h yatashi Amman yakasa takeyasoma kyala amai tabaki tahanciii 
       Yanason kiran aeesha Amman yakasa cen cikin zuciyarsa kawai sun an yakefitaaa yamatukar galabaita tunyana yunkuri amai nazuba haryazube warwasss

Gentle Lady馃拑馃徑

[5:31PM, 1/20/2017] gentle lady馃拑馃徑: *MATSALATACE!!*馃槳

      *101-102*

*DAGA TASKAR*

 Aisha Ibraheem

 kyauta tanayi tanakallon agogo ganin hargoma darabi baisaukoba tadanja tsakii sosai taso “”ganinsa kafin takwanta hakan yakan danragemata radadin sonsa “” dakuma kewarta “” tasanyau bazatayi wani barcin maidadiba””” tamike tana kallon saman hawayene suka saukomata tashare “”” tawuce dakintaa”””
           Gabanta yasoma faduwa alwala tayi tadaurah zani akan kayan barcinta tashinfida sallaya tafara sallah”” raka a biyu tayi tafara jero addua”” jikinta sam yakiyimata dadi”” tamike tafito wajen “” bataganshiba”” aranta tace kodai yaci abinci gidan mom ne?? Ammankuma aibaya fashin cin abincina barinaje dainaji

           Tahaurah saman”” harzata turah kofaa tatuna da gargadinda yamata da kakkausar murya akan karyasake ganin jemammar kafarta tashigo dakinsaa”” jiki asanyaye tadauke hannunta dagajikin kofar””

       Harzata wuce watazuciya tace kitunafa kinada muradin ganinsa koda zaiyimaki fadane karkidamu dama burinki dai kiga fuskarsa danhaka kishiga kawai dawan nan tasamu karfin guiwar sake komawa bakin kofar tasoma kwankwasawa tana sallama “”
Tsayin mintuna biyar ko motsinsa batajiba”” kodai yayibarshine??? Anya bai isah yinbarshiba yanzun”” ahankali tasoma turah kofar cikin tsoron abunda zaimata idan tashiga 

         Takardunsa tafara cinkaro dasu nankasa azube sai kayansa sannan wayarsa duk akasaa”” jiki asabule tasoma sallama tanakarasawa cikin dakin””” karar zubar ruwa tajiyo”” aranta tace kenan wanka yakeyi”” sauran kadan tafadamasa taji kafarta tadan shuri wani Abu akasa”” cikin tsoro tajada bayaa tanakallon kasa hankalinta bakaramin tashiyayiba dataga maleek malemale cikin amai bayako motsii”””tafara jadabaya tana girgiza kaiii tasoma kukaa bakinta tadafee jikinta yasoma rawa shikenan yakasheshi abunda ta iyah furtawa kenan””” yazanyi da mom””????
Ahankali taji yanakiran sunantaa”””dasauri takarasa tazube wajen””” hannu tasaka tadago kansa tadorah akan cinyartaa”” Murya narawa tace ya maleek ya maleek””
Meyake damunka””” ahankali yacemata cikinaa””” ta share hawaye”” gefe takwantar dashi tafita dakin dasaurii”” zuwa dakinta zuma tadauko tareda ruwan zamzam”” tadawo dakin”” tadibo ruwa tawanke masa fuskarsa””” dabakinsa tazuba zumar akaramin kofii tace buda bakinka”” saida tataimaka masa tadago kansa tabashi zumar sannan tafasa ruwan zamzam din”” tazuba akofiii tayi addua”” sannan takafamasa abaki tace yayi bisimillah”” duka yashanye”” tashafa masa sauran afuskaa”””
Saman cinyarta tasake maidakansaa””” yalunshe idonsaa”” gashin kansa takeshafawa ahankali””” tanasake tofa masa addua””” 
        Duk adu arda tazobakinta saitayita sosai tanaganin kamar zatarasa shine”” dantasadakarda aikin fuwail ne” zazzabine yatasomasa ciwon cikin yalafa jikinsa yayi zafiii sosai dagashi tayi tace ya maleek bari kasauya kaya ingyara wajen saman gado yazauna tadaukomasa wata jallabiyar yasaka yakoma yakwanta ”’ wajen dayabata da amai tagyara tagogo”’tawanke rigar fita tayi tahadamasa coffee dantasan bazai iyah cin abinciba”””
Saman gadon tazauna tanakallonsa harya rame tamkar wanda yayi jinyar satiii biyu mugun tausayinsa yasake kamata wasu hawayen suka saukomataa ahankali tace ya maleek katashi kasha coffee tunda bazaka iyah shin abinshiba”” dakyar yabude idonsa”” yalumshe jikinsa tataba dasaurii tajaye hannunta danyayi zafiii raurau kamar wutaa”” cup din ta aje tasake fita ruwa tadibo tareda karamin towel”” tana tsomawa tana dannamasa ajikinsa ahankali” zafin jikinsa yaragu kwarai””” tataimaka masa yasha coffee din sannan yakwanta”” ahankali yace tarufeshi sanyiii
              Ganin yanda yake rawar sanyiii yadunkule wajedaya,”” takashe Ac din tadauko bargo tarufeshi”””” gefensa tazauna tana kallonsa””” ganin kamar yasamu barci yasa tamike”” zatawuce yace essshaa”yaune karo nafarko da maleek yakirah sunantaa”””saitaji kamar babuwa帽da ya iyah kiran sun脿n yayi sweet kamarshi ahankali tatako kusa dashiii hannunsa yasa yajawotaa saman gadon”””
Wani dumie yaji maidadi Wanda yafi bargonda yakeciki””” tana mutsunniya”” jikintaa yahau bariii”” hijabinta yadage yashige jikintaa””” kokarin mikewa takeyi taji muryansa cen kasan makoshi yace please eessha kitsaya ahakan”” babu yanda zatayi dankuwa batason musa masaa”””idanuwanta talumshe wasu hawayen suka sauko hakika tanason mijinta

Kuma tana kwadayin zamadashi”” Amman fuwail yahanata jindadin rayuwartaa inama babukomai tacigaba dafaranta masa kodashidin bayasontaaa
Hannunta dasuke dunkule acikinta ahankali tadagosu tazagaya dasu jikin maleeek kusan tare suka saukarda ajiyar zuciyaaa”””
Kowacce zuciya tajisanyi haduwarta da muradinta kyauta arantaa tana tausayin kantaaa gasoyayyar maleek da sha awarsa datake damuntaa gakuma tsoron mummunan hukuncinda fuwail zaidauka inhar yagano cewa tuni zuciyarta ta afka soyayyar maleek””
Ahankali yabude idonshi jin zazzabin yasaukaa”” yakurah mata ido”” sosai tarame ammankuma ramar saitayimata kyau”” fuskarta tayi haske eesha inasonki sosai sonda bantaba yiwa wataya aduniyaba inakema zakisoni duk danasan abune maiwahala kisoni dankintsanene Allah yajarabceni da sonki Wanda baida adadi””” tsiwarki da shariyarki tana burgeni”” Allah yakaremunke ma abociya murmushi”” 
Murmushi yayi yashafo gefen fuskartaa””” duk da bakyasona ahankali zankoyarda ke””””yalumshe idonsaa kyautaa ma babarci takeyiba taji yashafiii fuska ahankali tabude idontaa”” 
Saiyanzu takarema fuskarsa kallo”” gaskiya bakaramin kyakkyawa banee”” Dan madaidaicin karamin bakinsa tareda dogon hancinsa Wanda yasauko yakara kayata fuskar”” dabadan kartazake dayawaba datace kocikin India wa baza asamu Wanda yahadakomai nashiba”” sumar kansakuwa takwantaa lufluf da itah baki kirin saisheki takeyi”” saidan madaidaici karamin siririn sajensa”” wanda yasake fitoda kyansaa””
Kananun idanuwansaa tamkar Wanda yakejin barcii sexy eyes”” idan yana magana suna lumshewa kaizakayi zaton tsabar iyayine. Idan yana fadama duk yanda yakebudesu adole gamai manyan ido Amman sambasa budewar”” anacewa idan kacika kallon mutum tozakagano muninsa脿 Amman sam niban gakomaiba sai tsantsar kyau
Allah yasa ya maleek zaisoniii talunshe idontaa tuni tama manta dawani fuwail dakuma mummunan kudurinsa nakashe maleek duk ranarda yafara sontaaa”””
Tomezaifaru idan maleek yafurtawa kyautaa cewar yanasonta??????? Togamudai ganiii馃檮馃檮

Gentle Lady馃拑馃徑

[8:33PM, 1/20/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        103-104

DAGA TASKAR 

Aisha Ibraheem

Barci maicike dajindadi tareda mafarkai masu bansha awa” sune suka wanzu ga ma auratan guda biyu takowanne bangare zuciyar kowanne tana kwadaituwa da gangar jikin Dan uwansa “” maleek yayi barcinda rabon dayayi irin barcin haryamantaaa”””
Basu suka farkabaa””” sai asuba kyautaa tafara tashii kasancewar dakin akwai wadataccen hasken wutar lantarkii”” tarr dakin yake dahaske fuskarsa takurah wa ido batako kyaftawa”” 
Fuskarsa tayi haske “” tamkar ba barci yakeba sanadin kyakkyawan murmushi datagani kwance akan fuskarsa”” sannu ahankali yasoma motsawa”” dasauri takawarda idonta daga kallonsaa ganin yasake jantaa jikinsa yasa murya nadan rawa tace katashi lokacin sallah yayi “” ahankali yabude idonshi yadorah akan idontaa yalumshe ido””” kwayar idonta tasaukar kasa danbazata iyah juran hada ido dashibaa””” 
Hannunsa yasaka yadago habarta”” yace anfara kirane??? Batareda tabude idonba tadaga masa kai”” yadan muskutaa please kidan taimakamun inwatsa ruwa”” to tace dayar siririyar muryartaa”””
               toilet dinshi tashiga saiyanzu takaremasa kallo danjiya hankalinta bakwance yakeba Sam batalurah datsarinsa ba”” tagyada kai lallai masu Abu da abunsu wannan kamar wani dakii “” komai tsaf tsaf yake””

                Tahadamasa ruwan tareda sakamasa turare ruwan sukayi kamshii””” tafito tace nagama”” dakyar yayunkurah yazaunaa””” yadafe kansaa”” dasauri takarasa tana tambayarsa lafiya dai ya maleek ??? Ko kanne??? 
Yadago tareda murmushi wanda bata tabaganin yayi irinshiba saiyasake karamasa kyau yace bakomai kidan taimakamun bazan iyah yin komaiba””

             Tadanyi jim sannan tace dame zan taimaka maka??? Hannu yamika mata yace kirikani intashiii””” bamusu tarika hannunsa Wanda saura kadan tasakeshi dagashi har itah wani Abu sukajiii yatartsu cikin jininsu tamkar sunrika wutar lantarki””” 

              Dakyar yamike yadafa kafadarta harsuka kai toilet din yayi addua sannan yashiga”” itah kuma tafita”” waje tajirashi haryayi wanka yadauro alwala tashinfida masa darduma”” tarikoshi yashirya saida taga ya kabbarta sallah sannan tafito dakin””” zuwa bangarenta”””
             Tunkafin taturah kofa takejin kukaa kamar na mace kamar kuma na miji” addua tasomayi aranta dan tuncikin dare takejin kukan kamar akusa da itah”” 

    Saiyanzu takedanjin sautinsa””” cikin tsoro”” tashiga toilet dinta tanayi tanadan dube dube””” alwala tadauro”” tashimfida sallaya”” takabbarta sallah”” bayan tagama tayi addua””” ahankali tasomajin sautin kukan yana ragewa hartadainajinsaa””” 
Babu jimawa barcii yayi awon gaba da itah”” tafiya takeyi ahankali cikin dajiii tasomajin kukan yana tashii”” takallah gabas dayamma sambataga wani mahalukiba””” wani lambu tacikaro dashi mai kyau ma abocii kayan marmari dakuma furanni masu kyau tanan takejin kukan tasoma shiga cikinsa kukan yana matsotaa tanasakeyin gabaa”” saman wani gadon alfarma tahangoshi kwance batasan kowayeba saboda fuskarsa arufe takee”” ahankali tatako cikin tsoro hannu tasaka zata tabashi 
Yayi sauri tashi zaune dasauri tadafe kirjintaa tafadiii dabass akasa tana dafe dakirjinta Daketa harbawa tamkar zaifito”” sanadin abunda taganie”” fuwail ne idanuwansa sunyi jajirr wasu ruwa sunafitowa tacikinsu jajir tamkar jini gabadaya suffarsa tasoma sauyawaa
Ganinta dayayi yasashi mikewa yana tunkarotaa tamkar zakiyaga nama””tasoma matsawa baya dahannunsa yake nunata hannun sairawa yakeyiii murya na sassarfa yace eesha meyasa zakimun haka??? Meyakaiki wajensa daharxaki hadajikinki da

Nashi kinkuwasan halinda nashiga jiya dadare??? Kalleni kiga eeshaa kitausayamun haka nasan haryanzu kinasona kicewa maleek yasakeki Dan Allah banajin zan iyah hakurin ganin yanataba jikinki tunjiya naso daukar mataki adduarda kikamasa itah tahanani karasawa wajenku
Zamewa yayi kasa da guiwarsa yace kidainamun kallon makiyinki eesha aduniyar nan babuwanda yafini sonkii””” da mutuncina da mulkina Amman duka nawatsar saboda insameki”””
Tayi saurin katseshi cikin karajiii tace nibandamuba bansaka ka aje mulkink脿 sabodaniba” wannan ra ayin nakane”” baruwana dakukanka kama mutu”” bandamuba niba jahila bashe hakakuma banada matattar zushiya irintaka bazan iyah ganin mutum shikin halin taimako inkasa taimakonsaba”” bayan inada ikonyin hakan”””wlh bana sonkaaa fuwail natsanekaa”” natsani miyagun dabi unka insha Allah bazakayi kyakkyawan karsheba
 Wata irin kara yasakiiii wacce taisanadin sumewar””” kyautaa””” firfigit tafarka dagabarciii zufane yasoma karyomata tafara addua”” 賷賷鬲毓賷匕 亘丕賱賱賴 賲賳 丕賱爻賷胤丕賳 賵賲賳 卮乇賲丕 乇兀蹖 

Sau uku””” 
Dasauri tamike tsaye”” tabude kofa dagudu tahaye sama”” taturah kofar dakinsaa tawuce kuryaa kwance tasameshi rike da husnul Muslim” yayi barcii”” 
Tasaki ajiyar zuciyaa murmushi yasauka akan fuskartaa””” ahankali tafara sanda dankar tatasheshi “” hartakai bakin gadon”” tsayetayi akansa yabude idonsa suka sauka cikin idonta take ta daburce”” tace inakwana??? Yajikin??? Dama dama zuwanayi induba kokatashi inji mekakeso”” adafamaka???? 
Shiru yayi yanakallon dankaramin bakinta yanda yakemotsi tamkar bata magana””gashi jajir dashi tamkar tashafamasa janbakii”””

            Murmushi yayi yace kidamamu帽 Kunun gyadaa””” tace to shikawai zakasha??? Kaiyagyada yace zaiwadatar”” hartajuya yace am daukomun wayata zankirah likitaa”” tace to tareda fitaa yabi mazaunanta dakallo yalumshe ido”” 鈽篸ole insamu mafitaa ! kyauta ce tasake shigowa da sallama”” ya amsa wayar tamika masa sannan tafitaa yasake rakata da ido

Gentle Lady馃拑馃徑

[3:17PM, 1/21/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         105-106

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

  Lambar wayarsa yakamo yakirah kirah daya yadauka tareda sallama maleek ya amsa yace ya aiki daya bangaren aka amsa Alhamdulillah ya madam ??? Maleek yadanyi jim sannan yace mustapha Dan Allah inason ganinka 
Yadanyi jim saiyace inafatardai lafiya Abdul??? Yace balauba wlh nidai yaushe zakazo ???? Tobanaceba danyanzu hakama wlh banagarin maleek yadan zaro ido yace saiyaushe kenan??? ummm gobe zandawo Amman saida yamma kaga kuwa nadawo da marece bazan iyah zuwa ko inaba”” saidai muhade Monday””” hakan yayi??? 

                  Yanisa shikenan babu matsala Allah yakaimu”” ya amsa da Ameen Amman ina zan sameka??? Yadanyi jim kawai kasameni gida” yace shikenan””” inawani aiki sainazodai”” yace kodai kana kallon yan matanda kasaba ba”” mustapha yace idanuwa nakedasu dabanadasu saidai kuku kalla”” sukasa dariya sukai sallama”‘ daidai karasowar kyautaa””
Yakafeta da ido”” wannan saitayita fama da hijab kamar wata matar limami””” dukawa tayi ta aje kayan””” tashiga toilet tahadamasa ruwan wankaa”” tafito””” idonta yana kasa tace “” katashi kayi wankan””kai kawai yagyada yanuna Mata towel dinsa”” tadauko tabashi ganin zaitube agabanta kodar babu aransa hasalima murmushi yakeyi haryanzu baidauke idonsa akantaba”” dasauri zatafitaa yariko hannuntaa
Murya kasa kasa yace inazaki??? Tadan Sosa kai dama dama”” na aza abune awutaa karyakone””” baisaki hannuntaba itaakuma batajuyowa”” sakonni kawai suke aikawa junansu tacikin jinie”” yaso sosai tadago suhada ido Amman Sam kunya bazata bartaba”” ahankali yasaki hannunta aikuwa taruntuma dagudu”” hartana shirin faduwa”” yayi murmushi yadaura towel yashiga wankaa
Harya fito yashirya kana nan kaya yasaka yazauna saman gadon yanashan kunun””yanataje sumarsa haryagama batasake dawowa dakinbaa”” bayan yagama yayiwaya da mom bazaishigo yauba saboda zazzabi Amman yasamu saukii haka yakirah company nsu yasanar”” sukai masa Allah ya sauwake yace Ameen
Baisake saka kyauta a idoba saida rana”” da dareba ma tanakai masa abincin dare takoma dakinta tayi shirin kwanciya takwantaa”” Amman me saitakasa barcii duk juyinda zatayi saita hangota kwance akan kirjinsaa”” tanason yinbarcin Amman tunanin Maleek yahanata”” filo tajawo tarungume talumshe idonta tabude zuwa yanzu ta tabbatarda bazata iyah rayuwa batareda maleek ba”” Amman tayazata same shi??? Bayankuma yayimata nisa saidai tasoshi aboye””” nantake damuwa ta mamaye rayuwartaa mikeewa tayi tadauro alwala tafara sallah tanakai kukanta wajen Allah””
Bangaren maleek mahaka abunda yafaruda kyautaa yamafita jin yanayin” sosai sha awa tanaso tacikarfinsa”” hakazalika ga soyayyar eeshaa baisan yazai sanarda itaba yanagudun tace batasonshi”” 

                Sam yanason yaji dimin jikintaa Amman taya??? Bazai iyah tunkarartaba danbashida kwarin guiwar yinhakan yanisaa Allah kataimakeni kasa kartace batasona!!! Duk da haryanzun yanajin ciwo indayafadi”” Amman Sam yamantaa mikewa yayi shima yadauro alwala yafara sallah”” bangare biyu duka basu runtsaba har akayi sallar asuba
Yaukam sunshaki barcii bayan haske yafito dasuka kwanta sai shabiyu suka farkaa”” kyauta shabiyu harda rabii”” agurguje tahadamasa break kodatashiga dakin haryayi wanka yana waya tashiga”” ta ajemasa tafitaa 
Tanayin sallah tacigaba danarana”” dandama tadora”” shakwara tayi damiyan agushii taji nikakkiyar hantaa””
Kamshi tuni yagama game gidan”” bayan takammala”” tazubecikin kula tawanke kayanda tabata”” tasharewajen tsaf tamkar ba ayi aikin komai awajenba””” agurguje taje tayiwanka 
Yau kana nankaya tasaka”” bakaramin kyau tayiba kasancewar kayan sunada launin bakiii sosai saisuka kwanta akan farar fatarta””” hijab dinta tazunbula sannan tafitaa tadauki abincin takaimasa dakinsa””
                 Kwance tasameshi yana danna laptop”” tashigo da sallama”” ya amsa yanacigaba da aiikinda yakeyi””” tacemasa sannu dahutawa””” 
Yauwa kawai yace”” haryanzu baidago daga aikinda yakeyiba””” tayi tsaye jinkadan sannan tace ga abincinka”” kaiyagyada banajin yunwa yanzu kibarshi zuwa dare”” tace tosannan taduka tadauki tiren hartakai kofa yace”” kitaimakamun daruwa”” batace komaiba tafitaa”” dama tasan sakemata fuska dayakeyi kwanabiyu danbashida lfy ne”” gashiyanzun yafara dauke mata Kai””” ruwan tadauko tareda cup tadawo dakin”” dasallama ya amsa”” 

               Kusa dashi taduka”” taballe murfin”” taxuba Ruwan tamika masaa”” daga kwancen yamiko hannu zaikarba hannunsu yahadu yan yatsunsa sukasauka akan nata wani yarrr sukaji subiyun tarekowa yajaye hannunsa gabadaya ruwan sukazube akan gadon…….

Gentle Lady馃拑馃徑

[4:58PM, 1/21/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

          107-108

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Sai lokacin yadago yakurah mata ido”” sosai hijab dinda tasaka yahaskataa yayimata kyau karamar fuskarta tafito cikin hijab din”” 

Cikin kaduwa tazare ido”” tace kayi hakuri wlh bada gangan nayiba”” haryanzu baice komaiba bayan binta da kallo dayayi”” har idanuwanta sunkawo kwallah”” hannu yasaka yana karkabe jikinsa indaruwan suka taba yace bakomai bani wasuu”””

             Kofin tadauko tasake zubamasa wasu”” tamika Massa””” ya karba saiyahada da hannunta yarike””” taja taja”” yaki sakin hannun”” yakurah mata ido””” ahankali tadago idonta hawayen suka karasa saukowa”” kallon tuhuma yasoma aikamata ahankali yace menene kuma nakuka??? Kaita girgiza bakomai gani nayi najikaka”””

       Murmushin gefen baki yayi yace ninafadamaki hakan daman inajin zafiii daruwan suka sauka akaina sainaji sanyii zan iyah cewa nagode????

      Shiru tayi tareda saukar da kwayar idontaa kasaa”” cikin kasalallar murya yace tnx”” tare dasakin hannunta”” yadorah kofin abakinsa yasoma shan ruwan””” tadade tsaye wajen”” kafin tajuya tabar dakin”” tanason maleek kuma tanason zamakusa dashi musamman yanzu dayake jifanta dawani kallo Wanda takasa fassara kalarsa””murmushi ne kwance akan fuskarta data tuna lokacinda yarike mata hannu wani abutaji ajininta waidama hakan akeji idan kana son mutum tomeyasa batajin hakan lokacinda tana soyyyada taneemu”” tanisa Allah yasa shima yanasonaa”” duk zancen zuci takeyi 

Batasake komawa dakinsaba har dare”” tanajin yafita sallar isha”i takaimasa abincinsa tafito bayan tagama sallah takwanta dangobe sunada test a skull bataso ta makara””” 
Koda yadawo yahaurah sama yasamu abincinsa””” aransa yace kash meyasa takawo abincin nan bayankuma bana nan?? Naso naganta kafin nakwantaa””
Jiyayi baxai iyah kwannciya batared脿 yag脿ntaba saukowa yayi dasauri zuwa bangarenta yaune karon farko dayanufi dakinta gabansa yanafaduwa baisan meyasakaba takemasa kwarjini haryakai kofar yaturah saiyajita akulle”” yaja dogon tsaki tareda juyawa Yakoma saman abincin makasa cinsaa yayi baifi loma uku yayiba yature abincin yakwantaa!”
Washe gari dawuri tafarka tagama duk aikinda zatayi tayi wanka tashirya”” bakwai darabi tagama komai”” tadauki break dinsa tahau sama””” tasameshi zaune yayi shiru”” sallamarta tadawo dashi hayyacinsa tagaidashi ya amsa ciki ciki”” dantabashi haushi jiya datayimasa rowar ganin fuskartaa tace zanwuce skull kokana bukatar wani abune??? Yace ah ah”” tamike zatawuce yace kibuda drawer kidau kudi”” batareda tajuyoba tace wadanda kabani basu kareba tawuce abunta
Yabita da kallo yanajin wani Abu azuciyarsa!! Yana nanzaune wayarsa tasoma ringing yadauko ganinsunan mustapha yadauka”” tareda sallama”” ya amsa kaigani kofar gidanka”” 
Tokashigo mana”” yace haba yazan shigo gidan mutane”” yace todan iska aibatanan”” nima danasan tana nan bazance kashigoba kodan inkareta dagamugun kallo irin aka”” dariya yasaka yace najidai kafito kashiga dani tundani bansan kangidan ba yace OK”” tareda kashe wayar”” yamike yasauko kasaa”” harabar gidan yasameshi yabashi hannu suka gaisa”” sukawuce ciki”” 
Yace Abdul gaskiya wannan bakaramin gidabane””” yaharareshi Cikin wasa yace kanabani mamaki saikace finnaka yayi”” mustapha yace autodakumafa inazaka hadanawa dawanan wlh nakayafi nawa girma”” kyan gidan nan mace hudu dakwalaii””” yalaso labbansaa”” maleek yayi dariya aikaidama maganarka matane bansan yazakayi damata huduba!
Yace abunda akeyi da dayarmana”” kasan Allah idan zankara aure yanzu biyu zanyi ranadaya maganarda nakemaka yanzun inadasu akasaa
Suna shiga dakin maleek yace kamar kayan sakawa waikanadasu kasaa”” yace sunfima haka kainifa bazan cutarda kainaba gashinan kai kanason kashe kanka”” murmushi yayi sukaxauna yace banyi break ba bisimillah yashafo cikin sa duk danakoshi bazanki tayibaa taresuka sadariyaa saida sukagama”” yajaye kayan sannan yakalleshi yace inacikin matsala musty”” yagyara zama yana fuskantarsa yace matsalar mene???
Yanisa I am in love”” wata dariyace tazoma mustapha”” tunyana zaune haryakai kasaa yadaure fuska haba musty wlh kai Dan iskane yazan fadamaka inacikin matsala kakoma kanamun dariyaa”””
Yasake kecewa da dariya yace aiwannan abun farincikine maleek”” inafatar batawaje bace??? Yadanja tsakii kodaya musty inajinta fiye dayanda nakejin sauran ada”” banajin zan iyah hakurah da itah”” kuma nakasa sanarda itah dannasan itah ma batasona!! Musty nakasa rike kaina kaikasan komai inada matsananciyar sha awa”” dalilinda yasaka nakeyin azumie dannatserarda kaina gafadawa halaka”” shekaranjiya wlh nadauka mutuwa zanyii
Yayishiru yanakallon musty”” tsakiyaja yacewaikai kananufin haryanzu kallonta kawai kakeyi?? Yalumshe ido alamar ah”” musty yace dakanka kananema kakashe kanka gakada magani cikin gidanka haba Abdul 
Yanisa bansan yazanyi insanarda itah ba”” inatsoron jin sabanin abunda zuciyata takeda muradinji”””
Musty yace ba anan takeba aidaga rashin tayi akanbar arhaa ninasan babu macenda zatace batasonka Abdul kanadakom脿i Wanda duk wata mace zatayiwa kanta sha awar kakasance abokin rayuwarta”” tuntuni nafadam脿ka maganinda nakebaka bazaisama maka lafiyaba shawara daya Abdul kasanarda itah sirrin zuciyarkaa inyaso dagabaya”” komai yawakana kodabata sonka aikasan yandazaka koyarda itah soyayarka kadaina jinshakku帽 komai
Maleek yanisa shikenan nagode dashawar脿rk脿 inshaa Allah zansanarda itah ayaudin nan””” yadafashi cikin murmushi yauwa my man”” Allah yataimaka yace Ameen nansukai sallama yarakashi hargaban motarsa yanasake jaddadamasa sukai sallama yatafiii dafarinciki yakoma sama saman gadonsa yafada cikin jindadi lallaiyau zaisanarda eesha sirrin zuciyars脿a
Yamike yaudakai帽a za帽daukota makarantaa yalumshe idonsa yabude hannu yadaga sama ya Allah kasakarta莽e batason脿!!! yashafa

Gentle Lady馃拑馃徑

[12:59PM, 1/22/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         109-110

  DAGA TASKAR 

  Aisha Ibraheem

Yayi shiru yana nazarii yakamata inburgeta bazan fadamata ako inaba sai munxo gida “” yamurmusa meyasa tunfarko bansanarda itah ba dakomai takesha zuwa yanzu ainasan zankoyamata soyayyata””” 

                  Key din motarsa” yadauka dasaurii yasauya shiga yafitaa yasamu motar hartayi dankurah dole yakoma yasauya wata motar”” yashiga maigadi yabudemasa kofa bayan sungaisa yafita fream yasiyo masu kyau”” na kalaman”” soyayya””” tareda fulawowi””” masu kyau”” yasaka akaimasa cake maidauke dasunanta””” sosai yau farinciki yakeji Wanda shikanshi baisan iyakarsaba””” gidan yadawo tareda maidaura fulawowin””” 

Tun falon”” akadaura fulawowi saicikin dakinsa shima yasha decoration”” komai yayi chaf chaf””” dakansa yashiga kichin yahada abinci danyau bayaso kotsinke Aeesha tadauke”” 

                Yana kallon agogo yaga daya saurah agurguje yayo wanka””” yafito kayanda zaisakama saida yayita dube dube duk kalarda yadauko saiyaga tamkar batayiba saiyasake wata saida yakusa kai karshen kayansaa”” daga karshe”” wata shadda yasaka ruwan antaa anyimata adon kwalliya da zare pink”” hularsa ruwan anta takalma haka tareda agogonsaa”” karkuso kuganshi nitunda nake bantaba ganin yayi haduwa irin tayaubaa””” shikanshi yasan yau yahaduu bakaryaa”” dasauri yafito yadauki motarsa yafita karatun Qur ani yakunna harcikin zuciyarshi yakejin shaukiii yana kaiwa skull din sunatashii”” 
Bayan yayi faking yafito gabansa yana faduwa”” tundaga nesa yahangota tareda wataa””” murmushine akan fuskarsa”” itah ma taganshi”” hafsat tace ke gafa mutuminki yau yazo daukarki bakince bashida lafiyaba””馃槵 yake tayi tace towayasani koyaji saukiii hafsat”” Amman aranta tace duk gargadinda naimaka bakajiba saikaga Wanda zaikulaka””” hafsat tace muje mana waike meyasa bakyaso ina gaisawa dashii”” 

      Kyauta tamere baki tace kawai idankuma saikintafi tokije kidawo danbazaniba””” badan hafsat tasoba tawuce kyauta tarakata harbakin motaa saida taga tafiyarta sannan tasoma tafiya tamkar batasan dazamansaba””
Baiyi mamakin hakanba tunda hankali yakegani ba idoba”” motarsa yakoma yabi bayanta yanamata hon tai banza dashi aranta addua kawai takeyi”” yasha gabanta da motar”” dasauri yafito yatsaya tagabantaa yace waike menene matsalarki tundazufa naketa hon kinkyaleni”” kallon uku saurah kwata taimasa tace to inaruwana??? Nakirakane danka taimakamun motarkane bazan shigaba”” maleek yazaro ido yace menayimaki eesha dabazaki shiga motataba??? Cikin daga murya tace saboda natsanekaa banason ganinka kabani hanya zanwuce”” kalmar harcikin ransa yajita saida yarufe ido jiyayi tamkar wata katuwar guduma akabugamasaa”” asaitin zuciyarsa tuni mutane sukafara kallonsu ganinhakan yasa yakoma marairaice murya yace naji kintsaneni eesha Amman kiyi hakurii kisaurareni”” tace insaurareka ???? Mezaka fadamun Wanda bansaniba gamedakae??? Mugu kawai”” wlh bazantaba yafemakaba”” sosai maleek yatsorata da kalamanta tamkar ba eesharda yasanibace kamar mai aljanu dazufa sukarabu lafiya”” yagirgiza kai yace kinga ana kallonmu mujegida mayimaganar acen””yayi maganar yanariko hannunta”” dasauri tafige hannunta tadaga hannu tawankeshi damari””” tace banasonkaa !! Natsaneka!! Mugu ! Azzalumi!! Wanda baisan darajar aureba!! Allah ya wulakantaka”” 

In sha Allah yarda kashutardani kaima saikasamu Wanda zaimaka fiyeda abunda kamun””” maleek yanarike dakuncinsa Sam bazafin marinta yajibaa maganganunda take aikamasa masuzafiii sune suke konarmasa zuciyaa””” 
Mamakinta kwarai yakeyi sambaiyi tunanin zata iyah daga hannu tamareshiba”” shirabonsama dawani yadaga hannu yamareshi tunbaiyi wayoba danshikam dasaninsa babuwanda yataba marinsaa
Mutanenda sukai cincirindo sunakallo kowayayi mamaki yanda akamari maleek Amman bairamaba wasuma basuyi tunanin maleek dinda sukasanibane”” dantsohon govno kumadankasuwa fitacce wanda yayisuna wajen kasuwanci yammatanda suka hademasa yawu”” saisukafara jinhaushin kyautaa 

                 Ar脿帽su suna tunanin kodai budurwarsace??? Gayenfa yahaduu harcikin ransu”” sukejin sonshi”” haryanzu idonsa yanakan eeshaa””” wacce taketa rusarkuka”” batadamu damutanend脿 suke tsayeba dantasan basajin abunda takecewa fuwail kamar ance tadaga kai tahango fuwail jingine jikin motaa yanadariyaa”” dasaurii takalli maleek Wanda yasoma tafiya dabaya yanakallonta”” tasake kallon fuwail”” dariya yakeyi harda kyakyatawa”” cikin daga murya tace ya maleek Dan Allah katsayaa!!!! Inah aikingama yagama”” dantuni yashiga motaa yatada itah yanajin tanakirans脿 Amman bayajin zai iyakara minti biyar awajen””

.

Kanta tadafe nashig脿 ukuna dama yamaleek ne!!! Kirjinta yahau harbawa tasake kallon fuwail Wanda yaketa dariya hartana amsa amo takeyabace dashida motar”””
Mutanen wajen bakaramin haushi kyauta tabasuba dasukaji takira sunan wanda tacewa batasonsa yanzu

Dasauri tatari Dan adaidaita tanakuka kasayimasa kwatance tayi saida sukai nisa yatambayeta inaza akaitaa tafadamasa”” 
Ikon Allah ne kawai yakai maleek gida lafiya”” yanashigaa yasoma cire fulawowinda aka manna yayi watsidasu dasauri yahaye sama”” dakinsa yatura kofar kafa yasa yayi shurida cake din”” yadauko fream din yahau yagesu yana zubarwa
 Abunda akadaura bakin kofa Wanda yakedauke da kyalkyali da kananun fulawawi talmaninsa yacire yafasa mabusar”” yasakawa dakinsa key yashige dakinsa yayikwance akan gado gabadaya zuciyarshi tatunkushe ahankali hawaye suka tsiyayomasa muryan kyauta莽e kawai takemasa amo cikin dodon kunnensa

Natsaneka!! Banasonkaaa!!!kunnuwans脿 yadafe dakarfi yace Noooooooo!!!!!
Zan iyah hakurinjin wannan Kalmar abakin kowa Amman bandake!! Wlh bazan iyah rabuwa dakebaa””” inasonkiii

Wani abuyakeji wanda tunda yazo duniya baitabajin koda kwatanka莽in hakanba
Mai adaidaita yana ajeta tadauko dari biyar tamikamasa dasauri tawuce hartana hadawa dagudu Dan adaidaita yana hajiya cha帽 jinki Amman inakojins脿 batayiba”” taturah get din tashigee dagudu tawuce tatur脿h kofar falon”” fulawowinda yazubar t脿bidakallo saman tahaye dasaurii taturah kofar kulletajita tasoma bubbugawa tanakiran sunansa脿 yaaaa maleeek Dan Allah kabude!!

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:54PM, 1/22/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

       111-112

 DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Kuka takeyi dakarfiii tana bubbuga kofar”” ya maleeek kabudeee Dan Allah shiru yayi tamkarma baiji abunda takefadaba””” Sam jinsa yakeyi tamkar wani mutum mutumie shikoyaushe haka rayuwarsa zatarika juyawa
Ada yayi alkawarin bazaisake cewa yanason wataba!! Dangudun faruwar abunda yafaru dashi saigashi kwatsam soyayyar eesha tafada kogin zuciyarsa batareda tambayarshiba!!! Tunkafin yasamu yasanarda itah sirrin zuciyarshi tarigada tafadamashi batasonshi ta tsaneshi”””” toshi menene laifinsaa???? Meyayimata dabata sonsa tace yaci amanar aure”” amanar meyaci bairageta dakomaiba yanabata duka hakkokinta kwanciyane da itah kawai bayayi
Kyautace ta tsananta bugun dakin”” tana rusar kuka wanda maleek yakejinsa harcikin kokon ransaa Amman bazai iyah nudewaba danbayason ganinta ahalinda yakeciki yanzu””” 
Dan Allah kabude wlh bansan kaibane ya maleek kabude kajiii zanfadamaka”” dalilinda yasaka naimaka hakaaa wata kara tajiii wadda tayi saurin toshe kunnuwantaa””” sosai jikinta yasoma kyarma””” kayan saman sukarika juyawa “”” kantaaa taji yana juyawa tamkar ana juyarda itah”” wata kakkausar murya taji wacce bata taba jin irintaba tana amsa amo tamkar faduwar araduuuuu
       Karki kuskurah!!! Idan yabude mezaki fadamasa???? Kina nufin zakice masaa inatare dake??? Wannan babban tsautsayine zaki aikata cikin ganganciii kisanie muddin kikasanarda wani mahalukiii wannan sirrin bamakawa saina kasheshiiii kirjin kyautaaa yasoma harbawa dasauri dasaurii saizagayenta akeyi anajuyata kaf gaba dabaya bataga mai maganaba saidai tashin muryar takejiii yakece dawata hatsabibiyar dariyaa maikamada kukan jakiiiii”””””
Wlh natsaniii maleek tundahar yabar zuciyarsa tafara sonkiiii kiriss yarage ingamadashi”” zan yimasa uzurine saboda mom dinki taimako daya zaki iyah Masa karki sake kikarbi tayin soyayyarsa yinhakan zai tseratarda rayuwarsa daga fadawa tarkonaaaaa yasake kecewa da dariya wacce tasaka gidan amsa kuwar dariyarrr””” wasu zufane sukasoma karyowa kautaa”” idan harkinason yacigaba da rayuwa to tabbas kinisanceshi kihana kanki sanardashi abunda yake tsakanina dake akanki babu abunda bazan iyah aikatawabaa”””” saboda inasonkiii sonkiii sonkiiii shine abunda yayita yawo akan kyautaaa take tasulale kasaa sumee!!!
         Yana kwance saman gado yakurawa silin dakin ido”” abunda yafaru shekarun baya sukasoma dawomasa”” 
 *WAYE ABDUL-MALEEK?????*
Takai taccen labarinsaa””” kamardai yanda kuka sanie”” Abdul maleek dane daya tilo ga Alhj kabeer sunan mahaifiyarsa hajiya Ameena”” marainiyace mahaifiyar Alhaj kabeer tayi rikonta yayinda daga karshe sukahadata aure da Alhj kabeer”” sosai sukeson junansu tamkar suhadiye Kansu baburuwansa dakowa agabankowa zai iyah nuna yanda yakeson matarsa!! Dan uwansa daya alhaji jameelu”” Bayan shekara hudu da aurensu Allah ya albarkacesu dasamun danamiji sukasamasa suna Abdul-maleek sosai hajiya ameena takeson yaronta duk da Allah yajatabceta Dason yamace kuma tunda tahaifeshi sai haihuwar tayi tsayenta”” yayi karatunsa harya kammala bangaren kasuwanci maleek kyakkyawane ajin karshe kuma kamiline” wanda yasan dattako baburuwansa darigima hakaxalika bayashiga sabgarda batashiba” baifaye yawan surutuba Amman akwaishi dadaukar zafiii dankokadan bayason rainiii”” bayaraina kowa hakazalika bayason hulda damata!! Hakan yasamo asaline daga yanayin halittarsa yakasance mutum naiyawan sha awa tundaya ganohakan saiya rageyawan farardamutane musamman mataa danyanagudun afkawa rudin samartaka karshaidan yasamu nasarar jefashi cikin hatsarii sosai alokacin dayana skull yakasance shiru shiru zakasameshi shidaya yana karatu bayason yawan hayaniya baitabayin budurwaba duk wacce takeson sama bayakulataa 
Watarana yashigo skull cikin hanzarii saboda yamakaraa””” sam bailurah da itah ba””” suka bugijuna”” gabadaya littafan hannuntaa suka watsee tayi luuuu ganin zatafadiii tareda ihuuu tayi baya dasauriii yasa hannunsa yajawotaa”” saura kadan tafada kirjinsaa””” dasauriii yajabaya tareda sakin hannuntaa hakan yasa tafadiii hannu yasaka yadafeee kansaa””” 
Ido takurah masaa tasamu tamike Sam batadamu dafaduwarda tayibaa murmushine akan fuskartaa “” hannu tamikamasa cikin murmushi tace hye””” sunana”” samrat”” 
Harara yamakamata yace shasha sha””” waya tambayeki sunanki dasaurii ta jaye hannunta””takuramasa ido””tana muzuraii””” wucewa yayi abunshi tabishi dakallo daga murya tayi tace Prince””””” tanadaga masa hannu”” kowaigenta baiyiba saida yayinisa yawaigo haryanzu tanakallons脿 batadaina dagamasa hannuba tanaganin yajuyo tace yeee tanadaga hannu””” 
Yatsanta tasaka cikin bakinta kaamar maijin kunyaa “”” ihu tasakeyi tanajuyi tawuce sauran wadanda suke wajen sunakallon duk abunda yafaru sukaja tsakie 

      Matanda””” suke tsaye subiyu dayartace wannan batasan halin guy dinnanba”” aigashinan yadizgata Amman danrashin zuciya batawani damuba”” dayar tace toke ramlat inaruwanki zatayi tagajine tabarshiii wanne abune bamuyiba akanyakulamu Amman yayi tamkarma baisan munayiba”” 
Wacce akakirah daramlat tace Amman yarinyar nan daganinta sangar tattace kumazatayi rawarkai

Dayar tace ruwanta脿 batasan bayason shishshigib脿

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

          113-114

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

 Dayar tace mudai meyadame mu akan idonmu zaimata wulakancii

 Motar ta tashiga s脿i hotel din datake zama farinciki fal ranta tunda take bata tabajin son wani damiji arantaba saiyau”” samrat kenan”” ya mace kwalli awajen hajiya falmata”” babanta babban dankasuwane kuma shine nahannun daman”” sugwaban kasan Nigeria tana da yayyu uku duk maza sannan itah”” sosai iyayenta sun sangartata dabiunta sak na turawa kokayan jikinta irin nasune bata taba daurah atamfaba ballantana kuma rigarda hausawa suke sakawa gabadaya kayanta English west ne”” saifa kayan India wa saboda tana mutuwar son kayansu shiyasa take sakawa Allah kuma yayita kyakkyawa tamkar yan India sosai idan tasaka kayansu saitadawo sak su”” sunanta na asali sameera”” Amman tamiyarda kantaa samrat”” kuma sunan yabita sosai danbamai kiranta sameerah

          Gabadaya kusan zamanta akasashen waje tayishi duk saurayinda yace yanasonta batajin komai zatacimasa mutuncii 
     Yaune tayi katari da Prince acewartaa””” talaka masa suna shugaban kyawawa””” ranar jinta takeyi kamar wata sarauniyaa aranar gidansu babuwanda baiji labarin prince ba
      Sukansu suntayata murna kasancewar idan tanason abu tofa takama rawar kafa kenan” tundaga ranar batasake saka maleek a idontaba babu inda batanemeshi acikin skull dinba Amman bataganshiba duk tadamu abincima tadainaci masu kula da itah kuka kawaitake masuu

     Gashi suna tsoron kar mahifinta yazo yasamu yarsa tarame surasa albashinsu”” 

             Bayan kamar satiii biyu dafaruwar hakan”” tana tareda kawarta safina wacce tamiyarda sunanta safna”” kusan tare suke yawo saboda hali yazodaya””” sunje lab zasu duba wani assignment da akabasu”” tsaye tayi bakin wajen tacewa safna kishiga kidibo nizandan zagaya nan”””

     Tace haba samrat kizo mushiga mana bawani jimawafa zamuyiba”” tayatsina fuska toni bazaniba kawai kisameni nan baya tayi wucewarta batareda tajira jincewar safna ba
      Ahankali take tafiya tana kallon bishiyoyin waje”” tana rangaji tamkar zatafadi”” tanasaukarda kwayar idonta taganshi zaune yanarike da littafi yana rubutu akan daya””” bakitarike tace wow!! dat my Prince””  
               Karasowa tayi kusa dashi”” sai alokacin yadago kansa fuskarsa adaure tamkar baitabayin dariyaba””” batadamu da yanayinda yakecikiba tasaki murmushi sannuko””” ciki ciki yace yauwaa””” yamaida hankalinsa wajen abunda yakeyi””” 

      Tace amm bakaganeni bane???? Batareda yadago kaiba yace taya zanganeki bayankuma nibansankiba””” ido takwalalo kenan haryamanta da itah itace kawai take azabtuwa da mafalkinsa”” tasake yin murmushi tace nice taranar damuka hadu””” wajen holl””” harnabigeka”” katunani???? Baki yamere yace nibanwani tunakiba! Abu mai mahimmanci arayuwa shiyake samun muhallin zama akaina”””

           Tace kana nufinnn nidin banidawani mahimmanci??? Murya narawa tafurta hakan””” yadago yanakallonta yace awajena bakidashi danbawata alaka atsakaninmu awajen wasu zaki iyah zama mai mahimmanci menene matsalarki agamedanie?????? 
Murmushi tayi tanawasa dayan yatsunta tace “” kawaidai tunranar naketa nemankaa””” yace nemana??? Nidin??? Akanme kike nemana??? Jere dajuna yajeromata tambayoyin””” tace wai wai Prince aitambayoyin sunyimun yawa”” dakamun daibayan daya zanfibaka amsa cikakka”””
Yace ahakan zanfiganewa kiyimun adunkule””” tace”” to sunanka zakafadamun kuma idan bazaka damuba inaso muzama friend””” 
         Kallonta yasomayi cikin mamaki yace sunana baizama dole kisaniba anasanin sunan mutum ne domin kullah wata alaka dashi banajin wan an zaifaru tsakaninmu
Sannan nibana abota damataa”” kisamu mace yar uwarki””” yamike tareda tattara littafansa””” zaiwuce tace kaga Prince Dan Allah kasaurareni 
Batareda yajuyoba yace inada aikinyi agabana””” yawuce abunshiii tsaye tayi tanakallonsa harya bacewa ganintaa”” 
Safnace tafito rikeda littafin tasameta tsaye harta takowajenta batasan takawoba saida tadafata tace meyafaru samrat????
Tadan zabura sanna tayi murmushi tace bakomai Prince dina nagani anan”” safna tace habadai toyanzu inayake??? Batareda takalletaba tasoma tafiyaa tace yatafiii safna tamere bakii dansosai tunakafin samrat taganshi tarigata fadawa soyayyarsa Amman yakikulata babu biyarsa dabatayiba ko maganarsama batasamuba””” guntun tsaki tayi aranta tace wlh baki isah kiyi soyyya dashibaa!!!
Tawuce tabibayantaa “” tundaga ranar kullum saitazo lab dantalurah yanayawan zamawajen kasancewar wajene dabaicika yawan jama aba””” 
Kullum saitamasa magana yayi banza da itah””” yauma tasameshi zaune yana waya littafaine ahannunsa yaune kawai taga murmushinsa Amman yanaganinta yadaure fuska””” yayi sallama da mom din”””
Kallonta yayi yace waike meyasa bakyajine saunawa nasanardake kidainashiga rayuwata waidolene sainayi abota dake”””
Arayuwata banason shishshigi kekuma nalurah kankiyana rawa wlh zanyimaki abunda bakitaba tunanib脿”””yaja dogon tsakiii

           Tunda yafara fadansa hawaye sukasoma sauka akanfuskarta””” dukawa tayi tarage tsawo””” tashare hawaye kayi hakuri bansan zuwana anandinba takurane awajenkA 

                 Banice nasakawa kaina sonkaba Prince bazan boyemakaba wlh soyyarka tahanani sukuni kataimaki zuciyata bantaba jin sonwani aduniyaba samadakai wlh bazan iyah rabuwa dakaiba  
Miikewa yayi yawuce yabarta anan jikisanyaye tabishi dakallo sosai tasan wulakanci帽da takeyiwa samarinta shine yanzu takedauk脿r sakamako
Maleek yayini yanatunanin maganganunta脿 duk yanda yaso yakawarda tunani帽 yakasa saiya dauki hakan amatsayin tausayintane yakeji

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        115-116

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Daga ranar saiya sauya wajen zama kullum saitaje batasame shiba sosai tashiga damuwa ita ma saitafara dakaicewa itah kadai tana tunani ranar tazagaya bayan holl dinsu gindin wata bishiya tasameshi “”” batayi maganaba tsaye tayikawai tana kallonsa ajikinsa yajihakan yadago kai yanaganinta yacika da mamakiii “””hannu yasaka yadafe kansaa””” murmushi tayi maikamada kuka””” ahankali tatako indayake murya sanyi sanyi tace yanzu sabodani kadaina zama bayan lab???? Dankawai nace inasonka??? Nimafa bani nasakawa kainaba””kaji tausayina Prince wlh nashiga damuwa sosai Dana daina ganinka babu inda bandubaba a skull din nan Amman bangankaba””””tayi shiru”” shima baice kokaiba”” tanisaa
Kayi hakuriii nasan ina takura maka bayanda zanyine”” dagowa yayi yana kallonta yace  

Hakuri zansake baki “” kibawa zuciyarki hakuri nibanada lokacin soyayya Dan karatu nakeyi”” 

    Tayi saurin tarar numfashinsa tace nima ai karatun nakeyi””” basaimuyi aureba idan mungama””” 

               Mikewa yayi yana kallonta sama dakasa””” saikuma yabushe da dariyaa””” cenkuma yasha toka yace dawa zakiyi auren??tunkafin nacema inasonki??? Tokisani idan mafarki kikeyi kifarka nibazan iyah aurenkiba””” danbakya cikin tsarin matanda nakeso”””
Tayi saurin magana cikin kuka””” haba prince meyasa bazaka iyah aurenaba menarasa Wanda duk wata diyamace take tutiyar tanadashi””” nasan banada makusa kokadan””””
Hannu yadaga mata yace natsu banason hayaniya”” kafin kije ko ina kalli kanki”” dubatayi izuwa kayanda suke sanye ajikintaa””” kayan indiyawane”” jajaye sunada adon fulawa dafarin dazare”””” rigar iyakarta cibinta kadan kawai tasauko””” sai siket shima harkasa tamkardai yanda kukasan nasu””” gashin kantaa anrabashi gida biyu antufke dakaton ribon”” sai jelar datake yawo akowanne bangare””” saiwani silin gashin dayake rito akan fuskartaa””” katon gyalen kayan”” tarufoshii””” tazagayo dashi akan cibintaa”” tadora akan kafada””” sai awarwaro na tabo”” masu amsakuwa akanduka hannu wantaa”” afuskarta digon go shine Wanda India wasukeyi””” takalmanta bamasu tsunibane””””

                 Tamaida kallonta wajenshi tace menene ajikina Prince naga kayana basuda illah””” yace awajenkiba””Amman awajen wadanda sukasan mutuncin addininsu wannan babbar illace
        Kina tutiya cewa ke musulmace iyayenki musulmaine Amman kiikalli shigarda kikeyi kindauki dabiun yahudawa da narasa aganinki burgewace???? Duk abunda yadace ace mijinkine kawai zaigani kinbarshi bude samarin duniya sunagani bayankowa yagama gani sannan kiyi aure 

             Menene zakikaiwa mijinki??? Abunda kowayagama gani??? Menene illar suturar hausawa??? Kekanki idan kikasakata zakifijinki kin kammala babu yankame kame zaki iyah shiga ko inane dashigarki babuwanda zaimaki kallonyar iska””” koyarainaki””” zan iyah baki shawara amatsayinki na musulma kikama kanki dabi.un yahudawa sudaina burkigeki”””” yamike yawuce abunshi tunda samrat take iyayenta basutaba nunamata illar kayanda take sakawaba idanma tasaka mom dinta hargidadata takeyi tace sunayimata kyau
Tashare hawaye jiki asanyaye tajuya tabargurin”” tundaga lokacin maleek baisake ganintaba””” gashiyanzu yana azabtuwa da tunanintaa”” yaubabu skull zaune yake hotel dinda yakezama wayarsa tahau ringing””” yaturah hannu yadauko yaduba sabuwar number yaganie yadauka tareda sallama
Maimakon ta amsa saitace hye my Abdul really miss u muaah!!tayi kiss awayar dasauri dasauri tamkar bakin maleek din帽e Wani mugun tsaki yaja yakashe wayar””” wai itah zahra yaushe zatayi hankali uncle gabadaya yasangartata”” yasakejan tsakii yazama dole insake nomber idan bahakaba wannan maishegen nacin bazata kyaleniba””” bangaren zahra sosai ranta yabacii maleek yana nema yamaida itah mahaukaciya kullum cikin siyen sababbin sim card take dandazaran yajimuryanta zaikashe kuma bazaisake daukaba karshema a black list yakesakata”” 

Aisa arshidaya”” batasan skull di帽d脿 yakeba wlh dasaita sameshi acen”” tayi tagumie tana tunani
 

*2 months letter*
Maleek nezaune bayan lab””” yanarubutu Amman sakeda hannu danbakomai yake rubutawaba zuwayanzu yasadakar son samrat yakeyi”” duk dayasan yamakaro danbaisan a inama zaisake ganintaba”””” 

              Murya yaji maitaushi tace Asslamu Alaikum dasaurii yadago Dan tabbatarda mai muryan”” wacce yakeson gani ahalin yanzuu””” murmushine yakubce masaa”””
Yace Wa alaikumus salam”” wanakega帽i kamar sameera????murmushi tayi tace nice Yayana””” sosai taburgeshi atamfane jikinta tareda babban hijab””” nikab ne afuskarta””” amman tanazuwa wajensa tadageshi””” 
Daga nesadashi””” akwai wani dakali tazauna cikin girmamawa tagaisheshi”””ya amsa cikin sakin fuska””” yace wai inakikashiga kwana biyu”””???
Tace wlh gidanaje mom dina da dad dayayyuna duka sunagaidakai””” yace ina amsawa””” sukai shiru nawasu seconni takauda shirun tahanyar cewa Yayana
Ya amsa tace dama zanyimaka godiyane akan abunda kamun””” cikin rashin fahimta yakalleta taredacewa nameke帽a帽??? Tanisa hakika saiyanzu nakejina nacika mutum”” yanzu nafisamun natsuwa hakika tupapinda musulunci yakoyardamu musaka danrufe tsaraici帽mu sune daidai sakasu zaisa mubanbanta dayahudawa 

 

Nikam ko ayanzu nagodewa Allah dannaci ribar soyayya””” nakuma gode dafadakar warka gareni inamaka fatan alhairi”” Katayani addua Allah yabani miji kamark脿” tamike tanashe tsirarun hawayenda suka saukomata””” tawuce abunta””” zuciyarta tana harbawa”””
       Yace samraaat!!! Chak tatsayaa tashiyayi yatako har indatake yana fuskantarta yace sakozanbaki””” tadago idanuwanta dasuka soma chanza kala takirkiro murmushinda baiwuce fatarbakiba tace inajinka Yayana””” murmushi yayi jin muryanta narawa””” yace kifadawa zuciyarki cewa Abdul-maleek shima yanasontaa!!!
tasake dagowa dasaurii takalleshi haryasoma tafiyaa dama sunansa Abdul ne??? Kowani Abdul din daban””””馃
Yakai kan kwanar lab din yajuyo”” yace nine zanzam脿 mijinki inshaa Allah *INASONKI !!!*

gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         117-118

DAGA TASKAR

 Aisha Ibraheem

Yasakar mata wani lallausan murmushi yawuce”” wani dadine yakama samrat”” Tace Alhamdulillah godiya ta tabbata ga mahaliccin sammai da kassai”” tunranar rabuwarta dashi batakwana kasarba”” tayiwa gidansu tsinke tunda suka ganta sunsan ba lafiyaba danbata sanardasu zata zoba”” batayi magana dakowaba kuka kawai takeyi saida aka Kira babanta”””

      Yazo yasameta tahade kai da guiwa dukawa yayi yadafata tareda kiran sunanta”” tadago tana kallonsa ganin fuskarta shafe shafe da majina yashiga rudani yana tambayarta waye yatabata??? 

            My baby kifadamun me akaimaki kowaye yatabaki zanyi mumunan sabamasa Kodan gidan waye””” tasake gado kantaa tace wazai sakani kuka bayan kai!!! Kaine baba dakuma mom harda su ya Ahmad 

   Cikin kaduwa yace mekuma mukayi yar Lele”” tasake sharbe hawaye tace meyasa bakutaba sanardani illar kayanda nake sakawaba???? Meyasa baku koyardani shigar musulunciba””” dad meyasa hakan??? Gabadaya jikinsu yayi sanyi””” suka dukadda kai””” tasharbe hawaye banada laifi saboda tunda natashi kayanda nake sakawa kenan kuma irin wadanda kuke sayamun kenan””” bantaba saka hijab ba bantaba sak atamfaba”” gashin kaina kullum abude yake”” naji takaicin nakasance cikin zuriyar gidan nan” inatama namutu kafin wannan rana””

         Dad yarufemata baki””yana girgiza kai yace karkice hakan samrat Hakika munada laifi sosai wlh sonda muke makine yajawo hakan kiyafemana
        Taja ajiyar zuciya Inda mom da yayyuntama sunata lallashinta””” tace zatahakurah Amman sai sunsamo wanda zaikoya mata karatun islam dayanda zatakame kantaa kuma asamo mata wacce zatakoya mata saka kayan hausawa gabadaya kayanta ta tattarasu tasamasu wutaa
     Cikin sati uku nakoma tamkar ba itah ba watarana bayan maikoya mata karatu yagama zaitafi take tambayarsa yamutum zaiyi idan yanason Abu kuma yazamana abunda yakeson bayatare dashi 
Shine yacemata tayawaita addua da azumie dakuma sadaka saboda addua tana kare mutum daga dukkan masifu””” kisanarda Allah bukatarki idan alkhairice Allah yamallamaki abunda kikeso idankuma ba alkhairi bane atattare dake Allah yaciremaki sonsa”” tace nagode malam tundaga lokacin tadage da sallar dare da azumie yauburinta yacika prince yace yanasontaa”” murna sosai takeyi””” ranar batayi barciba tayita nafilaa dannuna godiyarta ga Allah”” 
Tundaga lokacin sukafara soyayya “” soyayya sukeyi cikin mutunta juna kuma mai tsaftaa safna tayi bakincikin hakan kuma tadauki alwashin saita rabasu haka sauran masoyansa dakuma nataa idan akagansu tundaga nesa za afara zundensu

      Anahaka tsayin wata biyar soyayyarsu tayi karfi alokacin yasanarda itah zaije gida yagasu mom kwana biyu ranarda zaitafi kamar tayi kuka jitakeyi kamar idanyaje bazaidawoba saida yayita rarrashinta da alkawarin bazaiwuce kwana ukuba””
Ahakan sukarabu suna mararin juna””shabiyu narana jirginsu yasauka kano”” driver yazo daukarsa ranar tamkar hajiya ameena tamaidashi aciki””” 
Kwanansa daya zahra tasauka dantasamu labarin yaxo gida”” kusan marece tashirya taje gidan”” kaitsaye bangarensa tanufaa wasu arnayen kayane”” ajikintaa tamkar diyar kabiluuu ansagalo karamar jaka agefe fuska tasha zanen kwalliya”” taturah kofar dakinsa saitasameta arufe
Hakan yasa tawuce cikin gidan tanashiga yanasaukowa dagasama””” tasaki fara”a wow Abdul dina kaganka kuwa wlh kasakeyin fresh”” dasaurii tarungumeshi”” cikin azama yatureta yafallamata marii hagu da damantaa”” yace kewacce irin dabbace shashasha zakizo ki chakumeni kamar kanin ubankiii wlh zarah kinkaini bangofa nace banasonki banasonki shinwai anaso dolene 
Tanadafe dakunci bakibude take kallonsa tace nikamara Abdul??? Yazare ido yace anmareki idankikai wasama zankara maki wani tagirgizakai bakomai ninakawo kaina kome kamun bakada laifii nasan kanayin hakanne dannarabu dakai to wlh bazanrabu dakaiba kumadole saikasoni saika aureni danbakada wata matar faceni”” tsawa yadakamata yace ni inada wacce nakeso tunwuri kifita harkana ko inyimugun sabamaki””wacce batasan darajar kantaba idanma na aureki ince na auri wa”” yaja tsaki zaiwuce tasake jawo rigarsa afusace yajuyo yasake dauketa damari Wanda yafi nafarkon zafiii dansaida tas脿k脿 karaaa sanadin abunda yasaukoda hajiya ameena dagasama cikin sauri tajiwaye yake ihu
Tagado dafe dakunci tace nikasake Mari wlh kasani bashikaci danbazan kyaleba kuma yazama dole ka aureni idankuma bahakaba kaida aure har abada!!! 
Yadaga hannu zaisake marinta mom tana saukowa tace kaikai karnasake naga kamareta kanwarkacefa””
Yacije leben kasa yana huciii tace Aida kamarenin wlh abdul soyyya dani yazamemaka dole kuma saika aureni danbaka dawata matar aduniya bayanni 
Koka aureni kokuma katabbata bakai aureba har abada”” mom takatseta ahirdinki karnaji kinsake yin mummunan furuci akandana inshaa Allah kuma saiyayi aure saidai bakinciki yakasheki tsakiii tayi “”
Mom tace kewacce irin shasha shar yarinyace??? Kodayake balaifinki bane””tanunamata kofa kama hanya kifita tayi kyacci tareda nunawa maleek yatsa tawucee fuuuuu shima dasauriii yabi bayanta hartashiga mota tafita atsiyace 

                   Koda yashiga mortar yabi bayanta baisametaba”” danranar yaso saiyakaita kwance Dan ayita datushe”” itah kuma ranarne takirah teema sukaje wajen bokantaa
Kwana biyu dafaruwar hakan maleek Yakoma skull saidaime duk inda yahadu da samrat saitaruga tashige cikin mutane abun yasoma damunsa””
Ranar yarutsa da itah cikin holl bayan angama karatu”” ganinsa yasaka tatashi dasauri jikinarawa zatafita
Yayi saurin shangabanta”” yace waimenene haka kikeyi samrat sai wahaldani kikeyi yautsawon satiii biyu kenan nake biyarkii Amman dakin ganni saikifara gudu menayimaki samrat ??? Wlh ina azabtuwa dayawa”” duk maganar nan dayake idonta arufesuke
Yana matsowa tadaka uban tsalle gefe tace karkamatso kusadani wlh banasonkaa kabarniiii katafiii banason ganin fuskarka”” muryarda tafurta hakan yakemamaki kodai mafarki nakeyine”””
Cikin damuwa”murya narawa yace samrat ninefa??? Dan Allah idan wasakikeyi kidaina fadar hakan””yakikeso inyi daraina”” cikin karaji tace kamutuma bandamub脿”” nidai nafadamaka banasonk脿a脿!!!
Sake matsowa yayikusa da ita aikuwa takwatsa ihu tayiwaje”” gabadaya ancika holl din anakallonsu
Wasu suna tausayinsa wasu sunacewa gwai”” Allah yakara”” jiki asanyaye yabarwajen
Kullum saiyaje duk inda yakesaran ganintaa” dataganshi takerugawa”” karshe saiyadai帽a ganinta tsayin satiii biyu kuma”””safna ma yadaina ganintaa gabadaya skull din tafita ransaa””
Ranar yanazaune yaji tx yashigo wayarsa dasaurii yaduba saiyaga nomberta kafinma yakaranta yayisaurin danna calling”” 
 Hartakusa katsewa”””akadaga”” murya narawa yace samrat kinajin脿 inakika shiga kwanabiyu ??? Dan Allah kimun magana shiru batace komaiba
Yace hlo kina jina?? Kuka tafashedashi tace nashiga uku takashe wayar hannu yanarawa yasake kiran akace kashetake
Yayita gwadawa fiyedasau biyar amman takishiga tx din yakamo yaduba Assalamu Alaikum Yayana dafatar kana lfy inaso zanbaka hakuri akan abunda yafaru inasonka ammankuma yanzu banasonka duknaganka tsoronakeji”” hakazalika ganinakeyi kasauyamu帽 kadawo tamkar dodo nakasa natsuwa dansaboda duk inda kaganni saikamun magana shiyasa nabar makara帽ta
Karka kirani mayaud脿riya danvan yaudarekab脿 Kuma karka wahalda kanka wajen nemana danbazaka ganniba inamaka fatan alkhairi bissalam

Wayar yayi cillida itah yace Allahumma ajirni fimusibatii wa akhirni khairan minhaa wanizufa yasoma karyomasa
 

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

       119-120

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Menaiwa samrat??? Inazame mata tamkar dodo ya ALLAH!!! gabadaya yarasa natsuwarsa shikenan yarasa samrat bayan yasakata acikin ransa”” tundaga ranar”” yadawo sukuku”” baisake marmarin son wata diya maceba suna gab dagama skull yasake haduwa dawata khadijaa ranarda yanuna yanasontaa itah ma tasoma gudunsa tamkar samrat hakan yayita faruwa dashi karshe yace bazaisake cewa yanason wataba idankuma harsaiyace tosaidai yatabbata baiyi aureba””” 
Har alokacin zahra batadaina damunshiba acewarta idanhar yaga kowacce mace batasonshi dolene yadawo garetaa Sam kocikin abokansaa “” bayason ana firar mata”” abokansa biyu ne Usman da doctor mustapha”” hajiya ameena kanta abun yanadamunta ganin koda wasa maleeek baitaba furta yana son aureba gefe guda matsananciyar sha awa yakeji wannan dalilin yasaka haryasoma azumie 

Bayan aurenshi da kyauta a bun saiyadada karuwa “” shine yamatsawa musty akan yabashi magani yarika sha kozairage masa yawan bukata”” Amman gabanza wai anshuri kakkausa”” takaitaccen tarihinsa kenan””
     *Cigaban labari*
Yanisaa tareda share zufanda yasauko masaa”” yamirgina yanakallon agogo dasauri yamike ganin time din sallah haryawuce”” toilet yashiga yadauro alwala yatada sallah”””

         Ahankali tasoma motsawa tamkar wacce tai barciii tamike tasauko kasa”” tayi mamaki ganin har karfe”” uku taje dakinta tai sallah””” hanyar kicin tayi domin sama masa abunda zaicii saitasamu abinci saman dinner tabude jelof din taliyace taji naman rago”” tamurmusa ya maleek kenan”” 
Fasazuwa kitchen din tayi takoma saman”” tabuga kofar ya maleek Dan Allah kabude banza yayi da itah bakalar magiyarda batayiba Amman yashareta””” ranar dakin yawuni hardare”” kyauta tayita bugun kofar yabude koda bazai yafemataba yaci abinci Amman fafur yaki budewa yanda yawuni baici komaiba haka itah ma””sallah cekawai take tada itah wajen datagama sallah zatadawo wajen tazauna harbarci barawo yakwashetaa””” 
Maleek Sam kasa barci yayi yataso yabude kofar tanakwance ta kudundule cikin jikinta””” dukawa yayi yadauketa yakoma cikin dakin da itah” saman gadonsa yashimfideta””” 
Barci takeyi Amman saboda kukanda tayi sai saukarda ajiyar zuciya takeyi hannu yasaka yashafo fuskarta”” cikin zuciyarsa yace yanzu eesha itah ma adodon takeganina?? Danduk wacce nakeso guduna takeyi meyasa harnaso furtamata danasani danabar abuncikin zuciyata””” komawa yayi yakwanta yana kallon silin daren ko runtsawa baiyiba
Ganin barcin ma bazai daukeshiba”” yatashi yadauro alwala yayi nafila yana nan saman darduma”” anafara kiran sallah yawuce masallaci
Sannu sannu tasoma bude idonta dasauri tamike tana kallon dakinda takeciki taduba bataga maleek ba””” jiki asanyaye tayo alwala tayi sallah”” tazauna zaman jiranshi shiru shiru harwani barcin yadauketaa
Koda yadawo yasamu tayi barci kitchen yashiga yahadamata break dankarma yatasheta bangarenta yaje yayiwanka yashiryaa yafita 
Shadaya tafarka tareda mika tayi addua”” saukowa tayi akan gadon takara karewa dakin kallo bataji motsinshiba toilet tashiga bayanan”” dasauri tafito dakin””” taduba ko ina bayanan””” 
Taduba waje bataga motarsa ba”” wani kukane ya kubce mata dagudu tayi dakintaa shikenan maleek gudunta yakeyi
Wayarta tadauko saitasamu sako”” sabuwar nomber ce tabude sakon ga abunda yakumsa
Amincin Allah yatabbata agareki ma abociya murmushi” dafatar kintashi lafiya”” ga abincinkinan akan dinner kitabbatar kinci Kanwata banaso kizauna dayunwa 
Kihuta lafiyaa””” lambar takamo takirah saitajita kashe tajefarda wayar”” abincinda bataciba kenan””””
Tundaga ranar sai maleek yafara wasan buya da eesha bayadawowa saiyatabbatar tayi barcii””” 
Kwana uku tsakani””” yadawo dadare yanakulle gida yawuce dakinsaa yanaturah kofar sukai ido hudu da eeshaa””” dasaurii yakawarda fuskarsa zaibude kofa yafita hartakawo tadafe kofar dahannuntaa sosai kirjinshi dukan uku uku yakeyi yarumtse idonshii””” 
Hawayene sukasauko akan kumatunta murya narawa tasoma magana ya maleek meyasa bazaka kalleniba?? Ninasan na aikatam脿ka laifi Dan Allah kayafemun dukawa tayi akan kafafunsaa tace Nina San katsaneni abunda naimaka badason rainabane inajima tamkar nahaukace !!! Dan Allah ya maleek kodabazaka yafemunba kadaina guduna”””
Shiru yayi nayan dakiku yaduka yatasheta tsayee yatsansa yasaka yana gogemata hawaye yasakarmat脿 murmushi yace bakimun komaiba eeshaa gaskiyar zuciyarki kikafada kaitasoma girgizaw脿 Amman batayi maganaba”” 
Yajuya tareda dauke hannunsa akan kafadarta nibanga kaifinkib脿 dankince bakyaso帽脿 tunfarko laifinane danaki sanardake inasonkii hakazalika nayita nunamaki kiyayya ace war kinshigo rayuwata 
Dafari banyiniyar sanardakeba dangudun wanan ranar saigashi tunkafin nafurtaa kince bakyason脿a kintsa帽eni

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         121-122

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Dasauri tace wlh ya maleek nibadakaii nakeba!! Dasaurii yajuyo yace eesha tomeyasa kika furta hakan??? 
Takowa yayi zuwa inda take”” yace nimai laifine agareki”” Amman Dan Allah kiyi hakuriiii karki gujeni bazan tilaas tamakiba”” Amman kisani inasonkii kuma bazan tabadaina sonkibaa kinzama bugun zuciyataa gaban tane taji ya tsananta bugawaa” tabbas fuwail yana wajen””” dube dube tafarayi””” dasaurii tabude kofar dakin tayi dakintaa dagudu bakii sake tabar maleek yana mamakin eesha tamkar ba itah ba
Saman”” gadonta tafada tafashe da kuka meyasa hakan?? takasa sanarda maleek tana sonshi””” muryan fuwail taji tafara magana”” dakarfiii yakirah sunantaa eeshaa tazaburah tamike zaunee””” dakinta ne taji yasoma juyawaa””” wani haskee ya bayyana saiga fuwail fuskar nan tashi tayi wata iri”” cikin kakkausar murya yace eesha dagayau bazan sake barin maleeek ba kifadamun kinasona kobakyasona””” cikin kuka tace banasonka fuwail wlh banasonka bazantaba aminta dasonkaba wlh dana aureka nafison namutu ahakan!! 
       Wato kinfison nayikoma mezanyi??? Lallai yau babu makawa saina kasheshi tundahar yafara tasiri azuciyarkii idan nakasheshi saikiyita zama ba auren nima zankasance ahakan har karshen nunfashina take yazama guguwaa dakarfiii tace fuwail Dan Allah karkayiii
Saukowa tayi daga kan gadon”””” zanen gadon yatadeta tafadii kasaa Sam batadamuba labbanta take zuka soma zubarda jini tafito dakin zuwa cikin falonta kofar”” zata budee akajata da karfiiii gagab tarufee tayi Jan duniyaaa Amman kofar taki budewa kuka take tanakiran sunansa ganin badawowa zaiyiba 
Takoma dakin dagudu mabudan kofar tadauko tabude hannunta sairawa yakeyii tayi saman “” dasaurii taturah kofar””” maleek yana zaune jin an banko kofa dakarfiii yasashi saurin mikewa arazaane tsaye tayi tana kallonsaa
Sannan tasake fashewa dakuka dagudu tafada jikinsaa “”” wani iskanee mai karfiii yaturee maleek yayarbashi akan gadon””””
Kyautaa tasake tsorata dasauri takomaa gaban gadon”” takareshi da hannuwa cikin muryar kuka tasoma magana ya isah haka fuwail abunnaka yasoma kaini bango””
Karka kuskurah katabamun mujina karigada kamakaro tundahar kabari na auresi “”cikin kakkausar muryaa mai amsa amo wacce itah kawai takejinsa yace kenan kina sonsaa tayi saurin gwatseshi tace kwaraai inasonsa kayi duk abunda zakayiii 
Nadaina boye abunda yake zushiyana dagayau”” fuwail inason mijinaaa kuma dashi kadai zanyi rayuwa bazantaba daina rokar maka Allah yawulakantakaba kar Allah yabaka abunda kake nema duniya dalahira””” 
Wataaa kururuwaa tajiii”””” take dakin yasoma juyawa”””wata irin guguwaaa tasoma tashi inda tasoma daukar kayan dakin tana jujuyasu sunafaduwa komai nadakin yahargitse fankar dakin gudutakeyi nafitar hankaliii cikin sauriii tajuyaaa wajen maleek Wanda yasoma tariii fadawa tayi jikinsaa tana kiran sunansa”” komai bai iyah furtawa ta kankameshiii ajikintaa wurgiii da itah akayi gefe harkanta yabuge dagini take yasoma jinie Sam daga kyauta har maleek addua tabacemasu ganin abunsukeyi tamkar shirin film
Cikin karajiii tace wlh fuwail duk wani Abu yasameshi wlh sainakashe kainaa duk tsiyarkadai bazaka aurii gawabaaa”” chak iskan dakin yatsayaa””wata kururuwa yayi wacce taisanadin fashewar gwalof din dakin duhu yawanzuu bamaiganin tafin hannunsa sannu ahankali komai dayake yawo yadaina motsiii komai yakomaa daidaiii
Kyauta tana rakube jikintasai rawa yakeyi idanuwanta kulle suke gam maleek ne yasoma lalubar wayarsa yadauko yakunna fitilar cen rabe dabango yahangota jikinta har mazari yake saihada gumie take kamar wacce tayiwanka daruwa dasauri yasauko saman gadon zuwa indatake yana dafata tazabura””” cikin saurii yariketaa yace ninefa bude idonki”” cikin tsoro tsoro tabude idontaa yahaska fuskarsa dafitila kuka tafashe dashi tafada jikinsaa tace inafatar babu abunda yasameka bazan bari yacutarmun dakaibaa
Hannunsa yasaka yana bugabayanta alamar rarrashi yace kidaina kuka eesha babu abunda zaisameni””” 
Dasauri tadago tanakallonsa hawaye wasu nakorar wasu tace wlh mugune ya maleek zai iyah aikata komai nidai tsoro nakeji karyarabani dakaiii mubar gidan nan Dan Allah ya maleek tasake shigewa jikinsaa tanakuka馃槶

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

         123-124

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Tashi yayi daga dukinda yayi yamikarda itah tsaye haryanzu tanalafe ajikinsa saman gadon yakoma”” yace zauna nasake wani golof kaitagirgiza tace nidai muje tare””” 
Tanarike da gefen rigarsa kamar Wanda zaigudu haryasaka wani kwan”” gabadaya dakin ya gauraye da haske”” saman gadon suka koma yakalli goshinta inda haryasoma yinfushii”” haka labbanta”” yashafo labban da yatsansa”” yace menene yajimiki ciwo abaki””” itah ma labban tashafo saiyanzu tatuna abunda yajimata saikuma tacemasa bakomai
Yanisa sannan yace please eesha kisanardani menene yake faruwa??? Wanene fuwail???? Shiru tayi kanta yanakasa”” yadago fuskarta yace meyasa baxaki fadamunba???? Tace kayi hakuri yace duk wanda nafadawa saiya kasheshi”” tayi saurin toshe bakinta saboda kukanda yatasomata”” kaiyagirgiza yace eesha menene akeso dukkan musulmi yayi imani dashi??? 
Tace Allah yace sannan??? Tace mala.ikunsa saime??? Tace da littafanda aka saukar” uhum tace da manzanninsa “” yace uhum tace daranar lafirah”” yace sannan kuma me??? Yayi imani da kaddara maidadice komarar dadice”” yace yauwa 
Munyi imani da kaddara kowacce irice sannan kuma babu wani abun halitta daya isah yacutarda wani saidai idan abunda akarubuta masa 
Duk abunda yasamu bawa todama hakan yake rubuce a lauhul mahfuz”” idan harkikaga namutu tokisani kwanana yakare koda baki fadamunba zan mutun 

Babu Wanda ya isah yasauya kaddararsa eesha karkiji tsoron komai kisanardani “” kaitagyada taja ajiyar zuciya tace tundanake bantaba sanarda wani wannan labarin ba”” tasake nisawa sannan tabashi labarin rayuwarta tunfarkon samarinta dayanda fuwail yake kashesu”” harzuwa marinda taimasa a skull tana tsammanin fuwail dinne dazuwan dayake amatsayin shidin yanadaukarta makarantaa
Tace inajin tsoro akan gargadinda yamun nakarna yarda nabar zuciyata tafara sonka dayake banishe nakeda ikon zushiyanaba kuma zushiyana ba tashar kallobashe dazansa remote insauyata yanda nakeso”” saigashi shikin lokashi kankani nakamu da sonkaa babu yanda banyiba dazushiyana karta tsunduma asonka saidai namakaro duk nayi sallah inarokon Allah yashiremun sonka maimakon inji hakan sainaji nasake afkawa soyayarka abinshi kanshi nadainashi 
Kawata tayi tambayar duniya akan nafadamata damuwata Amman nakiii tadago tana kallonsa tace nidai gobe kamiyardani wajen innah Dan Allah”””aransa yace kenan mafarkin danakeyi anamun gargadii akan karnabar zuciyata tasota dama eesha akenufiii
Murmushi yayi yace zaki iyah tafiya kibarni??? Kaitagirgiza tace haitare dakai zamuje saikazauna wajen mom”” murmushi yayi yace atunaninki suzasu karemu idan har Allah yanufa zanmutu??? Bakinsa tarufe tace karkasake kiran mutuwa ya maleek wlh inhar yakasheka nima sainakashe kainaa saidai ya auri gawaa”” kaiyagirgiza Yace bama zaki kashe kankiba kinsan makomar Wanda yakashe kansa dakansa duk tsanani duk rintsin rayuwa karkisake ki aikata hakan kinjiii””” kaitagyada masaa yanisa eeshaa ta amsa batareda tadagoba yace yanxu kinasona????
Murmushi tayi tashige jikinsa”” 鈽簊hima murmushin yakeyi yace bakice komaibaa”” kaitagyada”” yasake murmusawa nibajin takurame kiyimun magana najiii”” hannu tasaka tatushemai kunne sannan tace inasonkaa sosaiii dariya yasoma yace toni aibanjikiba”” tace au hakanefa”” to miyidima masin yakwalalo ido aikinsake batardani”” 
Cikin shagwaba tace kai Yaya !! 鈽筜ace kinsan sarai banajin yarenki tokifada da larabcii”” tace to idonta tarufe馃檲 sannan tace ana ahabukaa ya habiebie!! Yace inyeee ashedai ta iyah larabcii jikinsa tafada tana dariyaa Sam tama manta da abunda yafaru yanzun

  Yace a ina kika ajeni??? Hannu sa tariko tadorah akan kirjinta tace shen shikin zushiyana””” wani dadine Yakama maleek yasake kankameta

“”Cikinta yashafo yajishi cen lafe yace Amman bakici abin莽i ba””” tace aikaima bakashiba”” yace aini banajin yunwaa tarausayar dakai kai kenan ballantane nidabanje ko inaba”” kinga bari nasama maki koda tea ne kafin kikwanta”””
Tace idan bazakasha ba nimafa Bashan zanyiba “”” yace tonajiiitashi muje””” zatamike yadauketa kamar diyar beby haka tafara witsil witsil da kafafuwa tamkar wacce akewa chakul kuliiii”” 
Saidariya yakemataa”” yabude kofar datake kusa datashi kyautaa taware ido ganin wani hadadden kitchen”” bakisake take kallonsaa
Saman lokokin wajen yadorata yace bari nagama””” gass yakunnawa wutaa haryadorah ruwan tea din binsa kawai takeyi dakallo”” 
Bayan yagama yajuyo wajentaa murmushi yayi yahurah mata iska ga ido yace yadai???/ 

Murmushi tayi tace bansan dawanna帽 kitchen dinba haryafi nawa kyau
Juyawa yayi yadanyi tsalle yazauna saman drawer ta kitchen din yace wannan namaigidane kokindauka kune kawai kuka iyah girkii??? Tayi fari da ido tace todakumafa???? 
Dariya yayi yace kina kara kyau idan kikai haka”” tasakeyin far farrr da ido”” tace bawannan ba Amman waya koya maka girki???
Yace wai santii kikeyi tunk脿fin kiji kalar girkina idan kikaci abunda nagirka saikin katse yan yatsunki dariya tasomaa tazungureshi akafada tace ba anan takeba saikayii naci idan banyi santiiba kayarda mata sunfiku iyawa””” takasan ido yake kallonta脿 yace nayarda yayi maganar tareda dirkowa saboda ruwan sai tafasasukeyi”” 
Cikin kitchen din yahada tea din maikauri yazuba cikin cups din””” zata saukoo yace dakataa”” 
Tsayawa yayi yana kallonta dahannu taimasa alama yadai ??? yace kitaimaka kicire wannan hijabin”dafe jikinta”tayi taturo bakii tagirgiza kai umm umm””馃槰 
Yace please” itah ma tace please”” taresukasa dariyaa”” yajuya hautomuje saman bayansa tahaye yadauki cup kowane ahannu daya yace kirikeni dakyaufaa

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        125-126

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

 Dariya tayi sannan ta kankameshi”” saida sukashiga dakin yaduka tasauka”” sannan yamikamata dayan cup din shima yazauna yasoma shan nashii”” 

Bayan sungama yace takwantaa ganin tanajin barci kuma har biyu saura”” takwanta yatofeta da addua sannan yadauro alwala yashimfida abar sallah yasoma nafila
Saida akayi kiran asalatu sannan yatasheta”” tadauro alwala yawuce masallaci”” baidawoba har saida haske yafara game gari”” 
Bayan tayi sallah”” kitchen tashiga tahadamasu break taje tayi wanka”” tashirya”” tunda”” yashigo gidan yashaki kanshiii tareda lumshe idonsa wani farincikine yake ratsashi harcikin ransaa”” dadan gudu yahaye saman””” cikin falonsa yasameta zaune tanaduba littafanta””
Tsaye yayi bayan yaturah kofa tadago tana kallonsa murmushi tayi tace karaso mana”” kafada yamake cikin shageaba yace saikin taso”” murmushi tayi tarufe littafin tataso”” hannuwa yabude alamar tataho””” cikin jinkunya tatafi tashige jikinsa yamaida hannu yarufeta tareda saukarda sansanyar ajiyar zuciya yalunshe idonsa”” ahankali tace morning yayana””
Dagoda itah yayi yace banason wannan gaisuwar”” talangwashe kai tace to wace kakeso”””馃 yace yauwa bari nakoyamaki 
Tsurutayi tana kallonsa taga kalar gaisuwarda yakeso”” yace kamar haka saukar labbansa taji akan labbanta””” yadago yana lumshe ido””yace tokamar haka zakiyi”” hannu tasaka tarufe fuskarta tace wlh kunya nakejii”” 馃檲yace saifakinyi idankuma bahakaba bankarba gaisuwarba”” tace tozanyi Amman saika rufe idonkaa”” yace naji zanrufe 
Idanuwansa yarufe kasa kasa yana kallonta”” kirjinsa tabuga dawasa tace naki wayon wlh bakarufe idonba”” yasake runtsewa toyanzufa??? 
Saida tadanyi Jim sannan tasunbaceshi akumatu””” yace keyahaka aiba anan nacekimunba anan”” yayinuni dabakinsa tace to kamar tayi kuka 馃槴sannan taimasa”” yamurmusa kokefa antashi lafya”” tace kalau tana noke kantaa yace waiii kina nufin kunyana kikeji??? Lallai akwai aiki ja agabana”” 

Tayi murmushi muje kakarya karfa namakara skull Yace inazuwa bari nayi wanka nashirya saimufita tare kafin nan kidamamun coffee tace to tareda fita shima yayi shirin wanka yashiga toilet kusan tare sukagama kodata shigo harya shirya””” 
Taresuka jerah zuwa saman dinner din tazuba masa tea yace tasha kawai shi coffee zaisha 

Bayan yasha yadorah da soyayyar doya maikwai da farfesun kayan ciki sosai yaketa faman santiii kyauta tana dariyaa”” 
Saida suka gama yadauko mata littafanta suka fito”” wata sabuwar mota tagani sai kyalli takeyi”” wajenta suka karasa yabudemata tashiga sannan yagaya mazaunin driver”” 

            Yatada motar suka gaisa damai gadi yabude masu kofa sukafitaa tana kallonsa tace motarkafa??? Murmushi yayi yanakallonta yace yaune sarauniyar kyawawa zatashiga motana aganina baidace nahau tsohuwar motaba saboda mutunta wannan ranar””
Zatashiga cikin tarihin rayuwata dagajiya zuwa yau jina nakeyi tamkar wani sabon mutum daban bantaba jina awannan yanayinbaa
Hankalinshi yanakan tukinda yakeyi”” yace yakikeji ayau??? Murmushi itah ma tayi tace wani yanayi Wanda bazai faduba fiye danaka””” 
Ajiyar zuciya yayi yace meyasa tunfarko bamushiga wannan shaukinba””” talangwashe kai tace saboda fadanda kakemun”” 
Dariya yayi wacce take kara haskaka fuskarsa” aranta tace waidama kana dariya haka??? Azuciya tayi maganar Batasan tafito filiba yace inayi mana 
Tace waikaji abunda nafada shikin zushiyana fanayi maganar??

Yace kikegani Amman ainajiyoki””” daidai sunkawo get din makarantar 
Kaitsaye yawuce ciki gindin wata bishiya yatsaida motar yajingina dakujerar yana kallontaa”” tace waikasan me??? Kaiyagirgiza yace saikinfada”””
Tace wlh kunya nakeji kagafa ranar abunda yafaru a idon mutane yace toshine me mijinkine kikamara bamijin wataba ko saurayin wata oyaa fita muje harbakin holl dinku zan rakaki naga Wanda zaiyi magana””
Yayi maganar tareda bude kofa yafita yazagayo kofarta yabude tanazaune ko motsi batayiba hannunsa yadorah akan motar yace kifito mana””” cikin shagwaba tace kallifa tunkafin nafito yanda akebinka dakallo
Yace banisuke kalloba motarnan suke kallo yarike kugunsa yace kokifito wlh kona daukeki cikin saurii tace ah ah zanfito wlh”馃 littafan dasuke saman jikinta yadauko yajawo hannunta”” tanafitowa tayi saurin jaye hannunta tana sanne kanta ganin idanuwan mutane sunyimasu chaaa
Sunsoma tafiyaa yana kallontaa bakaramar dariya tabashiba yace hankali ramifa agabanki”” tayi saurin kallawa yakyalkyale da dariyaa yana tafa hannu”” bakitaturo tace kai ya maleek”” gwalo yamata yace sowie
Dariya tayi ganin yanda yayi maganar yakwaikwayi muryantaa”” cikin so dakul脿awa yake kallonta shibaitabaganin Wanda komai kyau yakemasaba samada eeshaa komai nata burgeshi yakeyiii
Duk abunda tayi saikaga yasakefito da kyanta脿 gabaday脿 hankalin mutanen skull din yadawo Kansu idanuwa kam bazasu kirguba馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖馃憖

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        127-128

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Kasa kasa tace kanaganifa yanda ake kallonmu” “” yace karkidamu”” nasan mamaki sukeyi aikinga narufemasu bakin maganar abunda yafaru ranar”” 
Hafsat ce tahangosu tafe tatunkarosu tana murmushi”” tace yau ango rakiya harcikin skull??? Murmushi yayi yadan matsa kusa da eesha cikin kunne yaradamata wannan wacece Dan Allah karna kwabsa “”

Murmushi tasakar mashi tace kawatace””sake radamata yayi yace sunanta zakifadamun tace hafsat”””
Yace yauwaa hafsat kam ganin suna kuskus yasakata dariyaa maleek yace kawarmu meyabaki dariya??? Tasake darawa tace tobazan daraba”” naga kuna gulmata””
Baki yarike yace mun boniii 馃檴taya kikasan gulmarki mukeyi??? Tace ahab bagashi naji kunce kuskusba”馃檮” yayi murmushi yace mungane wayonki sokike mufadamaki abunda mukace tomunkii sirrin mata damijine duk wanda yajishi kurma yake zama”” 

Baki tarike tace waihaka Kawata??? Kyauta tace yanda kikaji yafadadin”” tace au waikina nufin wariyar launin fata zaku nunamun??? Dadin abun nimadai inada nawa farin鈽�
Taresukayi dariya su ukun””” yace yagida yakaratu kawarmu??? Tace Alhamdulillah ya amarcii”” takasan ido yake kallon eesha wacce taballawa hafsat harara”” yayi dariya yace. Muna nan munashaa sauranku”” bakinsa yarike yasake matsawa akunnen kyauta yace Allah yasadai batayi aureba??? Dariya tasaka tace kaikajiyo tunda bakinka bayaciwo dasurutu kasanfa aiki zakaje”” 
Yadan marairaice fuska wlh banason tafiya koda naje hankalina yana nan Amman bakomai dazaran aiki yaragemun zakiganni inafatar kinzo dawaya
Tace nazoda itah Amman aini zaka hanani karatu idan kazo kasamu inatsakiyar karatufa”””
Hannuwansa yasaka cikin aljihun wandonsa yace ba damuwa sainashiga ajin nima akoyardani””” sukasa dariyaa tace mujenidai narakaka sainadawo kagafa ankusa shiga”” yacee umm tomuje yakalli hafsat yadaga mata hannu kawalli tosai anjima”” tace uhum Allah yakai lafiya yace Ameen
Taresuka jerah suna tafiya yace Amman kawarkin nan akwaitada fara.a”” takalleshi tace ganidayafa kaimata”” yace waya fadamaki ainatunata ranar bikima naganta saidai sunantane bansaniba shiyasama kikaji harna tambayeki
Tace hakane natunaa”” wlh sosai akwaita dason mutane kaganta wlh banadawata Kawa samada itah kokadan ban yarda damatan skull nandinba Amman hafsat nayarda da itah 100%

       Yajinjina kai yace hakane nima nayabada hankalinta saudaya danaganta daidai sunkai wajen motar”” yace kashh kalli books naki inda nabarsu”” zatadauka yarigata dauka Yace bari narika maki””
Tarausayarda kai kaikuma dazaka wuce??? Yatari nunfashinta bayan nasake rakakiba”” ido taturo lallai rakiyar zomo za ayi”” yace um um danarakaki sainadawo nikadai”” 
Tace kanason wahalda kanka”” yace banjinta ajikina??? Suka juyo tace menene??? Yace wahalar sunkusa kaiwa wajen da Hafsat take jirantaa takarbi littafanta 
Taredacewa nagode hannu yagyada yace aikinane ai””” yanisa nizan wuce kikularmun dakanki kinji idankuma akwai wata damuwa kikirani ayikaratu dakyau
Tace kaima haka”” yawuce abunshi”” tajuya zuwa wajen hafsat””” tasamata dariya wlh kinburgeni sosai  

                Bakiga yanda kukai kyauba nadade inajiran wannan rana”” wlh kai yau inacikin farinciki marar misaltuwa!” Kyauta ma murmushi takeyi hafsat tarage murya tace Amman banyi tunanin maleek yanada Faraa har hakaba adafa gaisawa kawai mukeyi kodai danyaga sarauniyar batason yakulataa
Kyauta tace hmm arantakuma tace ai hafsat dakinsan kowaye kike gaisawa dashi alokacin dazaginda zakimasa nikaina bazanyimasa irinshiba””
Hafsat takatsemata tunani tace yakikace hmm kodai angyarotane???? Kyauta tace sosaima tareda kanne ido daya”””

Taresuka shiga holl din”” inda daukacin mutane sukebinta dakallo bayan sunraka motar maleek damayen kallo nasanwani haryace Allahumma arzukuni gadai kyau gakudi gatsaleliyar mata ga katon gida ga motaa
Shikam aiyamore”””” 

Bayan sunfito lecture suna zaune”” hafsat tace waikinsan me??? Wlh tunda mukashiga aji tunaninku nakeyi sosai naji inason aure”” inaso mijina nima yadinga tarairayana kamar kwai””” kyauta tayi dariya tace ina Aliyun ki??? Murmushi tayi cikin nunajin kunya yana nan wlh”” kyauta takaimata dukan wasa tace ja irah nikikejiwa kunyaa”” hafsat takauce tana dariya
          Tace dolene najikunyarki”” mana aikinga yanzu kece babba tunda kinada aure idan zanyi aure kece zaki koyamun yanda ake tarairayar miji””” tayi maganar tanaboye fuskarta jikin hijabin kyautaa
Um um nidai daina boye washikin hijabina bayan kingama”” magana””” nikam bansan komaiba”” hafsat tace bawani wanne karatunne baki hardaceba””” kyauta tace narashin kunyaa
Sukasa dariya hafsat tace waikwana biyu banzo skull ba Amman koki kirani””” kiji kolafiya”” kyauta tace hakuri wlh Nima banzo skull ba tunranar Monday damuka rabudake
Hafsat tace kaihaba Allah yasadai lafiya kinkuwaji gulmarda akeyi a skull din nan??? Inashigowa akafadamun kinsan magulmata basagani saisun magantaa tsabar hassadane kawai ganinku danayi yakoremun shakku wlh”
Kyauta tace mesukashe maki??? Tace hm waicewa sukai Kawata tamari Wanda yakezuwa daukarta dangidan senator bakiji yanda jikina yakama rawabs wlh natsorata sosaifa dannasan zaki iyah
Kyauta taharareta tace kenan harkin yarda”” ???馃檮

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        129-130

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheen

Hafsat tace bancebafa”” ainasan karyane”” tokibarshi ahakan tunda bakiyardaba kyauta tacemata haka””
Tace nabarshi Amman sainayimata rashin mutunci tunda take gulmarki”” tace wafa???? Baki tatabe tace wacece banda rabi atu”” 

Tace Dan Allah kibarta nibanason kina fada dakowa”” hafsat tace aidolene akanki babu abunda bazan iyah yiba tamurmusa Allah yabarni dake my hafsat “”” tace amee帽 waime yajimaki afuska”” sai lokaci帽 tashafo goshinta tace cikin duhune nafadii sainabuge Kaina 馃槰tace ayya sannu tace uhum yauwa Hafsat

           Waime yasa naji kawayenki sunacemaki hansai ko iyya hansai ko mai shareef””” hafsat tayi dariya tace baryan iska rainani sukayi bakamar haneefatuwa”” kyauta tasa dariya tace wacece kuma hakan??? Tace bar yar iska wata kawatane tarainani sosai kamar wata abokiyan wasanta aikibari watarana zanzo da itah hargidanki”””

          Baki tatabe kima barta nibanaso inajin ana batamaki suna iyah hasy sunan tsoffine”””

              Hafsat tace Kawata kenan to idan zatayi aure zakije aiko?? Itamafa bafulatanace”” difff kyauta tasha toka tareda mikewa”” fuskarta hartasoma sauyawa hafsat tamike dasauri meyafaru Kawata?? 

Kodai maganar fulanin ne bakyaso???? 
Batace komaiba tace tashi muje lab muyi assignment kinsan anjima kadan zaishigo kuma wlh banyiba saboda bansamu lokaciba””
Hafsat badan taji dadiba ganin yanayin kawarta yasauya sukadau littafansu sukayi hanyar lab
Karfe shabiyu yakirata””” lokacin zasu shiga aji tadauka tareda sallama daya bangaren ya amsa tace barka da aiki”” yaja ajiyar zuciya yace wlh banyi aikin komaiba kudin dad kawai naturah wadanda za ashigoda kaya ga aiki gabana Amman nakasa komai””
Talumshe ido tace saboda me ya maleek”” ??? Murya akasalance yace saboda kemana”” tadan zaro ido tace nikuma??? 馃槼Kaiyagyada kamar tana ganinshi sosaima kuwa gabadaya tunaninki yahanani sukuni 
Inaganin zandauki hutu konasati ukune nimadai insha Amarcina aikuwa kamar kasa ta tsage kyauta tashige tunda yajishiru yasoma dariya kunyakike jine”” taturo bakii aikaine saikarika fadar abunda kaina bazai daukaba”” 
Yace afuwan bazan sakeba yanzun kungama inzo??? Tana kallon hafsat tace saizuwa daida rabi”” yace okay sainazo bari nadan duba wasu takardu kikasance cikin amincin Allah tace Ameen taredakai sukai sallama tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya takalli hafsat mujeko

         Suka wuce”” tare””” karfe daya da minti goma suka gama bakin get din sukafito har anzo daukar hafsat”” tace bazanje ko inaba sai ya maleek yazo”””

           Da motar sukadan jingina jiransa tsayinsu baifi mintuna biyarba motarsa takawo harzaiwuce ciki yagantaa yadawo dabaya “” bayan yadaidaita motarsa yafito

            Da murmushi akan fuskarsa”” hafsat tace badai harkazoba da rabifa akacemaka??? Agogon hannunsa yakalla yace tomeyayi saurah banason tatsaya jirana saigashi Kuma saida namakara””
 Sukai sallama hafsat tawuce”” zasu shiga mota gabanta yabada rasss dasauriii tahau dube dube”” illai kuwa cen nesa dasu tahangoshi cikin kananun kaya”” yadorah rigarnan mai hula tarufemasa fuskaa””” aikuwa kyauta dasaurii tafada jikin maleek akideme yajuyata yace lafiyaa eeshaa??? Hannunta yanarawa tace shi shi nagani””! Yace wanene??? tace fu fu fuwail nagani””” yace mata a ina dahanzari yadago kansa yabi yatsanta dakallo inda tanuna wayan bakomai yamaida kallonsa wajenta yace banga komaiba”” tace wlh anan naganshi ya maleek saikuma tafashe dakuka tace muje gida nidaii
Rirrikeshi tayi dakyar yasamu tashiga shima yazagaya mazauninsa””” ajikinsa talafe inda jikinta yaketa faman”” kyarma”” 

                 Sunsoma tafiya Gaban tane yasake faduwa”” dasauriii tatashi daga jikin maleek tahau waige abayan motar taganshi zaune yadorah kafadaya akan dayaa
Ihu takwatsa tace ya maleeek dakarfiii馃檳 Wanda hakan yasaka yataka burki dakarfiii sauran kadan motar takwacemasaa””” 
Daidai gefen hanya yatsaida motar””” yana jijjiga kyauta wacce tajima dasomewa””

Gabadaya maleeek yakidime addua yasoma tofamataa””” bayakokai karshen wata yajawo wataa ruwan dasuke cikin motar yadauko yasoma yayyafamata Amman komotsi batayibaa”” 

               Karatu yakunna kira ar sudes yaja motar dasaurii yajuya hanyaa zuwa hospital”””

Fuwail dayake gefen wajen yayi wata kururuwaa wacce babu maijint脿a sosai yawahala akan maleek duk yanda yaso cutardashi yakasa koda tabajikinsa 
Shiyasa yabitawan nan hanyar atunaninsa dazaran eesha tafirgita脿 sai maleek yasaki kan motar shikuma alokacin zaicire tayar motar saiyadauke kyautaa motar tanafaduwa yakonata ko tokar maleek baiso asamuuu””” saigashi Allah baibashi sa aba”” yasake kecewa dakuuwa Wadda tai sanadi帽 firgicewar dabbobi sukafara gudu wadanda suke daure suka furgice suna zagayen inda akadauresu take yabace!!!

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

      131-132

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Sun soma tafiya ahankali tasoma motsawa””” zumbur tamike lahaula wala kuwatii illah billah””” saiyanzu hankalin maleek yakwantaa ahankali yakoma gefen hanya yatsaida motarsa”””
Shiru yana nazarinta daga bisani yakirah sunanta”” tace na am hawaye yana saukomata akan fuskarta yace meyasa kikayi ihu lokacinda kika ganshi??? 

Tashare hawaye tace wlh ya maleek danaganshi natsuwata bashewa takeyi””” 
Ni wlh atsorashe nake dashi Dan bayada imani banajin tsoron komame zaimun banasodai yarabani dakai”” murmushi yasakar mataa yashare mata hawaye kikwantarda hankalinki babu abunda zaifaru dayardar Allah kikaddara daga kaina bazai sake kashe kowaba
Allah baya barin azzalumie banga dalilinsa nafirgitamun keba”” gabace dani yakeyi saboda na aureki kuma narigada na aureki danbakida wani Miji bayan Abdul maleek””” murmushi tasaki harsaida hakoranta suka bayyana””” yace kokefa banason kina kuka kuma kidaina ihun idan kikaganshi kiyawaita addua insha Allah babu abunda ya isah yamaki”” 
Yanisa yaukinyi azkar dasafe???? Shiru tayi saida yasake tambayarta tace wlh namantane”” inasauri indorah mana break”” 
Yace toda gayau kirikayi kafin kidorah break karki damu zanrika dawowa masallacin dawuri saimu hada break din tare tagyada kai taredacewa to yace yauwa yanzu yakikeji kodai nakaiki hospital???
Tace ah ah bazaniba ailafiyana qalau”” yace tsayadai kodai tsoron allurah kikeyi????馃 Tanoke kantaa yace kuma kike so kizama Norse???? Lallai akwai aiki za ayi doctor matsoraciya 
Tasa dariya tana boye fuskarta”” motarsa yajaa”” yawuce kaitsaye gida yanufa bayan yabiya yasiyamasu abinci””
Bayan sunci sukai wanka yace yau gidan inna zasuje kyauta sai murna takeyi”” yauzataga mom”” sukai wanka kaya iri daya suka sakaa”” tuncikin dinkunan bikinne daga itah harshi babu Wanda yataba sakasu shaddace ruwan omo sosai tayi masu kyau”” 
Sukafito yabude mata motar tashiga yazagaya mazauninsa”” bayan yazauna yajuyo yakurah mata ido bayako kyaftawa””” dariya tasoma wacce tasakeyi mata kyau”” tasaka hannu tarufe masa ido wani laushi yaji ahannunta tamkar auduga”” kiss yasakarwa hannu tajaye dasauriii tana yarfe hannu”””
Tace waiba tafiya zamuyiba?? Yalumshe idonsa yabude ya girgiza kai”” sainagama kallon kwalliyar nan wlh kinyi kyau sosai”” tamkar insaceki ingudu”” Masha Allah godiya ta tabbata ga mahaliccin sammai da kassai girma yatabbata ga mahaliccin wuta daruwa”” hakika bazantaba daina godiya ga Allah daya mallakamun wannan kyakkyawar matar amatsayin abokiyar rayuwata”” ba
Tace kaimafa kayi kyau harkafini”” hancinta yalakuto yace banyardaba” yatada motar yace anya kinama kallon madubikuwa???/ tace sabodame kashehakan??? 
Ah to naga idan har kina duba madubi tozaki tabbatarda kinfini kyau nesa bakusaba “”” bakita murguda tace nimadin banyardaba kainedai bakaduba madubiii
Hon yasoma yiwa maigadii”” dagudu yafito daga baya”” yana rike dawando dayan hannunsa yanarike dabutaa”” ya ajebutar””” yakaraso yace ayihakuri yallabai nadan zagayane”” yace hakomai baba””babu wata damuwako???
Yace ah to dama dai”” dayan yaro nane aka koroshi makaranta waisai an sake masa littafai saboda Na aji hudune yashiga ajibiyar dasu kumani banada halinsiya masa wasuu ataimaka aciki帽 albashina a bani dubu biyu

Maleek yace haba baba yazakayi haka nafadamaka duk abunda kakeso karika sanardani”” banason kanaboye damuwarka akan abunda baifi karfinaba
Yace haba yallabai”” dawainiyar tayi yawa ko watadaya ba ayiba daka siyamun gida kuma gatufafi ga abincii baidace inadoramaka dawainiyaba!!
Maleek yace Amman bakaji nace kadoramun dawainiyaba ninasa kainafa””” kudii yazaro masu yawa yamika masaa zaiduka yace Haba baba Dan Allah kadaina hakan kaifa baba nane”” yakarba kudin yana jinjinawa nagode nagodee yaron nan Allah yabaku zaman lafiya yabaku Yaya nagari masu jinkanku Allah yakade duk wata fitina dazata tunkaroku”””
Allah yakareku daga sharrin duk wani abun halitta”” suka amsa da Ameen maleek yace budemana kofar dagudunsa yabudemasu kofa sukawuce yanadaga masu hannu
Yadubi kudinda suke hannunsa wasu hawaye suka saukomasa Allah nagode maka daka hadani dayaron kirki 

Sosai jiyakeyi tamkar yafikowa kudiii murna kawai yakeyi””
Yakalleta”” yace mezaki siyawa muhd???? Tarausayarda kai tace asiyo sweet da biscuit”” yana kallonta kasa kasa yace daganan saikisha ko???
Ciiikin zuciyarta tace kamar kasanii yajimetace saiyace mekikace??? Tace labanyi magana bafa”馃” yace ainaji mekikace”” 

Dariya takamayi totunda kajiii shikenan”” super market sukaje suka kwaso kayan makulashe”” kamar haukaa ahanyarsu tazuwa gidan taga mai agwaluma tace saiya siyamata”” 
Dayawa yasiyo mataa””” sukakama hanyar gidan”” gidan mom sukafara zuwa bayan yayi fkng taresuka fito da ledar agwalumar ahannunta””
Yanagava tanabiye dashi dasall脿ma sukashiga “” muhd ne dagudu yarungume maleek yanamasa oyoyo
Dagashi yayi sama””” shikum脿 Yakama dariyaa”” kyauta tsaye tayi kanta yanakasa mom ce tafito kitchen tace Kaine tafe tanaganin kyauta tawashe baki kace tarekuke da yata”” murmushi yayi yanakallon gefen da kyauta take yace ah bakin dameni datambayar kinason ganintab脿 shine nakawom脿ki itah dukawa tayi tagaid脿 mom ta amsaa cikin Faraa”” tace kuna lafiya dai””” tace kalau muhd ne yace Adda menene kikawomun cikin Leda
Maleek yace adda batasiya maka komaibaa agwalumace tasiya muje kadauko sweet dinka amota”” sukafitaa mom kam tasake washe hakurii jin an ambaci agwaluma”””taresuka shigo da kayan sauran yadaukar masaa”” kyauta tace inadai anragemun nawa””” yace anragemaki adda
Maleek yace aida kace ba aragemat脿ba”” mom tace Abdul meyasa kake barinta tanasha帽 zakiii zaicutarda itah fa””” saman kujerah yazauna muhd yadane akan cinyarsa

Yace mom babu matsala “”” itah kadai take ai haryanzu batadago kaiba

Yanzu kunyar mom takeji sosai 馃槍

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        133-134

DAGA TASKAR 

Aisha Ibraheem

Mom dai batace komaiba dan itah duban maiciki takeyiwa kyautaa ganin tafada”” maleek yace yadai mom naga kinata kallonta””

Murmushi tayi tace”” nagafa duk tarame Allah yasadai bayabata wahala””” ido kyauta tazaro aranta tace kardai mom taji labarin fuwail???
Maleek daya gane abunda mom takenufii yayi dariyaa kawai”” mom talurah bayason firar tace yata mekikeso inkawo maki??? Kaitagirgiza dasaurii”” 

           Maleek yace bari mudawo gidan innah”” tace toh”” saikun dawo Amman karkuje da muhd Dan damunta yakeyi da fitina”” maleek yace to tare sukafito kyauta harda saurii take hadawa”” 
Sunafita waje maleek yasoma yimata dariya takwabe fuska”馃槖” tace menene haka”” yace kece naga duk kinwani takura bayankuma nanne wajen zamanki barito nagani wajen inna yazakiyi””
Murmushi tayi tace aigwanda mom kam danni inna kowata magana bamayi da itah mom dinma ganinkane dabakanan zamusha firanmu
Baki yarike yace dagaske toni menatare maki”” tace wainaji mom tanashewa baya wahaldani kana nufin kasanarda itah labarin fuwail????

           Dariya yayi yace”” ah ah bakigane metake nufiba??? Tace um um Dan Allah kafadamun akunne yarada mata tadauka ciikine dakefa
Tana nufin cikin baya baki wahala”” kyauta taboye fuskarta”” tace nashigesu mom zatasa nasoma jinkunyarta””馃檴
Dariya yayi yace barikiji wani Abu saitin kunnenta yaje yace yauzanyi kokari nasama mata jikaa kartadauka nidin ragone”” baki tarike tace wannan kayan kunyar badaniba wlh daidai sunkai kofar gidan tashige dasaurii”” 
Cikin harabar gidan yatsaya “” Dan duk yazo gidan bayashiga sai yakirah muhd yafadawa innah zaishigo”” su gaisa duk da”” bata iya kodago kantaa””” 
Tanashiga tasamu innah Zaune saman tabarma”” tana sauraren redio tayi sallama tadago ta amsa mata sallamar”” kusa da itah tazauna tagaisheta ta amsa dasakin fuska tace kuna lfy”” qalau inna”” tace ya maigidan nakii””
Batace komaiba saidai tasosa kai”” innah tace inapatar babu wata matsala”” tace babu innah”” 

Shiru sukayi nadanwani lokaci Sam takasa cewa innah taresuke da maleek sallamar malam sukaji”” yanacewa kashigo mana gidan nan kamar bakonka “”
Yanashigowa yace Ahab waikana nufin tare”” kuke da kyauta??? Murmushi yayi kawai”” inna kam kunya taji sosai yaduka yagaisheta ta amsa cikin jinkunya tashi yayi yamasu sallama””” 

Malam yace katsaya mana mushi abinshi saimuje sallah tunda ankusa la asar”” yadan sosakai yace Alhamdulillah Abba”” dama inason zuwa gidan usman ne””
Yaron wajensa ne bashida lafiyaa”” yace Allah sarkii toka gaisheshi”” dajiki yace to zaiji yasake yimasu sallama yafita shikanshi kunyarsu yakeji yanzu
Bayan yafita kyauta tadago tace Abba inawuni yace lafiya qalau diyar Abba haryanzu dai sangar tarnan tana nan??? 
Boye fuskarta tayi tanadariya!” Innah tace wai Ashe tundazu taresuke Amman tabarsi waje”” nikam bansan lokashinda kyauta zatadaina shiriritaba”” 
Tamike tadaukomasa abincinsa “” kusa da kyauta yazauna yace wanko hannunki mushi “” tana murmushi tamike tawanko hannunta taresuka ci abincin yanayinda yatunowa da kyauta rayuwarsu ta rugarsu”” harsaida tayi hawaye tagogesu danbatason iyayenta sugani zasu shiga damuwa malam jiyakeyi tamkar yahadiye kyauta yanasonta sosai dantana kama da mahaifiyarsa 

Dun yanada hoton mahaifiyarsa kullun idan yaga kyauta saiya tunada itah”
Gidan inna tawuni saibayan sallar isha I yashigo gidan waje yatsaya yakirata yace tafito suwuce”” zaune tayi takasa tashi inna takura mata ido tace waibashewa yayi kijeba”” mekike jirah sai alokacin tatashi taimata sallama”” innah tace kishiga daki Abu nanan kishanye tace to

             Nonon rakumi ne maiyawa takafa kai said a tashanye sannan tafito tayimata saida safee tace Allah yatashemu lfy
Tafito sukawuce gidan mom”” sunsamu malam da alhaji kabeer sunacin abinci”” taduka tagaidashi ya amsa yana tambayar zamansu tace lafiya qalau”” dakin mom tashiga tabar maleek anan”” mom tajata kurya tabata wasu kaya tace kisha ahankali saboda abunda kike Dauke dashii batace komaiba”” sukafito lokacin maleek yahau saman Sukamata sallama kyauta tasoma saukowa” mom tacewa maleek tafara zuwa asibitine”” juyowa yayi yace mom wlh yarinyar nan batada komai””
Mom tace to Allah yabada masu albarka yace Ameen”” tare suka sauko yamasu malam sallama yawuce mom harwaje tabisu saida taga fitarsu tadawo
Tunda suka soma tafiya maleek yake Satan kallont脿 takasan ido jinsa yakeyi tamkar yaune aka kaimasa kyautaa””
Harsuka kaigidan itakuwa gabanta faduwa yakeyi danbata manta da abunda yaceba”” taresuka fito yadauki ledar kajind脿 yasiyo sukajerah tace ya maleek agwalumatane kadaukomun”” yace ah ah kinmanta da itah gidan innako”” wadan nan kajinki帽e Na amarcii inafatar ashirye kike”” 
Tadone kanta kawai zatawuce yarike hannunta inakuma zakije??? Tace wanka zanyi”” yace shikenan inajira帽ki tawuce dakint脿 shikuma yahaye saman
Tanashiga tazauna akan gadon tanatsoron jin abunda yace Amman batajin zatahan脿shi hakkinsa jiki asanyaye tarage kayan jikinta tadaura towel tashiga toilet
Bayan tafito tatsane jikinta turarukka masu kamshi tashafa simpul makeup tayi tadauko kayan barcinta masu kyau bamasu shararaba tasaka”” tacire hijabinta tawarware Sumarta tasoma tajewa Dan taharde mantawaa matakeyi dabatayi kitsoba dama kitson baishamata kaiba””
Hannunsa yadoramata akai tace wash tareda dafe goshinta jinyayi mata nauyii”” iska yasoma huramata afuska talumshe ido”” take tasoma hamma tasulale kasa saibarci
Fuwail ne yabayyana yana murmushii”” take yasoma girgiza saigashi yadawo sippar kyaut脿 harkay脿帽da suke jikinta

        Yashafa sumar dahannuns脿 take tadaure kantaa”” wasu takalma yadauko yasaka yasake kallon kyauta wacce taketa sheka barcinta yakece dawata mugunyar dariyaa tsayin mintuna sannan yagimtse fuskarsa tamkar bashine yayi dariyaba
Nant脿ke yasoma kuka”” eesha nikika ki akan Abdul tokisani yauzan gamad脿shi bake bashi har abada bakida wanimiji bayan帽i bazan bari maleek y脿kwanta dakeba!!!
Fitowa yayi dakin yasa key yarufeta sannan yayijifa damabudan”” yasake gyara rigar yawuce saman cikin takun Jan hankali

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        135-136

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Ahankali yaturah kofar””” cikin falon yasamu maleek yana danna laptop””” kamshin turarenta yashaka yalumshe idonsa sannan yabude””” “” 
Kuru maleek yayi yana kallon halittar jikin kyautaa tsaye yayi abakin kofar yanajifarsa dawani mugun kallo”” azahiri maleek zai dauka kallon soyayyane Amman awajen fuwail kallon yau kwananka yakare yana Balain jin haushin maleek kasancewar yanason rabashi da farincikinsa
Bayajin zai iyah hakurah dakyauta saboda tashice saboda shikawai akayitaa””” 

 Cikin kasalallar murya yace mata karaso mana”” yanda takejuyi kaikace gasar sarauniyar kyau akeyi taku takeyi najan hankali tamkar batason taka kasaa””” 
Kusa dashi tazauna yana riko hannunta tayi saurin jayewa saboda wani zafiii taji ajikin maleek wani kallon tasake watsa masa Wanda yasaka duk yarikice””” dole yarufe laptop din”” tashi tayi dasauri yashige dakin Sam bayajin dadin jikinsa waimenene maleek yake sakawa ajikinsa Wanda yake jin wani yanayi duk lokacinda yaso hallakashi yana wannan tunanin maleek yashigo dakin!! Saman gadon yanufa”” yazauna yana jawota jikinsa tana nonnokewa”” ahankali yaradamata inadai kinshigo dashirinki batace komaiba yace tashi muyi sallah gashi ko wankan banyiba harkinshirya bari nayi wanka sainayi alwala muyi nafila Allah yakade mana duk wata fitina dazata tunkaromu
Shagwabe murya tayi tamkar zatayi kuka”” ahankali yasake matsawa yace meyafaru eeshaa”” cikin shagwaba tace nidai bayanzuba kafara bani labari
Shiru yayi yana kallonta ahankali tadago ido idonsu suka sarke cikin najunaa”” wani abune mai haske yafito dagacikin kwayar idonta yashige cikin ta maleek take shima yasulale sai barciii hakan bakaramin dadi yayiwa fuwail ba”””
Bangaren kyauta kuwa barcinta taketa shekawa cen cikin barcinta tasoma mafarkii sunatafiya tareda maleek cikin wani kurgumin dajiii maiyawan duhuwa””” 
Bakajin komai acikin jejin wanda yawuce kukan tsuntsaye Amman babuwani mahalukiii”” wata murya sukajiii mai kuwa da amsa amo””” tasoma maganaa
Abdul maleek!Abdul maleek !!Abdul maleek!!! kayi taurinkai kayi jayayya dani akan abunda nakeso batunyauba nake maka gargadi kafita hanyar eesha Amman kaki saida ka aureta 
Kasani iyayenka sunsiya maka bala I dahannunsu dakasan koni waye bazakayi gigin jadaniba! Kasani eesha batadawani miji bayan nii kuma yaune karshen labarin Dan ayaune zangama dakai kuma yaune zan dauke kyauta daga duniyarku zuwa duniyarmu tunda tunfarko tafara jayayya da maganataa
Kyauta tace karya kake fuwail in Allah yayarda bazaka taba shimma wannan burin nakabaa karshenka neyazo badai namijinaba
Wata dariyaa yasake kecewa da itah yace kimadaina kiransa mijinki dandagayau bazakisake ganin koda hotonshiba yanzun nan agabanki zan yagalgala namansaa
Maleeek yace karya kake”” haryanzun dube dube sukeyi danbasa ganin mai maganar saidai sujita kamar akusa dasu sujuya basaganin komai saikuma sujishi gefe dayaa”” dariyaaa yasake kecewa da itah yace kabi ahankali maleek kallon gawanake maka shiyasa duk abunda zakafada bazai batamun raibaa””” 
Amman idan harkakaini bango zanyimaka mummunan kisaa Wanda ko gangar jikinka baza asamuba”” 
Maleek yace kayi duk abunda”” zakayiii Amman kasani bazantaba rabuwa dason kyautaba kodanamutu ruhina zaikasance tareda itah”””
Yasake kyalkyalewa da dariyaa Wanda dajin ya amsa kuwa sanadinda yasaka suka rufe kunnuwansu”” wani dim sukajii dakaji wannan dariyar tashi yafimaka kayikwana uku bakasa kwayar hatsi abakinkaba
Maleek ciiikin karajiiii yace ya isah hakaaa fuwail kawai kafitooo gaba dagaba mu gwabzaa inamaiyi maka albishir nine zanzamo karshen zaluncinkaa
Yabarke da dariyaa kallaikai jarumine najinjina maka koyanzu nakasheka nasan nahadu dajaruminda bantaba ganiba acikin bil adamaa take waniii waske yafitoo su kyautaa saida suka kare fuskokinsu
Sunabudewa sukaga wani wargajejen zakiiii take abunda yafaru da dahiru na rugar ja.eh yafadowa kyautaa tatuna da mafarkinda tayi yanda zakin yayita yagalgalal naman jikinsaa”” 
Idanuwa tazarooo tarumtse idonta ganin yanda zakin yake girgizaa wutaa tanafita tabakinsaa”” zumbur tamike zufa yana karyomataa””tome yasakata yinbarcii”” tatuno da mafarki帽taa tashi tayi dasaurii tayiwaje saidai tasamu kofar falon kulle”” taduba babu key kuma tayita bugun kofar wama zaijitaa””” 
Dasauri takoma dakin tadauro alwala””” tashimfida sallaya tasoma sallah””” tanamai kuka Allah yakaremata mijintaa aduk indayake
Wajen sujjada tasanarda Allah duka bukatunta脿!” Allah yashiga tsakaninsu dawan nan aljanin”” cen bangaren maleek acikin barcinsa sunahakan saisukaga kyauta tabace
Fuwail yasheke da dariyaa yace meyasa kikatafii bakijir脿h kiga fadan masoyankiba dama anayin shadii arugarku kafin aure tomu wannan shine namu Wanda yarayu saiyacig脿ba dazama da itah
Take yayokan maleek gadan gadan tamkar kububuwa

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

       137-138

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

yana gab”” dakusa da maleek yadaga hannu idanuwansa arufe yasoma addua”” yanakai masa naushii saigashi yakoma bayan”” maleek yaturje””” wata kururuwa yasakeyi yayi cikinsaa nanma wani naushin yakomashaa Wanda yasakashi sakin wata wahalalliyar kara”” gabadaya ya abkowa maleek
Take sukasoma fada””sunata gumurzu awajen”” bangaren kyauta kuwa tana sallamewa ta dauko alkur ani tasoma karatu”” tana kuka gashi gabanta saidukan Tara tara yakeyi””” tun tanayi ahankali hartasomayi dakarfii 
Gabadaya anjiwa fuwail ajikinsa Amman baisamu yayiwa maleek ko rauni dayaba””” lura dayayi maleek zai iyah nasara akansa hakan yasa yashanmaciii maleek yabardajin 
Yarufe kofar tayanda babu yanda ruhin maleek zaibaro dajinn”” take yabayyana akusa dashiii saman gadon yana maida nunfashiii idan har ya salwantarda gangar jikin maleek dole ruhinsa yayita yawo acikin duniya harsanda zaimutu babu yanda zaiyi yadawo gangar jikinsa kuma alokacin yasan kyauta tayimasa nisaa saidai yazomata amafarki shima hakan zaiyi kokarin dakatardashi
Yasake kallon jikinsa inda maleeek yajimasa yanzu idan mahaifinsa yatambayesa menene yajimasa mezaice saidai yasanar yayi tafiyaa kafin wata daya yawarke alokacin zai auri kyauta yasha amarciii wani murmushi yayi daya gama tunanin Sam saiyaji tankarma baiji ciwoba Dan akan kyauta komaima zai iyah””

         Wata wukace ahannunsa yadagata sama zailuma ajikin maleek”” take wani haske yazo yamamaye saitinda maleek yake tundaga kafafuwansa har saman kansa””
Duk yanda fuwail yaso wukar tahuda hasken tashiga jikin maleeek Amman taki”” tamkar yanabugawa akan dutse daya matsa dabuga wukar saita lankwashe Duk da kaurinta
Sanadin dayasaka fuwail ransa yabaciii yayi wurgiii da wukarr””” yaufa bazaibar maleeek ba”” dakarfiii yatura hannunsa cikin hasken danya damki wuyansaa”” wata wahalalliyar kara yasakiii jin hannunsa cikin narkakkiyar dalmaa yayita kururuwa yacire hannunsa yakasaa
Take shima yasoma addua karfa kumanta shima musulmine yakan nemi tsari Kuma shima Allah zaikareshi danshima bawansane
Wannan azabar dayaji tamkar ana figar rayuwarsa yasakashi fara addua take darmar tasaki hannunsa aka yarbar dashi gefe
Hannunsa yakalla Wanda yayi jajir saboda azaba””” take yazube kasaa asome 

Maleek yanacen cikin jeji yaga kamar anjefo zakin Tim wajen yabude takeshikuma yabacee
Yajuya kwanciya da alamu barcin yasomayi masa dadi”” asubar fari yafarfado yabace batt alokacinne maleek yafarka jin ansoma kiran sallah”” 
Yaduba baiga kyautaba aransa yace to kuma yaushe ta tashi??? Waima ya akai yayi barcii??? Shifa kawai yasan yana zaunene saman gadon yana kallon kyauta daga hakan baikoma sanin abunda yafaruba 
Ahankali mafarkinda yayi yasoma dawomasa zumbur yamike yayowaje dasauri yasauko kasan muryan kyauta yasomaji tana karatun Qur ani ahankali yasaukarda ajiyar zuciya
Yakarasa yaturah kofar saiyajita kulle”” yabubbuga yaji shiru”” komawa yayi dakinsa yadauko wani key yazo yabude yashiga da sallama
Kuryar dakin yawuce Sam kyauta batajishiba gabadaya hankalinta ya帽a wajen karatun takawa yayi ahankali yasakeyin sallama sai lokacin tajishi tanadaga kai taganshi tasaki murmushi hannu tadaga tace Alhamdulillah
Tanakai karshen ayar tarufe Qur” anin”” dasauri taje indatake tanaduba jikinsa kamar maineman wani Abu”” babukomai ajikinsa rungumeshi tayi Allah nagodemaka daka karemun mijina”” sundade ahakan sannan yajata akan gadon yazaunarda itah yace yaushe kikabaro dakin???
Tadago atsorace tace banje dakinkaba inashiryawa kaina yasara sainaji barshi dagahaka bansan indakaina yakeba saina tsinshi kaina ashikin wani jeji maiyawan duhuwa fuwail yabayyana asuffar zakii yashe saiyakasheka zakin kamar Wanda yakashe dahiru narugar ja eh
Shine nafarka naje fita nasamu kofar arufe bangakuma key ba shine nayi alwala nafara sallah nasan Allah zaikareka da kariyarsa aduk inda kake”” gashi yakaremun kai
Maleek yashafi fuskarta yace hakika Allah yana karbar adduar mata gamijinta cikin gaggawa”” nagode da soyyyarki gareni nikaina abunda yafaru dake shiyafaru dani
Yakwashe komai yasanard脿 itah”” yace tunkafi帽 na aureki banmasan damaganar aurenba nakanyi irin mafarkin yanamun gargadin karna amince da aurenki idan nafarka nakan tambayi kaina akan wayake magana
Saida kikasanar dani labarinki sannan Nagano keyake nufii”” Allah yakara tsaremu tace Ameen yace eesha kinga karfinda addua takedashi
Baikam脿ta asamu musulmi yana sakaci da addua ba”” komeyayi tsanani arayuwa tosaimu koma ga Allah shine kadai zaisharemana hawayenmu
Bayagajiya duk lokacinda bawansa yarokeshi zaibiyamas脿 bukatarsa idankum脿 yagode yasake karomasa 丕賱賱賴 丕讴亘乇

Allahu Akbar “” Allahu Akbar

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        139-140

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

“” mikewa yayi yace kitashi kiyi sallah bari naje masallaci”” tace to tareda mikewa”” shima saiya fita”” bayan tafito””tafara sallah”” saida tayi raka atanul fijir sannan tagabatarda sallar asuba tana azakar bayan tagama”” tafara karatun Qur’an saiga maleek shima zaunaWa yayi kusa da itah suka soma karatu
Saida Haske”yafito sannan sukai addua sukashiga kitchen tare sukeyin komai harsuka kammala”” sukayi wanka tare sukayi break sannan yadauketa zuwa skull
Bayan suntashi yaje yadaukota”” dayake yau juma a ce yayi wanka yawuce masallaci”” baidawo tagidan ba saboda ayyuka dasukai masa yawa 

Amman kuwa duk bayn mintuna ashirin yakan kirah yaji Kotana lafiya”” 
Dadare kyauta tashirya masu abinci mairai da lafiya kajinda yasiyo jiya da dare tasake gasasu tayimasu yaji maidan romo tareda albasa” 
Wanka tashiga bayan tafito tazuba kwalliya”””tasaka kayan barcinta”” tasaka hijab tana fesa turare tajiyo sallamarsa”” dakinta yashigo yayi tsaye bakin kofa yana kallonta wani farinciki yakeji yana ratsashi ga kanshinta maishiga zuciyaa yalumshe ido haryanzu hakuri kawai yakeyi bainuna zakuwarsa!” Akanta kullum saiya sha magani””” da murmushi takaraso wajensa tasunbaceshi alabbansa yace yauwa nasameki lafiya”” tareda sunbatarta””” tace kalau saidai kewarka cikin rausaya tayi maganar””” murmushi yayi yace indai maleek ne gashi kinsamu”” yanzu yanatare dake””
Cikinsa yashapo nifa yunwa nakeji tun break din safe banci komaiba””” ido ta kwalalo tace meyasa Yayana”””
Kafada yadaga nikaina bansan abunda yahanani cinkomaiba saidai yanzu banajin dadin abincin kowa saina matata yakai karshen maganar yana cire mata hijab yace idan ina taredake kidaina zama dawannan bulunken haba nifa mijinkine kunyakuma name bayankuma anzama daya””

        Bata hanashiba saidai duke kanta datayi tanawasa dayan yatsuntaa hannunta yasagala cikin nashi yajuya suka fita zuwa dinner
Tare suka ciyarda juna tahadamasa ruwan wanka sannan tayi brush bayan yafito yakarasa wajen mirror yana taje sumarsa tacikin madubin yake kallonta yace kiyi alwala zamuyi sallah batace komaiba tamike zuwa dakinta alwala tayo tadauro zani tareda hijab koda tashigo haryakimtsa yashimfida masu abar sallah sukai sallah
Bayan sun kammala yadafa kanta yayimata addua taredayimata tambayoyi akan addininta”” 

Jikinsa yajawota “” yayinda jikinta yasoma rawa dasakon da maleek yake aikamata ganin zatasoma kuka yakyaleta Amman idanuwansa harsun sauya tashi yayi dasaurii yadauko maganinsa zaisa
Dasaurii tarike hannunsa takasa dagakai takalleshi yadago idanuwansa yace please akasalance””” tace maganin menene wannan???? Ahanzarce yace ciwon kai 
Murmushi tayi takarbe maganin tamiyar tareda kashemasu wutaa “” sunraya darensu cikin soyayya da kaunar juna taresukai wanka suka kwanta””
Lokaciii yanata tafiya tsayin watanni biyu maleek da kyauta saizuba soyayya suke tamkar suhadiye junansu kullum suna manne dajuna Sam sunmanta dawani fuwail tamkarma babushi aduniya
Bangaren fuwail kuwa yawarke sumul bayan doguwar jinyarda yayi wannan karon yasake shiri hardai yanda yagasu kyauta sunazuba soyayya””

Al amarin zahra kuwa”” sunacen sunashan soyayya da malam taneemu sosai yamaida itah gadon hutunshi duk sanda yakeson ganinta zaikirata tamutu akan sonsa saboda gaskiyarda teema take nasarda itah tarabu dashii sukai fada uwaka uwaka karshe suka rabuu
Rabuwarsu babu dadewa malam yasake hangowata hajiyar datazo akorarmata kishiya shikam malam yagaruwand脿. Sukaimasa yayimata kamardai yanda yayiwa zahra
Tundaga lokacin yadaina kula ta ganinma zata takuramasa yakare asirin tunda hankalinta yadawo saitadaina fitaa kwatsam sairashin lafiya bayan taje asiviti a katabbatar mata tanadauke da ciki wata biyu gakuma cutar HIV dalilinda yasaka gabadaya hankalinta yatashi tadainacin komai duk maganinda doctor yabata batashaa tarame kullum batads aiki sai kuka 
Bayan satii daya tace ga garinku dalilinda yasaka teema tatuba ganin mutuwarda zahra tayi”” mom har gaisuwa saida taje labarin zahra yakare

Zaune yake yana rubutuu wayarsa tasoma ringing yadauko sanin kowacece yanadauka kafin yayi sallama tace ya maleek kazo zaikasheni dif wayar yamutu
Dassaurii yafito yanawatsi dakaya sai tambayarsa ake lafiya Sam hankalinsa bayajikinsa bayajikinsa yanafitowa yashiga mota yajata dakarfii hannudaya yanasake kiran nomberta matarnan maimagana tanacewa kashetake
Yayi nisaa saii fiii fiii yakewa mutane abashi hanya “” kanmotar yakwace ahannunsa fuwail ne yasaukaa hanyaa da itah daganan”” yadagaa motar sama yakifetaa taketakama dawutaaa!!

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!!馃槳

          141-142

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Murna takama fuwail ganin motar takama dawutaa yana juyawa yaga maleek agefe daya cikin yan kallon abunda yafaru tareda al ajabin wannan lamarin””!!
Bakisake yake kallonsa taya akaima yafito cikin motar??? Dariyaa yaji abayansaa yanadubawa yaga gimbiya kultun tasake shekewa da dariyaa tace kana tunanin kai Allah bazai kama kabane??? Idan kayi tunanin hakan tokayi kuskure”” 

           Kanaso kakashe wannan bil adaman matarsa kuwa tanacen yanzun haka tana karatun Qur ani “” cikin ikon Allah saigashi nazo nataimakeshi Wanda nikaina banyi tsammanin zan iyah kawo kaina nandinba cikin sa o.i arbain”‘ lallai Allah majirokon bawansane
Kasani sultan banmanta da abunda kaimunba kuma akan soyayyarda nake maka yaune zanbiya ka harnamutu bazan manta da abunda kamunba dashi nake kwana naketashi””” harzuwa yau
Kasani zuwa yanzu babu abunda sarkii baisaniba dangane dazaluncinda kakeyiwa bil adama yanzun nan zakaji kiransa kuma yaune zaka amshi hukuncinka kuma zaka karbi sakamakon abunda ka aikata kafin katafiii wajen mahaliccinka aini karani nafika dakomai danbantaba cutarda bil adama ba tanakai karshen maganar tabace batt
Gabadaya fuwail yashiga rudani yasan kashinsa yabushe inhar dagaske take mahaifinsa yasamu wannan labarin bari yayi sauriii kafin tafada yalallasheta take shima yabace baikobitakan maleek ba””
Yana isah fada”” yasamu labarin mahaifinsa yana nemansa anjima idan akazauna fada cikin gaggawa al amarinda yatsorata fuwail kenan”” mahaifiyarsa sarauniya ladifatu ko amsa gaisuwarsa batayiba saboda labarin abunda yayi yagama bade fadar har kuyangin sun sanarda itah
Zaune suke afadar ancika makilll ana sauraren hukuncinda za ayankewa sultan sarki yasa gimbiya kultun tasake maimaita abunda tafada afada dazu babu wani kokonto tasake korah jawabii kuma tagabatarda kuyangin mahaifinta wadanda tasaka surika bin diddigin sultan suganomata meyake aikatawa”” 
Aka tambayi kuyangin suma suka maimaita duk abunda sukasani sarkii yadago raibace yace ashekai bakada imani??? Sultan yaushe kazama azzalumi??? Ahakan kuma kake tunanin zanbaka mulkin aljanu??? Idan harsarki yazama axzalumi babu shakka suma mabiyansa zasu zama
Inahana jama ata cutarda bil adama saigashi jinina dakansa yakashe mutane harguda uku menene gaskiyar wannan labarin inharkuwa hakane wlh zan yankemaka hukuncin kisa
Gaban fuwail yafadiii rasss murya narawa yace wlh bankashesuba babana”” duk lokacinda naga za adaurah mata aure dawani nakan jefashi dawata cutaa daga karshe saiyamutu Amman bashine yamutunba ina daukesune zuwa watakasa daban sai insa wani hadimina yayi siffarsa saiyakwanta shine sukewa sallah sukai makwancinsa dazaran sunrufeshi saiyabace sukuma nakanbasu kudii suyi sana a kuma namantardasu duka danginsu
Yanzu cikinsu ukun kowanne yayi aure harda yara biyu””wlh babana banso kwatanta zalunciba Allah ne yajarabeni dasonta
Babanshi yakatseshi cikin daga murya yace wannan maganar banzace sukuma yankauyensu daka koresu ka kashemasu dabbobi saboda kishifa yace baba kanaganin korar wulakancinda sukaiwa eesha 

Acikinsu duk dabbobin mahaifin kyauta sunanan sun hayayyafa da na baban innani duk wanda baida sahannu wajen korarta banyimasa komaibaa

Ina maineman afuwarka duk hukuncinda zaka yankemun zanxama maiyimaka biyayya Amman karkarabani da eeshaa
Dagabaya fadar tayi tsitt”” anajiran mesarkii zai yankemasa yayi gyara murya sa arka daya baka kashe kowaba Amman kasani dankana Dana bazanki yankemaka hukunciba daga yau narabaka da wannan bil adamar dasaurii yadago kansaa hawaye sunazuba tamkar tafashashshen ruwan dalma wani bahwade yake hukuncinka yatabbata sarki mai adalci
Yacigaba yauyau din nan kagaggauta maidasu wadancen garinsu sannan kanemi yafiyar wannan bil adamar dakatada mata hankali da iyayenta idankuma harbasu yafemakaba tokatanadi hukuncinda za ayimaka dakanka
Nabaka nandagobe””” jiki asanyaye yaduka yace za ayihakan babana takeyabace

Aranar yaciremasu komai yasakomasu labarin gida kowannensu yahau shirin komawa wajen danginsa脿

Maleek baisanarda kyauta abunda yafaruba”” dayasameta lafiya washe gari kafin yafita aikiii alhaji kabeer yakirashi yace maxa maxa yazotareda kyautaa yace meyafaru dad???
Bakomai kudai kuzo dasauri yasanarda itah dama shirye suke”” suka kama hanyar gidan tunda sukashiga get nabiyu gaban kyauta yasoma faduwaa
Tarike gefen rigar maleek dasukashiga gidan da sallama duka iyayensu suna zaune tanajuyaw脿 taga fuwail aikuwa tashige jikin maleek tace Yaya kaganshin脿n
Yace wanene??? Tace fu fu fuwail nant脿ke ta some ajikinsaa hankali帽 maleek yatashi sosaii mom dasaurii tadauko ruwa akazubamata tana farfadowa tasake ganinsaa tasake shigewa jikin maleek tanakuka Yaya wlh gashi帽脿n 
Dasauriii maleek yamike tareda itah zaishakii wuyansaa malam yadakatar dashii ya莽e yazauna haka yakoma yazauna yanahucii 
Malam yayi gyaran murya yace kyauta sultan yasanard脿mu duk abund脿 yamaku yanzun badaniyar cuta yazob脿 yazone kiyafemasa abunda yamaki dasaurii tadago tace inyafemas脿 baba??? Kamanta abunda yamana yasaka akakoremu rugarmu sannan yakase hamma da dahiru
Malam yace baikase subah yanzuhaka yashe sunkama hanyar komawa gida da iyalansu””” shiru tayi””” malam yace kisani Allah yanason mutum mai yafiya karkidubi abunda yamaki kiyafemasa mudai munyafem脿s脿 dama Allah yakaddara dole tasanadins脿 zaki auri maleek kuma tasanadin sa nazama hakan shiyasa komai kagani arayuwarka kagodewa Allah komai yasameka Allah shine kawai yasan hikimar yinhakan
Jikin maleek tashige batace komaiba malam yakalli alhaji kabeer yace tokasabaki kozata hakurah shima yayi magana Amman batace komaiba Alhaji kabeer yakalli maleek yace tunda takiyin magana kaikasa bakii
Yasake Janta jiki帽s脿a yace Allah ya yafemana””” mom tace aikyauta akeso tayafemasa “” yace karkudamu tayafemasa
 Malam yakalleta kaitadaga alamar eh yace to Alhamdulillah Allah yamaku albarka yakalli fuwail yace kajidai tayafemaka saidai karike alkawari karkasaba
Yace in Allah yayarda baxansake shiga rayuwartaba yashare hawaye yanakallo帽 maleek yace kamaryand脿 nafada Kaine kayinasara inamaku fatan alhairii
Tashiy脿yi yafita saifad脿r mahaifinsaa”” dama anturo wadanda zasu tabbatar k脿fin yaje har ansanardashi

Sultan yacika umurnii
Duk dahaka saida sarki yamasaa fadaa sosaiii akan abunda ya aik脿ta

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

        143-144

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

Bangarensu kyauta kuwa agidan mom tawuni sai dare suka koma malam yatattauna da Alhaji kabeer yakamata yaje garinsu Amman sai Allah yasauke inna lafiya haka sukayanke harshi yace zaibisuu
Rayuwa kenan yanzun bakuga yanda kyauta takomaba batada kokonton komai bangaren karatunta Alhamdulillah soyayyarta da maleek kuwa sai kara linkaya takeyi 

                Sam maleek baisan kyauta tanada cikiba saboda kokadan batayi laulayiba saidai tayi kiba acewarsa tasamun kwanciyar hankaline 

Innah tasauka lafiya ansamu mace ranar suna akasamata suna fateema”” 

            An aje tafiya dazaran tayi arba in” alokacin kyauta suka kammala skull tafitoda sakamako mai kyau”” inda tasoma zuwa hospital amatsayin mai taimakawa mata wajen”” haihuwa”” 
Alokacin cikinta yashiga wata takwas yanzu kam kowa yasanda cikin dan tunda yashiga wata bakwai yafito rigima sukasha da maleek akan boyemasa datayi saidai takama masa dariya wai itan kunya takeji yamazata iyah sanardashi
Alokacin sungama shirye shiryensu natafiya”” rugarsu tareda mom da dakowa mota biyu sukaje da itah saikuma motocin security””
 Koda suka karasa kauyen yana nan kamardai yanda suka barshi saidai yasauya sosai”” Dan alamu sunnuna kamar babu mutane kaitsaye wajen lamdo sukanufa sunsamesu afada gabadaya mutanen garin sunawajen anamaida magana dahiru da Dan lamdo dakuma taneemu suna zaune sunzama manyan mutane saidai sukaga motoci sunata tsayawaa sukabi motocin da kallon mamaki”” 

               Alokacin malam Abubakar yafito”” mahaifin innani yace malam habu Kaine??? Gabaadaya babuwanda yaganeshi sai dasukaji yafurta sunansa nan take waje yakaure””” 
Akasheka akadauko manyan buzu akashinfida masu suka zazzauna Amman kyauta tanamota tareda maleek tace bazata fitoba kunya takejii dole yakyaleta yafito
Suka gaggaisada anan akayita maida magana sukanemi malam yayafemasu abunda sukaimasu yace bakomai shibairikesu dakomaiba”” Allah ya yafemana”” hardo saikuka yakeyi yace wadan nan yarankane??? Cewa da muhd dakuma fateema yace ah”” “” hardo yace toya banga yata kyauta ba””

Malam yayi murmushi yace taremukazo da itah waikunya takeji yanuna maleek yace hai ga mujinta nan

 Wadan nan sune iyayensa nantake kuma akasake gaisawa hardo yace Dana kiramun itah mugaisa 
Maleek yamike yakoma motar yabude tana kallonsa yace saiki fito yanzu”” tama rairaice fuska kamar zatayi kuka tace ya maleek kallonafa za ayi inatura ciki ruku ruku
Yace toshine me baga ubansaba kitaso wlh konasake saki kiji kunyar maidalili yayi maganar yana tankwashe hannun rigarsa 

.ido ta gwalalo wai daukana zakayi ???? Yace yanzu Kuwa aikafin yakarasa maganar tayi burut tafito yanata mata dariya
Kanta yanakasa suka karasa taduka tagaidasu suka amsa hardo yace yata kiyafemana abunda mukai maku kaddarace Allah yarigada yarubutu babu mijinki anan rugar
Kanta yanakasa tace bakomai baffa taneemu yabawa maleek hannu suka gaisa”’ anata firar yaushe rabo mafiyawan maganarsu dayarensu sukeyi
Taneemu yace amman abokina kasan al adar rugarmu bama bawa bare yayanmu sai idan yayarda zaiyi shadii
Maleek yyi murmushi yace ai komenene zan iyah indai akan eeshane kuma ai muma munyi namu shadin tareda fuwail ko eesha yanakallonta yakanne mata ido daya  
Gabadaya fadar aka kwashe da dariya lamdo yace nakama yafinasu hatsarii Abdul Allah dai yadada karemana zuriar mu suka amsa da Ameen 
Inna da mom da kyauta sukawuce cikin gidan hardo””” mahaifiyar taneemu sai nan nantake da eesha taga matar taneemu Hauwa yayanta biyu tafarin Aisha anakiranta ihsan takwarace akaiwa eesha saikuma muzaffar
Dahiru ma dayasamu labarin zuwan kyauta saida yazo harda mahaifinsa “” sukam sam basuwani dauki abunda fuwail yayimasu ba acewarsu ta dalilin eesha gashi sunyi kudii bazasu taba mantawa da itah ba
Inani ma tazo dayake kauyenda tayi aure babu nida da garinsu”” sunso washe gari sukoma Amman lamdo yaki yace subari saijibi sai sutafi da baffa saiyaga waje hakan kuwa akayi
Kyauta tazagaya danginta sai haba haba akeda itah

Dasukacika kwana uku suka tattara malam yabawa alhji kabeer shanunsa duka Amman yace bazai karbaba saida jama a sukasa bakii yace toyayarda Amman dasharadin zasurika raba ribar badan malam yasoba yace ya amince
Anhadamasu shatara ta arxiki suma sunyimasu ruwan kudii”” yola sukafara yada zango hotel dinda yake zama kusan daki biyar suka kama anan suka kwana washegari sukaje company n aranar baban innani yakawo shanun
Cikin satiii biyu akagama aikin komai akabude company daganan sukarankayo gida”” hafsat washegari tazo gidan saboda tayi kewarta sosai duk dasuna waya maleek saitsiya yakemata tace tajidai komezaicema 

Ranar gidan tawuni saidare takoma gida
Al amarin fuwail kuwa ranarda yanemi gafarar kyauta aranar yabar masarautarsu 

 Kullum aikinsa kukane yayinisa zuwa dajin misra”” acikin wani dajii yakezama bayakomai sai Ibada”” 
Yana zaune gindin wata bishiya saigawata yarfulani tawuce tagabanshii kamarsu sak da kyauta”” cikin saurii yabi bayanta batt tabace 
Yanata yandube dube”” bayansa yaji sallama yajuyo dasaurii zaune take saman wata kujerar alfarma tana sanye dakaya irinna yayan sarakai “” kuyangi suna bayanta”” ta umurcesu dasu ajemasa kujera suka aje sannan suka bace””
Tadago da yalwataccen murmushi afuskarta tace kazauna ranka yadade babu musu yazauna yana fuskantarta
Tace nasan zakayi mamakin ko帽i wacece ??? Sunana gimbiya zahra ni diyar sarkin aljanuce takasar misrah
Wannan dajin yana karkashin mulkin mahaifi帽a anan nakefitowa idan inason kadaicew脿”” tunranarda nafara ganinka anan”” naji nakamu dasonka dukda alokacin bansan tarihi帽kaba 
Wannan dalilin yasaka natura hadimaina kasa kasa domin suganomun labarinka”” 
Najikomai gamedakai hakika labarin soyayyarka abundubawane saidai matsalarda akasamu bajinsinku dayaba
 Kasani ya shugabana Allah daya haliccemu mai hikimane komai yayi daidai yakeyinsaa yayi kyawawa acikin aljanu hakakuma yayi amutane sumacikinsu akwai munana muma akwai acikinmu
Saboda hikim脿rsa kuma acikin kowanne jinsin A kwai mace danamiji hakan yanuna kenan akwai cutarwa idan wani jinsin ya auri wata awani jinsin misali
Mutum ya auri macen dabba kokuma acikin dabbobin kare ya Auri akuya kokuma bunsuru ya auri saniya taya kake ganin rayuwarsu zata daidaita
Hukuncind脿 babanka yayanke m脿ka shine daidai yanzu haka yabaza jama arsa anemoka”” aganina baidace kayifushi da hukuncinsaba
Zaka iya samun wata amadadi帽 ta waccema tafit脿 kyau tasake murmusa wa nasan nadamek脿 da surutuko Kayi hakurii nabarka

Lafiya kafin fuwail yiyimaga帽脿 hartaba莽e
Aranar yabardajin damurna shikam yasamu matar aure ranard脿 yakai garinsu yanemi gafarar ” mahaifinsa”” kuma yasanardashi batun zarah y脿r sarkin aljanun misra
Ashedama abokaine da baban fuwail babu bataloka莽i akanema masa aurenta”” anyikomai akasabikin satii uku masu zuwaa
Fuwail yafara zuwa firah wajen gimbiya z脿hr脿 sunamutuwar son junansu

Gentle Lady馃拑馃徑

[6:48PM, 1/27/2017] gentle lady馃拑馃徑: MATSALATACE!!馃槳

          145
.

DAGA TASKAR

Aisha Ibraheem

*END*
bayan satii biyu dabarinsu kyauta rugarsu ta sullubo yayanta biyu kyawawa duk maza””” kuma sunacikin koshin lafiya zokuga murna wajen maleek tamkar yahadiye kyauta daga hospital gidan mom akawuceda itah maleek saimita yakeyi dama tunkafin tahaihu babu yanda mom batayiba yakawota gidan yaki datakafe saiya kawota shine yafadawa malam malam dakansa yacewa mom tabarmasa matarsa tunda ba ibada bane Amman yanzu tacemasa karma yawahalda kansa wajen fadamasa Dan bazata bashi itah ba saisunyi arba in

Kamar maleek yayi kuka haka yahakurah hafsat kam gaba daya ta tattaro kayanta tadawo gidansu mom alokacin ansa bikinta da Aliyunta wata daya”” 
Daki daya suke da kyauta taga soyayya itakam dankullum maleek yana manne da kyauta mom tayikorah harta gajii tasamasa ido” gabadaya ya tattaro kayansa yadawo gidan
Bayan sati daya ranar suna kenan inda Yakama aranar aka daurawa fuwail aure da gimbiya zahra wacce yakejinta tamkar jinin jikinsa”” sosai yama manta dawata kyautaa “” 

 Yaran ba asauya masu sunaba hassan da husaini ake kiransu taronsuna kam yayi anci ansha anyi hani an”” masu gurzurima sunyi yanrugarsuma sunzo maijego saishige da fice takeyi su hafsat sune uwayen buki yan group din Haneefa Usman sunkawo jiki hafsat tayita rabamasu kayan buki dama munsan wasu yartsokar nan takaisu dakuma ta tsane””馃槤馃槤
Kunsan halin taro Amman duk dahaka kausar takoma tanacewa wai ba abataba “” datasanima da bikinsu fuwail tatafi bana kyautaba馃槖
Tobari muleka bukin aljanu mugano”” waiwai fuwail yayi kyau cikin farar shadda sai kyalliyake ido nawaro ganin kausar harta rigani saikace wacce tashiga jirgii馃槼
Fateema zuhurah nahango acikin yanbikin nace tofa hardake anandin hafsat bata baki satipiket mai kwariba kenan””

Shafa atu Umar naji tace nima bata baniba”” nace Toni inaruwana tayiyu bakibada abun kwaraiba ai”” 馃檴馃槀
Cen nahango maryaty maryam(Lele style) Anty ameena”” fateema “” Jidda nace bangan shuwaba kodai tsoro yahanata zuwa馃 aikuwa banrufe bakinaba nahangota wajen da akezuba shinkafa””馃槀馃槀馃槀
Yan group din maman Khady sunje”” nace tabdi kuzaku cinye abincin ai””馃檮馃檮 fuwail yayi dariya yace sucisuci idan basu koshiba adafamasu wani albarkacin kyauta Dan itah tahadamu”
Nikam naga abun mamaki bikinsu tamkar irin namu mukan acen muka yada zango saida akakai Amarya mukaimasu fatan akhairi sannan mukagarzayo gida”” angama labarin fuwail
Koda mukadawo gida kowa yawatse yanbiki saimuyi mata fatan Allah yaraya”” yan group sukaki tafiya saida maleek yabisu dabandir din yandubu dubu sannan sukawuce sunamashi addua
Satin Hafsat daya takoma akasoma shirye shiryen bikinta 

Maleek duk yabi yadamu abashi matarsa anagama bikin Hafsat dasatiii biyu mom tatattara masa matarsa tace 馃檲sukarata cen itadai kyauta kunya kawai yaketurah mata
Gidansukam yasha gyara”” bayan sunyi sallah tayiwa yaran wanka yashiryasu itahma tayinata”” tachakale abunta yanafitowa yasaki bakii gabadaya saiyaga tasakemasa 
Agurguje yashirya Dan amatseyake yakashemasu wutar dakin 

Bayan wasu awanni kwance take saman kirjinsaa bayan sunyi wanka tace wainikuwa intambayeka??? Yashafo sumarkanta yace inajinki tace kafinni wakafaraso???? 
Yayi shiru sannan yace wata yer bauchi sunanta samrat kyauta tabata fuskaa馃槰 yace yakuma haka kefa kika tambay脿??? .

Tace towakafiso dani da itah???馃槖 Yace habadai aikobanfadaba kenafiso banda abunki eesha kifinda yekecikin talle aishine naka bawanda yake ruwaba tunfarko danasan akwai eesha ayola aida banfara giginson wataba aimun afuwa馃
Dariya tasaka tashige jikinsa”” yace nagodemaki eesha kece karshen* *MATSALATA!!*tace nima Kaine karshen *matsalata*
Tosaimugodewa Allah Wanda shine yakawomana karshen *MATSALARMU*

Suka rungume juna cikin kauna
Ananzance *TAMMAT BIHAMDULLAH*
*ALLAH KASHIGA TSAKANINMU DA MIYAGUN HALITTU KOWANNE IRINE AM3EN*
*ALLAH YASA MUCIKA DA IMANI*
*ALLAH YAHOREMANA ABUNDA ZAMUYI DAWAINIYAR YAUDAKULLUM*

*ALLAH KAJIKAN IYAYENMU DA KAKANNINMU DA M脌L脌MAMMU DA KULLUHIN MUSULMAI*
*AMEEN SUMMA AMEEN*
*NAGAIDA KOWA*

gentle Lady馃拑馃徑